Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx
Chapter 14 of 56
_*page*_ *```32```*
Shaye da toka ta janye hannunsa snn tace "Alhmdlh"
Shi kuma ya mà ida dubañsa gun mami yace"bani ruwa gasu can a bayanki kan bedside drawer, mami ta kawo mai ruwan ya kalli Rynt da tun d'azu ta juya bayanta dmn ci gaba da bacci,yace"tashi kisha magunguna idan ba haka ba ciwon zai sake dawo maki ne"
Ba musu ta tashi zaune ,har zai 6alla magungunan sae kuma ya kalleta yace"ko kina so na had'a miki da allura sbd naji jikin naki da zafi kuma zaki fi jin sauqi a take"kallon sa tayi ,sae kuma tayi shiru don dai tana son samun sauqi nn take kam ko don zuwa islamiyya ta kuma samu taje gidan inna, amma bata jin zata iya bashi wani guri a jikinta ya mata allura,cikin sanyin murya tace"Aa bana son allura zansha magani kawai"
Bai musa mata ba ya bata magungunan tasha, snn ya tashi zai fita,mami tace"nazo mu tafi yaya"yace"Aa mami asibiti zan tafi"tace"yaya ina zuwa ko can d'in ne"yace"mami idan yawo kike so bari gobe zaku fita keda Anti kinji"yaya to ai anti bata da lfy kawai wayo kake so kamin"ta qarashe mgnr ne kmr zatayi kuka yace"zo"
tazo gurin shi ,ya rage tsawon sa tare da kai hannu ya shafo fuskarta yace"kar kiyi kuka ba wayo nake miki ba dgske nake zaku tafi yawo gidan inna idan anti taji sauqi kinji"to yaya haka ko jiya da dare nayi ta jiranka kazo ka d'auko min chocolate har nayi bacci baka zo ba"eyyah mami ai kina ficewa aka sallama min sae ya kasance koda na dawo na samu har kinyi bacci amma yanzu nuna min inda chocolate d'in yake sae na d'auko miki ko"hannunsa taja tana fad'in "muje kaga ai a wardrobe d'ina ne amma can sama, nn ta bud'e wardrobe d'inta ya d'auko mata ya vata, ta kar6a cike da murna shi kuma ya fita, Rynt dake kallon su sae mamaki take irin yanda yake shiri da mami amma kaf sauran qannan sa tsoronsa suke ji.
A washe gari ne mohd ya cikawa Rynt alqawarinta yakaita gidan inna ita da mami suka yini sae dare ya maida su.
D next day Rynt ce a d'akin mohd tana gyara mishi d'aki sae ga malika ta shigo d'akin wacce saukar ta kenan, wani irin farin ciki ta sami kanta dashi ganin Rynt a d'akin,ta rufe qofa da makulli ta kuma cire makullin ta jefa a jakarta a cewar yau ko ita ko Rynt dole ne a kwashi gawar d'ayan su,sae da tayi d'amara snn ta shiga dube dube taga ko zata sami wani makamin da zai raba Rynt da duniya zama d'aya ,can taga tunda ta rasa makami , abnda yafi kawai taje da qarfin tsiya ta kwashi qafafun Rynt ta yanda idan takai qasa sae dai wata ba ita ba.
