Best Hausa Novels

Layleeh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: LAYLERH MALEEK.txt

Chapter 36 of 65

*Chapter 52

Oum Ayush dake tsaye, wanda jin abunda Laylerh’n ta fad’a ya sa ta sauk’e wani irin sassanyar ajiyar zuciya, k’warai ta d’anyi mamakin jin hakan daga bakin Laylerh’n, amma kuma sanin hak’ik’anin abunda ke cikin zuciyar Laylerh’n, yasa babu wani amfanin mamakinnata. D’an gyara tsayuwarta tayi, tare da sa hannu ta dafa kafad’an ta, cikin yanayin tausasa murya da kuma salon da tasan zai taimaka mata wajen jawo hankalin Laylerh’n ahankali tace.
“Kiyi hak’uri mutafi gida kinji, na miki alk’awarin cewa anjima kad’an zamu dawo, ko bakyaso idan Yah M.Jay d’innaki ya bud’e idanunsa, kuma yaji yana jin yunwa yaci abinci ne? kinsan dole dae zaiji yunwa ko? saboda haka muje gida ki tayani mu dafa masa abinci mai dad’i, nasan idan ya farfad’o zaiji dad’i sosae.�
Jin hakanne yasa ta d’anyi jim, tare kuma da d’ago kanta ahankali ta kalli Maleek d’in da har yanzu ke kwance kaman gawa, yayinda wata na’ura me yanayin computer dake gefensa ke tafiya yanda ya dace, wanda kuma acikin na’urar ne ake iya ganin bugun zuciyarsa.
D’an guntun hawayen daya fito daga cikin idanunta ta share, asanyaye ta d’an karyar da wuyanta gefe, cikin muryarta da har yanzun bata dawo daidai ba tace.
“Tsoro nakeji Oum Ayush, banason bayan natafi wani abu ya samesa, yanzu ma haka nasan yanajin zafi, ki kalli jikinsa fa kiga, duk ya d’anji rauni glasses duk sun caccaka masa jiki, tayaya ma zai misalta irin wannan zafin da yakeji? ko yanzu ma me yakeji? Nasan ma....� Kasa k’arasa maganan nata tayi, sakamakon wani kuka daya so k’wace mata, wanda bisa dole hakan ya tilasta mata lumshe idanunta, take kuwa ruwan hawaye masu tsananin zafi suka sauk’a akan kumatun ta.

Wani abun mamaki kuwa kusan atare hawayen dake cikin idanun nata, da kuma wanda suke cikin idanun Abbou Jaheed suka zubo, wanda duk yanda yaso hana hawayennasa fita ya kasa, saboda tsananin tausayin Maleek d’in da yakeji yasa gaba d’aya ya kasa controlling rauninsa, hak’ik’a ayau d’in da ace shi ba babban mutum bane me yawan shekaru da sanin ya kamata ba, to da ba abunda zai hanasa zama yayi kuka sosai kamar yanda k’ananan yara keyi, saidai kuma babu yanda ya iya, ya zame masa dole ya tausashi zuciyarsa, saboda bai isa hana Allah gudanar da Ikonsa ba.
Saurin saka hannunsa yayi ya share hawayennasa tun kafun su lura da hakan, saidai kuma abunda bai sani ba shine, tuni Abbou Khareem ya ga hawayennasa, domin kusan akan idanunsa ma suka zubo.

Oum Ayush kuwa hannu takai ta sharewa Laylerh hawayen dake kwanace akan fuskarta, batare kuma da ta jira cewar kowanne daga cikinsu ba ta jawo hannun Laylerh’n tare da mik’ar da ita tsaye, anutse ta nufi hanyar fita daga cikin d’akin, ba tare kuma da ta sake hannun Laylerh’n ba, haka suka fice daga cikin d’akin.
Fou’ad dake zaune Abbou Jaheed ya kalla, cikin yin k’asa da murya yace.
“Fou’ad kuje ku huta, ka kai su Laylerh gida, zaka iya dawowa anjima kaima.�
“To.� Kawai Fou’ad yace kana asanyaye ya mik’e daga zaunen da yake, na’urar dake bayyana bugun zuciyar Maleek d’in dake kwance ya kalla, kafun ahankali ya sauk’e ajiyar zuciya tare dasa kai ya fice daga cikin d’akin.

