Complete Hausa Novels

Bariki Auren Soja Complete Hausa Novel

Reading file: Bariki Auren Soja Complete Hausa Novel.txt

Chapter 50 of 86

Ya juya fuu batareda Ahmad ya ce tak ba, saida ya wuce yasamu sojojin Shima ya nuna nashi girman ta wurin basu warning, kafin ya koma cikin gidan yana fadawa maryam, "Amma dai Yasmin akwai wawuya wallahi Meye na wani tafiya don iskanci a haka zatayi nata Rayuwar Auren, "ki kirata first kiji dalili don Oga ihu kawai ya saukemin ban gane me yafaru ba,

MA falon shi ya koma kamar yayi ihu saboda takaici "why baby why zaki tafi just for small issue,, "ga wayarta ya kira taki dagawa wani irin jifa yayi da wayar tareda dagargajewa lokaci daya ya haye saman shi saida ya canja kaya kafin ya fita kotakan driver bai bi ba ya fada motar ya fisgeta,

Kofar gida mashin ya Ajiye ta tabiyashi tareda fadawa gidan ba tareda tunanin komai ba, saidai tana shiga taci karo da baba da y'ar butar shi zaiyi Alwala, tuni ta dawo hayyacin ta tareda natsa kanta kadan " waye haka kamar mamana? " ni ni c ce baba ta fada cike da jarumta da kuma rawar baki " yanzu nake cewa azo a kai miki motar ki gidanki tunda kinkai kanki, shiru tayi takasa cewa komai jikinta na rawa mama ta fito itama ta zuba mata ido " aa kaga Amaren zamani daga ina haka da yamman nan? Matsawa ciki tayi jikinta yayi mugun sanyi ta gaida su tareda shigewa dakin mama ta zauna,

" malam lfy kuwa wannan yarinya? "Aa kalau take jedai kiji bakya ganin yanda ta murje tayi wani bulbul cikin sati guda Inba lfy ai a jeme zaki ganta, dakin mama tashiga baba ya fita masallaci Abinshi, itama bata koma kanta ba saida tayi sallar kafin tace kije kiyi salla ko bakyayi ne? Ita kadai tasan irin kishin dake cin zuciyar ta kanta wani irin ciwo yake mata kamar ya tsage, a haka ta mike cikeda tangadi ta fita, saida ta shiga tsohon dakin su tayi salla tareda canja kayan jikinta ta dawo dakin mama,

Zama tayi tareda dafe kanta tana hango wata katuwa wai da cikin mijin ta bayan ya fada mata bai taba sex da wata ba to ina aka samu ciki,? Cikin hikima mama tafara yimata tanbaya domin tana hango tsantsar damuwa a idon nata, "ya me yafaru daga dawowar ku kidawo gida? "Bakomai dama wayau ya mun yasa aka kaini gidan shi, ," yanzu me kika dawoyi?
"Haba mama nima ina son nima akaini kamar kowace mace mai daraja wallahi bazan koma ba sai Anyimin biki nima kuma ankaini kamar kowacce AMARYA

"Hmmm yaro ho to yanzu kikasan da hakan ko akwai matsala ne tsakanin ku? "Bakomai ni inaso don Allah mama ki taimakeni ko yazo ku hana inkoma sai anyi bikin don Allah kodan mutunci na, "Yasmin kifada min menene matsalar? "Kifadamin ko kinada Wanda zaki fadawa sama dani? "Aa tace "to kifadamin ni uwace nasan mafita, badon taso ba ta fadawa mama komai tareda bata d'an labarin MA kadan, "Hmm Wanda yasai rariya yasan zata zubda ruwa Amma bakomai zamu gyara shi karki sake ki kuma guduwa daga gidan ki idan kin koma saboda wata karuwa ki tsaya ki kwaci yancin mijin ki wata kila sharri ne kawai saboda jin haushin bai Aure suba

"Don haka kidage ki kwato mijinki daga kadan garun BARIKI, ta danji sanyi sosai zantawar da tayi da mahaifiyar ta har ta rage jin damuwar Abin A ranta, sai maganar sharri da mama tace what if sharri ne? Dafe goshin ta tayi koma Meye bazata koma ba sai ta saita shi yanda ko gobe bazai yi wani gangancin ba,

Baba yadawo mama ta fara yimai maganar mijin ta ne yace ta dawo har Ayi bikin tukuna don haka kusa rana, "Wallahi wannan yaron saudatu sai A hankali yanzu sai bayan sun kwashe sati daya shine zai dawomin da y'ar wai wani biki, "to ai dole hakuri zakuyi ayi hakan bambami Kala Kala baba yayi kafin yayi shiru mama ko tak bata cemai ba yayi ya gama Yasmin kuwa KO mawa tayi dakinta dama tanajin fadan baba, wayar shi ya ciro ya kira baban zango " mamuda surikin ka Wallahi baida mutunci yafara fada mai komai kafin baban zango
Yace "to Yaya yanzu ya kakeson Ayi? "Ya kuwa za Ayi nidai banida isassun kudi yanzu na wani biki " tom zanzo mu ga yanda zamuyi,.