Tana gama yanke shawara ta nufi Rynt gadan gadan wacce sam bata san da shigowar malika ba sae aikin gabanta take,ai kuwa kai tsaye taji an kwashi qafafunta kafin takai qasa ta buga ihu cike da mugun jin tsoro,malika kuwa a maimakon taga Rynt qasa sae ganin ta tayi a jikin mohd,wani baqinci ne ya tokare ta a wuya ganin Rynt male male a qirjin mohd sae baqin ciki biyu suka tara mata,cikin azama ta ciro takalmin ta mai d'an karan tsini zata dokawa Rynt shi a ka mohd ya riqe mata hannu da d'ayan hannunsa sbd d'ayan hannun yana rungume da Rynt ne wacce tuni ta some kan tsoratar da tayi,ya fizge takalmin had'e da
daka mata tsawa yace"meye haka,me ta miki keda yanzu ne dawowar ki!bata kula shi ba sae d'ayan takalminta ta ciro tana fad'in"cabd'i har ka manta zagin ubana da tayi kenan,wlh yau sae tasan ba irin mu ake zagi a zauna lfy ba!tsaki yayi ya sake fizge takalmin ya kuma ture ta, tayo kukan kura ta ture Rynt daga jikin shi,
nn Rynt ta fad'i kanta ya daki gefen gado,bata barta ba tayi kanta zata fara kai mata duka,mohd ya rirriqeta ta shiga kokawa dashi na ganin ta qwace kanta,bata iya qwatar kanta ba sae mohd d'in ne yaga dama ya saketa tare da fad'in" can't u see she is unconscious,to bari kiji wlh duk kika ta6a ta zanyi maganin ki ne kuma ki gwada ki gani kin dai san hali na ba sae an gaya miki"
Tace"wlh ko ba yau ba sae na hallaka ta kuma bari ka gani kul ba dad'e kul ba jima kuwa"
Daga nn taje ta bud'e qofa ta fita sae masifa take tayi.
Mohd kuwa d'aukar Rynt yayi ya d'ora ta kan bed, snn ya samo ruwa ya shiga yayyafa mata a fuska, cikin ihu da firgici ta tashi ta qanqame mohd tana karanto addu'o'i sbd duk d'aukar ta aljanu ne suka cirata sama,duk tabi ta firgice tana ta mai kuka,ya qara rungume ta a jikin shi yana kwantar mata da hankali,sae can ya samu hnklinta ya d'an fara dawowa gareta,inda a hnkli yaga takai hannu kan gefen goshinta gurin da kanta ya daki gefen gado, ta d'ago hawaye tap a idonta tana kallon shi,yace"da zafi? tace"wlh d'akin nn naka aljanu ne dashi kaga har sun jimin ciwo"kallonta kawai yake bai ce komai ba sae hannun ta ya janye yana duba gurin, gurin yayi ja har ma yad'anyi lolo kad'an, nn ya lumshe ido tare da shirin maida ta kan qirjinsa had'e da cewa "sorry".
Cikin tsananin mamaki da jin haushi ta kalli abinda yake shirin yi don sae a lokacin hnklinta ya gama dawowa jikinta,ai kuwa tayi saurin hana faruwar hkn ta tashi da sauri zata bar gadon ,by mistake hannunta ya latsa wani guri a jikin gadon abin mamaki da ban tsoro a gun Rynt sae kawai taga wasu silalan fararen qarafe na fitowa kowane gefe ta jikin gadon,ihu ta saki ta sake komawa jikin mohd ta qanqame shi amma ta kasa d'auke idon ta akan abinda ke ci gaba da faruwa don wani farin qyalle tagani shar shar kmr net yana biyo ta jikin qarafen har ya lullu6e su sae gadon ya zama kmr suna cikin wata kyakkyawar rumfa ne mai kyan gaske.
Kuka ta fashe masa dashi tace"wlh na gaya ma d'akin nn aljanu ne dashi dan Allah ka ftr dani ,na roqe ka"
Kallon ta mohd keyi yanda ta rud'e sosai tana kuka don jikinta har qyarma yake,yakai hannu ya danna wani guri a jikin gadon sae kawai komai ya shiga komawa a hnkli har gadon ya zama tamkr ba shine ya musu rumfa a d'azun ba.
Ya kalli Rynt dake qanqame a jikin shi snn yace ni d'akina ba aljanu gidadanci ne kawai irin naki sae ki tashi ki fita duk kin wani cumuimuyen min a jiki haka"cikin kuka had'e da masifa tace ba aljanu amma d'azun aka kwasheni akayi sama dani"yace"wnn kuma ya rage naki nidai ki fita nace"tace"ai ko baka ce va ynxn fita zanyi"
ta fad'i hakane kawai amma kuma bata iya sauka kan gadon sbd tsoron kar ta sake ta6a wani gurin, ganin haka yasa mohd ya saukar da ita, ta kalle shi shaye da toka snn tabar d'akin,cike da alqawri a ranta bazata qara tako qafar ta a d'akin ba.
