Complete Hausa Novels

Batuul Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Batuul Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 56 of 124

D'akin Abuu Ammah ta shiga bayan Batuul ta shige toilet, har ya canja kaya lokacin yana zipping wani akwati, ganin Ammah da yayi 膹akinshi ne ya sashi barin abinda yake cikin hanzari ya k'araso inda take, bata ce mishi komai ba har ta k'arasa shigowa tukunna ta zauna daga bakin gadon, rabon da Ammah ta shiga 膹akinshi har ya manta, jiki a sanyaye ya bita ya zauna daga k'asa, ce mata yayi "Ammah ai da kin k'irani nazo ba sai kinzo da kanki ba" har ta bu膹e baki zata fara mishi magana ta fasa tace "in ka gama ka sameni a 膹aki toh", daga haka ta mik'e tayi waje, ajiyar zuciya ya sauk'e dan yasan da magana bakin Ammah, koh minti biyu batayi ba da fita shima ya fita yabi bayanta, zaune ta tadda Batuul bakin gado har lkcn, ganin Ammah ta shigo yasa ta sauk'e kanta k'asa zata sauk'a k'an rug 膹in Ammah tace mata tayi zamanta, kin zama tayi kan gadon ta sauk'o k'asa, da sallama ya shigo 膹akin shima ya zauna kan stool 膹in mirror, Ammah na kallonshi ta fara magana "Abuu ga amanan Batuul nan na baka da hannuna", da sauri Batuul ta 膹ago jin abunda Ammah tace, jiki a sanyaye ta sauk'e kanta dan har idonta ya fara tara ruwa, Ammah taci gaba tana kallon yadda ya sauk'e idonshi k'asa tace "tunda kayi aure kasa k'afa ka fita daga garin nan hankalina bai kwanta ba, ni bansan tsakaninka da matarka ba amma mu dai kam babu abin alheri da tayi mana, ni da kaina na sa aka nemo maka auren Batuul dan tun kamin aurenka da Ajiddeh Batuul naso ka aura amma Allah bai yi ba sai yanxu, ko sau 膹aya ban yadda kasa hawaye zuba daga idon Batuul ba, ban yadda ko da wasa matarka ta wulak'anta min ita ba, yadda take zab'inka haka nima Batuul take zab'ina sannan amana na baka ita kamar yadda iyayenta suka aminta dakai suka baka y'arsu, ka kula da ita fiyeda yadda xa ka kula da kanka, sannan makarantarta ba denawa zatayi ba, an sama mata admission a can, ka taimaka mata da dukkan k'arfinka har sai ta kamalla dan tana karatunta muka nema maka aurenta, Allah ya tayaka rik'o ya baka ikon yin adalci tsakaninsu", ta juya tana kallon da Batuul da ta jik'a gyalenta da hawaye a lokacin tace "Bitti ga yayanki nan xa ku tafi, na fa膹a miki duk abinda zaiyi miki mara da膹i, don't hesitate in zama ta farko da zaki fa膹awa, ki zama mai respecting 膹inshi kinji, he will be your guide In sha Allah, tsakanin ki da matarsa girmamawa, ki goge hawayenki kinji, kuma duk lokacin da kike son dawowa ki fa膹a mishi zai dawo dake kina yin kwana biyu kinji", Sadiq ne ya turo k'ofan tareda sallama, da murmushi a fuskanshi ya dubi Abu yace "ba dai kun fasa tafiya ba yau", Abuu ya dubeshi fuskanshi babu walwala yace "We are coming", Ammah ta dubi Batuul ta 膹agota tace "Bitti share hawayenki ki tashi kuje, Allah yayi muku albarka, ya baku xuri'a dayyaba", da k'yar Batuul ta iya mik'ewa tana gyara gyalen dake kanta har wani shidewa take don kuka, Sadiq sai tsokananta yake sae dae shi ma xuciyarsa fal yake da tausayinta, suna sauk'a k'asa suka tarar da Massa shima yazo, gaba 膹ayansu suna zaune palon sun gama shanye drinks 膹in da aka kawo musu, Ammah tace "jeka Abui ya shigo yanxu kuje kuyi sallama dashi, tare sukaje sukayiwa Abui sallama yana gaba tana biye da shi a baya, Abui ya sake musu Nasiha tareda yi musu Allah ya kiyaye hanya, mota uku suka yi suka nufi airport.

