Complete Hausa Novels

Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx

Chapter 2 of 56

_*Page 2*_

Komawa tayi daga ciki cike da kewar Anwar da Sarat .

Bata yarda ta bud'e ledar ba ta ajiye kusa da ledar rogon da Sarat ta kawo mata a cewar sae Mahaifin ta ya dawo ko za a bud'e komai.

Har guraren la'asar mahaifin ta bai dawo ba haka taci zama duk yunwar da take fama da ita bata ci rogon ba iya karta ta qara sakawa cikin ta ruwa .

Sae guraren qarfe biyar mahaifin ta ya dawo yayinda fuskar shi take cike da damuwa.

Rayyanat taje a natse cikin murna tana tarbon mahaifin ta inda ta kai hannu ta d'auke fartanyar da ke kan kafad'ar sa ta kuma d'obo ruwa ta bashi,

bai sha ruwan ba sae hannun sa ya tara ya wanke ya zauna a sukwane tare da dafe kan shi.

Rayyanat da ko kad'an bata son ganin mahaifin ta cikin damuwa nan take idanun ta suka ciko da qwallah ta durqusa a gaban shi tare da jaye hannayen sa da ya dafe kansa.

Muryar ta na rawar kuka tace "me yake faruwa ne Baffa dan Allah ka sanar da ni"

A hankali mahaifin ta ya d'ago idanuwan sa da sukayi jajir ya goge en guntayen hawayen da ke gefen su yace"Rayyanat na kasance bani da wani buri a rayuwa sae don ganin na faranta miki hakan yasa tun lokacin da mahaifiyar ki ta rasu ta barki kina jinjira naqi nayi aure don kawai kar ki shiga quncin rayuwa domin bansan matar da zan auro wace iri bace shiyasa na haqura da aure gavad'aya sbd zan iya zamowa auri sake idan har na had'u da matan da ke quntata miki ni kuma bana son kasance wa haka kuma gashi bani da wasu en uwa da zan kaiki a gurin su shiyasa na za6i na raine ki da hannu na,yayinda na zame miki tamkar uwa na kuma so na kasance uban da ba wani abu da zaki nema ki rasa amma talauci bai bar na miki haka ba kiyi haquri Rayyanat da na kasance uban da kullum sae kin nema kin rasa ba yin kaina bane wannan jarabtar ubangiji ce wacce a kullum nake roqon Allah ya kawo muna qarshen ta muna masu lashe jarabawar ba tare da mun sa6a masa ba.

Rayyanat nasan ke 'yace ta gari zaki fahimci abinda nake nufi da kuma abinda zan fad'a a yanzu.

Rayyanat a yau zamu kwashe komatsan mu mu koma daji da zama can gurin gonar mai gari da nake masa noma....Baffa me yasa zamu koma inda ba kowa ?dole ne Rayyanat sanin kan ki ne wannan gidan ba nawa bane kuma bani da wani gida na kaina haya muke kuma sanin kanki ne duk wata na kanyi qoqarin ganin na biya kud'in haya koda kuwa su kad'ai ne suka rage mana na abinci amma a yau Bala yaje har gurin mai gari yakai qara ta kan cewa bana biyan shi kud'in haya wai har ma yana bina na wata biyu naqi na biya shi, duk da cewa nayi ma mai gari bayanin cewa ba gaskiya ya fad'a ba amma mai gari ya zare kud'in noman da nake binsa na wata d'aya ya bawa Bala na zamo bani da ko sisi kuma Bala ya nemi na bar masa gida wai yana so zai saka wad'an da ke biyan sa duk wata.

Ba irin haqurin da ban bashi ba amma yaqi shiyasa mai gari yace idan har zan iya ya bani dama naje can kusa da gonar shi na haqa bukka mu riqa zaman mu a can tunda ba wasu namun dajin da ke cutarwa a gurin.

Cikin kuka Rayyanat tace"Allah yasa haka shi yafi Alhairi Baffa"Amin Rayyanat bari naje cikin gari naga ko zan sami wani aikin da zanyi a biyani mu samu abinda muka ci kafin mu kwanta"

Kallon mahaifin ta tayi kafin take share hawayen da ke kan fuskar ta tace"Baffa akwai rogo da Sarat ta kawo min ka bari kaci tukun ko zaka fita"

Aa Rayyanat ki dai ci in yaso idan Allah yasa nayi nasara sae mu qara cin abinda ya samu,, Baffa rogon fa mai yawa ne kuma tun safe na ajiye shi sae kazo muci tare,,,girgiza kansa yayi yayinda yake qara jin son er shi sbd yasan halin Rayyanat komai qanqantar abu bata yarda taci ita kad'ai sae tare da shi.

Nan ya dafa kanta yace"Allah yayi miki albarka Rayyanat ya kuma sanya nasara da albarka a cikin al'amurranki ya kuma sauya miki wannan rayuwa da muke ciki ma'ana nan gaba kad'an ki kasance cikin wadata da walwala had'e jin dad'i mai d'orewa har izuwa qarshen rayuwar ki"Amin Baffa na gode.

Nan ta d'auko musu rogo suka ci bayan sun kammala ta d'auko ledar da Anwar ya bata ta bawa Baffan ta ba tare da tace da shi komai ba yace"Rayyanat daga ina wannan ledar ta fito? Cikin jin kunya ta duqar da kanta ta kasa cewa komai wanda hakan yasa nan take ya fahimci inda ledar ta fito yace"Anwar ko sun tafi kenan? Eh sun tafi tun d'azu ,,to Allah ya kiyaye hanya ,,Amin Baffa,,tace"Baffa kayi haquri ban kar6a ba sae don ya had'a ni da Allah"ba komai kuma ai ba a maida hannun kyauta baya.

Nan Abban ta yace ta bud'e kayan koda ta bud'e kala biyu ne masu kyau less da atamfa kuma da hijab kala biyu wato kalar kayan sae takalmi taki d'aya da kuma tokar wanka mai had'e da set d'in turare sae wata envelope da aka d'ora akai wacce ta bawa Baffan ta tace shi zai bud'e sbd tana ganin kamar kud'i ne a ciki koda mafahaifin ta ya bud'e en dubu dubu ne sabbi dal har dubu biyar sae wani tsadadden zoben azurfa black an white da wata er guntuwar takarda soke a cikin zoben.

kasa had'a ido tayi da Baffan ta yayinda yake miqa mata kayan bata kar6i kud'i ba sae zobe ta kar6a had'e da takarda tace"Baffa ai a gurin ka kud'in ya kamata su kasance da kuma wad'anan tufafin"Rayyanat ki ajiye komai a gurin ki sbd kinga fita zanyi naje naga gurin da ya kamata mu haqa bukka na fara aikin kafin gobe sbd tun da safe yake so mu bar gidan"

Baffa muje na taya ka ba musu yace "to adana kayan muje"

kwalla taje ta bud'e ta saka kayan suka fita.

Da suka fita basu suka dawo ba sae yamma liqis.

Da dare Rayyanat bata iya bacci ba sae da ta d'auko wannan takardar ta fara karantawa kamar haka

*_"Rayyanat ina so ki saka wannan zoben a yanzu kuma kimin alqawari baza ki ta6a cire shi ba har abada domin cire wannan zoben tamkar kin cire ni a cikin zuciyar ki ne_*

Murmushi ne ya bayyana a fuskar ta yayinda take sanya zoben inda ta rufe idon ta a hankali tace"

*_yaya Anwar nayi maka alqawari wannan zoben ba zai ta6a fita a yatsa ta ba sae dai idan mutuwa nayi aka cire shi_*

Daga haka ta kwanta sae kallon yanda zoben yayi matuqar kyau a yatsan ta take har ta shiga magana a ranta cewa

_"Da ace ko mutuwa nayi baza a raba ni da zoben nan ba da nafi kowa farin ciki"_

Yaya Anwar ina ma ace zoben nan mai 6acewa ne da na bashi umarnin ya 6ace a lokacin da na mutu har akaini makwanci na don dai kawai ya kasance ina tare da kai a duk inda nake ko da yake ko ba zoben nan kana tare da ni sbd kana cikin zuciya ta ba kuma zan ta6a iya fitar da kai ba kamar yanda hanta bata iya rabo da jini.

Tana maganar ne a fili cikin natsuwa tamkar anwar na kusa da ita.

Washe gari tun da asuba ta had'u da mummunan labari su Anwar sunyi had'arin mota kuma ba wanda ya rayu a cikin su kuka taci tamkar ranta zai fita Baffan ta kuwa sae bata baki yake yana aikin rarrashi.

Suna cikin haka ne Bala yazo cike da masifa yasa aka yi ta fitar da kayan su ana watsi da su wanda hakan ya qara sa Rayyanat cikin wani yanayi ganin yanda ake wulaqanta mahaifin ta da ke ta ba Bala haquri kan su daina watsar musu da kaya bai saurare shi ba sae da suka fitar da kayan kaf tare da jan hannun Rayyanat suka ingiza ta waje wacce ta kasa yin komai sae kuka .

Mahaifin ta ne ya kama ta ta tashi sbd fad'uwar da tayi garin ingiza ta da akayi har ma suka fasa mata baki.

Nan suka fara kwasar kayan su suna zubawa a cikin wani tsofon baro da mahaifin ta yayi yayin tallar ruwa a ciki wanda maya biyu sukayi suka gama kwasar kayan na su hakan yasa basu koma cikin gari ba sae qoqarin ganin sun qarasa bukkar da suke su samu su zuba kayan su.

Bayan sun kamalla ne mahaifin ta ya zauna yana qara bata baki kan tayi haquri da komai na duniya sae haquri kuma mai wuce wa ne amma Rayyanat tamkar mahaifin ta na qara mata qarfin kuka ne domin da zarar ta kalli zoben da ke kan yatsar ta sae ta sake fashewa da wani sabon kuka .

Haka Rayyanat tayi sati tana kukan rashin Anwar da Sarat duk tabi ta rame ta zamo tamkar ba ita ba,sae dai yanzu suna samun d'an abinda suka ci ta hanyar amfani da kud'in da anwar ya bawa Rayyanat.

Yau kusan wata biyu kenan da komawar su jeji tun Rayyanat na tsoron zaman jejin har ta saba sae dai har yañzu mutuwar anwar bata sake ta ba bcs duk lokaçin da ta kàlli zoben da ke kan yatsar ta sae ta zubar da qwallah.

Tafe suke ita da mahaifin ta sun fito daga cikin gari suna qoqarin tsallake titi nan wata mota tazo a gurguje ba qaqqautawa inda Rayyanat tayi saurin jawo hannun mahafinta don ganin sun kaucewa motar amma tuni motar tayi awon gaba da mahaifinta,a rikice ta d'ora hannu aka ta kurma wani irin ihu mai cike da tsànàñin firgici ganin yanda motar ta sake dawowa kan mahaifin ta tare da jefo bunch d'in 1k kan fuskar mahaifin nata aka kuma ja motar a tsiyace inda duk tashin hankalin da take ciki bai hana ta qure lambar motar da kallo ba wanda bata kauda idon ta ba sae da ta hadda ce numbar.

Sannan ta koma kan mahaifin ta da ko shurawa bai yi ba ta shiga girgiza shi cikin kuka tana kiran"kai kad'ai ka rage min Baffa dan Allah ka tashi wlh nayi ma alqawari ko shi waye *BA ZAN BAR SHI BA!*sae na rama abinda ya maka dan Allah Baffa ka tashi kar kace zaka tafi ka bar ni,kasan bani da wani a duniyar nan bayan kai,ka tashi Baffa! Baffah!! Baffah!!!

Kuka ta shiga yi sosai har da majina ganin Baffan nata yaqi ya motsa nan ta rungume shi qam a qirjinta tana ci gaba da kuka mai mugun ban tausayi .

*_Billy giro😊_*

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

09/12/2016

🔮```3```🔮

Haka Rayyanat taci gaba da kuka har ta gode Allah dmn ta fahimci tuni Allah ya kar6i ran mahaifinta.

Sati d'aya da rasuwar mahaifinta ta baro qauyen su ba tare da kowa ya sani ba.

Kuka takeyi sosai a cikin mota har suka iso garin kano ta shiga qarewa garin kallo ba tare da tasan inda zata je ba wani kuka ta shiga yi sosai shike nn yanzu bata da kowa a duniya sae wanda yaga Allah ya taimaka mata,yanzu bata san wace irin rayuwa zata shiga ba kawai dai tasan duk rnr da Allah ya had'a ta da wanda ya kashe mahaifinta Baza ta bar shi ba! koda kuwa itama zata bar duniya ta dalilin hakan.

Zaune take kusa da wani gidan mai sae rusar kuka take kamar yanzu ne mahaifin nata ya rasu.

Mabaratan da take zaune kusa da su sae kallonta suke abin tausayi dmn ganin suke har sunfi ta dama a yanayin da suka ganta ciki.

Ta jima sosai a gurin ga yunwa ga qishi ta tashi tsaye da qyar sbd jirin da ke d'ibar ta, kallon mabaratan da ke kusa da ita take ta hango er gorar ruwa aje kusa dasu ta fara tako cike da son taje tace su en mata ruwan tasha ba tare da ta damu da ganin su mabarata bane ita dai ta samu ta kawadda qishin da take ji.

Gab take da isa gurin su wata irin tsaleliyar mota ta tsaya a gurin wanda ke ciki ya sauke glass d'in motar a hankali yana kallon mabaratan cikin wani yanayi na qyama kamar wanda zai yi amai.

Hannu yasa ya zaro kud'i a aljihun sa 1k bunch ya jefa musu kud'in dai dai Rayyanat ta juyo kan ganin yanda taga mabaratan sun qure guri d'aya da kallo, yanayin yanda ya jefa musu kud'in yasa gabanta yayi mugun fad'uwa kuma tabbas kalar motar da ta kad'e mahaifinta ce take gani tsaye a gabanta

Mabaratan sukayi ruu! dmn d'aukar kud'in da aka jefo musu sae qoqarin kada Rayyanat suke da kud'in ke tsakiyar qafafunta ita kuwa ko qwaqqwaran motsi ta kasa sae qarewa motar kallo take ba tare da ta iya hango wanda ke ciki ba dmn tuni ya mayarda glass d'in motar sa ya rufe.

Tako ta fara a hnkli dmn ta kai idonta ga numbar motar,taga ba ko shakka ita ce numbar motar da ta kad'e mahaifinta wani irin yanayi Rayyanat ta tsinci kanta a ciki marar misaltuwa idanuwanta suka ciko tap da qwalla ta samu da qyar ta d'aga yatsarta tana nuna numbar motar, cikin rasa iya motsa koina na ga66an jikinta take ci gaba da kallon numbar.

firgigit tayi ganin motar ta fara tafiya sauri sauri ta shiga bin motar wacce still yatsarta na kan numbar motar tana nunawa........"ke! ke!! ke!!!" shine abinda mutanen gurin keta fad'a amma sam hanklin Rayyanat na tare da motar hakan yasa taji an kwashe ta kai tsaye kanta ya daki wani guri tun daga lokacin bata qara sanin inda take ba.

Matar da ta kad'e Rayyanat ce keta faman zarya a asibiti cike da takaici se faman duba wristwatch d'inda ke hannunta take....wayar ta ce ta shiga ringing ta d'aga cikin sauri tace"yauwa honey pls kazo *MAN HOSPITAL* na kad'e wata yarinya ne"

daga haka ta katse wayar ba jimawa ya iso sae ga doctor ya fito yace taje yanzun zata iya ganin yarinyar.

Sosai Rayyanat ta samu rauni har dai saman goshinta sae dai bata farfad'o ba sae bacci take ana mata qarin jini.

"Garin yaya haka ta faru?cewa da mijinta

Tace

"Honey kasan matsalar talaka da baqin hassada duk inda motar mai kud'i ta wuce sun fara binta da ido kenan shine fa ita bata tsaya a kallo ba har bin motar take kamar motar ubanta! sae wani qoqarin kamo motar take ana faman kiranta amma a banza! gashi yanzu duk ta 6ata min tsari har yaya ya tafi ya barni may be ma har jirgin su umma ya sauka ya kai su gida,eyya sorry yanzu ki tafi kawai in yaso ni na tsaya.

Tunda Rayyanat ta farfad'o bata da aiki sae na kuka duk yanda yaso tayi mai magana taqi har kusan kwana biyu snn aka sallameta .

Gidan shi yaje da ita suna shiga falo yaji qarar fashewar glass da sauri ya kalli inda yaji sautin yaga matar sa ce ta saki glass cup tana masa wani mugun kallo cikin tsananin kishi .

Da mamaki yace"lafiya pretty"har ka tambaya! wnn wace er iskar ce ka shigo min da ita a gida!

Yace"ikon Allah yarinyar da ki kad'e ce fa aka sallame ta yau......to dan ita ce sae ka wani kwasota ka kawo min ita a gida har da wani riqo mata qunshin ledar ta,to pretty ina kike son taje bata qarasa jin sauqi ba kuma kinsan har yanzu ko magana batayi ba bare asan daga inda ta fito....fuuu! tazo ta fizge qunshin Rayyanat dake hannun shi tace"Ai tunda ba gidan ubanta bane wlh sae ta fita!da gani ma irin shegun yaran nn ne da iyayen su ke jefarwa suna gantali a hanya shine tayi shiru taqi fad'in inda ta fito ita ala dole taga ta samu mafaka,nn ta jefa ma Rayyanat qunshinta tace"oya! fitar mana daga gida shegiya! kije can ki qarata da baqin gantalin ki da uwar ki taja miki!

