Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx
Chapter 50 of 56
*page 88*
Sae can Ryynt ta samu da qyar tace"Mk bana jin dad'i ka bari da safe mayi waya"
Daga haka bata jira me zae ce ba ta katse kiran ta ajiye waya ta soma kuka a hnkli sbd zafin ciyon abinda take ji ya soma kaita maqura.
Mohd kuwa duk ya rud'e sae kiranta yake tayi amma bata d'aga ba nn kawai ya kira Nasir da inna ya sanar dasu halin da ake ciki.
A cikin daren Nasir ya tashi ya shirya yaje ya d'auko inna suka zo gidan.
Kai tsaye suka nufi d'akin Ryynt Nasir ya tsaya a bakin qofa inna ta shiga daga ciki ta sami Ryynt kwance cikin jini duk ta galabaita sae kuka take a wahal ce tana juyi a qasan tiles d'in d'akin.
A rud'e Inna ta qwalawa Nasir kira ya shigo d'akin wanda bae tsaya wata wata ba ya kama Ryynt inna ta kama masa suka fito da ita suka saka ta a mota ,
inna ta zauna baya tare da ita Nasir yaja motor a gaggauce suka bar gidan.
Nan itama malika ta fito ta shiga motar ta ta bisu dan tun shigowar su gidan tana sane asali ma ita da kanta ta bud'e musu qofa a lokacinda taji suna knocking.
Man hospital suka nufa ta parker motar ta tayi zamanta a ciki tana kallo aka shiga da Ryynt ta saki shu'umin murmushi d'auke da chewing gum a bakinta tana taunawa ta d'auki wayarta ta kira fa'iza ring d'aya biyu sae ga fa'iza ta d'aga ,
malika tace"au bakiyi bacci ba knn"
Fa'iza tace" inafa hubby bae barni ba kinsan yau ya dawo daga tafiya da qyar ma na samu ya saurara min yanzu haka ma yana bathroom yana wanka sae dae kuma ke ya akayi bakiyi bacci ba har yanzu?
Hm lallai fa'iza har kya tambaya ae yau banga ta bacci ba sae komai ya gama faruwa a gaban idona tukun don yanzu har wnn abar ta kira wnn tsofuwar da ake kira inna sun zo ita da Nasir suka kawo ta asibiti shine na biyosu sae kallon su kawae nake dan na tabbatar ba abinda likitawan zasu iya mata don kafin ma su iya yin komai abinda ke ciki ya riga ya gama hallakewa haka itama zafin aikin maganin da wahalar naquda bazai bar ma ta rayu ba don kan aje koina ma har ta fara bleeding"
Fa'iza tace"Au haba?
Malika tace"Wlh kuwa ae overdose na had'a mata maganin ynx jira kawae nake in ga an fito da gawar er banza.
Fa'iza tace"kae kinyi dae dae wlh,
ashe koni banga ta bacci ba yau sae dae najira kiran wayarki dmn naji kyakkyawan labari"
Malika tace"lallai
dae kam ki saurari kirana ko yaushe don yau kan farin ciki ma har sadaka sae nayi abinda ban ta6a yi ba a rayuwata kuwa"
Fa'iza tayi er dariya tace"kinga bye sae kin kirani dan naji alamar hubby zae fito daga bathroom baccin qarya nake so zanyi dan nasan halinsa in yaga ban koma bacci ba ko yayi wanka wlh zai iya sake nemana a second round"
Malika tayi er dariya tace"ae kima yi baccinki dan koni idan naga zasu 6ata min time gida zan koma dole dae da safe zanji labari don mutuwa dae ba 6oyuwa take ba kawae dae ki saurari kirana"
Fa'iza ta fashe da dariya tace"kae malika bakida dama wlh"
Malika tace"uhm kedai sae anijma"
nn suka katse wayar.
Daga nn ma kawai malika taja motar ta ta koma gida.
Ryynt kuwa har washe gari ba kanta sae wahala da take ta faman yi ita bata haifu ba ga jinin yaqi tsayi duk da irin taimakon da nurses keta bata kuwa.
