Complete Hausa Novels

Batuul Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Batuul Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 88 of 124

D'akin da ya zama nashi ya koma, a bakin gado ya tarar da Ajiddeh zaune da wata irin shiga, d'auke kanshi yayi kamar bai ganta ba ya shiga cire kayan jikinshi, tasowa tayi ta shige jikinshi, had'e rai yayi ya turata daga jikinshi, sosai ranta ya b'aci amma da yake nema take su shirya haka ta koma gun nashi, ta sake mannewa a jikinshi, hannu yasa zai janyeta tace "Haba babe meye ne haka kake min, indan abinda nayi d'azu ne am sorry, I promise you bazan sakeba, d'azun ma sharrin shaid'an ne da kuma irin son da nake maka, bana iya jure ganin wata mace kusa da Kai, amma kayi hak'uri kaji babyna", cire hannayenta yayi daga jikinshi yace "Ai this is not your first time na bani hak'uri, kinsha bani kuma kike sake aikata laifin, abinda kikaga yafi dacewa dakene kikeyi, keep on with it", marairaice mishi fuska tayi kamar dagaske tayi nadama tace "Am serious this time, bazan sakeba kaji?, in kanaso har ita zanje in bawa hak'uri", ajiyar zuciya ya sauk'e yace "Ban aike ki ba", tace "toh ka hak'uran?, tsakanin mata da mijinta sai Allah, kai kawai ya gyad'a mata ya juya yayi toilet, biyoshi tayi tana cewa "Let me help you", tare sukayi wankan, shi ya d'aukota a hannunshi suka fita, bayan sun kintsa take ce mishi "Baby jibi fa Aunty na zata koma", ya kalleta yace "Soon?, mey tazo yi dama?", shiryayyar k'aryar da zatayi mishi ta rasa, batasan lokacin da tace "kasan dama d'an mijinta anan yake karatu, toh wai zasuyi convocation d'insu shine tazo tayashi murna", kai kawai ya gyad'a yace "Okay Allah ya kaimu, gobe kamin in fita you remind me", saida suka gama shiryawa yace "Food is downstairs, sai ki d'ebi na Aunty ki kai mata", da haka ta fita shi kuma yayi shirin fita, washe gari ma haka yaje ya samo musu abinda zasuci, da yamma Batuul take ce mishi Farida zata kai wa wata k'awarta da tayi aure ziyara a Birmingham saida ya gama musu tambaye tambayenshi tukunna ya yadda sannan ya had'ata da David suka tafi.

Washe garin ranan da Aunty Jainaba zata tafi, da safe Batuul ta sauk'o, wainar fulawa kawai takejin ci tunda asuba, tana kitchen tana y'an aike aikenta taji su Ajiddeh sun sauk'o, bata bi ta kansu ba ta tab'e baki taci gaba da aikinta, zama sukayi a parlour suna cin abincin da sukayi ordering, a guje sukaga Batuul ta fito toshe da bakinta, bata bar parlour ta tsuguna ta dinga kwarara amai a wajen, da ido suka kalli juna, Aunty Jainaba ta xaro ido tayi kasa da murya tace "Keh anya wannan shegiyar yarinyar ba ciki gareta ba kuwa, kullum sai tayi amai, toh na menene?", Ajiddeh dake ta kallon Batuul ita ma murya can kasa tace "Ai ni so nake ma hakan ya kasance ta tattara ta barmin gida, nasan in har ya tabbatar cikine toh ba yadda za ayi ta zauna, maidata gidansu zaiyi, ya Allah ka tabbatar da hakan", dai dai nan Abutturab ya sauk'o don shima ya ji k'ak'arin aman nata, da sauri ya k'araso ya d'agota ya rungume yana k'iran sunanta, suna ganinshi suka mik'e, gaba d'ayansu sai da zuciyarsu ta doka ganin yadda ya rungumeta, ita kam Ajiddeh ma sai gani tayi sun mata kama, Aunty Jainaba ce ta wayance da cewa "yi sauri ki mik'a mata ruwan Ajiddeh, sannu kinji", Batuul kam bata ma san mey suke cewa ba, haka shi ma don duk hankalinsa ya tashi ganin yanda take aman, k'arasawa wajensu Aunty Jainaba tayi damuwa dauke fuskarta kamar gaske tace "Aliyu bai kamata a barta haka tana ta ciwo ba a gida, akai ta asibiti dan aman nan nata yayi yawa, kar aje ba a saniba wani ciwon ne yake damunta har yayi mata illa, ku kaita asibiti yanzu gskya, dubi yanda duk ta galabaita" sai da ya tabbatar ta gama aman snn ya d'auketayayi sama da ita, Ajiddeh ta bi su da harara xuciyarta na tafarfasa, jikinta ya gyara mata ya canja