Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx
Chapter 42 of 56
*page 80*
Basu kai koina ba sae gashi sun dawo Ryynt ta fito da sauri ta shiga cikin gida jim kad'an ta fito riqe da wayar ta a hannun ta wacce ta manta da ita a d'akin inna.
Taje zata bud'e gambun mota knn sae saukar ball taji tim a kan cikin ta, a tsorace ta fasa ihu ,yayinda mohd ya fito motar a fusace ya nufi yaron da ya jefo ball d'in cike da niyar kai masa mari Ryynt tayi saurin zuwa ta riqe masa hannu tace"Mk dan Allah kayi haquri yaro ne fa"
Yace"dan ubansa ko yaro ne kan me zae jefo ball akan cikin ki ko kuma shi abinda ke cikin ki ba rayuwa bane!
Yi haquri dae dan Allah tun da kaga bada gayya bane.
Mohd dake kallon yaron rae 6ace yace"oya duqa ciro ball d'inka a qarqashin mota ta ko kuma wlh na taka ta na wuce"
A tsorace yaron ya duqa ya ciro ball d'in sa zae wuce man ya bisa da ido yace"kae xo nn"
Jiki sanyaye yaron ya juya,
mohd yace"wa na gani ya fito a qarqashin mota ta d'azun?
Yaron ya sadda kansa qasa yace"nine"
Mohd yace"uban me kamin a qarqashin motar to?
Yaron yace"ball d'ina ne da ya gangara na d'akko"
Mohd ya kalli Ryynt yace"u see kince bada gayya bane bayan wnn ne karo na biyu koma fiye dmn muna fitowa naga lokacinda ya fito a qarqashin motar da sauri ya fice shiyasa sam ban cika son barin mota na a waje ba dan irin yaran nn marassa ji sae su maka 6arna a banza,bari kaji idan na qara ganin kana ball a guraren gidan nn wlh sae nayi maganin ka,oya tafi in daina ganin ka a nn very stupid!
Sim sim yaron ya bar gurin.
Ryynt ta kalli man tace"dan Allah ka rage yawan fad'an nn bana so wlh"
Mohd yace"Ryynt nasan yaron baya ji wlh ko kad'an,
musamman yake da filin ball a cikin gidan su banga uban me yasa ya fito yana ball a waje ba har yake qoqarin hallaka min ke da babyna ,
wlh gwara ma ace motar ce ya daka glass d'in motar ya fashe kan ya doka min ke .
Tace" to yi haquri dae dan Allah ya wuce.
Yayi murmushi had'e da jan hancinta yace"ni a gurina bae wuce ba sae naga lafiyar babyna tukun"
Tayi murmushi yayinda yaja hannunta suka shiga mota yakai hannu ya yaye rigarta yana shafa cikin yace"ya kika ji a lokacinda qwallor ta dake ki?
Tace"naji zafin saukar ball d'in ba sosai ba na kuma tsorata don har sae da abinda ke ciki ya motsa.
yace"da qarfi sosai ya motsa ko kuwa?
Tace"da qarfi ba sosai ba"
Man yayi shiru yana kallon ta can yace"Ryynt ya zama dole muje asibiti nayi scanning dmn naga lafiyar babyna"
Ryynt tace"plz Mk ba sae ka duba ba inshaa Allah ba wata matsala"
A natse ya girgiza kansa yace"No Ryynt abinda zaki d'auka ba matsala ba shi zae zo ya zama matsala kuma hankalina zae fi kwanciya idan na duba kiyi haquri muje kinji baza mu wani jima ba"
Ta gyad'a masa kai snn yaja motor suka tafi sae asibitin shi.