Tunda suka 膹au hanyan airport take kuka ba k'akk'autawa dan tasan farin cikinta ragagge ne tunda har ta yadda tabi Abu wani garin da babu kowa nata, tausayin kanta take sosai tana kuka, sai da tabi y'an uwanta 膹aya bayan 膹aya tayi hugging 膹insu tana kuka su din ma kukan suke, har ta iso kan Farida dake kukan itama ta rungumeta, da k'yar suka sake juna don itama kukan da take ya hanata yin magana, ta kasa yin komai sai gya膹a kanta da takeyi, cikin hanzari ta sake Farida xata bi Sadiq da ya kasa ci gaba da kallon emotional scene din ya juya xae bar wajen, Abuturrab ya fixgota jikinshi, sosai ta shiga yin kukan kmr ana tunxura ta, dai dai saitin kunnenta ya sunkuyo a hnkli yace "control, its a public place baza mu tafi kina kuka kamar wacce na sato ba", kwanciya tayi jikinshi tayi lamo tana ajiyar xuciya, yana jin yadda heartbeat 膹inta ke up and down, hannunshi 膹aya ya 膹aura bayanta, 膹ayan kuma yayiwa su Sadiq alamun suja su Ahmad su tafi, hakan kuwa akayi, takai minti biyar kwance jikinshi, can da ta tsagaita kukan ta fara dawowa normal ta 膹ago kanta, jinta jikinshi yasa ta kallon fuskanshi taga shima ita yake kallo, da sauri ta matsa baya ta juya bayanta ganin ko su Farida na nan, taga wayam babu kowa wajen, kallonshi tayi da idonta da yacicciko tace "Yaa Abu dan Allah mu koma kar mu tafi plss", wani irin kallo ya bita dashi yaja akwatin dake gabanshi yace "When you are done ina ciki", babu yadda ta iya haka tabi bayanshi a sanyaye tana share hawayen dake sakko mata, a departures waiting room ya xauna yana jiran jin announcement din departure'n su sanin few minutes ya rage, ya juya yana kallonta ganin a tsaye take, a hnkli ta xauna nesa da shi kanta a kasa, tabe baki yyi ya kauda kai, bayan kusan minti takwas akayi announcing cewar passengers din Abuja to UK su fara boarding ynxu jirgi xae tashi, mikewa yyi yana kallonta, wasu sabbin hawayen ne ke sauko mata duk jikinta yyi sanyi ta kasa tashi, har ya fara tafiya yana jan trolley dinsa ya tsaya, juyawa yyi yana kallonta ganinta xaune yasa ya dawo yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace " Ko in daga ki ne" a hnkli ta mike tana rufe bakinta da mayafi kar ta saki ihun da taji na shirin fitowa, sauke idonsa yyi daga kallonta ta kama hannunta ya shiga tafiya tana binsa har suka isa inda jirgin British Airline (B.A) yake tsaye, yana rike da hannunta suka shiga jirgin, a first class ya samar masu empty seats, a hnkli ta xauna ta jinginar da kanta jikin kujerar tare da lumshe ido, ya saka trolleyn hannunsa daga sama inda ake ajiye luggages, snn shi ma ya xauna, announcement aka shiga yi na cewa "Passengers on board shud pls fasten their seat belts, British Airline flight is about taking off" Abuturrab yyi fasten din seat belt dinsa yana kallonta, gani yyi ko motsi bata yi ba, ranan da suka yi boarding same plane daga Maiduguri xuwa Abuja ya tuna, yyi shiru yana kallonta, a hnkli ya kai hannunsa ya mata fasten din belt din da kansa, ta bude rinannun idonta tana kallonsa, lkci