Batuul Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Batuul Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 100 of 124
parlourn
Da murnarta ta kara wayar a kunnenta tace "Hello Aunty ina wuni", sai kuma ta fashe da kuka, "Yasalam", kawai Abu ya iya furtawa snn ya rungumeta yana kad'a mata kai alamun tayi shiru ta bar kukan da takeyi, daga d'aya b'angaren Aunty tace "Kukan na meye kuma Batuul sai kace wata Yusra, ya jikinki", cikin sheshek'a tace "Aunty naji sauk'i, Aunty inaso inzo in ganki", ji tayi Abutturab ya sassauta rik'on da yayi mata ya saketa ya ja baya, kallonshi tayi idonta cikeda hawaye, maganan Aunty ya katseta daga kallon da take mishi Aunty tace "keda bakida lafiya yawon mey zakiyi, kiyi zamanki har sai kinji sauk'i sai kizo kinji", kamar Auntyn na gabanta ta kad'a kai a hankali tace "Toh", Aunty tace "yawwa maza goge hawayenki bana so a ganki kina kuka kinji, ga Yayya nan za a kai mata wayan kuyi magana da ita", muryan Yayya taji tana cewa "Kaji ja'irar yarinya kukan na meye kikeyi, yaro na zaman zamanshi kinsa ya baro aikinshi, laulayin cikin kikewa wannan rakin, maga yadda zakiyi idan lokacin haihuwar tayi", Zumb'uro baki Batuul tayi tace "keh ina ruwanki, wama ya fad'a miki hakane", Yayya tayi dariya tace "zauna can, ina uwargida har sai an fad'amin, maigidan naki da kanshi duk sati sai ya kiran a waya kuma duk ya fad'a min tab'arar da kike mishi, ai nace mishi ma had'ani dake zaiyi in wuce dake Yerwa, maga ta fad'i", Batuul tace "keh Yayyan nan ko, babu inda zan biki, wajen Aunty kawai zanje", Yayya tayi shewa tace "Aunty taki ma basai in tafi da ita Maidugurin ba, dama naji tana wani rarrashinki dan lalacewa, ita ke dad'a tunzuraki nasani", "Ni kinga tunda ba abun arziki zaki fad'amin ba sai anjima", Yayya tace "gantalallu duk halinku d'aya da y'an uwan naki, ku masu uwa ba'a fad'in lafinta koh, in Baban naku ya dawo ya kawoni gun naki dan ni na raba kaina da tuk'in gantalallun k'annenki, wataran sai nasa shi Baban naku ya tasa su su d'auki tasu uwar suyi gudun da sukeyi dani akan titi, mugaye kawai", dariya Batuul tasa tace "toh keh ki koyi tuqin mana nan gaba basai ana gudu dake ba", Yayya tace "Ina nan tafe ne badai dariya kike min ba", haka sukayita hira, saida suka gama wayan ta kalli Abu dake daddana wayarsa, saida gabanta ya fad'i ganin irin kallon da ya jefeta dashi, zatayi magana yace "tashi ki shirya in kaiki", kallonshi tayi tace in shirya? Ina zaka kaini?", mik'ewa yayi ba tareda ya kalleta ba yace "inda kika gama cewa zaki yanzu", raurau tayi da ido ganin he is so serious, hawaye ne ya cika idonta, a hankali ta tako gabanshi tace ta fad'a jikinshi ta fashe da kuka, cikin shesheka tace "Yaa Abu nifa kawai na fad'a ne, am sorry toh na fasa, kaji bazan sake cewa Zani ba dagaske", hannu yasa ya zagayeta, hakan da yayi ya sata sauk'e ajiyar zuciya, ya d'aura fuska kan gashin kanta tareda lumshe yana shaka'ar kanshinta mai dad'i yace "Its