Kan hanyar su ta dawowa daga asibitin ne Ryynt ke kallon man wacce gabad'aya jikinta a sanyaye tace"mk nifa na tsorata don sae naga kmr yara har uku a cikina"
Saurin kallon ta yayi don sae da fa yace ta rufe idonta ashe ta bud'e bae sani ba,bae dai ce mata komai ba yayi d'an guntun murmushi yace"Ryynt knn kije ina da yara har uku photon ne kawae ya rarrabu"
Ajiyar zuciya ta sauke tace"ai ni har na soma shiga tension wlh"
Yace"tension name dan Allah ya baki babbar kyauta.
Tace"um um wlh ni ko biyu ne bazan iya ba bare uku"
Yace"to idan Allah ya baki fa sae kiyi yaya?
Tace"hm nima ban sani ba amma na tabbatar cikin da kanshi zae zube kan tsananin tashin hankalin da zan shiga"
Mohd yayi murmushi kawae ba tare da yace komai ba yaci gaba da jan mota.
Suna isa family house basu zarce koina ba sae 6angaren iyayen sa.
Basu sami kowa a falon ba mohd ya umarce Ryynt da ta zauna bayan ta zauna ya haura sama jim kad'an sae gashi ya fito shida mahaifiyar sa da suka qaraso Ryynt ta zame kan kujera ta russuna cike da ladabi tana gaida ta.
Ba yabo ba fallasa mahaifiyar sa ta amsa mata har tana tamvayar ta ya hanya tace"Alhmdllh"
Mohd yace"Abba fa ko har yayi tafiyar dan jiya da na shigo gaida shi naji yana waya kan cewa zae je abuja"
Tace" Aa bae tafi ba tukun sae gobe yanzu haka yana d'akin shi bari naje na dubo maku shi.
Nan ta tafi zuwa sama mohd ya kalli Ryynt wacce ke durqushe still bata koma kan kujera ta zauna ba sae zama tayi a takure nn qasa gun gefen kujera.
Yace"Ryynt koma mana kan kujera ki zauna kin wani takura kanki haka sae kace kinxo baqon guri"
Tace"um um barni a nn kawai ya isa"
Bai ce komai ba sae hannun ta ya riqo zae maida ta kan kujera tayi saurin qwace hannun cike da jin kunya sbd Abba da ta hango tafe shida umma.
Mohd da bai gansu ba yaje zae sake riqo hannunta tayi mai wani kallo na alamar ga fa su Abba nn tafe suna kallon mu.
Nan ya juya had'e da d'an sosa bayan kansa alamar jin kunya suna qarasowa ya durqusa cike da ladabi yana gaida Abba,Abba ya amsa snn ya kalli Ryynt wacce tayi qasa da kanta tana gaida shi ya amsa d'auke da murmushi a fuskar sa yana tamvayar ta ya hanya tace"Alhmdlh"
Bayan sun gama gaisawar ne Abba ya koma daga ciki umma ta kira mai aikin ta ta kawo musu ruwa da lemu da kuma abun motsa baki.
Umma da kanta ta zubawa Ryynt lemu a cup ta bata ta kar6a ta samu da qyar ta kur6a kad'an ta ajiye don gabad'aya kunyar hjyr take ji gashi sae kallon ta take.
Kuma su biyu ne kawae zaune a falon sbd mohd ana kawo masu ruwa da lemu aka kirasa a waya ya fita.
Hjyr mohd kuwa tana kallon Ryynt ne sbd ganin yanda Ryynt ta canza tayi kyau klr ta ta koma kmr tashin er abuja ga natsuwa sae duk taji ta soma son Ryynt sosai a ranta,nn ta tsinkayo muryar Ryynt na tambayar Ameera fa.
Allah sarki taga dae ko kad'an Ameera bata ta6a nuna mata so ba amma kuma har take tamvayar ta ai kuwa sae taji ta qara sonta,
ta sakar mata murmushi tace"Ae Ameera na can gidan pretty,pretty taje da ita dmn ta samu ta riqa rage mata wani aikin kafin hutun makarantar su ya qare.
Ryynt da kanta ke qasa tayi d'an guntun murmushi tace"Allah sarki"
daga hk tayi shiru bata sake cewa komai ba .