A hnkli Rayyanat ta duqa ta tsince en kayanta da suka fito cikin ledarta snn ta tashi tana mai share qwallah a idonta ta fita.

```Billy giro😊```

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BAR SHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

11/12/2016

🔮```4```🔮

Cikin hanzari mijin pretty yabi Rayyanat yana fad'in ta dakata.

Kamar kar ta tsaya sae kuma ta tsaya ba tare da ta juyo ba sbd kuka take yi sosai har yana so yaci qarfinta. Kafin ya qarasa gurinta pretty tayi sauri tasha gabanshi tace"wlh bafa zata zauna a gidan nn ba!bai kula ta ba sae qoqarin wucewa yake tana tare mai hanya ya tsaya tare da nuna ta da yatsa snn yace"kinga pretty kar ki kaini qul fa!

daga haka ya ra6a ta gefenta ya wuce yace da Rayyanat "muje"ta sake shan gabanshi

tace"ban gane kuje ba ina zaka tafi da ita? Koma ina ne ba ruwanki yanzu,tunda ke baki san ki tasauya ma bayin Allah ba!ta wani le6ace baki tace"meye abin tausayi wa talaka ko talaka mabaraciya wad'anda basu da burin da ya wuce ganin bayan dukiyar mutum kullum cikin roqo da fad'in a basu,basa nema sae dai a nema a basu sbd baqin lalaci irin nasu.

Ki iya bakin ki pretty kullum cikin aibata talaka kike talaka ba abin gori bane dmn kema baki wuce Allah ya jarrabace ki da talauci ba........ Tuf!bakin ka ya sari d'anyen kashi wlh ni Allah tsare ni da baqin bakin ka!

Ganin abin na son zama musu fad'a Rayyanat tace"ka bar shi kawai nagode ni zan tafi koma ina ne"

Yace"Kwantar da hnklin ki ba nn gidan zaki zauna ba gidan kakata zan tafi dake har ki qarasa jin sauqi tukun....cabd'i!lallai ma Nasir kai baka ji me tace bane "wai zata tafi koma ina ne" hakan fa na nuna ba tada asali amma shine har kake qoqarin kaita gidan kaka!

Wai pretty me yake damunki ne ya zaki kama fad'ar magana akan abinda baki da tabbacin sa! Murgud'a mai baki tayi tace"wane tabbacin kuma zan nema bayan sanin kanka ne duk er asali bazata kama gantali kan hanya ba har ma tana fad'in koma ina ne zata tafi ai duk d'an asali ba zai ce haka ba sae dai yace zai koma gurin en uwansa!

Guntun tsaki yayi snn ya kalli Rayyanat yace"baiwar Allah gaya min sunanki"

Sae da ta share hawayen da keta faman sintiri a kan fuskarta snn tace"sunana Rayyanat..... Mtsw kaji wani kilinbibi d'an qauye ne yasan ya qawata suna haka ai sae dai Rayyanatu hm!wai Rayyanat....yi mana shiru a nn pretty meye ruwanki da sunanta kuma!

yace"Rayyanat yi haquri sanar dani abinda ya kawo ki garin nn dmn na fahmici kamar ke ba er garin nn bace ko"kuka kawai Rayyanat ta fashe dashi ,Nasir yayi shiru yana nazari inda ya fahimci tabbas akwai abinda ya faru da Rayynat wanda bata son a tambaye ta inda ta fito tunda ko asibiti haka take ajiye mai kuka idan ya tambayeta nn ya tsara a ransa bazai qara mata tambayar ba har se taji sauqi tukun.

Yace"daina kuka zo muje"

pretty tayi saurin riqo hannun shi tace"honey bafa inda zaka je da ita"wani mugun kallo ya watsa mata ya kuma fizge hannun shi,cikin tsiwa tace"ai ko wlh sae dai ka za6a ni ko ita! don duk ka fita da ita nima sae nasa qafa na bar gidan nn na tafi gidan mu"yace"in kin iya kivar duniya gabad'aya ba ma gidan ba!

Daga haka yasa qafa ya fita shida Rayyanat.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BAR SHI BA```🔮

```Na Billy giro😊```

11/12/2016

🔮```5```🔮

Suna shiga gidan kakar ta tarbe su da murna kamar har

Rayyanat d'in ta sani dmn akwai ta da son mutane sosai.

Bayan sun zauna ta kawo musu ruwa snn ita ma ta zauna suka qara gaisawa tace"daga ina haka muka samo baquwa nasir?, Nasir yace "wlh kaka pretty ce ta kad'e ta a bisa qaddara shine bayan ta kaita asibiti da kwana biyu aka sallamota to har yanzu dai bata fad'i ita wace ce ba dmn duk na tambayeta sae tayi tamin kuka ,

kawai dai ta sanar dani sunanta Rayyanat ,naso ta zauna can gidana har ta qarasa jin sauqi amma kinsan halin pretty shine naga kawai na kawota gurinki dmn zata ma fi jin dad'in zama a nn.

Kakar da ta bude baki tun fara mgnr sa tace "ikon Allah, wani irin tuki take har xata buge yar mutane snn kuma ta ki Bari ta xauna gidanta har ta warke, ni dae yaran Kabiru suna bn mmki da irin halinsu" Nasir dae yyi shiru bae ce komae ba, ganin sae fada kaka ke tayi kmr xata ari baki yasa yace "ynxu dae kaka kiyi hkuri hka, sae ta xauna gun ki har Allah ya sa a samo yan uwanta" kaka tace "yo in bata xauna nn ba ina xata xauna da" Nasir yyi murmushi yace "gskya ne kaka" Rayyanat kam sae kallon tsohuwar take nn da nn taji ta kwanta mata taji kuma xata iya xama da ita.

Kakar ta tashi ta shiga kitchen ta d'ebo abinci ta kawo mata tace "ki saki jinkinki fa ki d'auka nan tamkar gidan ku ne kinji, ita kuma xata xo ta sameni har gida, tukin ma daga ynxu sa xanyi Khabiru ya hanata tunda abun nata har da buge mutum, kwanaki ma hka ta buge dan mutane" Nasir dae bae ce komae ba,

Rayyant ta sunkuyar da kanta tana mai share qwallah had'e da ajiye d'an ledar da ke hannunta.

Kakar tace "kawo ledar na shigar miki da ita idan kin kammala sae ki watsa ruwa ko kyaji d'an damar jikin ki, ki kwanta ki huta"

Bayan takai ledar ta dawo tana mai duban Nasir tace"ina ce ka siya mata magungunan da zata ci gaba da sha? Nasir yace Eh akwai magunguna a cikin ledar ta idan ta gama cin abinci sae tasha kafin tayi wanka dmn lokacin shan magunan ma yayi.

Yana gama fad'ar haka ya tashi yace"inna ni zan tafi sae anjima idan na dawo " inna ta washe baki tace "To Allah yyi maka albarka" ya amsa da Ameen yana murmushi ya nufi kofa xae fita, juyowa yyi yace "am yau man bai shigo bane inna? Inna tace " waye kuma hka?" Nasir yyi dariya yace "Mai gidan ki mana" ta tabe baki tace "Tun da safe ya shigo da dan rashin mutun cin sa, amma na taka masa burki, to har ynxu dae bn gansa ba" Nasir yyi dariya yace "to shknn" inna tace"ko da wani abu ne?" Aa ba komae naga ko yaushe na xo yana nane da ke ne,"

Har gurin motar sa ta rakashi ta dube shi da kulawa tace"Nasir gaskiya yarinyar nn da akwai alamomi ban tausayi a tare da ita jifa tunda kuka shigo bata da aiki sae na share qwallah,ai ma inna kad'an kika gani baran idan aka tambayeta inda ta fito, shiyasa yanzu nafi son sae taji sauqi tukun ko zan sake tuntu6ar ta.

To Allah yasa ta kirki ce kamar yanda nake ji a raina ni dae ta kwanta min wllh, Nasir yace Amin inna.

Daga haka ya shiga motorsa ya wuce, inna kuwa ta koma daga ciki.

Nasir kuwa yana zuwa gida ya samu gidan a hargitse duk pretty ta farfashe abubuwa ta kuma tafiyarta gidan su kamar yanda tace.

6angaren pretty sae kuka take sosai a jikin wata mata da nake sa ran ummanta ce ita kuwa sae masifa take inda take fita ba nn take shiga ba na ganin har dare Nasir yaqi zuwa ya sasanta shida pretty.

Wani gaye ne ya shigo d'akin Alhmdlh ya had'u ta koina baya da makusa tamkar balarabe fari tas dashi,yana d'auke da d'an siririn saje kan fuskarsa .

D'ayan hannunsa yana riqe da suit baqa kalar wandon da ke jikin sa,yayinda rgr jikinsa ta kasance fara mai ratsin layi layi.

D'ayan hannunsa kuma yana sanye a cikin aljhun wandonsa.

tsaye kawai yayi yana kallon su ba shi da niyyar cewa komai .

Mamar ce ta fara ganin shi ,ya gaishe ta ta amsa inda cikin nuna damuwa sosai tace"man kaji abinda Nasir yayi wa qanwar ka pretty.

Nan mamar ta zayyana mai abinda pretty ta fad'a mata.

Bai ce da mamar komai ba ya kalli kanwar tasa fuskar sa ba yabo ba fallasa yace "garin ya akayi kika kad'e ta? Kmr xata yi kuka tace yaya ina lokacinda zamu tarbo su umma har ka tsaya wani gidan mai ka bada sadaka? Yyi shiru yana kallonta, hkn yasa ta turo baki tace yaya ni fa ba laifi na bne yarinyar ce Jaka, ina ga daga kauye ta fito, wani mugun kallo ya shiga yi mata, ta dauke kai tana murguda baki, ya gyada kai yace "daga yau kar ki kuskura ki kara jan mota" ta xaro ido tana kallonsa tace "sbda me, ko mijina fa bae hanani va yaya" tsawa ya daka mata yace "nace kar ki kuma jan mota"

Daga haka ya fita ba tare da ya tsaya jin me zata ce ba .

Tafiya yake a hnkli har ya isa 6anfarensa.

D'akin sa wani irin d'aki ne mai masifar kyau da tsari komai fari tas sae qawar da akayi da golden ga tsarin d'akin ba wani tarkace kamar tsarin d'akin turawa.