okay, bana son kukan nan", da sauri ta d'ago tace "kayi hakuri dagaske?", kai ya gyad'a mata yana murmushi yace "I can't be angry with you Fatima, bana so kina tadawa Aunty Hankaline, in taji kina kuka she might think wani abun ke damunki", sake k'ank'ameshi tayi tana girgiza kai tace "nace bazan sake ba", ya sunkuyo yayi pecking lips d'inta yace "that's my princess, muje Malamin na jiranmu", Hijab d'in da ya gani kan gadon ya janyo yasaka mata ya riqe hannunta sukayi waje. Suna fitowa corridors ta kallesa a hankali tace " Ya Abu ina take?" Ya d'ago kanta yace "Wa?" Ta d'an yi shiru sai kuma tace "Ita" sai a sannan ya tuno da Ajiddeh ya d'an bude ido yace "Ohh Ajiddeh? She might be at the parlor" daga haka ya ja ta suka sauko parlor, janye jikinta ta shiga kokarin yi daga nasa jin muryar Ammah da Anty Amnah a parlon da alama shigowarta kenan don gaisawa suke da Ammah
Am not actually so good with words but imma thanking these lovely girls for their love
Meenarh parrot馃挅
Rahma lurv馃挅 and every single soul that loves BATUUL馃挅馃æŒÂ
[12/1, 15:42] 80k: 馃挅馃æŒÂBATUUL馃挅馃æŒÂ
83
By phartiemarhk
Dedicated to *KHALEESAT HAYDAR*
Bayan Mum ta bar parlour rai b'ace ta fito ta dawo parking lot, da k'arfi ta shiga k'walawa driver k'ira, a guje ya taho yace "Hajiya gani", kallonshi Kawai tayi ya ciro makulli daga Aljihu ya bud'e motar ya fad'a, daga ganin yanayin yayar tata tasan ba lafiya ba, batace komai ba saida ta Shiga ta zauna tace "Yaa Zuwaira mey ya sameki naga kin canza daga shiga ki fito, wani abun ne ya faru?", Mum taja wani dogon tsaki cike da masifa tace "Dan uwarka kai jahilin ina ne iyye?, ina zaka kaini da ka karyo kwanan nan", Driver da duk ya rikice yace "Hajiya ranki shi dad'e ca nake kasuwa za....", bai gama rufe baki ba a hasale tace "bukkar uwarka zaka kaini ba kasuwa ba, shasha Kuje zamu, jahili", shidai baice komai ba dan inda sabo ya saba indai ran Mum b'ace yake a rana toh sam bai son ya zama shike duty, jiki a sanyaye yace "Ayi min afuwa Hajiya, kuskure aka samu", daga haka ya d'auki hanyar Kuje, Jainaba da ta gama tabbatarwa babban abune ya tab'a Mummy ta tab'a baki tace "Wai Daddy ne ya bata miki rai", Mum tayi k'wafa tace "Abun nayi ne Jainaba, wato ina saka ban sani ba warwara nakeyi, bamuga ta zama ba, wannan karan da zafi zamu shigi kowa, da zafi zafi akan daki k'arfe, bazanyi sanya ba wannan karon, sai naci uban kowama, baza a d'aga min hankali ina zamana ba wlh sai nayiwa abun tufkar hanci", wayarta ta d'auko daga gefenta ta shiga dialling number tasa a kunne, har ya katse ba a d'aga ba, Jainaba taja d'an siririn tsaki tace "Yaa Zuwaira nifa bakice min komai ba har yanzu, mey ya faru kuma banda matsalar Ajiddeh", Mum ta sauk'e wani nannauyan ajiyar zuciya tace "Shifa wannan baban nasu ne ya sani gaba da surutunshi na banza da wofi, akan mene zai dameni nida rayuwata, kinji wai wa'azi ya zauna zai min wai ina abubuwan da basu dace ba", Jainaba tayi dariya tace "baki mik'a mishi microphone ba dan kifi jin wa'azin da kyau", Mum tace "birki na taka mishi, inji da