Sae ga mohd ya dawo yace"umma bari muje other parts mu gaida su"
Tace"to sae kun dawo"
Nan Ryynt ta tashi suka tafi.
Sae da suka tafi d'ayan 6angaren snn suka je 6angaren su saliha.
Da murna sosai umman saliha ta tarbe su yayinda man da Ryynt suka gaida ta ta amsa musu cikin sakin fuska tana tambayar su ya hanya suka ce Alhmdlh nn Ryynt ta wuce d'akin saliha ta bar mohd suna qara gaisawa da umman saliha.
Ryynt na shiga d'akin saliha tayi tsaye tana kallon saliha dake chat tana qyalqyatar dariya.
Ryynt ta girgiza kanta taje ta zauna kusa da ita tana fad'in"keda waye haka?
Da sauri saliha ta kalli Ryynt tace"yaushe kika shigo har kika zauna ban ko ji ba?
Ryynt tace"hm inafa zaki ji hankalin ki na gun chat.
Saliha ta tashi zaune tare da fad'in"wlh kedai wata qawata ce er ban dariya keta sani dariya har cikina yayi ciwo wlh.
Ryynt tayi murmushi tare da ajiye jakar hannun ta saliha da ta kafe ta da ido tace"waih barikallah yau sae kika qara yin kyau sosai wlh har dae pink lipstick d'in nn da kika shafa kan d'an mitsilin bakin nn naki mae matuqar kyau kmr na qwace maki shi na gudu.
Da wasa Ryynt ta harare ta had'e da turo baki tace"kin fara koh saliha?
Saliha tace"to ae gsky na fad'a ina kika samo kalo d'in nn da na jima ina neman irinta bana samu daga dark sae mae haske sosai nake samu,
Ryynt tace"wlh a dubai kedai na siyo wata er kit ta cosmetics ciki sae ki samu komai da kike so,kema taki na nn na siyo miki ae"
Ihun murna saliha tayi tare da rungume Ryynt tace"kai amma wlh naji dad'i na kuma gode"
"oyoyo Aunty!
cewar mami wacce ta shigo da gudu, Ryynt ta d'auke ta cike da murna ta d'aura ta kan qafafunta.
Umman saliha da suka shigo tare da mami tace"Ah sauketa kar ta zunguren min d'an jika"
Sosai Ryynt taji kunya tayi saurin sadda kanta qasa tana murmushi .
Umman saliha da ita ma murmushin take taje zuwa sauke mami,mami ta qanqame Ryynt tace"um um mama nifa ba inda zanje tare zamu koma nida Aunty idan zata tafi"
Umman saliha tace" mami nafa gaya miki baza ki koma ba gwanda tun wuri ki fidda ranki"
Ryynt ta d'ago ta kalli umman saliha tace"meyasa mama?
Umman saliha tace"Ryynt takuraku kawae zata yi dan yanzu ba d'aya bane da wancan lokacin kawae dae zan riqa barin ta tana zuwar miki ko weekend ne.
cikin fushi mami tace"wlh mama ban so"nn ta sauka kan jikin Ryynt ta fita daga d'akin cikin kukan shagwa6a.
Umman saliha ta bita da ido d'auke da dariya a fuskarta,Ryynt kuwa ta qwala mata kira a cewar tazo umma wasa take mata amma mami taqi dawowa.
umman saliha ta kalli saliha da ke bin mami da kira itama, tace"kinga tashi je kawo ma Ryynt lemu da ruwa ae kinsan mami in ta fara fushi ba rarrashi take ji ba dan kanta zata sauko ta dawo.
Ba musu saliha ta tashi ta fita umman saliha ta kalli Ryynt tace" gobe ne zaki koma koh?
Ryynt tace"eh inshaa Allah mama"
Umman saliha tace"dama wasu turarukka ne nasa aka sake had'a miki dan nasan wad'an can sun isa qarewa koh?
