Complete Hausa Novels

Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Bazan Barshi Ba Part 1 Complete Hausa Novel.docx

Chapter 37 of 56

*page 75*

Har ya samu tayi shiru, ya d'ago fuskarta ya share mata hawaye, nn Ryynt ta ciro zoben azurfar ta ta kamo hannun sa tasa a tafin hannun sa tace"gashi na amince ka yar sae ka saka min naka"

Tayi maganar ne cikin muryar kuka had'e da sadda kanta qasa.

Mohd ya d'ago fuskarta yana kallon manyan idanuwanta da suka ciko tap da qwallah kmr zasu zubo, yace"ina sonki Ryynt, zan kuma so abinda kike so koma mene ne indae bana sa6on Allah bane don haka na amince kici gaba da zama da zoben ki har abada dmn ina son ki kasance mae cika alqawari"

Nan ya kamo yatsar ta zae maida mata zoben Ryynt dake kallon sa tace"Aa ka fara samin naka tukun"

D'auke da murmushi mohd ya ciro zobe a aljihunsa ya kama yatsarta ya saka mata snn ya maida mata nata da ta cire.

Nan Ryynt ta rungume sa d'auke da murmushi had'e da fad'in "nagode"

Mohd ya d'ago ta yana murmushi yace"ni ba godiya kad'ai nake so ba"

Ta kalle sa tace"To me kake so"

Nan mohd yakai bakinsa saitin kunnen ta ya rad'a mata magana,Ryynt bata iya kallon sa ba ta sadda kanta qasa cikin murmushin jin kunya tana wasa da zoben diamond d'inda ya saka mata.

Mohd dake kallonta ya riqo yatsunta ya sarqe da nashi yace"ko baza kimin bane?

Ryynt wacce still kanta yana a qasa tace"zan maka amma sae ka rufe idonka tukun"

Ba musu mohd ya rufe

Idon sa a hnkli yace"to na rufe"

Nan Ryynt taje a hnkli kan kumatun sa ta d'aura masa kiss ta kowane gefe ,mohd ya bud'e idonsa cike da jin dad'i ya sauke su akan Ryynt wacce tayi saurin sa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta.

D'auke da murmushi ya girgiza kansa snn ya janye hannuwanta da ta rufe fuskarta ya kama kumatun ta yaja yace"iyayen kunya to bud'e idanun naki"

Ryynt bata bud'e idanun ta ba sae murmushi ta sakar mae tare da kwantar da kanta a qirjinsa tana wasa da buttons d'in rigar sa, ya d'ago fuskarta had'e da d'aura mata kiss gefen fuska snn ya tashi tare da fad'in"u have to eat, ina zuwa ko"

Ta gyad'a masa kai ta kwanta dan duk yunwa ta cinye mata d'an qarfinta.

Jim kad'an sae ga mohd ya dawo d'auke da abinci ya jawo stool ya d'aura akai snn ya tada Ryynt zaune ya rungume abar sa yana bata abinci har sae da tace ya ishe ta snn ya bata ruwa tasha ya zaro tissue ya goge mata bakinta yayinda Ryynt ta qara lafewa a qirjinsa sbd wani irin bacci da take jin yana fizgarta.

Mohd ya shiga shafa bayanta har tayi bacci sae kallon ta yake har sae da baccin nata yayi nisa snn ya shimfid'e ta,ya zagaya ya kwanta tare da rungume ta ya rufa musu blanket snn ya kashe bedside lamp.

Washe gari bayan sunyi sallah suka koma bacci.

Kamar a mafarki mohd ya jiyo ihun Ryynt ya tashi firgigit yana lalubar inda take bata nn ba shiri ya yaye blanket d'in jikin sa ya tafi bathroom bae sameta ba sae kukanta da ya shiga jiyowa kad'an kad'an ya kuma kasa gane inda sautin kukan ke fitowa gashi sae tafka ruwan sama ake.

Cikin sauri mae kmr gudu mohd ya fita yana qwalawa Ryynt kira jim kad'an sae gashi ya dawo d'auke da ita sae kuka take dafe da ciki,

Mohd dake d'auke da ita duk ya rud'e ya shiga damuwa yakai ta kan bed ,da sauri ta zame kan gadon had'e da fasa ihu dafe da ciki tana yarfi da hannu.

Nan gabad'aya mohd ya rasa natsuwar sa ya janyo ya Ryynt zuwa jikin sa yana fad'in"plz Ryynt nace ki gaya min me ya faru dake?

Da qyar cikin kuka tace"wanka naje inayi a cikin ruwan sama shine santsin ruwa ya jani na fad'i akan cikina"

Kmr zae yi kuka yace"haba Ryynt me ya kai ki zuwa wanka a cikin ruwan sama dan Allah"

Ryynt kam bata iya bashi amsa ba sae ihu take tana juyi.

Nan mohd ya tashi a agurguje ya canza mata kaya ya kwashe ta sae zuwa asibiti.

Bayan wasu awanni da fitar su ne,mohd ya dawo d'auke da Ryynt dake bacci yaje kan bed ya kawantar da ita ,ya qure d'an tulun cikinta da kallo yana shafawa d'auke da murmushi a fuskar sa.

Nan yaji knocking ya tashi yaje ya bud'e qofar.