daya ya hade rai, da sauri ta sunkuyar da kanta, wayarsa ya fiddo ya maida shi flight mode ya jona earpiece ya sa a kunne ya lumshe ido, jirginsu na tashi ta fashe da wani kukan tausayin rayuwarta, bude ido yyi yana kallonta sae dae bae ce komae ba, tayi mai isarta bayan wani lkci tayi shiru ta kwantar da kai jikin kujeranta lkci daya bacci ya dauketa, sae a snn ya cire earpiece din kunnensa ya rike kansa dake sara masa xuciyarsa a dagule, from Where is he going to start this long explanation to his Ajiddeh, just ta ina xae fara ce mata iyayensa ne suka makala masa Batuul, ya xata dauki xancen, will shi even believe him, tunanin hkn ya sa ciwon kansa ya tsananta, jinginar da Batuul tayi jikinsa tana bacci ya dawo da shi duniyar tunanin da ya tafi, juyawa yyi yana kallonta ya ga bacci ssae take, ya fuzar da iska tare da lumshe ido ya jawota jikinsa don gyara mata kwanciya, muryar wata hostess din jirgin ya sa shi bude idonsa, tana tsaye dai dai kujeran da suke plate holder din seats dinsu ta jawo ta dora ruwa a kai a karamin disposable cup, murmushi dauke fuskarta tace "Sir what would yhu like to have?" Yace "Just coffee" kallon Batuul tayi xata yi magana yace "She's OK" juyawa tayi ba a dau lkci ba ta dawo da cup din coffee ya karba yace "Thank you" d'an bow din masa tayi tana murmushi tace "Yhu are welcome Sir" daga hka ta juya ta bar wajen. Karfe sha biyu saura na dare Batuul ta bude idonta ganinta jikinsa yasa ta kallesa, idonsa lumshe yake alamar ya fara bacci, a hnkli ta xame jikinta ta xauna da kyau, ta shiga rera kuka tunawa da tayi shknn fa ta rabu da Anty, bude ido yyi yana kallonta, ya gyara xamansa a fusace yace "God! What again? Ke wae baki gajiya da kuka ne, am tired of this pls, aiki kawae su Ammah suka hada ni da I knw" jin ta kara sautin kukan yasa ba tare da yyi wani tunani ba ya jawo ta jikinsa murya can kasa yace "are yhu hungry" kin cewa komae tayi, ya watsa mata wani kallo yace "Kina jina dae koh?" Girgixa masa kai tayi, ya hade rai yace "Gud! Go back to sleep ynxun nn" rufe idonta tayi, tayi lamo jikinsa sae dae yana jin ynda xuciyarta ke bugawa. Har asuba daga ita har shi basu rintsa ba, da ta bude ido xae tambayeta ko tana jin yunwa ta girgixa kai ta kuma rufe idon, Karfe bakwae na safiyar washegari jirgin British Airline ya sauka airport a UK, nn fa Abuturrab ya ji duniyar gaba daya tayi masa xafi, da ya tuna Ajiddeh sae gabansa ya fadi ba kadan ba, da kyar ya mike yana kallon Batuul da idanuwanta suka rine ssae, hade rae yyi lkci daya ta mike kanta a kasa, ya fiddo trolley dinsa ya shiga tafiya, bin bayansa tayi hawaye cike idonta har suka sauko daga jirgin, duk da ta sha xuwa kasashen turawa da Baba har ma da Anty Hafsat yau komawa tayi kmr bakauyiya a haraban airport din, don sae shishshige masa take, ba komae kuma ya janyo hkn ba sae don duk a tsorace take, ba kuma wae turawan suka bata tsoro ba sae don tunawa da tayi da Ajiddeh. 馃挅馃挐BATUUL馃挅馃挐

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.