Tace"Aa mama akwae saura,
Tace" to indae kin tashi zan baki ki tafi dasu .
Cike da jin dad'i Ryynt ta mata godiya don sosai take son turarukkan har dae yanda ta fahimci mohd na jin dad'in qamshin turarukkan ba kad'an ba.
8:30pm
Sae a lokacin zasu koma.
Mohd ya kalli Ryynt wacce ta shigo mota fuskar ta d'auke da damuwa yayi shiru yana kallonta shidai a sanin sa hjyr sa ta fara sake mata bare yayi tunanin ko ita ce ta mata wani abu bare kuma duk yinin nn a 6angaren su saliha tayi shi.
Hannun ta ya riqo ta kalle sa yace"me aka miki?
Cikin muryar kuka tace"umman saliha ce tace wae baza ta bar mami ta koma gurina ba sae dae kawae ta riqa zuwar min weekend da farko na d'auka wasa take ashe da gske take yi yanzu haka mami na can sae kuka take"
Mohd yace"to ae sae gobe ne ko zaki koma koh?
Tace"eh shine da zan fito nace gobe a shirya wa mami kayanta idan zan koma zan biyo mu d'auke ta a nn take gazgata min cewa itafa da gaske ne mami bazata koma ba"
Yace"meyasa ko kin ta6a yiwa mami wani abu ne da bata ji dad'in sa ba?
Tace"Aa ba haka bane wae zata takura mu idan ta koma"
Man yace "wace irin takurawa kuma?
sae kuma yayi shiru yana nazari can yace"haka ne Ryynt tayi tunani kuma"
Da sauri Ryynt ta kalle sa tace"kmr ya nifa banga wani takurawa ba tunda ba d'aki d'aya muke zaune da kai ba"
Yace"to ae rnr dutyn ki ne magana dmn dole a d'akina zaki kwana,
Kinga ba zae yiyu ki barta ita kad'ai a d'akin ki ta kwana ba koh.
Ryynt tace"to ae sae naje da ita mu kwana a d'akin naka mana"
Hm Ryynt knn wa ya gaya miki ana zuwa turakar miji da yaro.
Idon ta tap da qwallah tace"ba wani nn kai ma dae baka so ta koma d'in na fhmce ka"
Ryynt ba haka bane ki fhmce ni.....haka ne mana.
Ta qarashe mgnr ne cike da son fashewa da kuka hkn yasa yayi shiru bae sake ce mata komai ba yaja motar suka tafi.
Suna isowa gidan inna cikin fushi Ryynt ta fita mota ta wuce wacce bata zarce koina ba sae d'akin ta.
Mohd kuwa d'akin inna ya nufa d'auke da sallama abakin shi inna ta amsa sallama washe da baki tace"kun dawo?
Yace"eh inna mun dawo"
Nan ya nemi guri kan sofa ya zauna inna tace"Ryyh fa?
Yace"tana d'akinta rigima take ji yau"
Inna tace"rigimar me kuma ko so tayi ta kwana a can ka hanata?
Yace"Aa inna zancen komawar mami gurinta ne nn yayi wa inna bayanin komai wacce tayi shiru snn tace"to muhamnadu gsky fa kasan xama irin gidan ka ba d'an yaron da ke tayaka xama ba dad'i ne dashi ba,tunda kai dae ba zama kakeyi ba snn qarin abun ma kasan Ryynt bata iya bacci ita kad'ae a d'aki tunda kaga ba ita kad'ai ce matar ka ba da za'a ce kullum kuna tare don haka zancen rashin komawar mami a gurinta bae taso ba,
kawae abinda naga yafi shine zan samar mata er yarinya mae aiki da zata riqa kwana tare da mami idan ita tana naka d'akin ko kuwa hakan bai fi ba,don gsky bazan so a takura er marainiyar Allah ba bayan akwae yanda za'ayi.