Kamar rak’umi da akala haka Laylerh kebin Oum Ayush dake rik’e da hannunta, har zuwa wajen da sukayi parking motarsu.
Gefen me zaman Banza Oum Ayush ta bud’e mata, jikinta amatuk’ar sanyaye ya shiga ta zauna, tare da juya kanta tana me kallon cikin asibitin, hakanan takeji ajikinta kamar idan tayi nesa da asibitin wani abu zai sake samun Maleek, sam Allah Yasani har acikin zuciyarta bataso ta fiya ba, amma babu yanda zatayi.
Isowar Fou’ad garesu ne yasa Oum Ayush d’agowa ta kalleshi, asanyaye tace.
“Fou’ad Ina kuma zakaje, badai kaima tafiya zakayi ba?.�
Gajerar ajiyar zuciya Fou’ad d’in ya sauk’e, cikin kuma yanayin nutsuwa yace.
“Abbou Jaheed yace nazo nayi driving d’inku, amma ba damuwa zuwa anjima kad’an zan dawo, kafun nan ma nasan Maleek d’in ya dawo hayyacinsa.�
Kai Oum Ayush ta jinjina cike da gamsuwa, take kuwa ta mik’a masa makullin motar, tare da bud’e murfin motar ta shiga gidan baya.
Shi kuwa Fou’ad b’angaren driver ya shiga, anutse ya tada motar suka bar farfajiyar wajen.
Tunda suka d’auki hanya kuwa babu wanda yace da d’an uwansa k’ala, domin kuwa ko wannensu da abunda yake sak’awa acikin rai da zuciyarsa, musamman Laylerh da gaba d’aya ma tunaninta baya jikinta.
Ahaka dai suka k’araso gaban makeken gate d’in gidan, jin k’aran horn d’insu ne kuma yasa take mai gadi ya wangale musu wawakeken gate d’in, anutse Fou’ad ya tura hancin motar ciki, tare da neman waje yayi parking.
Kusan atare dukansu suka fito daga cikin motar, ganin yanda Laylerh’n ke layi kaman zata fad’i ne yasa Oum Ayush tayi saurin rik’o hannunta, kana cikin kulawa tace.
“Laylerh ya dai kina lafiya kuwa?.�
Kanta tad’an girgiza tare dasa hannu ta dafe daidai saitin kanta dake masifar ciwo har wani sarawa yake kaman zai rabe gida biyu haka takeji.
“Kaina ne yake ciwo sosae.�
Tafad’i hakan cikin muryarta dake shaking.
“Ayya sannu to kije kisha magani sai ki kwanta kinji, dole dama da irin wannan kukan da kikayi sai kanki yayi ciwo.�
Cewar Oum Ayush tana me k’ok’arin sake hannun Laylerh’n.
Ahankali ta soma d’an taka k’afafunta, saidai bai wuce taku uku tayi ba ta tsaya tare da juyowa ta kalli Oum Ayush d’in, cikin wata irin sassanyar muryar dake bayyana rauni tace.
“Dan Allah Oum Ayush kada ki koma kibarni idan zaki koma ki gayamin!�
Yanayin yanda ta k’are maganar cikin karyar da wuya ne yasa Oum Ayush ta sake jin matsanancin tausayinta, asanyaye tace.
“Insha Allah Zan gaya miki, kuma kema ki tabbatar da cewar kinsha magani.�
“To.�
Tace tare da juyawa cikin tafiyarta na rarrabe hanya ta nufi sashin su.

Ajiyar zuciya Oum Ayush ta sauk’e tare da kallon Fou’ad daya kafe Laylerh’n da idanu baya ko k’yaftawa, yayinda idanunsa kuwa suka zama jajur dasu.
“Fou’ad.�
Oum Ayush ta k’ira sunansa cikin tausasa murya.
Jin K’iran da Oum d’in tayi masa ne kuma ya sashi d’auke idanunsa daga kan Laylerh wanda harma ta isa sashinsu, dawo da kallonsa ga Oum Ayush d’in yayi, cikin yanayin bayyana damuwar dake cin zuciyarsa yace.
“Yanzu shikenan Oum Ayush haka rayuwar Laylerh da Maleek zata ci gaba da tafiya? sai yaushe ne zasu samu farinciki arayuwarsu? sai yaushe abunda dukkanin su ke b’oyewa zai zama kammalalle? Tabbas Ina matuk’ar jin tausayinsu, musamman Laylerh da ta kasance yarinya k’arama dudu du ko 20years bata cika ba, amma k’addara nata wasa da rayuwarta, dama duk wani burinta, lallai na gamsu cewa akwae abunda Allah Ya b’oye atsakanin Laylerh da Maleek, domin kuwa abune me girman gaske soyayyar da Laylerh keyiwa Maleek, domin na fahimci cewa bawai da iyaka zuciyarta take son shiba, harma da gaba d’aya rayuwarta, wata soyayyace ta daban atsakaninsu bawai kuma irin normal soyayya da kowa ya sani ba, soyayyace ta musamman wanda Ina da tabbacin cewa har abada bazata tab’ayin k’arshe ba.�

Ajiyar zuciya me k’arfi Oum Ayush ta sauk’e tare dasa hannu tad’an sharce hawayen dake idanunta, lallai tabbas ta gamsu da duk kalaman Fou’ad, domin kuwa babu kuskure acikinsa komai ya fad’a gaskiya ne.
Ita kanta ayanzu tsoron soyayyar Laylerh Maleek takeyi, saboda ta fuskanci cewa, ba soyayya bace irin ta kowa, wata sabuwar halittace da bata tab’a ganin irinta ba, duk da kuwa cewa daga Laylerh har Maleek d’in Miskilai ne amma hakan bai hana Soyayyar tasu tumbatsa har ta bayyana kanta a idanun mutane ba, hak’ik’a da ace Laylerh bata da auren Najeeb akanta, to da babu wata k’addara da ta isa hanata aurawa Maleek Laylerh, koda kuwa su Abbou Jaheed basa so, amma kuma saidai k’addara ta riga fata, Auren Najeeb dake kanta ya zama shamak’i.
Numfashi taja tare da soma k’ok’arin daidaita nutsuwarta, kallon Fou’ad tayi kana cikin nutsuwa tace.
“Baka kaini jin tausayinsu ba Fou’ad saboda dukansu yara ne da suka taso cikin maraici, Laylerh tataso babu Uwa da Uba, Maleek kuwa ya taso babu Uwa, tabbas maraicin Uba akwai wahala, amma Maraicin Uwa yafi komai ta gayyara da k’unci saboda Uwa itace gaba d’aya duniyar duk wani bawa, ba komai Amma akwae Allah, muje ciki kaci abinci.�
(Yah Allah Kabarmin Mamana Araye, cikin koshin lafiya da farinciki, saboda itace komaina itace Haskena, kuma farincikina🙏🏻 dama duk wasu mutanen duniya, wanda kuma nasu suka rasu Allah Yajik’ansu da rahama Ameen.)
Asanyaye Fou’ad ya bi bayan Oum Ayush kaitsaye suka nufi sashinta.

Laylerh.
Ahankali ta tura k’ofar falon nata ta shiga bakinta d’auke da sassanyar sallama.
Shiru haka falon yake ba abunda yake tashi acikinsa sai k’amshin turare da kuma sanyin A/C, harta k’atuwar tv plasma d’in dake aje akan wani had’add’en glass table dake d’an manne da jikin bango wanda girmansa yakai 65inch shima akashe yake, Banda k’aran A/C ba abunda ke tashi acikin falon.
Dama ita ba gwanar son zama afalo bane wannan yasa kai tsaye ta nufi bedroom d’inta.
Sam ko da wasa bata tab’a kawo cewar Najeeb na d’akin ba, shiyasa anutse ta tura k’ofar d’akin ta shiga, sanin da tayi cewar ba kowa acikin d’akinne yasa tana shiga ta cire hijab d’in dake jikinta, tare dasa hannunta abayanta ta zuge zip d’in rigarta, batare kuma da ta juya bayanta ba, ta zauna abaki bakin had’add’en original royal bed d’inta.
Tafukan hannayenta duka biyu tasa ta rufe fuskarta dasu, haka takejin zuciyarta na wani irin bugawa, yayinda wani sabon kuka ke shirin zuwar mata, duk da kuwa cewar kanta na mata ciwo sosai amma babu yanda ta iya da wannan kukan dake cinta, lallai tabbas tana buk’atar tayisa ko hakan zaisa taji zuciyarta ta d’anyi sanyi.
Take kuwa ita kanta batasan ya akayi ba kawai sai jin kanta tayi ta fashe da kuka mai sauti.
Najeeb kuwa dake zaune a gefen gadon kan sofa yana wasu rubuce rubuce ganin shigowarta ne yasashi saurin b’oye paper’n dake gabansa, tare da k’ura mata ido domin da’alama ya fahimci cewar idanu da hankalinta basu gane mata shiba.
Ganin kuma da yayi ta fara kuka ne yasa shi sake k’ura mata ido tare dasa hannu ya zare AirPod d’in dake kunnensa, ahankali ya mik’e tsaye daga zaunen da yake, cikin nutsuwa ya zauna adaidai bayanta, batare kuma da ya k’ira sunanta ba yasa hannunsa ya dafa kafad’anta.

