Complete Hausa Novels

Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx

Chapter 52 of 56

*page 90*

Da dare Ryynt na d'akin inna ta gama shayarda yara sunyi bacci tana zaune tana shan farfesun naman kaza yayinda mohd ke zaune kan sofa yana sauraren inna dake tambayar sa abinda ya had'a sa da malika har ta kai ga saki uku.

Nan Mohd ya gaya mata komai bae 6oye mata ba har ma zubar da cikinta da tayi ta laqawa Ryynt.

Inna ta jinjina kae tace"cabd'i lallai wnn ba matar zama bace ja'ira gwanda da ka sake ta dan dama tun farko ni bata kwanta min a rae ba ashe kuwa da mugun nufi take ,Allah kuwa ya fita dan inshaa Allah bazata ta6a yin nasara ba har abadah.

Mohd yace"ae har umma da Abba sun so ganin laifina akan saki ukun da na mata zama d'aya amma dana musu bayani suka fahimta har ma Abba ya bani wasu addu'oin tsari yace mu riqa yi nida Ryynt har ma da yaran mu.

Inna tace"lallai ba'ayi sake ba Allah dae ya qara tsarewa"

"Amin"cewar mohd wanda ya miqe tsaye yaje gun 'ya'yansa sae kallon su yake sunata sharar bacci abinsu cikin d'an qaramin gadon su da kowannen su ke kwance cikin wali.

Sae da mohd ya gama kallon 'ya'yan sa snn ya musu sae da safe ya fita.

Inna ta kalli Ryynt dake ci gaba da shan farfesu abinta ba alamar zata raka shi

tace"yo ryynt ke har yanzu baki san hausar ki raka miji ba idan zae fita ae kya tashi kije ki masa sae da safe koh"

Ryynt tayi murmushi ba tare da tace da inna komai ba ta zari tissue ta goge hannunta da bakinta ta fito ta samu mohd har ya kae qofar fita falon ya juyo yana kallonta dan yaji motsin fitowar ta,ta qaroso gurinsa yana kallon ta yace"ae har zanyi fushi dan na d'auka baza ki fito muyi sae da safe ba"

Tace"uhm ni kuwa naga kmr ma baka ci abinci ba gashi har zaka tafi"

Yace"to ba ke bace kikayi zaune kina shan farfesun ki baki koh taya min ba"

Tace"eyyah ban d'auka zaka ci ba bari na d'auko maka akwai wani a kula amma na qassan naman rago ne"

Yace"um um da wasa nake miki ni naci abinci kawae dae zan kwana da kewar ki keda yarana"

Tace"uhm su yaran da aka haifa yau yau"

Yace"baki san yanda nake jinsu a raina bane Ryynt da bazaki fad'i haka ba inaga ma da anyi biki zan d'auke ku ne mu koma dan bazan iya baqura ba har ayi arba'in"

Tace"uhm kaima dae da wasa kake nida komawa gidanka sae nayi wata biyar"

Mohd yayi er dariya tare da jan hancinta yace"da wasa kike kema dan kina wuce arba'in baki koma ba kayan mu kawae zan kwaso mana gabad'aya sae mu dawo nn da zama"

Tace"shike nn ko inna ta sami abokan zama"

Yace"to lallai dae kam sae ki gaya mata ta tanadar min gurin da zan zauna nida matata da yarana inda zan sakata na wala ba wani wanda zae je ya takura mu"

Tace"Aa aiko d'akinta kad'ai ya ishemu mu dukkan mu har ita sae ma ka sakata ka wala ba wanda zae hanaka"

Mohd ya girgiza kansa d'auke da murmushi yace "kin ganki koh muyi sae da safe dan naga alamar tsokanar ki ba qarewa zatayi ba"

Ryynt tayi murmushi yayinda mohd yakai lips d'insa kan goshinta ya d'aura mata kiss snn ya d'ago yana kallonta yace"ki shafa min kan yarana ki masu addu'a kafin ki kwanta bacci kinji"

Ta gyad'a masa kae tare da fad'in"inshaa Allah,Allah ya tsare min kae sae da safe"

Yace"Amin my Ryynt"

snn ya fita.

Ita kuma ta juya ta koma daga ciki.