Mohd ya nisa yace"hakane inna zan sami umman mami sae muyi magana"
Inna ta washe baki tace"to shike nn d'an albarka ko me tace sae kazo ka gaya min ni kuma sae nasa baaba hurera ta samo mata er yarinya mae hnkli da natsuwa,dan hk tashi maza je lallaso min ita.
Mohd ya tashi d'auke da murmushi ya tafi d'akin Ryynt ya same ta zaune kan bed ta had'e kai da guiwa sae kuka take.
Yaje ya zauna gab da ita tare da janyo ta zuwa jikin sa bata jira me zae ce ba ta zare jikin ta daga nashi ta sauka kan gadon ta shigewar ta bathroom ta rufe.
Mohd bae bita a bathroom d'in ba ya koma d'akin inna tace"ya naga har ka dawo?
Yace"inna mutuniyar taki tayi fushi da yawa inaga shiga bata ko tsaya ta saurare ni ba ta shigewar bathroom ta rufe"
Inna tace"muhammadu nasan halinka wata qil kan hanya fad'a ka mata sosai koh?
Haba inna meye abin fad'a a ciki sam wlh ni ban mata fad'a ba.
Inna tace"to jeka abinka ni naje na rarrashe ta"
Yace"to inna zan tafi d'in amma zan dawo zuwa an jima"
Tace"to sae ka dawo"
Daga haka ya tashi ya fita.
Inna kuwa ta tashi ta nufi d'akin Ryynt .
Ryynt na cikin bathroom zaune ta had'e kai da guiwa tana ci gaba da kukanta taji muryar inna ta kira sunan ta,da sauri ta share hawayen fuskarta tace"Na'am inna"
Inna tace"yi haquri bud'e qofa fito muyi magana kinji Ryynh"
Ba musu Ryynt ta tashi ta bud'e qofar ta fito.
Inna taja hannunta suka je kan bed suka zauna ta kalli Ryynt da kulawa ta dafa kanta tace"kwantar da hankalin ki Ryynh indae mami ce tare zaku koma kinji"
Ryynt ta gyad'a kanta snn inna tayi mata bayanin duk yanda sukayi da mohd sosai taji dad'i har ma tayiwa inna godiya.
Nan inna ta tashi ta koma d'akinta Ryynt kuma ta rage kayan jikiñta ta fad'a bathroom zuwa wanka.
Ta kwashe kusan awa d'aya kafin take fitowa d'aure da towel.
Bayan ta shafa Vaseline ta d'auko turarukkan ta na jiki ta shafe jikinta dasu tsaf sae zuba qamshi take snn ta nufi wardrobe dmn ciro kayan bacci sae jin tayi an rungumo ta,
a d'an tsorace ta juya taga mohd ne ta lumshe ido had'e da rungume shi murya can ciki tace"mk kaine har kasa naji tsoro"
Mohd dake shinshinar qamshin jikin ta ya shafo bayanta a hnkli yace"am sorry"
Nan ya qara qanqameta a jikin sa yana ci gaba da shaqar qamshin turaren ta kamar yanda itama take shaqar nashi suka jima a haka sae can ya d'ago yakai hannu a cikin wardrobe ya ciro kayan baccin da yaga zata ciro yaje da ita kan bed suka zauna yakai hannu zae yaye mata towel d'in jikinta dmn saka mata kayan baccin Ryynt tace"um um Mk kar inna tazo ta same mu bari naje bathroom na shirya"
Ba musu ya bata kayan taje bathroom ta saka ta fito ta same shi yayi kwance yana fuskantar silin idanuwan sa a rufe kmr mae bacci.
Taje a hnkli ta zauna kusa dashi nn ya bud'e idanun sa sae kallonta yake tana kallon shi can ya sauke idon sa akan cikinta ya jawota zuwa jikin sa yana shafa cikin.