MA na fitowa da nufin zuwa gidan nasu aka kirashi office baida zabi dole ya tafi, saidai bacin ranshi ya kara karuwa jin wai zai kwashe rundunar shi zuwa birnin gwari nan da kwana biyu signal ya fito saboda barayin da suka addafi garin, gaba daya ya fita hayya cinshi tafiya daga dawowa kuma ga matsalar datafi kowacce damun shi yanzu yasmin, don haka malali kawai ya wuce ya samu hajiya, bai iya boye boye ba ya fada mata mai ya faru tareda bayyana mata komai na Rayuwar shi ta BARIKI, "yayi kyau ai yanzu gwara da ta tafi kuma bari kaji karka sake ka koma gidan su har sai Anyi mata biki kamar kowacce y'ar Gata don haka bana sonjin wani Abu daga gareka idan ka ga dama ka koma kaci gaba da bin karuwan kuma wallahi in har maganar cikin nan tana nan kuma naka ne baba na bazan yafe maka ba babu shege a zuri ar mu don haka bazaka gurbata min tawa zuri ar ba shiyasa kakiyin Aure tun tuni a she har gida kake kawosu ko,

.
Ranar yayi nadamar Rayuwar BARIKI don bacin ran mahaifiyar shi kawai ya isheshi ishara bare aje kan Yasmin da tariga tasani bazai iya second daya batareda ita ba shine take neman ta daga mai hankali gashi hajiyar shi ta yimai gargadi, dole yaje yaganta ko zai iya bacci yau,

A kofar gidan ya faka tareda yin sallama kai tsaye lokacin suna zaune a falon mama suna hira tareda cin danbun naman da mama tayi Mai shegen dad'i na. Kaza yayi sallama a tsakar gidan, tana jin muryar shi ta matse fuska tareda gyara zama dakyau don ta kara daga mai hankali,
Baba ne ya fita tareda bashi kujera suka zauna gaishe shi yayi cikin girma ma wa, mama ma tafito suka gaisa ta koma cikin falon gaba daya hankalin shi na wurin son ganin ta don yasan tana gidan

Kwanciyar ta ma tayi a falon tareda runtse idanun ta tanajin muryar shi Tanason kallon kyakkyawar fuskar shi Amma Tanason ta nuna mai ita ba kamar sauran mata bace tanaso ta nuna mai ita Mai mutunci ce kuma y'ar gidan mutunci yanda nan gaba dole zai tsare mata mutuncin gidan ta na Aure, kasa har kusan Karfe goma ya yi musu sallama zai tafi a gidan yaci Abinci sukaje har massalaci tareda baba Amma bai sata a idoba mama saida taji tausayin yanda duk yayi sanyi gaba daya baya tareda walwalar shi kamar yanda ta lura dashi akoda yaushe,

Son ta yakeson yi ita kawai yakeson gani he is missing he want to kiss her swwt lips hug her impact he really need his wife yariga yasaba da jikinta bazai iya daurewa ba, har ya fita ya kuma dawowa "mama don Allah yasmin fa tunda nazo banganta ba, "ai bacci takeyi tundazu ko intaso tane? "Aa yace badon yaso hakan ba ya tafi cikeda damuwa tun a hanya ya gwada kiranta kota bude wayar yaci sa a wayar na bude ta hau wtsp Aunty maryam na mata magana tafada mata kudurin ta ta goyi bayanta itama bayan ta mata fadan rashin zuwa gidan nata ta fada mata, "Aunty nasan bazaki Barni intafi ba shiyasa kawai kuma raina ya 'b'aci yanzu inda gaske ne cikin nashi takeda shi ya zanyi? "Ba gaskiya bane baban Auwal yayi bincike yagano cewar ba gaskiya bane zuby ce ta aiko ta don ta bata zamanku kuma tayi nasara don haka ki shirya next time kiyi maganin Abin karki bari su sami nasara akanki anzo mishi da cikin karya bakisan dame za azomishi wani karon ba kuma,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.