Washe gari fa'iza ce taje gidan su malika dmn jajanta mata abinda ya faru,ubanta baya gari sae mahaifiyar ta kad'ae da abin yayi mata zafi sosai har tana ikirarin sae tasa mohd qara kan irin dukan da yayiwa malika na fitar arziki.

malika bata barta ba tace ta barshi kawae don ita ta jawo komai har abin yakae ga haka,kan dole mahaifiyar ta ta bar zancen amma ba don taso ba dan ganin take ba qaramin cin zarafi akayiwa erta ba duka da saki uku a lokaci d'aya duk da cewa sane tasan abinda malika ke aikatawa na mugun nufinta akan Ryynt amma bata ga laifin ta ba sae laifin mohd da ta gani.

Malika na kwance sanye da drip a hannun ta fa'iza na zaune gefen ta tana mata sannu d'uke da alamar tausayawa a fuskarta tana kallon malika dake kallonta tana fitar da qwallah a idonta wacce ta bud'e bakinta a hankali tace"fa'iza wlh ina matuqar son my man bana jin zan iya rayuwa bashi amma gashi ya sake ni har saki uku ba wani gyaran da za'ayi na koma gareshi,shike nn yanzu gabad'aya rayuwata ta lalace ko ma nace na lalata rayuwata da kaina dmn nice na janyo faruwar komai.

Ta qarashe maganar ne cikin muryar kuka sosai.

Fa'iza ta nisa tace"malika ni kaina na tausaya miki dmn ban d'auka haka abun zae kasance ba duk a tunani na mune zamuyi nasara sae gashi Allah ya nuna mana ikon sa akan mu amma abinda nake tunani shine tunda man bae ta6a sanin kina tarayya da wani bayan shi ba zaki iya koma masa"

Da sauri malika tace"ta yaya fa'iza bayan saki uku ya min"

Fa'iza tace"ta hanyar auren d'ibar wuta"

Ni kuwa wa zan aura fa'iza?

Sweetat d'inki mana amma kar ki yarda yasan auren d'ibar wuta zakiyi dashi kinga idan anyi auren sae ki samu hanyar da kika bi ki fito masa sae ki koma ga man d'inki.

No fa'iza ko nayi hakan nasan my man ba zae maida ni ba ya riga da ya tsane ni.

Hm kawai kedae kiyi abinda nace sae dai ko idan kina shakku ko sweetat d'in naki ba zae yarda ya aure ki ba koh?

No fa'iza nasan ma zae aure ni sbd ba kad'an ba yana matuqar son kasancewa dani a ko yaushe kinga kuwa kae tsaye zae amince da aure na,matsalata d'aya shine man dana nasan ko nayi aure na fito ba zae maida ni ba.

Fa'iza tace"kedai ki gama idda kiyi auren ki fito ni nn zan gaya miki hanyar da zaki bi har ki samu ya maida ki ba boka ba malam.

Malika tace"nagode fa'iza da wnn shawara taki da tasa naji sanyi a raina domin bani da wani burin da ya wuce naga cewa na koma ga my man na kuma haifa masa yara kmr yanda yake so kuma har abadah bazan sake tarayya da wani d'a namiji ba face shi sbd bana son mu sake samun sa6ani nida shi bare zancen rabuwa.

Fa'iza tace"that's gud tun daga yanzun ma kar ki sake bari wani abu ya shiga tsakanin ki da sweetat d'inki har sae kunyi aure"

Malika tace"zan kiyaye"

6angaren Ryynt kuwa kullum man na zuwa gidan kuma sosai take samun kulawa a gun inna ita da yaran ta,ga yaran sam basa da rigima kwata kwata dan ko suna farke sam basa kukan banza sae dae idan sunji yunwa suke d'anyin kuka da kuma ta basu mamma aka had'a musu da madara shike nn suyi bacci abinsu kuma suna jimawa kafin suke farkawa.

Koda rnr biki ta matso su saliha sunyi hutu ae kuwa ba qaramin dad'i Ryynt taji ba duk da dae saliha tafi ta jin dad'in haka ma Ameera taji dad'i dan yanzu ta fara sakewa da Ryynt ba kmr daa ba ,don ko preety ma yanzu alhmdlh bata nuna tsana ga Ryynt sae ma wani janta take a jiki.

Ranar suna sosai akayi biki shagali da mohd ya darje yasa aka yankawa 'ya'yansa kowannen su

Sa da Rago biyu yayinda yaran suka ci suna.

Muhammad Ammar, Muhammad Anwar,and Aishatu Razeenah.

Billy giro😊

[10:07PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```

🔮🔮🔮🔮

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.