Amir ne tsaye a bakin qofar ,

mohd ya fad'ad'a murmushin sa yace"yanzun nn kuwa nake shirin zuwa gurinka dmn na snr da kae wani babban albishir d'inda ya sameni a safiyar yau"

Amir dake kallon sa ya saki murmushi snn yace"Au haba na qaraso daga ciki knn"

" Aa muje daga waje dae"

Cewar mohd wanda yaja hannun Amir suka fito suka je can gurin shan iska suka zauna kan resting chairs snn mohd ya kalli Amir d'auke da murmushi a fuskar sa yace"wae ka san me, Ryynt triplet take d'auke da su"

Amir ya fiddo ido yace"what! triplet fa kace?

Mohd ya lumshe ido ya ware su d'auke da murmushi yace"wlh kuwa baka ji irin tsabar dad'in da nake ji a raina ba har ma na rasa ta yanda zan godewa ubangiji na"

Amir ya nisa yace"wlh wnn ba qaramin abun farin ciki bane amma Ryynt she is too young ta yaya zata iya renon su"

Mohd yace"Uhm Amir knn ae Allah baya d'aurawa bawa abinda yafi qarfin sa, mu ba gamu ba da taimakon sa mun taso cikin qoshin lafiya da samun kyakkyawar kulawa ba tare da umma ta gaza damu ba,kawae abinda nake tsoro shine bana son Ryynt taji dmn idan taji zata tashi hankalinta sosai shiyasa bayan kai bana son don Allah kowa yaji har sae idan ta haifu"

Amir yace"inshaa Allah but wlh am still really pity her with dis triplet siblings how can she feed them all"

Mohd yace"common sae kace ba Dr ba u know ko twins ne sae an had'a da madara bare triplet,kuma indae har ina raye wlh inshaa Allah Ryynt bazata wahala da d'awainiyar su ba,iyakar ta dasu shayarwa idan sun buqata fatana Allah yasa yaran basa da wata rigima don banida wani buri da ya wuce naga Ryynt cikin hutu, kwanciyar hnkli da kuma jin dad'i, kuma ina roqon Allah yasa ta haife min yarana rayayyu cikin qoshin lafiya da ita har su"

Amir yace"Amin amin"

Snn yace"ashe asibiti kuka ce knn dan my wife tace min taje kai muku break fast ta samu ba kwana"

Mohd yace"eh wlh asibiti muka je a rud'e shiyasa ma ban samu na snr daku ba"

Amir yace"subhanallah me ya faru?

Mohd yace"Uhm wae Ryynt ta fito wasa cikin ruwan sama sae santsin ruwa ya jata ta fad'i kan cikinta shine ina cikin bacci naji ihunta koda na tashi naga bata kan bed don tare nake da ita muna bacci, na tashi na duba bathroom na duba ban ganta ba sae sautin kukan ta da nake jiyowa a wani gun shine koda na fito na same ta kwance dafe da ciki sae kuka take na d'auke ta naje da ita ciki a can take gaya min abinda ya faru ,ba shiri na kwashe ta mukaje asibiti, Allah da ikon sa har ta fara bleeding wlh akayi nasara shawo kan matsalar kuma da aka duba yarana ba abinda ya same su suna kwance qalau abinsu.

Amir ya nisa yace"Allah to ya qara tsare gaba"

Mohd yace "amin"tare da fad'in"bari na koma daga ciki kar Ryynt ta tashi bata ganni ba"

Amir yace"ok to"

Nan mohd ya yunqura zae tashi sae kuma ya koma ya zaune tare da fad'in"sorry plz na manta baka gaya min abinda yazo da kae ba har zan tafi"

Amir yace"no ba wani abu bane it's just about fitar da kukayi ne kuma ka gaya min"

Mohd yace"olryt"snn ya tashi ya koma daga ciki.

Koda ya shiga kuwa ya sami Ryynt ta tashi sae juyi take,ya qarasa gurinta da sauri ya zauna gefen ta tare da shafo fuskarta yace"mene ne Ryynt?

Bata iya ce masa komai ba sae qwallar da suka ciko tap a idonta, a hnkli ya tada ta zaune ya kwantar da kanta a qirjinsa yana shafa bayanta yayinda yake kallonta ta kulawa yace"gaya min mene ne kinji, ko still marar ki bata daina miki ciwo bane?

Ta girgiza kanta had'e da fad'in"um um"

Yace"to mene ne gaya min wani abu kk so?

Ta girgiza masa kai,

Yace"to ko inda aka miki allura ne yake miki zafi?

Nan ta gyad'a masa kai shi kuma yakai hannu yana murza mata bayanta a hnkli.

Can yaji alamar zata yi bacci ya d'ago fuskarta yace"kar kiyi bacci kinji Ryynt bari idan munyi wanka munci abinci ko"

Ba tare da ya tsaya jin me zata ce ba ya shiga rage mata kayan jikinta snn shima ya rage kayan jikin sa ya tafi da ita bathroom.

Bayan sun fito har sun shirya sunci abinci har Ryynt ta koma bacci, man dake rungume da ita sae kallonta yake d'auke da murmushi yakai bakin sa a hnkli kan goshinta ya d'aura mata kiss snn ya qara rungume ta had'e da lumshe ido yana shafa cikin ta kmr wani mae shafa qwai, yayinda yake jin wani irin farin ciki fal a ransa kmr wanda akayiwa busharà da gidan aljannah.

Wayar sa da ke cikin aljihun wandon sa ce ta shiga ring yayi saurin ciro wayar ya sakata a silent ya zare jikin sa a hnkli ya fita.

Srry plz jiya har na gama muku typing wlh komai ya goge min gabad'aya😰😪.

Billy Giro😊

[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```

🔮🔮🔮🔮

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.