A hnkli Ryynt ta tashi daga kan jikin sa ta zauna nn mohd ya tashi zaune yana kallon ta yace"Ryynt wae baki daina fushi dani bane duk da inna ta miki bayani"
A hankali ta riqo hannun sa tana kallon sa tace"No Mk ba haka bane nifa ina gudun kar inna ta same mu ne"
Sae da ya janyo ta ya kwantar kan qirjinsa snn yace"inna fa tasan ina d'akin nn bazata shigo haka kawae ba tunda tasan mata da miji ta ajiye"
Ryynt tace"to ai dare nayi ka tafi gida"
Yace"korata ma kikeyi to ae ni a nn zan kwana"
Ryynt ta kalle sa d'auke da murmushi tace"ae nasan da wasa kake"
Yace"ni da gaske nake dan yau kin tsakaloni da yawa bazan iya bacci ba ke ba"
Tace"me na maka"
Yace"ba ke bace kika zauna kina shafa turarukka ba towel a jikin ki"
Tayi saurin rufe fuskarta da tafin hannunta tace"haba MK ya zaka tsaya to kana kallona"
Yace"to sae kar na kalla nida matata kuma ae laifin ki ne da kika wani sakankance ba kaya a jikin ki kina aikin gabanki"
Cikin muryar kuka tace"to mutum da d'akin shi kuma har ya rufe qofa uhm uhm,wlh kuma ae ma duk laifin ka ne da ka koya min haka"
Nan ta d'auki pillow zata doka mai mohd ya riqe pillown yana dariya rungume da ita a jikin sa taje zuwa tashi ya qara rungume ta yace"nifa wlh da wasa nake miki ban ganki ba qamshin turaren ki ne kawai ya nemi rikita ni"
Tace"to meyasa kace ka ganni?
Yace"sbd na koya maki na kuma san zakiyi"
A shagwa6e ta bugo qirjin sa tace"shine kasa na tashi yin kuka da gaske"
Yace"kan me to ni ba mijinki bane dan na ganki sae ya zamo wani abu"
Tace"to ai ba dad'i ne mutum yana yin abu bae san ana kallon shi ba"
Yace"to yi haquri bari inga babyna na tafi"
Bata ce komai ba sae kallon sa take ya yaye rigar baccinta ya shafo cikin tare da d'aura masa kiss,ya tafi a hnkli kan qirjinta zae yaye rigar tayi saurin hanashi ya kalle ta yace"ayi haka an barni naga baby amma kuma a hanamin ganin abincin baby"
Ya qarashe mgnr ne d'auke da murmushi a fuskar sa,itama cikin murmushi tace"eh mana ayi sbd baby naka ne abincin baby kuma nawa ne da samun ganin sa sae an yanka ticket"
Yace"ok ai kuwa yanzun nn zan yanka ticket nn yaje zuwa had'e bakin su tayi saurin tashi tana ja baya tana dariya tace"nidai dan Allah ka tafi dare nayi"
Mohd da ya miqe tsaye yace"to zo mana muyi sae da safe"
Tace"me zaka min in nazo?
Yace"zanyi pecking d'inki ne kawae kema sae kimin na tafi"
Ba musu taje ya janyo ta zuwa jikin sa ya kai bakinsa a hnkli kan lips d'inta ya d'aura mata kiss itama ta mishi snn suka d'ago suna kallon juna ta cikin ido mohd yace"gobe da safe ki shirya xanzo mu koma gidan mu"
Tace"plz Mk ka bari sae dare dan Allah sbd gobe da safe so nake na cire en tsarabar kowa na aika mishi"
Yace"To ae ba wani aiki bane wnn zaki gama shi in time"
Sosai ta marairaice fuska tace"nidae dan Allah ka bari sae dare guraren bayan isha'i haka"
Yace" to naji Allah ya kaimu"
Ya fad'i hakane tare da d'aura mata kiss kan goshi snn ya mata bye bye ya fita.
Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[10:05PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```
🔮🔮🔮🔮
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.