Guraren qarfe goma sae ga mohd ya diro asibitin da kallo d'aya zakayi masa kasan hankalin sa a tashe yake.
Ya sami inna da Nasir still su kad'ai ne a asibitin ba wani wanda yazo dan ba'a sanar da kowa ba tukun sae anga yanda abun ya kasance.
Yace dasu"ya ake ciki ne dan Allah ina Ryynt d'in take in ganta?
Kafin suce komai sae ga wata likita ta fito tana ganin mohd tace"yauwa Dr ur wife tana cikin wani yanayi gabad'aya ta galabaita sam bata iya pushing any more da kamar sae an mata aiki"
A rud'e Mohd yace"muje in ganta"
Nan suka tafi kai tsaye se d'akin da Ryynt take wacce ke kwance kan gadon haifuwa abin tausayi duk ta wahala mohd ya nufi gurinta kmr zae yi kuka yana kallon yanda take bleeding a fusace ya kalli nurses d'inda da ke kan Ryynt yace"wane irin abune haka kun bar min ita sae bleeding take kuma kun kasa fitar min da babies d'ina so kuke su mutu ne ko yaya!
Likitar da suka shigo tare da shi tace"Sory Dr wlh it's not our fault haka aka kawo mana ita kuma munyi iya qoqarin mu amma abu ya faskara kawae abinda na fahimta ba time d'in haifuwar ta bane da akwai maganin da tasha da ya mata qarfi har ya tashi naqudar shiyasa ta wahala har ma abinda ke ciki duk ya galaibata baya iya yunqurin fitowa"
Kwalla tap a idonsa ya kalli ryynt wacce ke kallon sa ta kama hannun sa ta riqe gam a cikin nata cikin muryar kuka tace"Mk zan mutu"
Da sauri ya girgiza kansa yana mae share mata zufar goshinta da d'ayan hannun sa yace"Baza ki mutu ba my Ryynt ki nisa inshaa Allah yanzun zaki haifu kinji"
Ryynt da ko numfashin kirki bata iya yi muryar ta na rawa tace"Mk bazan iya ba mutuwa ma zanyi na sani"
Girgiza kansa yayi had'e da saurin kai hannu yana share mata hawayen da ke sauka kan fuskarta yace"um um my ryynt inshaa Allah baza ki mutu ba ki daina fad'ar haka dan Allah"
Tace"uhm uhm mk nayi qanqanta da haifuwa ka sani kuma wnn qaton cikin bansan ma ya zan iya haifo abinda ke ciki ba"
Yace"my Ryynt Allah zae taimake ki kawae rufe idonki ki nisa kinji dan Allah"
Ba musu ta rufe idanunta a hnkli tayi iya qoqarin ta na ganin ta nisa amma ta kasa sae kuka ta fashe masa dashi muryar ta na rawa tace"bazan iya ba mk dan Allah kiramin inna in ganta dan Allah"
Nan mohd yasa aka kira mata inna tazo Ryynt ta kama hannun inna sae kuka take tana roqon inna ta yafe mata mutuwa zatayi inna ta shiga rarrashinta tana mata addu'a tana tofa mata man kuwa duk yabi ya rud'e komai ya kasa yi sae shafar goshin Ryynt yake yana ta rarrashin ta wacce ta soma salati tana qoqarin miqewa sbd wata irin azaba da ta soma ji ta koma da qarfi ta saki hannun inna ta kama hannun mohd sae kuka take tana roqon ya yafe mata ga kuma salatin da take ta faman yi a bakinta yayinda take ta faman qoqarin miqewa man yana maida ta sae addu'a yake ta mata dan ya fahimci haifuwar tazo mata gab.
Da qarfin tsiya Ryynt ta qara riqe masa hannu sbd wani irin nishi mae qarfi da yazo mata a nn man yayi qoqarin cire hannun sa daga nata yaje da sauri yana bata taimako ta hanyar sa hannun sa ya soma ciro 'ya'yan sa d'aya bayan d'aya santala santala dasu biyu maza mace d'aya kuma kowanen su cikin qoshin lafiya.
Plz sorry 4 diz one
Billy giro😊
[10:07PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```
🔮🔮🔮
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.