Frigde ya bud'e ya ciro gorar ruwa ya bud'e ya tsiyaya ruwan a glass cup yasha snn yaje ya cire kayan jikin sa ya sanya white bathrobe ya nufi bathroom.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA```🔮

```Na Billy giro😊```

11/12/2016

🔮```6```🔮

Ya jima sosai kafin yake fitowa yana gama shiri yaji ana masa knocking yaje ya bud'e qofa idanunsà suka sauka kan qanwar sa pretty dake tsaye riqe da trayn abinci fuskar ta fam kamar zata fashe don fushi tace"amma dai yaya zancen na daina tuqi da wasa kake min ko?mugun kallo ya watsa mata ya juyarwarsa ya koma daga ciki,ta shiga ta ajiye trayn sea qunquni take ita ba wanda ya isa ya hanata tuqin mota kan wata jaka can er qauye marar asali ma,

Bai kulata ba har ta qaraci surutunta ta fita.

Washe gari sallah kawai tayi tace da ummarta"ni xan koma"

Umma ta saki baki tana kallonta snn tace"amma pretty ni nasara ke wace irin mace ce wlh kowace mace na ganin ta samarwa kanta enci amma banda ke ,wane irin abu ne da baza ki bari sae nasir yazo da kansa ba ko zaki koma ,wlh kwata kwata kin 6ata kanki da sonda kike yiwa nasir kmr ba nice na haife ki ba....nifa umma ba haka bane naji kina waya da Abba yana kan hanya shiyasa zan tafi kar yazo ya sameni ya min fad'a kuma kinsan jiya da dare nasir yazo har yayi ta kiran wayata naqi na d'aga,to shi baqon gidan nn ne da bazai shigo ba sae ke zaki fita ki same shi ai inace yaje 6angaren uwar sa amma yaqi zowa nn,ai umma barshi don ni bama gidan sa nayi ba wlh gidan inna zan tafi,to idan inna ta tambayeki lafiya fa? Ai inna ce zan kwashe da ita dai dai ba kamar Abba ba ,to ai sae ki tashi kiyi niyya dmn gab yake da isowa garin nn.

Sauri sauri taje tayi wanka ta shirya sae neman makullin motar ta take duk ta jigata kamar zata yi kuka ta kalli ummarta da ta shigo tace"umma ina makullin mota ta? Yayanki yazo ya kar6a....haba umma meyasa kika bashi, kije ki roqe sa mana ai zai baki ,Allah umma kinsan da kamar wuya kidai roqa min shi ya bani, Aa ba ruwana can tsakanin ku ne kije ki gwada sa'ar ki idan ya baki to.

Wani abu yace miki da zai kar6i makullin motar ne?ba abinda yace min kawai dai ya kar6a ya tafi.

Cikin 6acin rai ta fito tayi kici6is da yayanta da kuma mijinta Nasir a nn harabar gidan kallo d'aya tayiwa Nasir ta kauda kai ta kalli yayanta tare da marairiace fuska tana roqon ya bata makullin motar ta,kallon nasir yayi yace"sae kaja matar taka ku tafi"

Ya sa qafa zai wuce tayi saurin shan gabanshi tace"pls yaya kayi haquri ka bani"

tsawa ya daka mata yace"wai ina wasa dake ne da kike tunanin zan kar6e abu na baki!

Le6ace baki tayi zuwa kuka tace"yaya ba fa laifi na bane na gaya ma"

Wayar sa da tayi ringing ya d'aga ya bar gurin ,kuka ta fashe dashi nasir yazo yaja hannunta ta fizge hannun taje ta shiga mota shima ya zagaya ya shiga yaja motar tana ganin ya hau titin zuwa gidan su ta dalla mai harara tace"nifa ba gidan ka zan tafi ba don ka sani gidan inna zanje gara tun wuri ka sauya hanya don ko munje gida ba shiga zanyi ba wlh ,kuma sae naci uban wnn er iskar yarinyar da ka kaiwa inna wacce a dalilinta aka hana ni jan mota sae naga ta yanda ma zata zauna gidan inna d'in dole ta barshi tunda ba gidan kakarta bane ko wani nata.

Nasir yayi shiru yana kallon pretty shidai ko kad'an baya son masifar nn tata gashi aikin kenan idan aka ta6o ta.

Hannun ta ya riqo tare da kai mata sumba snn yace"da kika yi shiru sae kika min kyau kamar ace ko yaushe haka kike ba ruwanki da fad'a"

Hm ba wani dad'in baki da zaka min nifa sae ka kaini gidan inna ,kallon ta yayi yana tunanin wayon da zai mata dmn yasan duk taje gidan inna ba qaramar rigima za'ayi ba,yace"gidan inna kwantar da hankalinki zan kaiki amma sae kin raka ni gida nayi wanka tukun,ta6e baki tayi tana kallonshi snn tace"wankan me zakayi da baza ka kaini gidan inna ba har sae na raka ka,banyi wanka ba da safen nn ina gama sallar asuba naje gida dmn nazo dake, kuma yunwa nake ji sosai kinsan kin tafi kin bar ni ba abinci kuma yau da safe ma haka,shine nake son ki had'a min breakfast kafin na fito wanka kinji,

ya fad'i haka ne cikin marairaicewa had'e da tsare ta da ido dmn yasan da ya mata haka bata iya masa gardama,

ta kauda fuskarta gefe kamar baza ta amince ba sae kuma tace "naji"

Karfe takwas da minti goma na dare Rayyanat na kitchen tana yi ma inna goge goge bayan ta gama wanke kwanukan da suka ci abincin ta ji an bude katon gate din gidan alamar mota xae shigo knn, duk lkcn da taji karan bude gate din sae gabanta ya fadi don ba sabawa tayi ba, bayan kusan minti bakwae inna ta shigo kitchen din ta gwalo ido tace "lahh bar maki aikin Hurera tayi" Rayyanat tace "A'a ni na karba inna" inna ta washe baki tace "ayyo!sannu da aiki jikata, ynxu duk ke kika gyara kitchen din nn hka" Rayyanat tayi murmushi ta sunkuyar da kanta bata dae ce komae ba, inna tace "to miko min wancan kulan abincin in kai ma mai gidana ya xo" Rayyanat ta dauko ta mika mata da ladabi inna ta fita tana cewa "yau ko dan kankanan da lemo bae siyo min ba ya kwaso kafafuwa ya xo xae cinye min abinci uwa shi ke siyo min" bayan minti goma da fitan inna Rayyanat ta gama abinda take a kitchen din baka taba cewa daga kauye take komae nata tsaf tsaf take yi, da kyar ta iya fitowa daga kitchen din a sanyaye tuno babanta da ta yi, hkn yasa kwalla ya cika idonta, tayi saurin sharewa bata tarda kowa falon ba sae hurera yar dattijuwar matar da ke goge tiles din falon ta kalleta tana murmushi tace "sannu Rayyanah, ki tafi can daya falon inna na can, amma ga furar ta nn da na dama mata ki dauka ki tafi mata da shi, Rayyanat ta gyada mata kai kawae ta dauki furan da ke rufe kan centre table ta nufi falon da Baaba Hurera ke nuna mata, inna na xaune kan tabarma ta tankwashe kafa ta kapa ma tv ido tana kallo uwa tasan abinda ake yi, shi kam yana xaune kan three seater rike da remote waya na kare kunnansa alamar waya yake, kallonsa kawae Rayyanat take a sace kuma a tsorace sae dae har lkcn bae juyo ba, inna ta juya da sauri ganinta a tsaye tace " A'a karaso mana Rayyanah" Sae a snn ya juya yana kallon da warce kakar tasa ke mgna, Rayyanat ta sake kwanon furar hannunta ba tare da ta shirya ba, inna ta mike da sauri tana salati, ya katse kiran da yake shi ma ya mike yana yatsine fuska yace "ina kika samo mai aikin nn kuma Inna, idan xa ku dauki masu aiki ku dinga bincike da kyau don Allah ku dena dauko yara irin hka masu kananan kwakwalwa, bnda hka meye xata shigo falon mutane ta sake masu kwanon fura a kasa kmr wata me tabin hnkli" juyawa Rayyanat tayi da gudu ta fice daga falon a rude.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

16/12/2016

🔮```7```🔮

Oh Allah yoni hajara!kai muhammadu ai wnn yarinyar iyakar hnkli da natsuwa tsautsayi ne kawai da in yazo ba mai tare shi.

Inna ina hnkli a nn da shigowarta ta 6arar da fura kmr wacce bata saba ganin mutane ba,kudai 'ya'yan kabiru haka kuke abu kad'an ya isheku masifa,

inna yau maigidan naki kike gaya ma haka, yo ai ko waye kai tunda ka ta6a er albarkar nn dole na maka magana yarinya tsakanin jiya iyau lafiya muke zaune sae gashi kazo zama d'aya ka rikita ta har ta tafi da kuka,nidai inna da wnn mitar kira hurera tazo ta goge gurin nn ,kuma dan Allah kidaina kwaso iren iren yaran nn sam ba abin yarda bane da har kike saurin bama yarda zama d'aya,wai er had'uwar jiya zuwa yau ce kike kora min bayani kamar kun shekara, masifa inna ta shiga yi dashi,Man ya bita da kallo yana murmushi har ta fita.

Taje ta samu Rayyanat a d'aki sae kuka take rusawa,

tayi zaune tana rarrashinta har ta samu tayi shiru.

Rayyanat ta tashi tana share hawaye tace"inna bari naje na kwashe furar"a'a ai nasa hurera ta kwashe, kika sata inna nifa na 6arar,kar ki damu indai hurera ce bata da wnn,bari na tashi naje nabar maigidana shi kad'ai ,tace"to inna"inna na fita Rayyanat ta kifa kai taci gaba da kukanta.

Da dare Nasir yazo ya samu sun kammala cin abinci sunyi zaune suna kallo ya gaida inna snn ya samu guri ya zauna ,Rayyanat ta sadda kanta qasa tana miqa gaisuwa ya amsa gaisuwar snn yace"ya jiki ?tace"Alhmdlh yace"kina dai shan maganin ki akan lokaci ko? Gyd'a masa kai kawai tayi tana wasa da en yatsunta.

Ya maida dubansa gun inna da ta miqe qafafu tana kallon Indian film kamar wacce kejin wani abu dmn duk ta tattara natsuwarta a can.

Sae da abin ya bashi dariya sae dai bai yarda yayi ba dmn yasan masifa zata aje mai in tasan dalili dryr dmn kallo d'an gidan ta ne ba mai shiga tsakanin su.

Yace"inna hln mai gidan naki ya koya miki indiyan ci ne naga kin maida hankali sae sauraren su kike?yo ina fa na iya Rayyanah na saka ma shine nayi zaune nima ina kallon abin tausayi naga sae wulaqanci yarinyar kesha a gun mijinta,dariya yayi yace"to ke inna ya akayi kika san mijinta ne? Yo kai Nasir banda idanu ne ko ko banda fahimta,gashi har gado d'aya naga suna kwanciya ai wnn sae miji da mata,dariya kawai yayi ya ajiye zancen dmn ya kalli film d'in ba miji da mata bane budurwa ce da saurayi ya mata ciki shine yake wulaqanta ta.

Hannu yakai ya shafi sumar kanshi yace"inna zan tafi "ah ah kaiko da wuri haka ,inna aski zanje sae dai gobe idan na sake shigowa ,to Allah kiyaye ,

sae da yace"Amin snn ya fita.

Ko minti ashirin bai yi da fita ba sae ga Man ya shigo gidan sae dai shi ba kallo ya samu suna yi ba tausa ya samu Rayyanat tana yima inna.

Rayyanat na ganin shi sae duk ta nemi natsuwar ta ta rasa, haka ta dake ta gaida shi ta kuma yi saurin tashi tabar gurin.

Bai ma amsa gaisuwar ba sae inna ya gaida ya ajiye ledar da ya shigo da ita kusa da inna snn ya zauna,inna ta tashi zaune tana washe haqora tace"me kuma kazo min dashi yau? Sae da ya jingina bayansa kan 2 seater d'inda yake zaune snn yace"gasasshiyar hantar rago ce na siyo miki kan hanya"

Kai Allah dai shi yi maka albarka kamar kasan nayi kewarta wlh,ai inna har fruit naso siya miki se na manta,,ayyo ai d'azun da rana Nasir ya shigo min dasu munsha har mun gode Allah har ga saura a fridge ko na d'auko ma zaka sha?Aa inna, to abinci kam zaka ci dai ko? shima haka dmn a qoshe nake, yau tawaye kamin kenan ,Aa naci abinci ne a gidan wani abokin mu da yayi sabon aure muka je, oh ni kakata talatu kai yanzu ka gwammace kayi ta zuwa gidan abokanai ba a zuwa naka ,

wai nikam yaushe zaka fara ra'ayin aure ne muhamnadu,hm inna ai aure lokaci

ne dashi kin sani in lokaci yayi zanyi har ma a wayi gari watarana kina zaune zagaye da en jikokin ki, nn inna ta washe baki tace"Allah nuna mana lokaci muna masu rai da lafiya"Amin inna.

Washe gari Rayyanat ta gama taya hurera duk ayukkan da take tazo tayi kwance qasan tiles tana jiran fitowar inna daga gurin wanka nn bacci yayi awon gaba da ita.

Pretty ce ta shigo gidan tayi tsaye tana kallon Rayyanat dake bacci tace"yau zaki ci ubanki yarinya"

Nan taje ta bud'e fridge har ta d'auko gorar ruwan sanyi sae kuma ta girgiza kai ta mayar ta nufi kici tana murmushin mugunta ta d'auko flask d'in ruwan zafi tazo kai tsaye ta bud'e tana kwara ma Rayyanat su a jiki ,

ihu Rayyanat ta saki ta tashi a firgice tana lalubar bayanta inda taji saukar ruwan zafi.

Mari pretty takai mata tace"er iska ai yau sae kin bar gidan nn wlh tunda bana ubanki bane!

Taja Rayyanat kamar wata kayan banza ta ingizata waje da qarfi sae kawai Rayyanat taji ta fad'a jikin mutum hkn yasa taji saukar wani irin gigitaccen marinda ya soma fitar da ita hayyacinta.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

17/12/2016

🔮```8```🔮

La'ilaha ilallahu Muhammadu rasulillahi sallallahu Alaihi wa sallam!

Cewar inna wacce ta fito daga gurin wanka tace"Muhammad me rayyanah ta muku ne da zaku mata taron dangi tun ina bayi naji ihunta Fatima na faman sirfa mata masifa yanzu gashi na samu ka tafka mata uban mari haka!inna ta qarasa magana cikin muryar kuka irin na tsafi d'in nan.

Nan take man damuwar sa ta bayyana ya shiga bawa inna haquri bata kula shi ba sae kuka take taja Rayyanat suka koma cikin d'aki.

Pretty ta kalli man dake qoqarin bin su inna tace"to wai meye abun damuwa kabar su mana tunda kasan halin inna dama saurin kuka ne da ita in ba don shi ba meye abin kuka wa wannan er qauyen,harara ya dalla mata yace ai duk ta dalilin kine banga uban me ya kawo ki gidan nn ba....kamar ya yaya...zan mare ki wlh idan baki 6ace min da gani ba!

Turo baki tayi tana faman gunguni har ta fita gidan.

Man kuwa shiga d'akin yayi amma a iya falo ya tsaya inna ta fito tana shar6ar hawaye zata d'auki wayarta dake kan TV stand yace"inna yi haquri Allah sam na d'auka rashin hnklinta ne yasa ta fad'o min a jiki ban san cewa pretty ce ta ingixo ta ba,amma Muhammadu ai ka saurara mata ko! yanzu gashi bayan fasa mata baki da kayi duk bayanta ya kwaye... Kamar ya inna nifa marinta kawai nayi... Yo kai ba kasan ruwan zafi pretty ta watsa mata a baya ba,shiga ka duba ta kaga ai nasan dole sae an yanke wnn ftr ,ta qarasa maganar cikin kuka snn tace"ka shiga mana ka duba min yarinyar mutane kazo kayi tsaye se kallona kake!

Ba musu ya shiga ya sami Rayyanat ruf da ciki se kuka take abin tausayi zip d'in rigar ta a bud'e fatar bayanta har yyi ja, kauda fuskar sa yayi tare da sauke ajiyar zuciya snn ya kalli inna dake tsaye kusa dashi tana matsar kwalla yace "inna ina ganin ta sosa bayanta ne a lokacin da aka watsa mata ruwan, kuma wnn da gani ma ba wani ruwa me xafi bne, Rayyanat da bata ji shigowarsa dakin ba sae maganar sa taji tayi saurin tashi xata rufe zip d'in rgrta, inna ta karaso da sauri

tace "A'a Rayyanah kar ki rufe ai shi likita ne zai duba miki bayanki in kuma baxae iya ba sae ya kira mana ubansa ya xo ya kai mu asibiti," Rayyanat ta girgiza kai ba tare da ta kallesu ba alamar bata so, inna tace "A'a ki yi haquri ya duba ki kinji jikata"

Man da takaici ya ishe shi yace "inna bari kawai zan turo a duba ta" yana kai wa nn ya fice daga dakin kmr xae tashi sama.

Sae da ya kira wani abokinsa likita snn ya bar gidan ya nufi gidan kanwarsa pretty.

Yana isa gidan Nasir ya samu kan dining sama sama suka gaisa yace masa "ina pretty" kafin ya basa amsa sae ga prettyn ta sauko, bata damu da ganin fuskar yayanta ba annuri ba ta daure fuska ssae tace "gani yaya lafiya dai ko"

Yyi mata wani mugun kallo yace "me wnn yarinyar ta miki da zaki xuba mata ruwan xafi a jiki," shiru pretty tayi tana kallon shi kamar bata san me ya faru ba har lkcn fuskarta a tamke, ya daka mata tsawa yace "ya kika min shiru kina kallona ina maki mgna?" Ta tabe baki tace

"To nifa yaya ban gane zancen da kake ba bare na iya ce maka wani abu," nn ya fahimci ta fita ne bada ixinin nasir ba shine take wani nuna kamar bata san da zancen ba.

mari ya kai mata don bata da nisa daga inda yake yace "yanzu kin fahimci zancen nawa!ko kuma sae na qara miki wani," da sauri taja baya tana kuka don ganin da gaske yake, tace "to shine zaka wani mareni wlh sae na gaya ma umma!

daga haka ta tafi da gudu tana kuka ta haura sama.

Duk da Man ya fahimci Nasir yana buqatar jin bayani bai tsaya yi masa ba ya tafiyar sa hakan yasa nasir ya tafi ya haura sama gun matarsa da shima ya fahimci gidan inna taje bai sani ba.

Da shigarsa ta taso ta rungume shi tana kuka tace "ka gani dai ko honey ban masa komai ba yazo ya mareni," mugun kallo yyi mata yace "bana son qarya pretty nasan halin Man ba zai zo haka kawai ya mareki ba ,ba makawa gidan inna kika je gun Rayyanat kika aiwatar da nufinki ko?" shiru tayi alamar can taje d'in, nn ya shiga yi mata fad'a sosai daga qarshe yace duk ta qara fita bada izinin sa ba sae ya sanar da Abbanta, fushi ta shiga yi dashi bai kula ta ba ya tafiyarsa yaci abinci ya fice daga gidan.

Gidan inna ya nufa yaje yaga aikin da pretty tayiwa Rayyanat lokacin ma har likita ya xo ya dubata, bata wani kone ba sae dae fatar jikinta da yyi ja ssae.

Sosai ya bata haquri daga ita har inna da abun yabi ya dama har tana cewa a kira mata kabiru, Nasir dae ya dinga bata haquri yace shi zai yi maganin abun amma fafau inna tace ita fa sae taje shima zai kaita gidan da kanshi.

Haka ko akayi dmn tare suka fita shida inna suka bar Rayyanat ita da hurera.

Wani makeken gida suka nufa kyace gidan shugaban qasa ne kan tsari da kyawo irin nashi, kuma ba wani gida bane face gidan su Nasir d'in da kuma su pretty wato qanwar man sbd gabad'ayan su family's ne en wa da qani ne,

Baban su Man shine babba snn mahaifin Nasir bayan shi kuma akwai wani Alhj sa'eed wato qanin mahaifin Nasir inda shi kuma yana da qanwa mai aure a garin kd dukkan su 'yayan inna ne shine maxan suka had'e kansu suna zama gida d'aya sae dai kowa da nasa 6angare.

Suna shiga gidan

inna ta nufi 6angaren su pretty sae ga wata yarinya tazo da murna ta tarbe ta tana fad'in "he inna nida nake batun zuwa gurinki shine kika zo, inna ta washe baki tace "tukuna saukar yaushe Ameera? Yau yau d'in nan aka bamu hutu inna ,to ina er uwar taki saliha? "Tana 6angaren su tare ma ne zamu tafi gurin ki nasan yanzu haka ta shirya tana can tana jirana wlh, inna tace "ayyo to ai yanzu komawa zanyi sae mu tafi tare je kira min Abbanku kabiru yazo ina da magana dashi, tace "to inna zauna na kira miki shi"inna ta zauna ita kuma ta haura sama.