mata kaya snn ya sauk'o da ita, numfashi kawai take mayarwa duk jikinta yayi laushi, David ne ya shigo daidai lokacin, Abu ya kalli Ajiddeh yace "Tunda ga david ku tafi airport kawae ni xan kai ta asibiti" caraf Jainaba ta anshe tace "Kai haba mu tafi asibitin gaba daya kawae Aliyu babu komai" yace "Xa ki iya missing flight kuma, kawae ku je bbu damuwa" bata so haka ba amma bbu yanda ta iya tace "toh shikenan, bari muje in d'auko kayana, Allah ya kara miki lafiya y'ar nan" ta ja hannun Ajiddeh sukayi sama, suna shiga d'aki tace "kina jina, kada ki sake ki wani bini airport, kije asibitin ayi komai kan idonki, sai muga ta fad'i, shegiyar yarinya mai kama da y'an Ethiopia ni na tabbata ba komai bane wannan banda ciki, ni kaina yanzu tsanarta k'aruwa yakeyi a raina wllh", Ajiddeh tace "toh", suka janyo akwatin suka sauk'o, inda tayi aman ya gama gyarawa snn ya koma ya d'auki Batuul d'in zasu fita, daidai nan suka sauk'o, har ranta takejin yadda ya rungume Batuul a jikinshi, danne zuciyarta tayi tace "Baby kaga why not mu tafi tare, kaga jikinta is very critical, you might need help, I will go with you, Anty xata tafi airport din ita kadai, she will understand", kallonta yayi yace "No ki tafi Airport din da ita its okay I will manage", Aunty Jainaba ce tace "Ah ah Aliyu ba komai ai, ba sai ta bini ba, ga mara lafiya nan, ita tafi buk'atarta ai, kuje kawai, Allah ya bata lafiya" ganin suna b'ata mishi lokaci kawai ya d'auki Batuul yacewa Jainaba, "Allah ya kiyaye hanya ya fita", Jainaba tace "maxa Bishi", da sauri Ajiddeh ta bishi ta shiga gaban mota, badan yaso ta bishi ba, a baya ya kwantar da Batuul snn ya dawo gaba ya seta rear mirror d'inshi daidai yadda zaina monitoring d'inta, motar su Jainaba ce ta fara fita sai nasu daga baya, kowa yayi nasa hanyan, suna isa asibitin ko reception bai tsaya an duba mishi file ba ya shiga office d'in doctor d'inshi kai tsaye, Ajiddeh ma jiki na rawa tazo zata kutsa kai cikin office d'in ya kalleta rai a had'e yace "stay outside, ki tsaya daga waje, bbu amfanin shigan ki", ba dan taso ba haka ta koma daga baya ta zauna kan d'aya daga cikin kujerun wajen rai b'ace, da sauri likitan ya taso ya karb'eta suka kwantar da ita kan gadon office d'in, gaba d'aya abin nan da akeyi batasani ba dan bacci takeyi abinta tun mota, hannu kawai Abu ya kalmashe sai rocking yake kan kujera yana ganin likitan na aikinshi cikeda k'warewa, saida ya ya gama gwaje gwajensa sannan ya dawo ya zauna kan kujera, Hannu ya mik'a mishi da murmushi a fuskanshi yace "congratulations, you are going to be a Father, your wife is one month and few days pregnant", gaba d'aya jin maganar yayi wani iri, ya kasa daina kallon likitan, he wasn't expecting it, Batuul is pregnant?, bai janye hannunshi ba har saida likitan ya janye nashi snn yayi maza ya janye hannunshi, ganin irin kallon da likitan ke mishi yyi saurin k'irk'iro murmurshi, take ya nunawa likitan yaji dad'i sosai, a kanshi kuwa Ajiddeh yake hangowa idan taji wannan lbrin da yake ji, likitan ne ya katse mishi tunani tareda prescribing mata magunguna da advises kan abinda zata riqaci, da kuma wad'anda are not good to her health, ita dai har lokacin baccinta takeyi, mik'ewa likitan yayi zai bar office d'in yace "Mr Kyaree, I will be right back" a hankali ya mik'e ya isa bakin gadon yana kallonta ko kiftawa bai yi, likitan na fita a bakin k'ofa ya kusa cin karo da Ajiddeh, da sauri ta koma baya tana yak'e, murmushi yayi mata yayi gaba abinshi, a guje ta biyo bayanshi da damuwa kamar gaske fuskarta tace "Excuse me doctor" juyowa yayi yana kallonta, tace "Hope she will be okay, I don't want anything to happen to her, she is my only Sister, tell me what is wrong with her Doc", murmushi yayi yana girgiza mata kai yace "Yeah she is okay, she will b fine surely, congratulation your sister