Haka ko akayi don tun daga rnr Rynt bata qara komawa d'akin mohd ba ,wanda yanzu an d'auki lokaci sosai don har su saliha sun dawo hutun makaranta suna batun komawa first term.
Duk tsawon lokacin nn mohd shi ke gyara ma kansa d'aki sbd duk lokacinda ya aika mami Rynt taxo ta gyara mai d'aki sae tace bata jin dad'i.
Malika kuwa takaici ma ne yace ta gyara mai d'aki don acewar shi in banda qara lalata mai d'aki ba abinda ta iya.
Yau ya dawo a gajiye daga asibiti ga d'akin nasa yana buqatar gyara ya aika mami yace taje ta gaya ma Antinta tazo ta gyara mai d'aki ta dawo masa tare da saqon wae anti tace bata jin dad'i.
Tashi kawai yayi ya tafi sae d'akin Rynt ya sameta zaune tana duba littattafanta na islamiyya sbd rnr,rnr alhamis ce basa zuwa islamiyya .
A fusace ya d'auke littattafan ya d'aura su kan bedside drawer snn yace"bana son raini tashi kije ki gyara min d'akina! Shaye da toka tace"nifa bana jin dad'i"da Allah maza tashi ai baki zo nn gidan dan kiji dad'i ba!tace"nifa ina nufin bana da lafiya.....cikin mugun hasala ya nuna ta da yatsa yace"kar ki kuskura na koma jin wnn kalmar a bakin ki, yau wata kusan nawa kenan duk nace ki gyara min d'aki kice ba kya jin dad'i sbd kin raina ni ko shine har kike tunanin zan ci gaba d'aukar miki rainin,to bari kiji wlh duk baki je kin gyara min d'aki ba ,ba ke ba zancen bokon nn kuma ba wanda ya isa ya tilsatani na saki!daga haka ya fita kmr zai tashi sama, yabar Rynt qwallah cike tap a idonta tana tunanin in taje aljanun d'akinsa zasu iya sake cirata sama su yar wata qil ma wnn karon mutuwa zatayi ba suma ba, gashi kuma bokon nn tayi bala'in qwallafa ranta akai har kullum ma qidayar kwanaki take inda yau sauran ta kwana uku ta fara zuwa mkntr boko gashi har ma an d'inka mata uniform saura littattafai da takalmi.
Tana cikin share hawayenta ne sae ga saliha ta shigo, tace"Rynt lafiyar yaya naga yaja mota a hasale ya fita! Rynt tace"Yauwa saliha tun da ya fita dan Allah taimakamin kije ki gyara masa d'akin sa...ke wlh ni bazan iya da halin yaya ba kawai kije ki gyara masa keda yasa,saliha bazan iya bane d'akinsa tsoro ake ban dan Allah ki taimakamin kije ki gyara masa kafin ya dawo wlh yace idan ban gyara masa ba bazan yi boko ba kuma kinfi kowa sanin yanda nake son nayi bokon nn"ta qarashe mgnr kmr zatayi kuka saliha tace"nifa fad'an sa nake yiwa gudu ba komai ba"Rynt tace"kawai kije ki gyara duk fad'an da zaiyi aini zai yiwa tunda bai san cewa ke kika gyara d'akin ba, shiyasa ma nake son kiyi sauri kafin ya dawo dan Allah.
Da qyar dai saliha ta yarda ta tafi,wacce ta fara gyra masa d'akin kenan sae ga mohd ya shigo d'akin fuskar d'auke da 6acin rai sosai.
Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: [1/22/2017]
🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮
🔮🔮🔮
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.