Nasir kuwa wani 6angaren ya nufa da alama shine na iyayensa dmn matar da ya samu zaune a falo sak suke kama dashi, cike da ladabi yaje ya durqusa ya gaisheta yana qoqarin tashi yaji an rungume shi ana fad'in "oyoyo yaya" cike da murmushi yake kallon wacce ta rungume shi yace "A'a saliha shin yau ne hutun ku ko to wa ya d'auko ku?

turo baki tayi snn tace "Abba ne yaje da kanshi tunda kai kaqi zuwa "oh no saliha yi haquri sam na manta da yau ne hutunku amma umma ya akayi ba a sanar dani ba sae Abba ne yaje da kanshi? Mamar tace "Abban ne yace akwai aikinda yasa ka shine ya tafi dakanshi ya d'auko su, Nasir yace "eh gaskiya ya bani aiki tun jiya ban samu na qarasa ba amma inshaAllah yanzu zanje office na kammala kafin ya tambaye ni, nn ya kalli saliha yace "ina zuwa haka naga kinci kwalliya? Tace "Gidan inna zamuje nida Ameera," eyyah ai tare muka zo nida inna tana ma 6angaren su Ameera, Saliha ta 6ata fuska tace "ita ko dai inna...ai ba jimawa zatayi ba dn inaga sae na maida ita gida ne ko zan tafi office ,yauwa bara naje na ganta, cewar saliha wacce ta tashi cikin murna ta fita.

Nasir ya kalli mahaifiyar sa da kulawa yace"umma ina yarinyar da na gaya miki cewa nakaita gidan inna? Hajiyar tace "eh na ji" "wlh pretty yau taje ta mata lahani a baya ta xuba mata ruwan zafi, inda Allah ya taimaka ma ba wani xafi ga ruwan ba" Hajiya ta gwalo ido tace "ni kuwa yaushe pretty zata yi hankali ne tukuna me ma ta mata da tayi mata wnn d'anyen aikin? Nasir yace "Kawai don tana jin haushin an hanata tuqin mota a dalilinta kuma kinsan halin pretty ta tsani talaka ba kad'an ba, cikin damuwa mamar tace "to kai nasir baza ka sallami yarinyar mutane bane ka huta, shawarar da nazo yi dake kenan umma don gsky bana son wani abu ya sake faruwa da ita duk da nayi ma pretty kashedi amma hankalina zai fi kwanciya idan ta koma ga en uwanta sae dai inna ce matsala don yanda Rayyanat ta kwanta mata a rai ba lalle bane ta yarda da hakan zata iya cewa a kaita gun en uwan Rayyanat d'in in yaso ta nemi alfarmar su bar mata ita ta riqa yi mata en wasu aikace aikace in yaso duk wata ta riqa biyanta kinga kuwa duk dai ba'a rabu ba dmn gsky nafi son Rayyanat ta komawarta gun en uwanta.

umma ta nisa tace"to ya kake ganin za'ayi haka? Ya dan yi shiru snn yace "Eh to ina ganin kawai zan maida Rayyanat ba tare da sanin inna ba sae bayan na dawo na snr da ita kinga dole zata haqura.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

19/12/2016

🔮```9```🔮

To shikenan Nasir amma ina son kafin Ku tafi kazo min da yarinyar na samu abinda na bata don yarinyar ta bani tausayi wlh har dai in na tuna ko wane hali en uwanta suke ciki na rashinta oho Allah kad'ai ya sani.

Wlh umma nima tunanina kenan kullum gashi taqi fad'a bare naji ko akwai lambar wayar su a kira a snr dasu halin da take ciki amma yanzu Alhmdlh tunda taji sauqi zan lalla6ata ta gaya min sae na maida ta.

Nasir Yayi mgnr ne yayinda ya tashi yace "to umma ni zan tafi "

Umma tace "To ka gaida innar" yace "to" snn ya fita.

Nasir na fita ya nufi 6angaren su pretty ya d'auki inna dasu saliha suka wuce.

Hajiyarsu pretty na fitowa daga bathroom sae ga mai gidanta ya shigo ransa a 6ace ta kalle sa da kulawa tace "lafiya Alhj me yake faruwa ne?" da taikaci ya kalle ta snn yace" ni nasara wace irin tarbiya ce kika bawa 'ya'yanki? kaf dangin nn ba wanda yakai su rashin mutunci idan suka tashi, musamman ma Fatima" nn cikin fad'an duk ya kwashe abinda inna tazo ta gaya mai har da yaron da pretty ta kad'e kwanaki don duk shi bai sani ba.

A fusace ya d'ora da cewa "kiramin ita yanzun nn tazo ina son ganinta, kwata kwata daga yau ma ta daina jan mota na hanata"

Umma ta dan tabe baki tace "ni dae kayi haquri Alhj, ai ba laifinta bane tsautsayi ne da kuma qaddara...." Rae bace Alhj yace "idan wnn tsautsayi ne me yakaita gidan inna har taje ta watsa ma er mutane ruwan zafi a jiki ko shima tsauyayin ne! Ku fa kiyaye ni ke da 'ya yan ki" ganin ynda ransa ya bace yasa tace "Ayi haquri Alhj bata kyauta ba dae, amma zancen tuqa mota tuni yayanta ma ya kar6e motar," Alhj yace "yayi dai dai don in kece baza Ki kar6e ba duk kinbi 'ya'ya kin lalata da baqin so sae kace kanki aka fara haifuwa.

Nasir na sauke su inna gida ya wuce office bayan sun shiga gidan, saliha da Ameera suka shiga kallon Rayyanat da ke zaune ta lanqwashe qafafu tana shan fura a falon, kallo d'aya Ameera tayi mata ta kauda kai sbd ta gano ita ce yarinyar da inna taje tana faman masifa akai don a gabanta akayi komai ita da saliha.

Saliha kuwa kallon Rayyanat take da d'an murmushi a fuskarta ta kalli inna tace "inna wnn itace Rayyanah?" Inna ta washe baki tace "eh ita ce er albarka babu ruwanta wlh" Saliha tace "eyyah sannu Rayyanat ya jiki?" D'an guntun murmushi tayi snn tace "Alhmdlh" a takaice.

Ameera ta ta6e baki taja hannun saliha tace "ke ni tashi mu tafi gidan inna hajjo mu gaidata" (wata makociyar inna dake nn kusa bbu nisa)

Inna ta washe baki tace "to in kunje ku kar6o min nono na samu na dama furar anjima" nn ta kwance ha6ar zanen ta ta basu nera d'ari tace "ku siyo na duka," Ameera ce ta kar6i kud'in tana walwale su tana dariya ganin yanda suka tamure tace "kai inna wai har yanzu baki daina dunqule kud'i a ha6ar zani ba" bata jira cewar Inna ba ta ja Saliha suka fice daga falon, sae a snn Rayyanat ta gaida inna da ladabi, inna ta amsa da fara'a tace "sae ynxu kike shan hurar, ya bayan in ga ni?" Rayyanat ta dan xuge zip din rigar jikinta inna ta duka da sauri tana kallon bayan, kmr xata yi kuka tace "Allah ya Isar maki, da bayan nn ya tashi yau da anga xube xuben ruwan xafi a jiki don duk sae na tafasa ruwa na bi ta har gidan mijinta na kona ta ni ma" Hurera dake kitchen ta fito tana dariya tace "A'a ba ayi hka ba Inna, Allah dae ya tsare" inna tace "ae ynxu ma daga gidan ubansu nake, kuma yace anjima da daddare xae xo ya gane ma idonsa" Bude kofar falon aka yi, duk suka juya don ganin wnda xae shigo, inna na ganinsa ta tsuke fuska, ya karaso falon fuskarsa a tamke, Rayyanat tayi saurin gyara rigarta, a fusace yana kallon inna ya soma magana "don me xa ki je ki hada ni da Baffana kan wata bnxa can yar kauye Hajiya," inna ta tabe baki tace "sae dae kae ne bakauye ko uwar ka amma ba yar nn ba," xaro ido yyi yana kallonta, ita ma ta yo waje da ido tace "kwarae kuwa!" Rayyanat da tun shigowarsa falon ta sunkuyar da kanta hawaye ya shiga bin kuncinta, ya huzar da iska ya cije lebe lkci daya idonsa ya kada, ya juya fuuu ya fice daga falon, inna tace "Wawa kawae." Baaba hurera ta sauke ajiyar xuciya tace "Ayi hkuri dae inna" mikewa Rayyanat tayi har lkcn hawaye na bin kuncinta, Inna na ganin hka ta rude ta shiga tambayarta lfya, Rayyanat ta kasa bata amsa, hkn yasa inna ta fashe da kuka tace "yo baki ji nace shine dan kauyen ko uwarsa ba, ni dae na shiga uku da 'ya yan kabiru" lkci daya Rayyanat ta hadiye kukan da take tace "kiyi hkuri inna, ni ba shi yasa nake kuka ba, naga ina ta hada ki da jikokin ki ne" cikin kuka ta karashe mgnr, inna ta hade rae tace "suke dae hadani da ke, kuma Allah ya fi su" Baaba hurera tayi murmushi, Rayyanat ta duka ta dauki sauran furan da take sha ta nufi kitchen.

Da rana nasir ya shigo gidansa, ya nufi dakin pretty ganin bbu kowa falon ga ko ina kaca kaca, xaune ya sameta sae fushi take, yaje kusa da ita ya zauna ya shafi gefen fuskarta yace "nasha gaya miki ki daina fushi baya miki kyau," hararar sa tayi snn taja tsaki tace baka son nayi fushi shine zaka kaini qara gun daddy," Nasir ya xaro ido yace "au kin dauka nine, to inna ce taje da kanta ta gaya mai aikin da kikayi don haka ko yanzu kika sake gigin aikata wani abu akan Rayyanat zata je ta snr dashi ne," cike da bacin rae ta tashi tana masa mugun kallo tace"ni yanzu banda lokacin wnn er qauyen bare na qara kulata" ta ja dogon tsaki daga haka ta wuce fuuu! ta barshi nn zaune" girgiza kansa kawai yayi ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyaya ruwa a cup yasha.

Washe gari ya gama shirin sa tsaf yaje d'akin pretty wacce yanzu ne tashinta zata shiga Bathroom dmn yin wanka.

Bai qarasa inda take ba a iya gun dressing mirror ya tsaya ya ajiye mata kud'i yace "zanyi tafiya ne ban kuma san yau ko gobe zan dawo ba" ta hade rae tace "ina zaka tafi?" Ya daga kafada yace "Kina da sako ne?" daga haka yyi ficewarsa, ta6e baki tayi gami da jan tsaki tace "aikin banxa, kadda Allah yasa ka dawo ma"

Nasir bai zarce ko ina ba sae gidan inna cike da niyyar ya d'auki Rayyanat ya maida ta gun en uwanta. Bbu kowa falon Inna, hkn yasa ya nemi gu ya xauna yana tunanin ynda xae fita da Rayyanat ba tare da sanin Inna ba, Baaba hurera ce ta shigo falon daga kitchen, da mamaki tace "A'a Nasiru yaushe kuma ka shigo" yyi murmushi ya gaisheta ta amsa da fara'a tana tambayarsa ya kwanan pretty, ya amsa da Alhmdllh snn yace "Baaba Rayyanat xa ki kira min amma fa kar ki bari inna tasan da ina gidan nn" tace "to bari in kirata" ba a dau lkci ba ta dawo falon Rayyanat na biye da ita a baya, hijab ne har kasa jikinta yasan inna ce ta sa aka dinko mata, ya kafa mata ido har ta karaso ta xauna kasa kanta a sunkuye ta gaishesa, ya amsa yana murmushi ya tambayeta ta tashi lfya, kai kawae ta gyada masa, bae kuma cewa komae ba har na kusan minti biyar hkn yasa ta dago kai tana kallonsa da manyan idanuwanta, murmushi ya sakar mata ta dukar da kanta da sauri, ya kira sunanta a nutse ta amsa ba tare da ta kallesa ba, yace "nasan yan uwanki na cikin tashin hnkli Rayyanat, kiyi hkuri ki gaya min ina ne garin ku" Rayyanat tayi kkrin ganin hawaye bae sakko idonta ba a karo na farko ta gaya masa sunan garin a hnkli, ya gyada kai da gamsuwa yace "to ina xa ki pretty ta kade ki da mota?" Ta girgixa masa kae da kyar tace "garinmu xan ko ma" yyi shiru snn yace "to da me ya shigo da ke kano? Shiru tayi taki cewa komae hkn yasa yace"kin shirya komawa garin naku gun yan uwanki ynxu?" Gyada masa kai tayi kawae, yyi shiru na wani lkci snn yace "to tashi ki dauko ledan kayan ki, amma kar ki Bari Inna ta ganki" tace "to" snn ta nufi dakin da Inna ta bata tana murmushi a ranta tace "don xan tafi ba yana nufin na bar shi bane, har abada baxan bar shi ba, nemo sa baxae min wahala ba tun da na ga gari."

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

22/12/2016

🔮```10```🔮

A sanyaye Rayyanat ta dawo falon rike da ledan kayanta ta samu har nasir ya fita xuwa gun motarsa, ita kad'ai yake jira taje ta bud'e gambun motar a hnkli xata shiga ta tsaya cak jin murya inna a bayanta tana fad'in "Rayyanah me zan gani hka ina kuma zakije har da leda a hannunki?"

Sake gambun motar tayi ta juya tare da sadda kanta qasa ta ki barin su had'a ido da inna, ba shiri Nasir ya fito daga cikin mota ya tsaya yana d'an kame kame sbd yanda inna ta tsare shi da ido baki bude.

Kmr xata yi kuka tace " kaddai mayadda rayyanah zaka yi baka ko snr dani ba Nasiru"

Ya dan sosa keya yace "Aa inna, dama wae da.." sae kuma yayi shiru. inna ta fashe da kuka tace "dama me nasiru! mayadda ita zakayi d'in knn, na rasa dalilin da yasa aka rainani hka, ynxu da bn fito ba sae dae in nemi yar nn in rasa" ta fashe da wani matsanancin kuka har da dukawa, Nasir yyi murmushi yace "kiyi hkuri Inna, kuskure ne" inna ta dago ta tsuke fuska tana kallonsa tace "rufe min baki munafuki kawae" dariya yyi yana shafa kansa yace "na yarda, amma inna baki tunanin halin da yan uwanta da iyayenta ke ciki ynxu? Ynxu misali lkci daya a nemi pretty a rasa wani hali kike tunanin xa mu shiga gaba daya" lkci daya inba ta marairaice tace "ni fa ban ce kadda a mayar da ita gun iyayenta ba, kawae rashin sanar dani da ba ayi bne ya bata min rae" Nasir yace "to ayi haquri inna," ta galla masa harara tace "yo da ban hkura ba da ban tara maka mutan anguwar nn ynxu ba," dariya yyi yana kallonta, tace "ynxu dae dani ya kamata muje gun en uwan nata su ganni nima na gansu na samu ko zasu bar min Rayyanah in rike, ni dae yarinyar ta kwanta min in sonta" ta karashe mgnr cikin kuka, tana matsar kwalla tace "ka ga idan Allah ya kawo mata miji na gari sae tayi auranta,"

Ba yanda nasir ya iya yace "to shiknn inna jeki d'auko mayafinki mu tafi"

Inna ta washe baki ta ja hannun Rayyanah tace "zo ki rakani er albarka bazan barki a nn ba don tunda yayi niyya zan iya dawowa na samu ya tafi dake ne kawae,

ko meye dalilin hkn da yyi ne oho," nn dai inna ta jata suka tafi ciki don dauko mayafinta.

Har yaja mota inna bata bar mitan da take ba, hkn yasa nasir sam ya manta da zancen kaiwa umman shi Rayyanat kamar yanda ta buqata.

Tafiya sukayi ba mai wani nisa sosai ba dmn da kano zuwa qauyensu awa biyu ne sae dai tun lokacin da suka kama hanya Rayyanat keta zubda qwalla a boye har suka isa.

A bakin shiga garin tace da Nasir ya tsaya a nn, ya juya ya kalleta yace "garin naku ba'a shiga da mota ne?" Rayyanat ta daure tace "Ana shiga da ita amma ku sauke ni kawai nagode, zan iya qarasawa da kaina," inna ta yo waje da ido tace "yo Rayyanah ai ni en uwan naki nake son gani ko zan samu sumin alfarmar bar min ke"

Shiru Rayyanat tayi hawaye suka shiga silalowa a hnkli kan kumatunta ta, inna ta saki baki tana kallonta, can tace "Rayyanah ko ba kya son komawa gu nane?" da sauri ta girgixa kanta muryarta na rawa tace "inna ni bani da kowa duk sun rasu"

Inna ta rafka salati da karfi ta fashe da kuka tana cewa "wayyo ni Hajara, wayyo ni" Nasir dae yyi shiru yana kallon Rayyanat amma ya kasa yrda da abinda tace, inna ta ci kukanta ta koshi Rayyanat na taya ta kmr a lkcn aka yi mutuwar, daga karshe tana fyace majina cikin kuka tace "Allah ya rahama masu, wayyo ni rayuwa" Da kyar Nasir ya iya bude baki yace "Allah ya ji Kansu" ba don ya yrda ba gani yake kmr karya tayi masu.

Cikin muryar kuka Inna yace "to nasiru muje muga mai garin nasu dmn haqqi ne akansa yasan Rayyanat zata zauna gun mu ko?" Nasir ya gyada mata kai kawae ya tada motar ya shiga tafiya a hnkli Rayyanah na nuna mai hanya har suka isa qofar mai gari.

Cikin girmawa aka tarbe su mai garin yyi mamakin ganin Rayyanah ya shiga tambayarta daga ina take, nn Nasir ya dan ji dama dama gnin mai garin ya santa, bayan an gama gaggaisawa Nasir ya zayyano abinda ke tafe dasu yana kallon Rayyanah, mai gari bai musa musu ba ya amince da abinda suka buqata ya Dora da cewa suyi kkrin ganin sun riketa amana don marainiya ce sun samu lbrin rasuwan mahaifinta, Inna tace "ka ji ka da wata mgna, kasan wacece ni kuwa," mikewa tayi tana washe baki tana kallon Rayyanat tace "tashi mu je jikata, Allah xae taya ni riko"

Bayan sun koma gida da kwana biyu inna ta fito cikin shirinta Rayyanat ma dake shirye cikin wani atamfa da aka dinko mata da hijab jiya tace "to Rayyanah jeki snr da hurera mu zamu fita."

Rayyanat ta nufi dakin hurera, dae dae nn Man ya shigo falon yana waya murmushi dauke a lebbansa, inna ta washe haqora tace "Allahu Akbar, sannu da xuwa d'an albarka dama kmr kasan neman wanda zai kaimu anguwar nake, sae gashi Allah ya jefo min kai"

Ya katse wayar da yake yana kallonta yace "kai Inna, ina xa ki cikin ranan nn" inna tace "yo ni rana da yana gasa mutum da bae gashe ni ba, kasan irin wahalar da na sha gidan mijina kuwa" ya tabe baki ya juya ya fita yace ina jiran ki a waje, tace "to to ynxu xa mu fito" tare inna suka fito da Rayyanah, yana jingine jikin motar yana jiranta don duk a tunaninsa ita da baaba hurera xa su fita, suna karaso gun motarsa ya zaro ido yana kallon innar yace "wae ke da wa xa ku fita?" Inna tace "yo Rayyanah mana" ya kuma xaro ido kmr wanda yaji abin tsoro cikin shan toka yace "nifa gasky baza ta shigar min mota ba, mgnr gskya knn, idan dai ke kad'ai ce to muje," inna ta tsuke fuska tana huci tace "yo naga ja'irin yaro, kai baka san tafiyar tata bace ma gaba daya, xuwa fa zanyi da it cikin dangi tasan kowa, kowa ya santa."

Girgixa kai yyi yana masu wani irin kallo yace "to ba da motata ba, ki kira Nasir da yyi maki hanyar ta ya kai ku" inna ta fashe da kuka tana girgixa kai tace "Ni ban san meyasa bn dace da jikoki ba a rayuwa duk sun rainani uwa ba ni na haifi ubansu ba" Muhammad ya girgixa kai yana kallon innar yace "bari to in kira wani ya kai ku inna kin ga fa sauri nake" inna ta hade rae tace "A'a sae dae ka kira ubanka Kabiru ya kai mu, idan ba shi ba kam al-quran bbu motar shegen da xan shiga" Muhd ya fuxa isa ya juya yana kallon Rayyanah yace "ke shiga muje" inna tayi murmushi tace "shiga Rayyanah" kasa shiga motar Rayyanah tayi fuskarta a daure, har sae da inna tace "ki shiga nace mana" snn ta shiga inna ma ta shiga motar tana goge dan kwallar idonta tana murmushi " sae da suka hau babban titi snn Muhd ya dake yace "ina muka nufa?" Inna tace "A'a wae da gidansu Murja xaka fara kai mu, daga can sae gidansu Fatee, daga gidansu fatee sae ka kai mu gidan bari'a, daga can sae mu garxaya gidan kawata hjya Laure, in mun fito sae mu shiga gidansu Audi, to ba wani ddewa xa muyi a can ba, muna fitowa sae ka garxayo da mu gidansu Alhaji bukar, to daga gidan Alhaji bukar sae ka kai ni gidan tanko ina son gninsa, idan mun fito sae ka kai mu gidanku, daga gidanku kuma sae ka dawo da mu gida kawae don ni ban fiye son yawan gidajen mutane ba" murmushi kawae yyi yana shafa sajen fuskarsa bae ce mata komae ba.