is pregnant", kwalalo ido tayi waje da dafe k'irji tace "What?", ganin irin kallon da yake mata yasa tayi maza ta kirkiro murmushi tace "Omg, Am happy, Thank you sooo much Doctor", ya mayar mata da murmushin yace "you are welcome" ya juya ya tafi, wani irin farin ciki da ta dad'e bataji irinshi bane taji yana ratsa ta, tana zama ta k'ira Aunty Jainaba dake airport ta sanar da ita komai, Anty junaiba tace "Wayyo ni da ban tafi yau ba" nan dai sukayi ta murnan k'arshen zaman Batuul gidan yazo karshe cikin ruwan sanyi tunda cikin shege ke jikinta, Abutturab kam jikinshi duk yayi sanyi, daidai kanta ya tsaya yana kare mata kallo, yasan yana da son yara, yanada burin ganin yayanshi amma bai taba sa damuwa ranshi ba na Ajiddeh bata haihu ba, tunda yasan Allah ke badawa a lokacin da ya dace but with Batuul, its totally out of it, yana d'aura ido kan cute face d'inta yaji wani courage yazo mishi na son ganin babyn da Batuul zata haifa mishi, wani abu da bai tab'a ji bane yau ke mishi yawo gaba d'aya jikinshi, d'an murmushi ya saki ya d'an sunkuya yayi kissing y'an cute lips d'inta da bai iya resisting, cak ya d'auketa ya rungemata tsam jikinshi yana jin abin nan na mishi yawo a jiki, barin office din yayi yana rike da ita ya fito, a zaune ya tadda Ajiddeh tana waya da sauri ta katse ganinsu, kamar ta samu wuk'a ta cakawa Batuul takeji amma ai k'arshen zamanta ma yazo, fuskarta d'auke da murmurshi ko tambayarshi abinda ke damun Batuul batayi ba sai murmushinta takeyi, shima d'in baice mata komai ba, kallonta yayi yace "muje", tasa kai gaba suka tafi, ganin gaba d'aya mood d'insa ya canja a ranta sai cewa takeyi, "wato so yake ya rufa mata asiri ko, toh ai ta Allah ba taku ba, Allah ya toni asirinta yau", mota ya bud'e ya kwantar da Batuul ya gyara mata kwanciyar kallonsa take tana lullumshe ido sbda irin baccin da take ji, ya zaga ya shiga ya tada suka fita, suna isa gida Ajiddeh ce ta fara fita daga motan ta shige cikin gida ya bi ta da kallo, da sauri ta haura sama ta shige d'akin Batuul ta shiga fiffido mata akwatinanta, kafin su Abu su shigo har ta sauk'o downstairs dasu, yana rike da hannun Batuul suka shigo parlon, da mamaki duk suka tsaya kallon ikon Allah, shewa ta saki tana tafa hannaye tace "In kana tunanin ni xa ayi ma wasa da hankali kayi karya Aliyu, don zaman karuwan nan ya k'are gidan nan," ta juya tana kallon Batuul tace "Munafuka algunguma, ashe karuwanci kike yi dama, toh yau Allah ya toni asirinki, iskanci ba a gidana za ayishi ba dan ban gada ba, a tafi can inda aka saba aci gaba dayi, Dan ni dai kam ban zama da mai cikin shege a gidana", kallonta kawai Abu yake da mugun mamaki don baisan ya akayi ta sani ba, Batuul kam d'aurewa kanta yayi ga jirin da ke d'ibarta, Jiki na rawa Ajiddeh tayo kanta ta fizgota da kargi tayi k'ofa da ita ta hankad'ata waje tana hakki tace "k'arshen karuwanci dai yau ya k'are gidana, aje gaba aci gaba daga inda aka tsaya," da sauri Abu ya k'araso ya d'ago Batuul duk ya gama rud'ewa ya shiga dubata ko taji ciwo, ita ko banda kuka babu abinda take, ganin komai normal babu abinda ya sameta ya mik'e, cikin zafin rai ya fixgo Ajiddeh ya wanka mata lafiyayyun mari har biyu ta both sides, ya shaketa cikin tsawa yace "kika kuskura ki sake tab'ata ko kika yi gigin k'iranta da karuwa sai na hallaka ki wllh, don matsayinta d'aya yake da naki a gidan nan" ranshine ya dad'a baci cikin kaushin murya yana mata wani irin kallo yace "Let me tell you what you don't know jiddah, kamar yadda kike matata a gidan nan, toh haka Batuul ma take matata ta sunna, snn cikin dake jikinta ba na kowa bane, nawane", yana kai wa nan ya Kama Batuul da komai ya tsaya mata yayi sama da ita, nan yabar Aunty Ajiddeh da numfashinta ke neman barin jikinta, idanunta sun firfito.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.