Cak kuwa kukan da takeyi d’in ya tsaya, a matuk’ar tsorace ta juyo dan ganin ko waye.
Ido hud’u da sukayi dashi ne ya sa ta k’walalo idanunta waje, tare dasa hannu ta dafe k’irjinta dake tsalle saboda tsoro.
Hawayen dake kwance akan kyakkyawar fuskartata ya kalla, tare dasa harshensa ahankali ya d’an lashi pink lips d’insa.
Ita kuwa Laylerh ganin irin kallon da yake matane yasa tayi saurin sanya hannu ta shiga share hawayennata.
Murmushin daya bayyana kyawun fuskarsa yayi, ahankali ya kamo hannayenta, Jin yanda hannayen nata keda zafi ne yasashi d’an zaro idanunsa waje, ahankali ya d’an matso kusa da ita, cikin yanayin damuwa yace.
“Kinyi kuka sosae gashi har jikinki yayi zafi, still kuma kinzo kina sakeyin wani kukan, sai yaushe ne zaki daina ta kura kanki da yawan kuka? kin manta cewar Dr. yace kina da hypertension? ko so kike kullum ya zama baki da lafiya?.�
Ya k’are maganan nasa cikin sanyin murya, had’e kuma dasa hannu ya jawo Laylerh’n jikinsa.
Tabbas awannan lokacin tana da buk’atar rarrashi da kuma nutsuwa, hakan yasa ta kwantar da kanta akan chest d’insa, tare dasa hannayenta ta zagaye cikinsa zuwa bayansa.
Jinta acikin jikinsa ne yasa shi sakin sassanyar ajiyar zuciya, hannunsa d’aya ya d’aura akan naked skin d’in bayanta, tare da soma shafa bayannata ahankali, bakinsa ya kawo daidai saitin kunnenta cikin murya me kama da rad’a asanyaye yace.
“Ya jikin Maleek?.�
Yanayin yanda yayi mata maganan acikin kunnenta ne yasa ta shagwab’e fuska, tare dajin wani irin motsawan tsikar jiki, kamar kuwa dama jira take ya tambayeta jikin Maleek d’in saiga hawaye sun sake cika idanunta, hakan yasa tayi raurau da idanunta tare da karyar da wuyanta gefe, araunace tace.
“Har yanzu baya motsi, kuma bai bud’e idanunsa ba, abu d’aya ne kawai me motsi ajikinsa, itace zuciyarsa.�
D’an tsagaitawa da maganan nata tayi tare da d’agowa daga jikinsa, hannayensa ta kamo ta rik’e acikin nasa.
Cike kuma da tsananin damuwa taci gaba da cewa.
“Inason naga ya bud’e idanunsa, Inaso naga yana motsi kaman yanda kowa keyi, banason nagansa acikin k’unci, sannan kuma banason duk wani abu da zai cutar dashi, saboda shi kad’aine Yayah nah, shi kad’aine acikin duniyar nan, bana tantamar basa rayuwata Idan har hakan zaisa ya zamo kamar kowa!!!�
Lumshe idanunta tayi wanda hakan ya bawa hawayen dake cikinsu daman sauk’a akan k’uncinta.
Najeeb kuwa idanu ya zuba mata baya ko k’yaftawa, yayinda yakejin wani irin soyayyarta na ratsa duk ilahirin jikinsa, daga wani b’angaren na zuciyarsa kuwa tausayinta ne yayi masa k’awanya wanda har hakan ya sashi kasa jurewa, har saida ya sake jawota ya rungumeta k’am, labb’ansa ya d’aura adaidai saitin forehead d’inta, tare da sakar mata wani irin kiss, take kuwa idanunsa sukayi jajur dasu.
Abundake yawo acikin k’irjinsa ya soma k’ok’arin dannewa, ta hanyar saita nutsuwarsa, d’an d’ago Laylerh’n yayi cikin kulawa yace.
“Jikinki yana k’ara zafi sosae bari na d’auko miki magani kisha.�
Baijira me zata ce masa ba kuwa ya mik’e tsaye.
Direct gaban bedside drawer d’insu ya nufa, murfin drawer’n ya bud’e ya ciro sachet d’in paracetamol, k’waya k’wayan paracetamol d’in guda biyu ya b’alla, tare da fita falo ya d’auko goran ruwa marar sanyi sosai.
Dawowa yayi ya zauna akusa da ita, had’e da mik’o mata k’wayan magananin.
Ba musu kuwa ta amsa Tasha.
Murmushin dake bayyana damuwar da yakeji acikin zuciyarsa yayi, ahankali ya kama kafad’un Laylerh’n ya kwantar da ita akan gadon, tare dajan blanket ya rufa mata, Dan ran k’wafowa yayi ya sake kissing goshinta, cike da kulawa yace.
“Zanje wani waje, bazan jima ba zan dawo ki d’anyi bacci ki huta kinji.�

Kai ta girgiza masa cikin muryarta da ta disashe tace.
“Anjima zamu sake komawa asibiti nida Oum Ayush.�
Jin ta ambaci asibiti ya sashi d’an lumshe idanunsa, kansa kawae ya jinjina mata alaman “To.�
Baatare kuma da ya iya cewa komai ba ya d’au wayarsa tare da juyawa ya fice daga cikin d’akin.
Ganin kuma ya fita ne yasa ta lumshe idanunta, duk da cewar kuwa sam sam batajin bacci amma lallai tana buk’atar nutsuwa.

Asibiti.
Akaro na barkatai kenan da Abbou Khareem ke d’ago kai ya kalli d’an Uwa kuma Yayan sa, da duk yanayinsa ke baiyana matsananciyar damuwa.
Gyara zamansa yayi tare da fuskantar d’an uwannasa kana cikin sanyin murya yace.
“Tabbas Kallo d’aya kawai za’ayi maka asan cewa kana cikin damuwa, amma ko kusa ban tab’a kawowa araina cewar akwai wata damuwa da zata dameka wanda har zaka iya kasa fad’amin ba, musamman damuwar da ta shafi Maleek domin koba komae shid’in matsayin d’ana yake.�

Jin maganan Abbou Khareem d’inne yasa Abbou Jaheed sauk’e ajiyar zuciya.
Hak’ik’a ko zai jinkirta fad’an damuwarsa to baga d’an uwannasa ba, sannan kuma matsalar da Maleek d’in ya gamu da ita ba irin wacce za’a b’oye bane, saboda haka ya zame masa dole ya gayawa k’aninnasa abundake faruwa.
Kansa ya d’an sunkuyar k’asa, tare da tattaro nutsuwarsa, duk dama baya da kuzari amma dole zai nemo jarumta, barayin da Maleek d’in ke kwance ya kalla, cikin muryarsa me d’auke da sanyi yace.
“Tabbas Maleek ya had’u da jarabawar Ubangiji, wanda kuma ya d’aura masa itane bawae don baya sonsa ba, ba kuma yayi hakanne wai don Maleek d’in ya aikata masa zunubi ba, domin kuwa jarrabawa ce da kowani bawa na duniya zai iya fuskanta, domin kuwa shafin dake cikin littafin k’addara yawane da su, bayan ka gama da wannan sai wata sabuwa ta sake bud’ewa, Dr. Mouhammad ya fad’amin cewa asanadiyar accident d’in da Maleek yayi, ya samu matsala acikin mararsa, wanda hakan yasa, k’waya k’wayan haihuwarsa ba zasu iya rikid’ewa su zama k’wayar halittan da zasu samar da d’a ko y’a ba, bi ma’ana Maleek bazae tab’a haihuwa ba saidai wani ikon Allah.�

Idanu Abbou Khareem ya zaro waje cikin matsanancin tashin hankali, Jin cewar wai Maleek bazai sake haihuwa ba.
Domin kuwa maganan ya zo masa amatuk’ar ba zata, wanda har saida yasa idanunsa suka ciko da k’walla, masu d’auke da matsanancin tausayin Maleek d’in.
Asanyaye ya shiga ambaton sunan Allah dan kuwa al’amarin ya sakashi a shock sosae.
Magana yakeson yi amma duk sai yaji ya kasa.
Daidai lokacin kuwa k’iran Alhaji Farouk wato Baban Munnira ya shigo wayarsa.
Take Abbou Jaheed yaji k’irjinsa ya buga, domin yasan cewa lallai acikin biyu za’ayi d’aya, abu me yiwuwar ce kuwa bazaiyyi dad’i ba.

*16February/2021

*4:13 pm*
2/18/21, 8:33 AM - Ummi Tandama: *L.M*

*Not Edit*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.