Billy Giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZANBAR SHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

26/12/2016

🔮```11```🔮

Sae da ya kaisu duk gidajen da inna ta lissafa snn ya kaisu gidan su wato family house.

6angaren hajiyar pretty suka fara zuwa snn 6angaren su hajiyar nasir wacce ta tarbe su cikin fara'a da murna ba kamar hajiyar pretty da ta kama kallon Rayyanat a yatsine ba.

Haka d'ayan 6angaren da girmamawa suka tarbi inna yayinda suke kallon Rayyanat ba yabo ba fallasa .

Nan inna tabar Rayyanat amma a 6angaren su hajiyar Nasir a cewar ta musu yini.

Saliha sai janta take a jiki sbd yarinyar tana da son mutane sosai ba kamar sauran yaran gidan ba hkn yasa Rayyanat ta d'an saki jikinta da saliha har ma tana jan Rayyanat da fira.

inda cikin firar take ta bata labarin rayuwar su ta school , ita dai Rayyanat saurarenta kawai take ba um ba um um sae dai idan taji abin dariya tayi d'an guntun murmushinta,saliha tace "wai nikam Rayyanat kin barni ni kad'ai keta zuba kamar parrot ba kuwa zan yarda ba don kema sae kin bani naki labarin makaranta,d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"aini banyi secondary school ba ma bare zancen boarding school,xaro ido saliha tayi tace "hm kedai ba kya son bani labari ne,a sanyaye Rayyanat tace"da gaske nake wlh"

Saliha ta kalleta tace"meyasa gashi da alama zaki kai s .s 2 ko 3 inda kinci gaba?Baffana ne baya iya d'aukar nauyin karatuna"

tayi maganar cike da qwallah a idonta kan tuna baffanta da tayi"

Saliha tayi shiru tana kallonta sae duk taji ba dad'i tace"to ynx idan kika sami dama kina so kici gaba da karatun?girgiza kanta tayi tare da share hawayenta snn tace"ai lokaci ya qure min"

lokaci bai qure miki ba Rayyanat kina da lokaci har yanzu"

um um ynz ba wnn ne burina ba sae nn gaba kad'an tukun"er dariya saliha tayi tace"hm Rayyanat har wani buri kike da shi yanzu da ya wuce karatu sae dai idan karatun ne ba kya so"kallonta kawai Rayyanat tayi yayinda idanunta suka sake cikowa da qwallah ta kauda kanta gefe ba tare da tace da ita komai ba.

Qofa suka ga an turo saliha ta tashi taje ta kar6i trayn abinci da ke hannun ummnta ,hjy ta bata tare da kama kunnenta ta murd'e tace"kina nn kin cika ta da baqin surutun nn naki ko kiyi tunanin d'ebo muku abinci ma bakiyi ba, dariya saliha keyi mai had'e da jin ciwo tace"wash umma Allah inada niyyar tashi na d'ebo mana abinci sae gashi kin shigo mana dashi "ta sake mata kunnen tare da fad'in"oya yi ki zuba muku abincin kuci ina so zamu d'an fita ne zuwa anjima,to umma,nn Hajiya ta fita saliha ta zuba musu abinci a plate d'aya suka fara ci sae dai basu wani ci sosai ba Rayyanat tace ya isheta sbd dama kafin su fito taci abinci.

Sea bayan sllr la'asar suka fita wani qatoton mall suka je Hajiya tace da Rayyanat ta d'auki duk abinda take so, Rayyanat bata iya d'aukar komai ba sae saliha ce ta shiga d'aukar mata kayan sawa kmr su Arabian gown da turarukku designers da kuma kayan kwalliya bayan sun gama siye siyen su ne suka maida Rayyanat gida da kayanta niqi niqi wad'anda saliha ta kwasar mata,

inna sae washe haqora take tana sama Hajiya albarka.

7 days later

Rayyanat ce a kitchen ta gama wanke kwanika tana goge kitchen bayan ta gama ta koma d'aki.

Saliha ce ta shigo gidan ta sami Mohd shida inna sae fira suke sae da ta gaishe su snn ta zauna har inna na tambayar ta ya mutanen gida tace duk suna lafiya tace"to ya na ganki yau ke kad'ai ba abokiyar yawonki Ameera? Tana gida wai yau bata jin fita tace"ayyo to ya hajiyarki tana lfy dai ko?lfiya qalau wlh ta ma ce a gaida ke,ina amsawa ai yau tama kirani a waya mun gaisa kmr kullum,eh inna Rayyanah fa? Shiga daga ciki yanzun nn ma ta shiga.

Rayyanat na zaune tana duba litattanfanta na islamiya sae ga saliha ta shigo da sallamarta ,da sakin fuska Rayyanat ta tarbe ta ta nemi guri ta zauna tare da jawo littafan Rayyanat na Islamiya tace"ke yau fa Alhamis ko kin manta" Rayyanat tace"ai ba shirin zuwa makaranta nake yiba ina muraji'a ne sae gashi na sami kaina da mantuwa da wani gun a cikin littafin ishmawee babun sallati janazatee gun da ake cewa....cab ai ke ban kai babin ba wlh kad'an dai ya rage,nn taja hannunta tare da fad'in "amma muje gun yaya Man ya tuna miki kafin ya fita "cikin rashin fahimta Rayyanat tace "waye kuma haka?oops baza ki san sunan ba sbd da Muhammadu inna ke kiran shi, Man kuma complete name d'inshi ne frnds d'insa suka had'e wato Muhammad Aminullah Nasir shine har mu qannansa ke kiransa dashi sbd koda muka taso mun samu ana kiransa da sunan.

Ta6e baki tayi ba tare da tace komai ba Saliha tace "muje ya tuna maki ko"um um nafi son na tuna da kaina sbd zanfi riqe abun da kyau"to amma dai zaki ajiye muraji'an nn har zuwa dare tukun sbd ina son muje ki rakani familyn mamana,a natse Rayyanat ta ware kyawawan idanuwanta tana kallon saliha snn tace"ni d'in nn? Eh man ai anguwar ba nisa da nn kuma wa ke kad'ai na biyo gidan nn wlh ,don hk ki tashi ki shirya mu tafi,nifa ban son shiga inda ban sani bane saliha ki tafi kawai abunki kinji,

,kinji Ki sae kace wacce za'a cinye dan Allah nidai tashi ki shirya mu tafi ai da sannu ake yin sabo ba wai zama zakiyi tayi kice ba kya shiga mutane ba.

Turo qofar da akayi ne ya katse Rayyanat da abinda tayi niyyar fad'a,Saliha tace"yauwa inna dan Allah ina son Rayyanat xata rakani gidan Baaba.

Ba musu inna ta amince da su tafi.

Duk da Rayyanat bata so ba amma haka ta haqura Saliha ta tasa ta gaba tana mata kwalliya yayinda tace ta rufe idonta har sae an gama kwalliyar ko zata bud'e,

byn an gama kwalliyar Rayyanat na bud'e idanuwanta ta wani ware su kan tsananin kyawon da taga tayi har ma ta fara shakkun anya ita ce kuwa tace"saliha wnn kwalliyar na tafi ina dashi nikam rage min ita don wlh ni ko kwalliya ma banayi bare na iya fita da wnn kwalliyar haka,,,um um gsky ba abinda zan rage maki ,

kawai don baki saba kwalliya bane kika ga kmr tayi yawa amma dai dai take, da qyar Rayyanat ta iya yarda aka bar kwalliyar saliha ta bata Arabian gown ta saka ta jawo qatoton hijabinta zata zuba saliha ta dalla mata harara da wasa tace"meye haka zan gani ki wani zuba hijabi har qasa sae kace zaki tafi islamiyya ?ban gane ba saliha to dame kike son na fita?saliha bata ce mata komai ba sae hijabin ta cire mata ta d'auko top d'in gown ta roller mata, duk da cewa Rayyanat ba wata fara bace amma shirin ya matuqar d'aukar ta sae dai faffau tace bata iya fita da shirin sae tasa hijab Saliha ta buga qasa da sama a cewar ta duba ita ma fa irin shirin ne da ita amma ina sam Rayyanat bata yarda ba, bbu ynda Saliha ta iya da ita hka ta kyaleta da hijab din suka sallami inna da ke kitchen suna wainar flower da baaba hurera, inna na ganinsu ta washe baki tace "Ma'sha Allahu" saliha tace "ku fa ajiye mana namu inna, don nasan kina iya kwashewa gaba daya ki ba ma yaya" saliha na kai wa nn ta ja hannun Rayyanat suka fice daga kitchen din, kwance suka tar da shi a falo idonsa lumshe kmr mai bacci, lkci daya ya bude ido yana kallonsu, Saliha ta dan hade rae tace "sae mun dawo yaya" Rayyanat kam kauda kai tayi ita ma fuskarta a daure, mikewa yyi xaune da sauri yace "ina xa ki?" Dauke kai tayi tace "gidan fa kaka xa mu, kuma Hajiya ta sani" kallon Rayyanat ya tsaya yi da mmki ganin ynda ta wani hade rae, can ya mike ya nufi kitchen sae ga shi ya fito inna na biye da shi a baya tana cewa "lfya me ya faru?" Sae da suka karaso cikin falon snn ya juya yana kallon innar da kyau yace "dama tambaya ce xan maki, wae wnn yarinyar me aiki ce ko ko a ina kika jajubo ta" ya fadi yana nuna Rayyanat, inna ta ja dogon tsaki ta balla masa harara tace "uwar ka ce ba me aiki ba, wnn tayi maka kama da mai aiki, hka kawae kasa ma yarinya ido a gida, uwar me ta tsare maka, to in kai maye ne sae dae ka ci kanka wllh" a fusace ya karasa gaban Rayyanah yana mata wani mugun kallo fuskarsa a daure ya dago fuskarta da kyau yana kallo, ta kuma hade rae ita ma tana kallonsa da manyan idanuwanta, a nutse ya fara mgna, "daga yau, I mean daga this vry moment kika kuma min wani irin kallo a gidan nn, ko kuma kika gan ni kika ki gaida ni sae na....." Kukan da inna ta fashe da yasa ya tura ta da karfi, ya juya yana kallon innar, kwashe wayoyinsa yyi da ke kan kujera ya juya ya fice daga falon kmr xae tashi sama, inna ta bi sa da ja'irin yaro kawai, ta karaso gun Rayyanat tana matsar kwalla tace "kiyi hkuri kin ji 'yar nn, tambada yake ji yau shi yasa yyi maki hka, amma ki kyaleni da shi, da ubansa ma xan hada sa ni ya ja masa kunne ya daina xuwa min gida don baya tsinanani da komae da ma, sae dae in dafa in basa ya ci ya bar min kwanukan a nn ya kara gaba" Rayyanah tayi murmushi kawae tace "bbu komae inna" saliha da ko kadan bata ji ddin abinda yayan nata yyi ma Rayyanah ba ta ja ta a sanyaye suka fice daga falon don xuwa inda xa su.

Sae da suka fita daga gidan Saliha tace "kiyi hkuri Rayyanah hka yaya yake wani lkcn" Rayyanah tayi murmushi tace "A'a ni bn ji haushi ba wllh," saliha tace "yauwa, kuma don Allah ki dinga gaishesa in kun hadu" Murmushi kawae Rayyanat tayi bata ce komae ba, saliha tace "ke komae murmushi, ba sae ki ce min to ba" Rayyanat ta kuma yi mata murmushin tace "toh naji Saliha" saliha tayi dariya tace "yauwa ko ke fa."

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

28/12/2016

*🔮```12```🔮*

Washe gari kaf gidan Rayyanat ce ta gyare shi har wajen gidan wato gun faka motoci duk sae da ta share tsaf koina ya haskaka.

Snn taje kitchen don taya baaba hurera aikin abinci, baaba hurera tace "Aa Rayyanah yau kinyi aiki da yawa je kawai kiyi wanka kinsan yau juma'a qaramin lokaci ce," Rayyana tace "aa baaba bari kawai na tayaki wlh," "wlh jeki ai saura kad'an na qarasa tafi kiyi wanka kinji er albarka," cewar baaba hurera knn, murmushi kawai Rayyanat tayi ta juya ta fice daga kitchen.

wanka ta je tayi ta shirya cikin riga da skirt na atamfa da inna tayi mata, sukayi mata kyau kmr ba tashin qauye ba kan yanda sukayi d'as a jikinta.

qur'ani ta d'auko ta shiga karatun suratul kahfi, a dakin da inna ta bata ita kadae duk da ba kwana take ciki ba don tsoro.

Tunda daga kan gate da mohd ya shigo gidan yake qare ma ko ina na gidan kallo ganin yanda gidan yayi haske yayi kyau, as in very neat ba wai don ba a share gurin ba a'a sae don ganin sharar yau ta daban ce da kullum.

Faka motar sa yayi ya fito cikin motar cike da tafiyar sa ta qasaita ya isa cikin gidan yana duba agogon wrist dinsa.

Inna ya samu xaune a falo ta miqe qafafu tana casbi har yana jin sautin salati na fita a bakinta, murmushi yyi hade da mata sallama, kin amsawa tayi sae ma wani kallon masifa da ta watsa mai tace "idan kasan yau ma tambad'ar ce ta kawo ka ftr min daga gida!"

Muhd yayi murmushi ya karaso cikin falon tare da ajiye ledar hannunsa gefenta yana kallonta yace "ni abinci naxo ci" inna bata kula sa ba sae hannu da takai tana bud'e ledojin da ya ajiye mata 'ya'yan fruits ne da gasasshen naman rago sae gassashiyar qullin hantar rago gefe, lkci daya inna ta washe baki tace "Auu! sannu da xuwa mai gida, Allahu yyi maka albarka ya kuma nuna min aurenka" daga haka ta qwalawa Rayyanah kira.

Cikin hanzari Rayyanat ta fito daga d'aki tana ganin muhd zaune ta rage saurin da take inna na washe da baki har lkcn tace "zo er albarka ki kai ma hurera 'ya'yan itacen nn ta yanyanka mana daga nn ki biyo ma maigidana da nasa abinci idan an kammala."

Rayyanah tace "to" ta kar6i ledar fruit wacce sae a snn ta gaida muhd, dake bin ta da harara tun shigowarta, ba yabo ba fallasa ya amsa.

Rayyanah ce ta yanka 'ya'yan fruits din da kanta ta had'o komai har da abincin mohd da inna tace, ta kawo ta ajiye ta wuce inna sae sa mata albarka take, inna ta dubi muhd washe da baki har lkcn tace "d'an albarka nn ina son muyi wata magana da kai a game da yarinyar nn Rayyanah ashe wae primary kawai tayi sae jiya nake ji a bakin saliha shine nace ka binciko min makaranta mai kyau mai tsada kabiru ya biya a sata, in yaso duk safe sae ka riqa zowa kana kai min ita, Nasir kuma yana dawo da ita idan an tashi"

Wani irin murmushi yayi da jin zancen inna kamar sa6o dan har ma sae da yayi istigifari a cikin rnsa had'e da shafo sajen fuskarsa yana kallonta har lkcn murmushi dauke a lebbansa yace "to ynxu dae duk yawancin makarantu an fara jarabawan second term, kawae ki bari idan shekara ta zagayo hkn xae fi kyau" inna ta yi shiru tana kallonsa sae kuma tace "to muhammadu idan shekara ta zagayo dan Allah kar ka manta da zancen nn dan dai wlh ina son naga Rayyanah tayi karatu kmr kowa ga ta da kkri sosai in ji saliha"

Yyi murmushi yace "to Allah kaimu" tace "amin" shi kuma ya jawo abinci ya fara ci.

2:30pm

Rayyanat ce zaune kan carpet ta gama sallah tana addu'o'i inna ta shigo d'akin kowane hannunta yana d'auke da plate d'ayan 'ya'yan itace ne da aka yanyanka, d'ayan plate din kuma naman rago ne da kuma hanta ta ajiye tana fad'in "Rayyanah keda nace kici abinci tun da'zu ashe baki ci ba sae yanzu da na fito naga komai inda na bar shi" Rayyanat tace "yanzu dama xan tashi idan na gama sallah" "to ai kin gama sllr tashi muje kici abinci a gaban ido na don na fhmci hlnki ba kya son cin abinci" ba yanda Rayyanat ta iya ta tashi tana linke sallaya had'e da d'an guntun murmushi a fuskarta don dai ita gsky tana jin dad'in yanda inna ke kula da ita.

Falo suka je inna ta kunna musu kallo Rayyanah na cin abinci suna kallon su cike da nishad'i.

Washe gari ranr ta kasance ranr asabar Rayyanat tayi shirin ta tsaf na zuwa islamiya da hijabinta sky blue har qasa na islamiya ta saka safar ta klr hijabin ta d'auko niqab ta d'aura bata dai sake shi a fuskarta ta ba ta d'auko Jakarta ta islamiyya ta riqe a hannnu snn ta nufi d'akin inna ta mata sae ta dawo, inna tace "a dawo lafiya er albarka"

Fuskar ta wasai ta fito d'akin ta saka takalmi ta rufe fuskarta da niqab snn ta fita, da kafa take xuwa makarantar don bbu wani nisa daga gidan can saman layi ne, yawanci duk gidajen masu da shi ne a layin don hka layin is vry cylnt, yau ma kmr kullum xaune ta gansa gaban kantamemen gate din gidan as usual, sae dae yau ba shi daya bne, shi da wani ne, bin ta yyi da kallo kmr ko da yaushe, ta wuce su da sauri tana harhardewa, ta rasa dalilin wnn kallon na mutumin nn da take gani kullum xata makaranta, ita dae fuskarta a rufe yake ko da yaushe, tsaki ta ja tana tunanin kila hanya kawae xata canxa don a rayuwarta ta tsani kallo.

Har aka tashi daga makaranta bata da wani walwala, ta hada litattafan da suka yi ranan ta xuba cikin jakarta snn ta sakale shi a hannu, ta dauki Qur'an dinta ta rungume a kirji ta sallami yan kawayenta da suka dan fara sabawa a ajin ta fito ta kama hanyar gida da sauri da sauri don Karfe shidda dama suke tashi, xaune ta sami mutumin daxu har lkcn sae dae wnn karan shi kadae ne, tsallakawa tayi ta d'ayan side din ta ci gaba da tafiyarta da sauri, sae da ta dan yi nisa snn ta dan juya don ganin ko yana kallonta,Xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin biyo ta ma yake, ta kara sauri gabanta na faduwa ssae, gashi bbu alamar mutum a layin, ganin duk saurinta har ya kusa cim mata yasa ta kwasa a guje ko minti biyar ba ayi ba ta isa gida har lkcn gudu take har da kukanta, mai gadi na tambayarta me ya faru bata ko sauraresa ba ta nufi kofar shiga falo da gudu, a bakin kofa suka ci karo da Muhd dake tsaye yana jujjuya makulin motarsa alamar xae tafi, suna mgna da inna, hkn yasa Rayyanat ta fasa ihu, ya koma baya da sauri lkci daya ya turata da karfi ta fadi nn kasan falon, inna ta mike da sauri ta karaso bakin kofar tana salati tana tambayar me ya faru, Rayyanat da ke mayar da numfashi ta fashe da kuka ssae, inna duk ta rude ita ma ta saka kukan ta xube nn gabanta, baaba hurera ta fito da sauri tana tambayar lfya, sae ga mai gadi shima ya taho da sauri yana tambayar me ya faru, Muhd kam don takaici komawa gefe yyi ya tsaya, cikin kuka inna ke kallon mai gadi da Baaba hurera tace "nima ban san kukan da take ba" baaba hurera ta shiga tambayar Rayyanat me ya faru, da kyar ta tsaida kukanta muryarta na rawa tace "wani mutumi ne sae yyi ta kallona idan xa ni makaranta, shine yau ya biyo ni sae na fara gudu yana ta bi na kuma" ta karashe mgnr cikin matsanancin kuka, juyawa Muhd yyi ya fice daga falon mai gadi ya bi bayansa, lkci daya inna ta tsuke fuska ta miqe tana share hawayen fuskarta tana huci tace "dan gidan uban waye shi xae biyo min ke da gudu, hurera dauko min gyale na" hurera tace "A'a inna, ba ga su Muhammadu sun fita ba" inna tace "da'alla bani mayafina in je in masa rashin mutunci" hurera ta dauko mata gyalenta ta bata, ta fixge ta fice daga falon kmr xata tashi sama, a bakin gate suka hadu da Muhd da mai gadi, Muhd yace "ina xa ki kuma inna" ba tare da ta kallesa ba tace "nemo dan iskan xan je yi mana" yace "bbu kowa a waje na duba, ita bakauyiyar wace gari ce da xata d'aga ma mutane hankali hka, kila ma harkan gabansa kawae yake xata shigo ta daga ma mutanen gida hnkli, tsiyar yan kauyen nn knn"