abinda shashashar yarinyar ta Sani ko kuma in biye mishi ya dad'a bata min rai, kuma fa duk sai nayi maganinsu, in banda taurin kanshi ma na jaraba duk abinda akayi kwana biyu yake barin jikinshi amma dai wannan karon alwashi naci sai na samu komai yadda nakeso", Jainaba tace "Yaya wai ina laifin wannan karan ayimana yadda Daddy kullum komai nashi zai koma naki, a badda hankalinshi da tunani ya zama komai a hannunki", Mum tayi k'wafa tace "Dan ubanki wace makarantar nayi da zan iya riqe wadannan abubuwan, ai sai yanxu nake takaicin kin zuwa makarantar da nayi ina Karama, da yanzu komai nashi nasan takansu", Jainaba tace "Ai ba sai Lallai ke din ba, dama su Zee ne zasuyi ai", "kinga fa dad'a tunzurani kikeyi kina b'atan rai, wadanne yaran marasa wayo ne zasuyi min abin kirki, kiga kayan takaicin da Ajiddeh ke k'unsa min, itakuma Zainab in banda yawo kamar wata hadari a cikin gari babu abinda takeyi, kedai bari duk na kusa kawo k'arshen komai", Jainaba tace "Toh Allah yasa", Mum taci gaba da k'iran wayan Zee da har lokacin taqi d'auka, Driver dake gaba yana jin komai Addu'a ya riqa Allah ya rabashi da masu irin halin Mum, kamar kullum yauma tafiya mai nisa sukayi kamin su isa gurin bokan nasu, da zuwansu Mum ta gama zayyane mishi duk abinda ke tafe dasu, k'asar dake gabanshi ya buga yace "itafa wannan yarinyar abinda muka tura Mata yana nan jikinta har yanzu kuma yana kan aiki saidai bansan mey ya hana aikin ci ta mutu ba, dan yaci ace ta mutu tun bayan kwana biyu", Mum tace "gaskiya ne yana aiki dan y'ar tawa da nayi maka bayani tanason kawo mana matsala tace min mutuwa zatayi, in da yadda za ayi ranka shi dad'e ta mutu a huta, kaga in ta mutun, ta wajen nawa zata dawo hankalinta sai musan nayi akanta itama", haka dai Mum ta dinga Zayyanowa boka abinda za ayi tun daga kan Daddy, Ammah, Abu da kuma Batuul, boka yace indai jaka a bud'e take zasuga aiki da cikawa, nan ya duk'ufa ya fara da na Batuul, Suna zaune a wajen wayar Jainaba ta shiga ringing, saida aka kira wajen sau shida snn ta d'aga, shiru tayi tana sauraren mai magana a wayan, sai da yayi shiru tace "Toh naji", ta katse wayar, boka ya gama masu tsubbe tsubbensu yace "kuje, kamin ku k'arasa gida zaku ci karo da lbrn mutuwarta" da murna fal ransu suka zube mishi kudi suka tashi akan zasu dawo in da wata matsalar, sai da suka fita zasu gun mota Mum tace "Wane d'an iskan ne yake damunki a waya, yaga baki d'au na farko ba ai sai ya rabu dake koma wani jarababben ne", Ajiyar Zuciya Jainaba ta sauk'e ta tab'e baki tace "Idrees ne", Mum taja tsaki tace "Shifa wannan k'aramin mara kunya ne, ko ba d'azun nan ya k'iraki ba", Jainaba tace "Shine ya k'irani, wai tuna min zai sakeyi indai ban dawo gobe lallai lallai ba toh inyi zamana a inda nake ba sai na dawo ba", Mum taja tsaki tace "Karamin mara kunya, sai yazo ya kinkimeki ya maidaki", da haka har suka isa mota Driver ya tada sukayi gaba suna ci gaba da hiran abinda zai faru
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.