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

30/12/2016

🔮```13```🔮

Cikin gida suka koma tunda ba a ga wanda ake neman ba, inna dai sae masifa take tayi kmr wacce ta sami wanda ake nema a gabanta.

Mohd kan takaici tun daga kan gate bai ma dawo ba jan motar sa kawai yayi yabar gidan.

Inna ta rarrashi Rayyanat ta samu har ta daina kukan da take taje d'akinta ta ajiye jakarta ta cire niqab da hijab da socks ta nemi guri xata kwanta sbd har yanxu jikinta bai daina rawar tsoro ba. Inna ce ta shigo d'akin riqe da kofin fura a hannunta,

ba ita tabar d'akin ba har sae da Rayyanat ta shanye furar tas.

Har dare Rayyanat bata sake kmr kullum ba kallo suke amma sae tunanin gobe take idan zata je islamiya.

Nasir ne ya shigo gidan da sallamar sa ,suna gama gaisawa inna ta bashi lbrn abinda ya faru da Rayyanat d'azun ,

ya kalli Rayyanah da kulawa yace"bai dai maki komai ba ko? Sae da ta girgiza kanta snn tace"bai min komai ba amma nasan ko gobe zan ganshi in na fita don kullum sae na ganshi idan zan tafi makaranta"

ta qarashe mgnr kmr wacce zata yi kuka.

Nasir ya nisa yace har da safe kike ganin sa idan zaki tafi makaranta? Aa bana ganinsa da safe sae da yamma"

To shikenan da yamma zanzo kiyi tafiyar ki kar ki nuna tsoron komai don so nake na gane dalilin bibiyarki da yake,kar kisa tsoro dmn ina nn a bayanki kinji,a sanyaye ta gyad'a masa kai .

Inna tace"ai kowane d'an iskan ne gobe ma kwashe ta nida shi"

Nasir yace"ai ba girmanki bane inna ki barni dashi kawai"...yo shi girma ya sani ne da zai biyo er qaramar yarinya haka duk yabi ya tayar mata da hnkli gabad'aya yau ta rasa sukuni.

Ai inna ina ganin irin en iskan samarin nn ne da basa da abinyi sae zaman banxa.

Inna ta tsuke fuska tace"to Rayyanah kam baza tayi komai dashi ba don ya ma kama

gabansa tun wuri.

Nasir yayi murmushi ya sauya wata firar suka ci gaba dayi,

can inna ke tambayar sa wai ina er banzar nn Fatima ta shige da na daina jin d'uriyar ta, Nasir ya shafi kansa yana murmushi snn yace"inna ai pretty ta jima bata jin dad'i sbd laulayin da take fama dashi"

Dad'i inna taji sosai har da su taka rawa ta kusa samun kama kunne tace"ai bari shi kuma d'an banzan nn yazo marar son aure ,yazo yayi auren nn ko shima zanga abinda ya haifa kafin nabar duniya.

Duk cikin taka rawa inna ke maganar nn Rayyanat har da er dariyar ta don rawar inna ta bata dariya sosai.

Washe gari da yamma har Rayyanat taje ta dawo bata had'u da kowa ba,

tare suka shigo ita da Nasir inna na ganin su ta shiga tambayar ko anga mutumin ?Nasir yace"ba muga kowa ba sae wasu masu zama gurin"

wani dogon tsaki muhd dake kishingid'e yaja yace"wai inna me yasa kike biyewa bagidajiyar yarinyar nn nikam,kawai mutane na harkar gaban su ta wani ce ya biyota in miji take nema taje can qauyen su mana ta samo irinta ba tazo nn tana fakewa da wani ya biyota ba,

wane kidahumi ma zata samu a nn da har zai yi lokacin ta in ba wanda uwar sa ta masa baki ba.

Sosai maganar mohd tayi wa Rayyanat baqiqirin a rai duk yanda taso 6oye hawayenta sae da suka gangaro kan kumatunta tayi saurin share hawayen ta shige daga ciki ,mohd dake kallonta cikin 6acin rai sae a snn ya kauda idonsa ya maida su gun inna da ta shiga sirfa mai masifa kan yafita harkar Rayyanah har tana fad'in "sae na had'a ka da ubanka kabiru idan baka fita harkarta ba wlh.

Nasir ne ya shiga bata haquri shida baaba hurera dake aiki kitchen ta jiyo fad'an ta fito"

mohd kam barin gidan yayi sai haushin inna yake ji dake fifita Rayyanah akan shi har tana sako ubansa a ciki.

Yau kusan kwana biyu mohd bai zo gidan inna ba inna bata damu ba sai ma harkar gabanta take.

Rayyanah ce a bayan gida ta gama wankin kayanta dana inna tana shanya wacce sae ta sharce zannuwan kafin take shanyawa.

inna tazo ta same ta tace"oh ni wai Rayyanah wanki kika xo kina mana keda ya kamata ace kinyi shirin islamiya !uhm inna ai na kammala yanzu zanje in shirya "to Rayyanah yi maza amma dan Allah ki daina wankin nn nasha gaya maki akwai mai min wanki har ma naki d'in duk ki daina wankewa idan sun taru ki kawo na had'a da nawa kayan na bawa abu mai wanki ya riqa wanke mana kinji.

Rayyanat ta gyad'a mata kai inna ta washe baki snn tace"to yayi er albarka yi maza ki shirya ki tafi makaranta.

Tafe take cike da fargaba don har yanzu bata cire ran zata sake ganin wanda ke bibiyar ta ba gashi yanxu nasir yayi tafiya bare ya rakota kmr yanda yayi mata a kwana biyun nn da suka wuce.

Sai sauri take har tana hard'e qafafu jin alamar ana binta a baya dmn har sautin tafiya tana ji ,

kan tsananin tsoro bata iya juyawa ba sae ma duqawa tayi zata kwashi takalmanta ta banka da gudu.

Sae taji an mata sallama cikin murya mai mugun taushi da sanya natsuwa ga duk wanda yaji hkn yasa ta fasa abinda tayi niyya sae dai cike da 6acin rai ta miqe dmn ganin wanda ke neman takurata a rayuwa.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

30/12/2016

🔮```14```🔮

Murmushi ya sakar mata duk da ba ganin fuskar tata yake ba kansancewar niqab d'inda ke sanye da ita.

Kafin ya ce komai ta buga mai uban tsaki tace"wai malam lfy kake faman bibiyar rayuwata!wani murmushi ya sake sakar mata yakai hannu cike da natsuwa ya shafo sumar kanshi snn yace"sbd ina sonki"harara ta dallah mai had'e da tsaki "ta tafi ta barshi nn tsaye,

Bai bita ba sae tsayuwar sa ya gyara tare da hard'e hannuwan sa a qirji yana kallonta har ta 6ace ma ganin sa.

Juyowar da zaiyi ne sukayi ido hud'u da Man dake masa wani mugun kallo na tsana yace"kai amma ka bani kunya wlh kai yanxu baka ga abin bibiya ba sae wnn abar "uhm man kenan wnn ce abar yrnyr da ta koina ta amsa kiran mace har mace ga natsuwa da kamala .....mtsw! Man yaja tsaki yace"ga dukkan alama ka fara shaye shaye shiyasa kake ganin abu baibai,nn ya tafi ya barshi kmr wanda zai tashi sama.

Gidan inna ya nufa ya sami inna da baaba hurera zaune a tsakiyar gidan suna fira.

Ya gaida su sae baaba hurera kad'ai ce ta amsa gaisuwar ,

inna dake harararsa ganin zai shigar mata d'aki tace"me kuma zakayi min a cikin d'aki bayan duk gamu nn a waje"baaba hurera tace"ke ko dai inna mai gida ne fa ai kya tashi ku shiga ciki kiji dame yazo,

ai nasan ba abinda yazo dashi face tambad'a da iya shege,ni kwana biyun nn ma da baka zo ba sae naji sat kmr an cire min qaya.

Kujerar zaman mata naga man ya jawo wacce su inna ke zaune kan irinta yasa farin handkerchief d'insa ya share snn ya zauna yana fuskantar inna d'auke da murmushi a fuskar sa yace"ashe inna in na mutu kin huta dani kenan... zaro ido tayi tace"me kuma ya kawo zancen mutuwa ana zaune qalau, to inna ke kika ce kinji dad'i da banzo kwana biyun nn ba, yo dan nace haka Muhammadu ai bazan yi ftr ka mutu ba nida nake son ganin 'ya'yanka kafin na bar duniya tukuna ma wai kai don ubanka yaushe zakayi auren ne kullum kana mana yawo da hnkli baka ko son ana zancen,

ni ka gaya min idan kana fama da rashin lafiya ne inji dan insan ta inda zan fara nemar ma magani, sajen fuskar sa ya shafo yana kallon inna wanda har lokacin da murmushi d'auke a fuskar sa yace"inna me kuka dafa yau? Ban sani ba ina ma magana kana wani zancen, oh ni Hajara wai ko dai muhamnadu gamo kayi da aljana da duk ana ma zancen aure sae ka canza da wata maganar,ta qarashe mgnr cikin kuka irin na tsafi d'in nn, mohd ya kalle ta da kulawa yace"nifa inna kinsan na tsani na ganki kina kuka indai aure ne nayi kusa nn bada jimawa ba inshaAllah"

Kai zo kuka farin ciki gun inna har da su rawa tana yiwa man kari kan irin farin cikin da yasa ta yau ta jashi zuwa d'aki sae zuba

masa albarka take yayinda baaba hurera tabi su da kallo tana dariya dn har lokacin inna rawa take man kuwa sae murmushi yake don shi yana son ko yaushe yaga inna cikin farin ciki .

Inna da kanta taje ta kawo mai abinci wacce yinin rnr duk cikin farin ciki tayi shi.

6:5pm

Rayyanat ce ta shigo gidan ta dawo daga makaranta ta sami man kwance a falo kan 3 seater kmr mai bacci don idanuwan sa a rufe suke, tsaye tayi tare da yaye niqab d'in fuskar ta tana masa kallo mai cike da tsana,

karaf idanuwansu suka had'u tayi saurin kauda idonta tare da gaishe shi ba tare da ta damu da ya amsa ko kar ya amsa ba tayi ficewar ta zuwa d'akinta.

Da sauri man ya tashi ya bita ya finciko hannunta da qarfin tsiya har sae da jikinsu ya had'u sae kuma yayi saurin ture ta daga jikin nashi ya nuna ta da yatsa yana fad'in"ba nayi warning d'inki kan wnn d'an iskan kallon da kike min ba ,wlh ina mai gaya miki duk na qara kama ki kina min irin wnn kallon na lafira sae yafi ki jin d'adi!dan ubanki inni sa'anki ne ko kuma abokin wasarki!

Zama d'aya qwalla ta ciko a idon Rayyanah kan jin zafin zagin da ya mata,ta d'ago tana kallonsa haka shima kallonta yake har hawaye suka fara sakkowa a hnkli kan kumatunta .

Ya watsa mata mugun kallo snn ya bar d'akin Rayyanah kuwa share hawayenta tayi snn ta ajiye jakar hannunta ta cire hijab da socks ta kai su a muhallinsu.

Tayi zamanta a d'aki har sae da ta tabbatar mohd ya bar gidan snn ta fito taje d'akin inna wacce tana ganinta ta washe baki tana tarbon ta da murna kyace ta kwana bata ganta bane.

Bayan sati d'aya da faruwar haka Mohd ne zaune a office d'insa yana waya kan cewa "a bashi ixini ya shigo"ya ajiye wyr ba jimawa aka turo qofa ya kafe wanda ya shigo da ido har ya zauna.

Hannu suka bawa juna suka gaisa snn wanda ya shigo ke cewa"Man magana naxo muyi mai muhimmanci kuma dan Allah kar kayi poking d'ina"man dake jingine ya lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya snn yace"ina jinka"

Kallon sa yayi da kyau yace"about wnn yarinyar ne da nake bibiya idan zata tafi islamiya ashe ma ka santa"da sauri man ya bud'e idonsa dake rufe yace"aka ce maka na santa who say so? Nop ba wanda yace kawai ni naga hkn sbd a kullum gidan inna nake ganin tana shiga haka kuma gidan take fitowa"to ban santa ba nima ganinta kawai nake a gidan"

A sanyaye mutumin yace"to naji ganin ta kawai kake da haka nake so ka taimaka min kamin jagora muje ko yrnyr nn zata fara kulani dmn wlh nayi nayi ta kulani taqi gashi ni kuma dgske nake sonta wlh"

Man da tunda ya fara zancen sa yake masa kallon ka ta6u yaja dogon tsaki tare da girgiza kansa yace"tabbas munir ynx na tabbatar ka fara shaye shaye amma ka 6ata kanka wlh ka kuma cuci iyayenka da tarbiyar da suka maka"

Cikin damuwa munir yace"wai Man meye hk duk a cikin frnds kafi kowa sanin halina fa....banda yanzu da ka sauya halayen ka don haka ni ka ma ftr min daga office,pls man.... Munir!nace ka fita ko!

Cikin 6acin rai munir ya tashi ya fita ya bar mohd dake juyi a hnkli kan kujerarsa yaja guntun tsaki yace"na rasa wace irin qwaya ce yake sha dake sauya mai tunani gabad'aya da har ya fad'a jin son wnn abar har ma wai yake cewa na masa jagora sae kace ni d'an makauniya ne ko makaho"

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

1/1/2017

🔮```15```🔮

Munir yaro ne kyakkyawa mai matuqar mutunci da kamala haka kuma yaro ne mai girmama manyansa ya kasance mai tausayin talakawa sosai sbd haka ya taso ya sami iyayen shi da son taimakon talakawa duk da irin kud'in sa kuwa basa da wulaqanci ko kad'an asali ma gidan su munir gida ne da ko yaushe zaka sami jama'a wad'anda ake bawa taimako.

Su biyar ne a gun iyayen su ,shine na farko snn hameed ,Hasheem,Hafsat snn er autar su safiyya.

Munir ya jima yana son yayi aure amma bai sami wacce ta kwanta mai a rai ba sae akan Rayyanat wacce ko da kuskure bai ta6a ganin fuskarta ba amma rnr farko da ya fara ganin ta yaji ta kwanta mai a rai ya kuma ji a ransa irin matar da yake son aura ce.

Ranar alhamis ba islamiya hakan yasa Rayyanat tayi zaune tana ta mitar littafanta,

ita kad'ai ce a falon tana karantawa da larabci tana fassarawa tamkar tana a gaban malami yanda ta taqarqare.

Ba komai yasa taxo falo tana yin karatun ba sae don inna ta fita anguwa baaba hurera kuma tana kitchen,gashi inna tace xa'a kawo saqo shiyasa taxo falo ta zauna kar wanda inna tace zai zo ya kawo saqo yazo basu ji ba.

Rayyanah yarinya ce mai tattara hnklinta gabad'aya akan abinda ta sa ma gaba hkn yasa bata san da shigowar Mohd ba duk da kuwa sallamar da yayi sae ganin mutum kawai tayi tsaye a kanta, a tsorace ta saki ihu tare da jefar da littafanda ke hannunta zata kwasa da gudu kenan man ya dakatar da ita cikin daka mata tsawa, sae kawai ta fashe masa da kuka tana kallon shi ,wacce sae a snn ta gane waye,ai kuwa kai tsaye ta had'e girar sama da ta qasa tare da share hawayen fuskarta, Mohd kuwa tsaki yaja yayi tsaye yana kallonta yayinda hannyen sa ke cikin aljihun wandonsa,ciki ciki ta gaida shi ta duqa ta kwashi littafan ta ta wuce ta kaisu d'akinta ta ajiye snn ta nufi kitchen dai dai baaba hurera ta shigo ta qofar baya duk a rud'e, tace"Rayyanah ba kece naji ihun ki ba ina bayi?

Kmr wata qaramar yarinya ta 6ata fuskarta tace"nice Baaba wnn d'in nn ne ya shigo ban sani ba sae ganin sa nayi shine na tsorata"

Baaba hurera tace"waye kuma wnn d'in nn ?Rayyanah tace"wnn d'in nn dake zuwa gun inna kullum.

Baaba hurare kam bata gane ba sae falo ta tafi dan ganewa idonta ,

tana ganin mohd ta washe baki snn tace"ayyo wai muhammadu kaine Rayyanah ke cewa wnn d'in nn sae duk ban gane ba shine nace bara na fito naga waye.

Murmushi ya sakar mata tare da gaida ta snn yace"inna fa na shiga d'akin nata ban same ta ba"

Baaba hurera da har lokacin murmushi take tace"ai ta d'an fita ne ita da Nasiru amma tace bazata jima ba zata duba Fatima (pretty) ne dake jin jiki,to Baaba ace da wnn yrnyr ta kawo min abinci na,Baaba hurera tace "to"snn ta koma kitchen ta snr da Rayyanat.

Tun daga qofar kitchen mohd ya tsare Rayyanat da mugun kallo har ta qaraso ta ajiye masa abinci zata juya yace"ke xo nn"

Juyowa tayi tare da watsa masa manyan idanuwanta a cikin nashi,

guntun tsaki yayi ya kauda nashi idanun sae kuma ya sake kallonta snn yace"wae ke wace ce da kika raina ni haka meye matsalar ki dani?kauda idonta kawai tayi ba tare da tace dashi komai ba, ya saki tsaki yace"tafi ki bani guri amma wlh duk rnr da na qara jin kince min wnn d'in nn sae bakin ki ya gaya miki"

Ta juyo had'e da ta6e baki ta fara tako kenan taji yo sallama ta amsa sallamar ta tafi ta kar6o saqo ,

kitchen ta tafi da saqon dan inna ta gaya mata abinda za'a kawo wato nmn kaji,tas Rayyanat ta wanke nmn ta zuba a freezer.

Washe gari rnr juma'a Rayyanat taci er kwalliyarta ta juma'a tana zaune abinta a d'aki ta gama karatun srtl kahfi ta jawo litattafanta na islamiya tana mita.

Tana cikin haka taji inna na qwala mata kira ta fito da sauri taje falo ta sami inna dasu saliha da Ameera nn ta saki fuska suka gaisa da saliha akasin Ameera da ta qi ko kallon gefen Rayyanat.

Inna ta kalli Rayyanat washe da baki tace"dama yanzu nake shirin kiranki kixo kici abinci sae ga su saliha sun shigo kinga sae kije ki d'ebo maku abincin kuci tare"

Rayyanat taje ta d'ebo masu abinci a qaton plate ,

fried rice ce da akayita ta da qoda tayi kyau sosai har ta gaji d'auke da paper chicken da aka d'ora a gefe.

A nn falon sukayi zaune zasu ci ,

saliha ta kalli Ameera wacce ta maida hnkli kan TV bata da niyyar tasowa suci abinci ,tace"Ameera taso muci abinci ke muke jira fa"da d'an mamaki Ameera ta kalli saliha snn ta nuna kanta da yatsa tace"ni d'in nn'sae kuma ta wani yamutse fuska tana kallon Rayyanat kmr wata abar qyama tace"kuci kawai ni a qoshe nake sae dai zuwa anjima ko zanci"kafin saliha tace komai inna tace"kinga bana son iya shege tashi kuje kici cikin taro ai yafi"

Wlh inna a qoshe nake sae dai zuwa anjima,ke kika sani cewar saliha wacce tuni ta fhmci dalilin da yasa Ameera taqi tasowa suci abincin.

Suna cikin cin abinci saliha ke cewa "yauwa Ameera idan mun qarasa cin abinci ina son muje ki rakani gidan su yaya munir gun safiyya na kar6o house wears d'ina sbd dai dai su nake son amin sabbin da za'a d'inka min"

Ameera tace"to gama d'in muje ko banza ina son naje naga safiyya"

Wlh kam safiyya nada qoqarin ziyartarmu"cewar saliha wacce ta kalli Rayyanat tace"tare fa zamuje dan ki hanzarta cin abinci naga sae ci kike kmr ba kya so"Rayyanat tayi murmushi tace"to so kike ina cin abinci sauri sauri naje har ya sarqe ni ai komai sannu a hnkli yafi"

Murmushi saliha tayi tana mai kallon Rayyanat tace"hakane amma kin fiye shiririta gun cin abincin naki in nice ma sae ya girshe ni kafin na qoshi, shiyasa nake sauri abuna sae na kammala cin abincin ina mai marmarin sa don nafi son haka,kema idan kika gwada yin haka zaki fi jin dad'i.

A sanyaye Rayyanat ta kalli saliha tace"har abada bana son sauya tsarin cin abinci na sbd haka na taso na sami Abbana yana ciyadda ni.

Tana kawowa nn hawaye suka sakko kan kumatun ta tayi saurin tashi ta bar gurin yayinda saliha ta bita da ido cike da tausayi.

Ameera ta ta6e baki tace"kukan name kuma ana zaune qalau? Ajiyar zuciya saliha ta sauke tace"bari kawai Ameera wlh Rayyanat abin tausayi ce dmn ta bani labarin rayuwarta ciki har da mutuwar mahaifinta da shi kad'ai ne gatan ta a duniya kinga dole tayi kuka a duk lokacin da ta tuna shi,Ameera ta wani ta6e baki tace" to Allah ji qan mamata"

Amin cewar saliha wacce ta tashi taje ta lallaso Rayyanat ta shiryo suka fito .

Ameera kam ganin da Rayyanat za a tafi tace ta fasa bata zuwa su dai gaida safiyya, ko kad'an saliha bata damu ba duk da ta fhmci dalilinta.

Inna suka je sukayiwa sallama suka fita ta bisu da Allah dawo daku lafiya.

Gidan ba nisa sosai dan qasa ma suka bi ,suna shiga gidan Rayyanat ta tsaya ta kasa shiga ba don komai ba sae don hango munir da tayi zai shiga mota,

sosai gabanta ya fad'i don ta rasa wane irin mutum ne shi da duk inda taje sae ta had'u dashi.

Saliha ce ta riqo hannunta tana fad'in"zo muje mana"

Haka Rayyanat ta dake tabi saliha sbd tasan idan ba gamo tayi ba ba zai gane taba tunda kullum cikin niqab yake ganinta.

Da sauri ta sadda kanta qasa ganin irin kallon da yake mata har ma ya fasa shiga mota ya nufo su yazo ya tsaya gab da ita,gam ta qara riqe saliha dmn ta gama yarda gamo tayi, saliha kuwa sae washe baki tayi tana kallon munir tace"yaya munir ina wuni? Fuskar sa wasai ya amsa mata har yana tmbyr ya su umma tace"duk suna lafiya.

nn taja Rayyanah zasu wuce, yayi saurin dakatar da ita kan cewa "ki shiga kawai qawar ki zata same ki daga baya"

da qyar saliha ta iya qwace hannunta daga na Rayyanat ta tafi ta barsu d'auke da murmushi a fuskarta.

Da hanzari Rayyanat ke qoqarin bin saliha munir yayi saurin shan gabanta yace"yau kam ba inda zaki sae kin saurareni"

Kuka kawai ta fashe masa dashi dan gabad'aya ta gama tsorata dashi.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

2/1/2017

🔮```16```🔮

Cikin muryar sa mai saka natsuwa ya shiga bata haquri har ta tsagaita kukanta da takeyi marar sauti.

Cikin kulawa ya kalleta da kyau snn yace"kin tsorata dani ko shiyasa kike kuka,ko kad'an baki da laifi a bisa tsoratar da kikayi sbd ban ta6a ganin fuskar ki ba amma yau ina ganin ki na gane kece ,

kin san sbd me na gane ki?

D'agowa tayi tana kallon shi ,

Shi kuma kmr wanda ke tsaye da er shekara shida yace"to yi min magana man sae na gaya miki"

A sanyaye tace"sae ka fad'a"

Murmushi yayi tare da nuna gefen zuciyar sa yace"ta nn na gane kece sbd duk lokacinda na gnki zaki tafi islamiyya bugun xuciyata ya kan canxa har sae kin 6acewa gani na,shiyasa nake tunanin idan na rasa ki ya zanyi dmn nasan zuciyata zata iya lalacewa ta bar jikina,da haka nake roqon ki kan dan Allah ki amince dani kinji.

Kallon sa tayi shaye da toka tace"kaga malam ni zan shiga ciki"

Sosai ya langwa6ar da kansa cike da son kora mata wani bayani tayi saurin girgiza kanta alamar bazata saurare shi ba ta kuma kama hnya ta bar gidan sae kiranta yake yana rarrashi kan ta dawo ya shigar da ita cikin gida amma fafau taqi tsayawa.

Tana isa gida dai dai ta kai tsakiyar falo sae kawai taji ta fashe da kukan da ta rasa dalilinsa ai kuwa da gudu ta shige d'akinta don bata son wani yaga tana kuka,sbd sam hnklinta bai bata ganin kowa a falon ba alhali kuwa Mohd da Ameera suna nn zaune.

Ameera ta kalli mohd da ya tsure qofar Rayyanat da kallo kmr mai wani nazari can ya maida duban sa ga Amira yace"ita wnn daga ina ta fito? ta6e baki tayi snn tace"gidan su yaya munir ta raka saliha ,saurin kallonta yayi jin gidan da ta ambata ita kuma ta qarasa da cewa"wata qil qauyanci ta nuna musu shiyasa suka koro ta"

Komai bai ce mata ba sae tashi yayi ya fita.

Rayyanat na cikin kukanta taji an turo qofa tayi saurin tashi ta share hawayenta ,saliha wacce ta shigo taxo gab da ita ta zauna ta riqo hannyenta cikin murya mai kama da ta rarrashi tace"haba Rayyanat meyasa kike ma yaya munir haka yace tsawon lokaci yake bibiyarki amma kinqi ki saurare shi,don Allah Rayyanat ki taimaki yaya munir wlh na fhmci mugun sonki yake ,Hawaye ne suka gangaro kan kumatun Rayyanat tace"saliha ki bawa yayanki haquri dmn tunda yaya anwar ya mutu na ajiye soyayya ba kuma zan qara ba ko banza ma bazan iya soyayya da mutumin birni ba ,meyasa zaki ce haka Rayyanat naga ko yaya anwar a labarin ki da kika bani shi d'an birni ne,eh amma shi asalinsa d'an qauyen mu ne nace maki ba tashin birni bane ,amma Rayyanat d'an birni da na qauya ai duk abu d'aya ne dmn duk Allah ya yisu'"um um ba d'aya bane saliha,akan me zaki ce haka? Sbd ba d'aya bane,ajiyar zuciya saliha ta sauke tana mai kallon Rayyanat tace"indai hali kike tunani to wlh yaya munir yana da halin kirki....a zahiri ba dmn baki san meye bad'inin sa ba"

amma kinji ance labarin zuciya a tambayi fuska "banda hali saliha ba kuma xaki gane dalilin da yasa na tsani d'an birni ba sae nn gaba,da mamaki saliha tace"tsana kuma,to wani abu d'an birni ya miki ne dmn naga a cikin labarinki anwar kad'ai ne d'an birni kuma kince lfy kuka rabu dashi asali ma in rashin mutnci ne ai d'an qauyen naku ya muku wato bala da yasa kuka koma daji da zama,ko kuma kin 6oye min wani abu a labarinki ne?idanuwan Rayyanat tap da qwallah take kallon saliha tace"Saliha ki daina min tambayoyi haka don Allah"

Saliha ta nisa tace "shike nn amma ga dukkan alamu ba duka kika gaya min labarinki ba"shiru Rayyanat tayi dmn tasan tabbas bata snr da saliha dalilin mutuwar Baffanta ba kawai dai tace mata ya rasu.

Tace"hm saliha ki yarda dani mana ni ban rage miki komai ba a labarina ba,kawai dai bana ra'ayin soyayya har da d'an qauyen ma dmn tunda yaya anwar ya mutu naji bazan iya soyayya da duk wani d'a namiji ba wnn alqawari ne nayiwa kaina dmn inaji idan na kula wani tmkr nayiwa yaya anwar butulce ne.

Hm Rayyanat kenan kina nufin haka zaki tabbata ba aure, d'an guntun murmushi Rayyanat tayi snn tace"To ce maki akayi rayuwar tawa tsawo ne da ita nida ma nake roqon Allah yasa rayuwata zata kai ga na cika burina" hm har akwai wani buri a gun 'ya mace da ya wuce aure? Kallonta kawai Rayyanat tayi ta kauda kanta,snn tace"inada wnn burin amma a da wato kafin yaya anwar ya mutu.

saliha tace"nidai Rayyanat al'amuranki na bani mamaki rayuwar ki idan mutum ya kalla kmr so simple n easy amma ashe in kika dake kan abu kin dake

kenan.

Ba hk bane saliha yaya anwar yana da matuqar muhimmancin da bazan iya kula kowa ba.

Cikin nuna 6acin rai saliha ta tashi tace"tunda haka kikace shikenan shi kuma yaya munir Allah ya bashi wacce ta fiki da komai ma"

Nn ta fito falo ta sami mohd zaune yana cin abinci ya tsare ta da ido kmr wani mai tuhumar ta,ta sadda kanta qasa tare da gaida shi snn tace da Ameera tashi muje gida ,nn ta tashi sukayi wa inna sallama zasu fita mohd ya kira saliha tare da zaro kud'i a aljihunsa,

saliha taxo cike da ladabi,

Ameera kuwa ta biyota cikin rawar kai ,

mohd ya dalla mata harara yace"bana son shisshiga fa ke na kira ko saliha"

kmr zata yi kuka tace"saliha"

Girgiza kansa kawai yayi had'e da d'an guntun tsaki don ko kad'an baya son hali irin na Ameera nn ya miqawa saliha two thousand a cewar suyi kud'in a daidaita tayi masa godiya suka wuce.

Bayan ya kammala cin abinci yaje d'akin inna zai mata sallama inna dake zaune tana lazimi tace"yauwa d'an albarka yanzu nake qoqarin tashi na same ka,sbd ina son zamu yi wata magana mai muhimmanci da kai,a natse man ya zauna kan gefen gadon inna yace"ina jinki inna".

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

3/1/2017

🔮```17```🔮

Muhammadu tafiya nake son zanyi a cikin satin nn zuwa qauyen mu dmn na jima rabona da zuwa shine nake son zan kai Rayyanah a can gidan ku har idan na dawo.

A natse mohd ya d'ago yana kallonta snn yace"shike nn inna amma kinyi magana dasu Abba kuwa.....Yo sae da izinin su zanyi tafiyar ne ko kuwa Rayyanah d'in ce baka son ta zauna gidan naku! Ba haka bane inna sanin dai nayi tafiyar ki idan kika yita sae wanda ya ganki,inna ta washe baki tace"ayyo ai muhammadu kasan en uwa dad'i ne dasu shiyasa nake d'an jimawa idan naje.

To inna wace rnr zaki tafi? Eh to rnr laraba nake son na tafi in Allah yaso,to Allah ya kaimu lokacin inna, Amin Amin d'an Albarka.

Tare suka fito shida inna ta nufi d'akin Rayyanat shi kuma ya fita daga gidan.

Zancen tafiyarta ne taje ta snr da Rayyanat ta fita ta bar Rayyanat cikin rashin jin dad'i da tunani sae take jin kmr kar inna tayi tafiyar nn ba don komai ba sae don sabon da tayi da inna.

Bayan kwana uku da faruwar haka cikin ikon Allah ynx munir ya fara shawo kan Rayyanat dan yanzu har tana d'an tsayi ta saurare shi.

Ko yauma tafe suke ta dawo daga islamiyya sae janta yake da fira ita dai iyakarta murmushi da kuma wasa da en yatsunta.

Har qofar gida ya rakota tana shiga gidan sae ga Muhummad ya fito zai tafi masallaci dan har an fara kirayen kirayen sllr magrib.

Cikin sakin fuska munir ya miqa masa hannu suka gaisa inda shaye da toka man ya zare hannun sa daga na munir ya wuce, munir ya bisa da murmushi dmn inda sabo ya saba da halin abokin nasa.

munir yaje ya nemi buta yayi arwala ya shiga masallaci sbd dama masallacin kusa da gidan yake .

Rayyanat kuwa tana shiga gida ta cire hijab, niqab da socks, ta jawo er akwatin ta da inna ta saya mata,ta ciro kayanta a wardrobe tana tsarawa da yake fashin sallah take shiyasa bata yi zancen sallah ba.

Komai da tasan zata buqata sae da ta zuba a ciki snn tayi zaune tana tunanin yanda zata yi rayuwa a gidan su man ,

sae roqon Allah take a ranta kan Allah yasa 6angaren su saliha zata zauna in hkne kam da sauqi.

Guraren qarfe takwas da rabi zaune suke a falo ita da inna suna cin abinci suna kallo inna tace"Rayyanah ina ce kin harhad'a kayanki dan kinsan na gaya miki sammako zanyi shiyasa ma na sallami baaba hurera tun yau, eh inna na harhad'a komai tun d'azun, tayi mgnr ne a sanyaye,inna kuwa ta washe haqora tace"to Allah miki albarka 'yannan idan kinje ki sakin jikin ki sosai don tamkar gidan ku ne kinji, Rayyanat ta gyad'a kanta wanda yayi dai dai da shigowar nasir d'auke da sallama a bakin shi,

inna ce ta amsa masa sallama, Rayyanat kuwa ta gaida shi cikin ladabi snn ta d'auki kwanon tuwonta ta shiga daga ciki.

Nasir kuwa bayan ya amsa gaisuwar Rayyanat ya gaida inna wacce ta amsa gaisuwar washe da baki snn tace"ka dai ji zancen tafiyar tamu yanda na snr da kai a waya ko, eh inna inshaAllah tunda sassafe zaki ganni,tace "amma fa ina son sae mun sauke Rayyanah a gidan naku, eh inna ai duk kin snr dani hk a waya.

To ya jikin Fatima da sauqi dai ko, wlh Alhmdlh inna taji sauqi sosai don harma tana cin abinci yanxu, to madallah Allah ya nuna mana ta sauke abinda ke cikin cikinta lafiya ,Amin amin inna.

Daga haka suka ta6a er fira ,

guraren tara da rabi snn ya wuce.

Washe gari tun da safe nasir yazo ya kwashi inna da Rayyanah suka tafi gidan nasu, inna taje kowane 6angare ta musu bankwana wacce duk 6angaren da taje tana riqe da hannun Rayyanah har saida tazo gun mota zata shiga snn ta saki hannun Rayyant tana mata sae ta dawo.

Su inna na wucewa Rayyanh ta ajiye kuka amma marar sauti,mohd dake tsaye sae kallonta yake don ya fahimci ba qaramar shagwa6a Rayyant zata yi ba.

Shida kanshi ya ja mata akwatin ta suka tafi 6angaren su,yana tafe Rayyant na bayanshi har suka tafi d'akin Ameera,sae da ya kalli Rayyanat ganin har lokacin kuka take snn ya kai hannu a hnkli ya fara qwanqwasa qofar.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

4/1/2017

🔮```18```🔮

Ya jima yana knocking snn aka bud'e qofar,wani mugun kallo ya watsa ma Ameera wacce ta fito cike da jin bacci sae miqa take ,tayi saurin daina miqar ganin kallonda yayanta ke mata, kmr da tsoro tace"yi haquri yaya ina bacci koda kake ta qwanqwasa min,bai ce da ita komai ba sae akwatin Rayyanat ya miqa mata tare da fad'in"ki ware mata gurin da zata saka kayanta a nn zata zauna har sae inna ta dawo.

Ba musu ta kar6i akwatin ta shigar da ita mohd kuwa ba tare da ya kalli Rynt ba yace"shiga daga ciki idan kika buqaci wani abu ki snr da ita Ameeran, daga haka ya wuce ita kuma tasa qafa zata shiga dai dai Ameera zata fito sae qunquni take ta bangaji rynt da qarfi har sae da ta nemi fad'uwa bata damu ba don dama da niya tayi snn tayi ficewarta sae d'akin hjyr su.

Ta shiga cikin kuka mai d'auke da shagwa6a tace"umma wlh ni bazan iya rayuwa da wnn yrnyr a d'aki d'aya ba, xaro ido Umma tayi tace"au wai a 6angaren nn zata zauna?eh yaya ne ya kawota wae har sae inna ta dawo daga qauye,ta qarashe mgnr cikin muryar kuka sosai snn ta d'ora da cewa"gsky umma ni d'akin masu aiki zan maida ta dn tafi cancanta a can"Umma ta nisa tace"kinsan hln yayanki ko dukan ki zai iyayi akan haka dn yafi son duk inda ya ajiye abu to yazo ya same sa a nn"uhm uhm umma dan Allah nidai ki masa magana ya sauya mata wani d'akin ai akwai d'akunan baqi ma,to shike nn zan masa magana,nn Ameera ta fita tana mai share qwallah.

Tana zuwa d'aki ta sami Rynt tsaye riqe da akwatin ta ,ta kalle ta a wulaqance snn tace" fita waje ki jira yaya zai zo ya baki wani d'akin, ba musu Rynt taja akwatin ta ta fita don sae ftr take ma a sauya mata 6angaren gabad'aya.

Ta jima tsaye a bakin qofar Ameera kuwa tuni ta shige blanket ta koma bacci.

Ganin ta gaji da tsayuwa yasa ta rage tsawonta bata jima da haka ba sae ga man ya shigo 6angaren cikin shirin sa na fita aiki yayi tsaye da mamaki yana kallonta snn yace"ke ba cewa nayi ki shiga ciki ba shine sbd qauyanci kika yiwa mutane durqushe a bakin qofa!shaye da toka ta d'ago tana kallon sa snn tace"to ai bayan na shiga wnn qanwar taka tace wai na fito zaka canza min d'aki"

Komai bai ce mata ba sae kutsa kai yayi ya shiga d'akin sae ihun Ameera taji ta fito aguje tana kuka awa wacce aka fasawa kai wanda hkn yasa iyayensu suka fito a rud'e ,

ta tafi da gudu jikin umma tana kuka Abbansu yace" lfy me yake faruwa ?Abba yaya ne ya mareni ban masa komai ba, Abba ya kalli mohd da ya fito yace"me Ameera ta maka ne wae? Abba kunfa san hln Ameera ta iya wa mutum qarya da fad'ar abinda ba'ayi ba,shine wae yau har abin ya fara kawowa kaina!nn ya matsa gab da Ameera kmr wanda zai bugota yace"yaushe nayi dake zan canza mata d'aki!dake nake magana ki bani amsa koni sa'anki ne! a razane tace"yi haquri yaya wlh qarya na mata baka yi dani haka ba.....er iska yrny wlh duk rnr da kika qara fad'ar abinda bance ba sae nayi maganinki fiye da na yau, daga haka ya wuce kmr wanda zai tashi sama.

Abba ya sauke ajiyar zuciya yace da Rynt shiga ki ajiye kayanki.

Umma kuwa taja Ameera suka tafi d'aki sae fad'a take mata tana fad'in keda nace zan masa magana me kuma ya kaiki yin haka gashi ynx kin 6arar da komai don yanzu dole ki zauna da ita d'aki d'aya ba kuwa zan nema maki alfarmar sa ba, Ameera dai sae kuka take bata ce komai ba don tasan ta riga da ta jama kanta.

Rayyanat na shiga d'akin ta nemi guri ta ajiye akwatin ta snn ta kalli agogon bangon da ke d'akin qarfe tara da rabi time d'in islamiyya ya tafi don ta makara sae dai zuwa yamma sae duk bata ji dad'i ba hkn yasa ta ciro littafanta tana mita.

Kwana Rynt hud'u a gidan kullum sae Ameera ta nemi tayi fad'a da ita amma tana basarwa duk da tana jin zafin abubuwan da take mata kuwa.

Haka kwata kwata hjy bata sakar mata fuska ko gaisuwa da qyar take amsa mata sauqinta d'aya saliha na zowa suyita fira abinsu snn duk zata je islamiyya Abba ke bata kud'in napep.

Sae dai babbar matsalarta shine abinci wanda sae da kulawar Abba ake kawo mata abinci idan bai kula ba haka zasu barta da yunwa,mohd kuwa kmr ma baya garin don tun daga rnr bata qara ganin sa ba.

Cikin shirin ta tsaf na islamiyya ta fito ta sami Abba zaune a falo ta durqusa har qasa ta gaida shi cike da ladabi ,ya amsa mata cikin sakin fuska tare da zaro dubu d'aya a aljihu zai bata ta girgiza kanta snn ta qara sadda kanta qasa tace"Abba ai kullum kud'in da kake bani sunyi yawa har ma ynx akwai canjin da zasu kaini yau da gobe, dad'i Abba yaji har ransa ba don komai ba sae don halayen Rynt dake matuqar birge shi,yace"to shike nn tashi ki tafi Allah yayi miki albarka"

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮

```Na Billy giro😊```

5/1/2017

🔮```19```🔮

Cikin yanayi najin kunya tace"amin Abba ngde snn ta tashi ta fita ,Abba ya bita da kallo d'auke da murmushi a fskrsa.

6:15pm

Rynt ce tsaye tana kallon rayuwar 'ya da mahaifi mai cike da ban sha'awa rayuwar su kmr rayuwar ta da Baffanta,a kullum sae ya rako ersa safe da yamma kuma idan aka tashi zata samu yazo yana jiran er tashi, da qafa suke zowa kuma da qafa suke komawa sbd ba wani jayawa da inda yake fitowa,sak yrnyr zata iya maida kanta gida amma so irin na 'ya da mahaifi kesa kullum yake zowa d'aukar er shi,hkn ba qaramin tuna mata rayuwarta da baffanta suke yi ba,sbd itama haka Baffanta ke mata a lokacin da take primary mkrntr ba wani nisa da gidansu amma kullum baffanta sae ya rakata haka kuma duk aka tashi zata samu yazo yana jiranta su koma gida.

Baffa shine sunan da yrnyr ke kiran Abbanta dashi hkn ke dawo ma Rynt da ryuwar ta sabuwa fil,shiyasa kullum bata da aiki sae na kuka idan tana kallon rayuwar su.

Ko yanzu hawaye ne suka silalo a hnkli kan kumatunta ta kai hnnu a cikin niqab d'inta ta share hawayen yayinda take magana a ranta cewa

_"Bazan yafe maka ba ba kuma zan ta6a barin ka ba, ka yanke min farin cikin rayuwata haka nima zanyi silar yanke taka"_

"Rynt"cewar munir wanda yazo gab da ita ya tsaya har tana jiyo qamshin turaren shi, bata kalle sa ba sbd lokacin wasu hawaye ne ke faman zarya kan kumatun ta,duk

da cewa da niqabi sanye a fuskarta sae take ganin kmr zai iya hangowa idan ta kalle shi.

A hakan ta gaida shi ya amsa yana mai kallon gefen da take kallo wato 'ya da mahaifi da sukayi er nisa a tafiyar su, ya nisa tare da fad'in"dama na jima ina son nayi miki wata tamvaya Rynt, meyasa kullum sae na ganki kina kallon mutanen nn shin kin san su ne? Cikin sanyin murya tace"ko d'aya haka kawai suke bani sha'wa"

Gama fad'ar hk takai hannu zata tsaida napep yayi saurin dakatar da ita ta hnyr cewa"dan Allah Rynt yau ki barni na kaiki gida kinji"Aa wlh ka barashi kawai ngde"pls Rynt baki san yanda nakeji ba wlh sam bana son ganin kina shiga napep bayan ni inada abinda zan riqa kaiki gida"um um nidai ka barshi nagode"

daga hk ta shige napep ta barshi.

Tana isa gida ta samu sae lokacin malamin su saliha ya tashe su sbd su a cikin gida ake karantar dasu.

Sae da ta d'an gyra fuskarta sbd har lokacin kuka take,snn ta cire niqab sae kawai sukayi ido hud'u da malamin su saliha zai fita,ga mamakinta kallonta yake har sae da ta gaishe shi snn ya kauda idonsa,ta maida dubanta gun saliha wacce ta qaraso gurinta sake da fuska Rynt tace"wae ku sae yanzu aka tashe ku?eh wlh kedai makara yayi bai zo da wuri ba,Rynt tace"wae nikam meyasa Abba bazai barku ku riqa zuwa isalimiyya ba don kmr hkn zai fi..... Mtsw!Ameera da ta biyo zata wuce taja wani dogon tsaki tana mai hararar Rynt kmr idanuwanta zasu fad'o tace"to wacce ta san dai dai ai sae kije da kanki ki snr da Abban namu abinda yake dai dai tunda shi bai sani ba, banxa er qauye mai banzar rayuwa!mtsw ta koma jan wani tsaki ta wuce.

Ita dai Rynt kallonta kawai tayi saliha tace"don Allah kiyi haquri haka hln Ameera yake kowa bata gani da gashi,murmushi Rynt tayi snn tace"nikam ko kad'an banji zafi ba wlh,nn dai saliha ta qara bata haquri snn kowa ta kama gabanta.

Rynt na shiga ciki ta had'u da Abba ya fito zai tafi masallaci tayi saurin durqusawa har qasa ta gaida shi, fuskar sa wasae ya amsa mata snn yace"Rynt an dawo daga islamiya?

Can murya qasa mai d'auke da tsantsar ladabi tace"eh Abba"

yace"to Allah taimaka tashi ki shiga daga ciki kiyi sallah ki kuma sami abinda kika ci kafin dinner kinji"tace

"to Abba" snn ta tashi ta wuce shi kuma ya wuce masallaci.

Yau satin inna d'aya da zuwa qauye.

A washe garin rnr ba islamiya sbd rnr alhamis ce Rynt ta shiga cikin en aikin gidan tana taya su aiki.

Abba ne ya fito ya same ta tana goge kan dining tana ganinsa ta durqusa ta gaida shi ya amsa

Yana mai kallon yanda idanuwanta suka kumbura yace"lfy Rynt me ya sami idanuwanki? Sadda kanta qasa tayi don dai baza ta iya cemai kuka tayi ba,sae dai ta gaya mai abinda tayi bayan kukan tace"Abba kwana nayi ina karatu"

Hln kun kusa fara jarabawa ne?Aa hardar qur'ani nakeyi,

Abba ya jinjina kansa snn yace"haqiqa kinyi dabara Allah ya qara miki kaifin baseera"

cikin sanyin murya tace"amin Abba nagode"

Yace "to ya naga kina aiki saki akayi ?Aa ina taya su ne kawai,to idan dai kinji kin gaji kar ki tilasta kanki ga qarasa aikin ki komawar ki kiyi zamanki kinji.

Gyad'a masa kai tayi yayinda ya ciro wyrsa a aljihu dake faman ruri ya d'aga ya tafi,Rnyt kuwa taci gaba da nata aiki.

umma ce a d'aki ita da Ameera yayinda umma ke matsawa Ameera kan ta tashi taje ta gyarawa mohd 6angarensa sbd yau zai dawo,cikin kukan shagwa6a tace"wlh umma kinsan halin yaya duk yanda aka gyra masa guri sae yayi fad'a wae bai yi ba, au kinsan dai baya son en aiki su gyra masa d'aki ko,ko kuma ni kike son naje na gyara masa? Aa umma ga wnn yrnyr mana mai baqin son aiki tana can yanzu haka tana taya su sahura aiki, don Allah umma kice taje ta gyara masa, to shikenan naji jeki snr da ita ki kuma nuna mata 6angaren snn ki dawo.

Sosai 6angaren ya matuqar birge Rynt har ganin take kaf gidan ba inda yakai 6angaren mohd kyau .

Sae da ta gama qauyancinta snn ta gyra dak'in tsaf har bathroom ta kuma feshe d'akin da room fresh kala kala da ta samu kan dressing mirro d'insa.

Bayan tayi wanka taci abinci ta tafi 6angaren su saliha ta sami umman saliha zaune a falo saliha na cire mata qumba, ta gaishe ta cikin ladabi yayinda mamar ta amsa cikin sakin fuska har tana cewa"er halak kmr kinsan zancen ki muke ina fad'in yau dai shiru saliha bata je ba baki shigo ba, Rynt tai murmushi tace"wlh mama na d'anyi wani aiki ne"

to sannu ,zaki iya zuwa kasuwa yau kuwa saliha ce ta matsa min wae tana son ku siyo inner wears da kayan kwalliya nace ta bari na bayar a siyo muku tace ita tafi son kuje da kanku, ta gefen ido Rynt ke kallon saliha dake faman roqonta kan tace eh, dako d'an murmushinta tace"eh mama xan iya"

To shike nn kuje ku rubuto duk abinda kuke so se kuxo na baku kud'i...a'a mama ki bamu kud'i kawai in munje zamu ga abinda muke so ai, Aa saliha nafi son ku rubuta sae na baku kud'in enuf, amma fa kar a manta da er autata ita ma a siyo mata nata, "to shike nn mama ai baza mu manta ta ta ba"nn taja hannun Rynt tace "muje ko"

Bayan sun shiga ne saliha ke cewa"Rynt ni kuwa wane aiki ne kikayi da duk yawan en aikin gidan baza suyi ba sae ke?hm na gyarawa yayanku d'akinsa ne wae zai dawo....cabd'i Allah ya cece ki da masifar sa, Rynt ta zaro ido tace"me?saliha tace "ba wani abu bane fa shidai matsalar sa d'aya duk yanda aka gyara masa d'aki sae yace bai yi ba yayita masifa kuwa.

Hm ni ba masifar sa ba ma ,zagin da yake yi ne bana so don wlh na tsani a zagar min uba ,"shi kuma yanada wnn"

cewar saliha snn tace" sae dai kiyi haquri don muma wlh haka yake zagin mu in ya tashi masifar sa.

Cikin muryar kuka Rynt tace"Ai gwanda ku naku iyayen suna raye ba zafi kmr ni da basa raye"

Saliha tace "haba Rynt meye na kuka kuma

"Baffa"cewar Rynt wacce ta rungume saliha tana kuka tace"saliha wlh ina mutuwar son baffana amma an raba ni dashi zama d'aya, ba a barni da zafin ba ana kuma zagar min shi"

Saliha tace"kiyi haquri Rynt haka mutuwa take bata barin wani don wani....

_shiyasa nima Bazan bar wanda ya kashe min shi ba koshi waye_

Haka Rynt ta fad'a a ranta yayinda saliha taci gaba da cewa"shi kuma yaya dake zagin ki ai kansa ya zaga ba kowa ba"

Nn ta samu ta rarrashe ta har ta daina kuka,snn ta rubuta abinda suke so ta kaiwa mama ta basu kud'i suka tafi kasuwa.

Guraren qarfe 3 mohd ya dawo shi kad'ai ba tare da kowa ba.

6angaren sa ya nufa yana bud'e 6angaren wani qamshin dad'i ya daki hancinsa ya kuma ga komai tas tas very neat ba kmr yanda ake gyra masa d'aki ba, dmn har bathroom ya duba bai ga matsalar komai ba sae ma wani qyalli da yake ,

ya fito ya durqusa tare da d'ora d'an yatsansa akan tiles ya shafo ba wani datti,

har ransa yaji dad'in gyaran ya kuma qudiri kyauta ga wanda yayi gyaran,don yauce rnr farko da ya ta6a samun d'akin sa hundred percent .

Sae bayan qarfe hud'u su Rynt suka shigo 6angaren su Ameera wad'an da dama tuni sun dawo da kasuwa suna can 6angaren su saliha zamansu.

Mohd suka samu jingine a jikin motar sa yana waya wanda kallo d'aya zaka yi masa kasan da masoyiyar sa yake waya.

Gaida shi sukayi ya d'aga musu hannu kawai, bayan sun d'an wuce saliha ke cewa"waeh!na miki murna kin huta da bala'in sa yau"

Cikin rashin fahimta Rynt tace" ko meyasa"sbd yana waya ne da masoyiyar sa Anti malika

da yake mutuwar so,wacce baya samun suyi waya kullum sbd aikinsa da kuma yanayin karatun ta shiyasa duk rnr da yayi waya da ita tofa bazai yi masifa a rnr ba,,Rynt ta girgiza kanta tare da fad'in"hm mugun gaye ashe yana soyayya har wae ma kuka sani"

tayi mgnr ne a ranta ashe ta fito

Har Saliha ke cewa"wa! ai ba wanda ya sani koni qanwarta qawata ce sosai a school shiyasa na san komai,dmn ma akanta yayi tafiyar nn zuwa UK don tayata murnar kammala karatun ta shine ya jirata suka dawo tare wanda inshaAllah mun kusa shan biki sbd tuni ita yake jira.

"Yayi Allah taimaka" cewar Rynt kafin take cewa

_"abin tausayi malika rnr aure mijinki gawa"_

Basu jima da shiga ba mohd ya shigo ya sami Ameera na saukowa ta fito daga d'akin umma yace"ke wa ya gyra min 6angarena "cikin inna inna na jin tsoron sa tace"bani bace wlh wnn yrnyr ce Rynt"

je kiramin ita"

ta tafi sae dad'i take ji yau kam fad'an bazai qare kanta ba.

Rynt ta fito sanye da qaton hijab d'inta har qasa ,

ta same shi zaune kan dining har ya fara cin abinci.

Taje kawai tayi masa tsaye tare da kauda kanta gefe ,ya d'ago fuskar sa a hnkli yana kallonta snn yace"kece kika gyra min d'akina wae?a taqaice tace"eh"

Ya ta6e baki yace"hm abun mamaki a qauyen naku ke ke gyarawa sarkin garin ku d'aki ne?eh har ma da sarkin kd duk ni ke gyara musu d'aki,da sauri ya kalleta sbd su asalin en kd ne yasan agun inna taji, baqa ta masa kenan,yace"ke ina wasa dake ne? um um kaidai ka nemi na maka haka amma ni ba halina bane raina wanda ya kama girmansa,d'an fari da ido yayi sae kuma yayi murmushi yace"to naji a wuce gun ga wnn ladan gyara min 6angare na da kikayi,Rynt ta kalli kud'in da ya ajiye gabanta zasuyi 20k tace"nayi dan Allah ne ba don wani abu ba"

Eh na sani ai kyauta ce na baki.... Kyautar ce bana so ,ya d'ago da d'an mamakinsa sae kuma ya basar yace"to me kike so? Har tayi niyyar saka mai wata maganar sae kuma ta fasa ,tace"waya nake son nayi da inna"

Ga mamakinta sae ya ciro waya a aljihunsa ya kira mata inna ya bata, bata san lokacinda murmushi ya su6uce mata ba ta kar6i wyr ta kwasa da gudu zuwa d'aki, mohd kuwa binta yayi da shu'umin murushi yayinda a ransa yake mamakin raina sa da tayi.

Duk abin nn da suke Abba na kallon su sae ya musu wata fahimta ta daban wacce tasa yaji dad'i har ransa,

da saukowa zai yi amma ya fasa ya juya zuwa d'akin umma ,

ganin yanda yake murmushi yasa ita ma ta shiga murmushi tace"yadai Alhj?

Sai da ya zauna snn yace"zauna tukun"

nn kusa dashi ta xauna.

Yayi gyran murya snn ya fara da cewa" haqiqa tun zuwan Rynt a gidan nn na yaba da hnklnta da kuma natsuwarta har hakan yasa na kwad'aitu da son ace ta zamo cikin wnn family namu ma'ana ta kasance suruka a gidan nn mata ga mohd.

Billy giro😊

🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮

[2:43PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA! ```🔮

_1/06/2017_

🔮🔮🔮

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.