Baroroji Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Baroroji Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 51 of 64
BABI NA HAMSIN DA BAKWAI.
HMMM NIDAI YAR KALLO CE!
Zuɓewa yayi akan gwiwar shi, ya rasa meke mishi dad'i baki daya, wayar shi ya ciro. Ya shiga gurin kira, ya kira Abie.
"Abie ta tafi" ya faÉ—a kamar yaro karami. "Kuka zaka yi?" Ya tambaye shi yana murmushi,
"Karka damu, zata dawo Insha Allah ba zata tsallake boda ba, zata dawo."
"Abie Mommy tace tana da juna biyu! Abie rayuwar su da abincin ki ta!"
"Karka damu zata dawo, baka yarda dani bane?"
"Na yarda da kai"
"Kwanta kayi barci zata dawo Insha Allah. Sai dai idan ta dawo ka rabu da ita kayi watsi da ita"
"Ba zan iya ba"
"Zaka iya, domin zata cutar da kai da abinda soyayyarta. Ka cigaba da hakuri Mahaifinka ma kayi ta bashi hakuri. Itama Mahaifiyarka ka bata hakuri."
   "Toh" ya faɗa, Abie ne ya kashe wayar ma.
*
Bayan sun gama wayar yayo alola tare da É—aukar Alqur'ani, addu'o'in kawai ya shiga yi yana ambaton sunanta. Bai tashi ba zai da yaji a ranshi Allah zai amsa addu'o'in shi sannan ya mike tare da turawa Dr Zainab sako.
*_Ina kara baki hakuri don Allah ki taimaka mana da addu'a ke uwa ce Maimunari tana bukatar addu'o'in ki._*
 Sannan ya mike tare da fitowa falo yana labarta musu tafiyar Maimunari.
  ***
Tafiya muka yi bana kare ba, dab zamu fita bodin Nijar, mu shiga hanyar Libya, hukumar shige da ficce suka kamani, nayi juyin duniyar nan amma fir suka ki sake ni, karshe wayata suka amsa suka duba Number Hammah Mohan.
 Aka kira shi. Kamar a mafarki ya ji kiran dan haka bai b'ata lokaci ba, ya kira Dan Ba'are, aka yi magana da hukumar sojojin sama, aka bada jirgi. Har bakin bodar yazo daukata, sai da yayi kome sannan ya shiga inda aka ajiye ni, na kifa kaina da hannuna.
"Tashi muje" mik'ewa nayi a hankali, ya dauki jakar kayana ya fita dashi. A hankali naga yana tafiya. Da gudu na bishi tare da rungume shi ina kuka. Tsayawa yayi yana sauke ajiyar zuciya. Shi kanshi dan Ba'are goge kwallar da yake zuba mishi yayi.
   Muna shiga cikin jirgin yayi mishi magana da buzanci.
"Ka dauki matar ka ku bar kasr nan."
"Taya?"
"Zaka iya mana"
"Zan bar Abbu cikin kad'aici ne"
"Toh ai Ammyn tana kan bakanta sai ka auri yar masu kudi."
"Toh nagode! Amma ka tattauna da Abbu duk yadda yace"
Haka suka yinta hira ina jikin shi a kwance, ina shaƙar kamshi turaren shi, har muka isa Niamey.
   A hankali ya dauke ni, muka wuce gidan Abie, Khalil na parking ya wuce dani dakin da ya tab'a kai ni, lokacin karfe biyu na rana, haka ya kwantar dani. A hankali ya janye rigar jikina yana kallon shafaffen cikina zuwa maran bai ga alamar kome ba, babu alamar cikin fa. Maida kanshi yayi kirjina da ya cika. Murmushi yayi yana shafa kirjin, su kam ya yarda dan sun dauke kome, har wani kumbura suka yi, addu'o'in yayi mata tare da shafe ta, sannan ya fito ya sami Abie.
Mika mishi fura da nono yayi, a hankali yake sha. Shigowar Khalil shima Abie ya mika mishi.
"Abie zama haka babu dad'i fa? Kayi aure mana"
"Hmm"
"Ko Mommyn mu zamu maka bikonta."
  "A'a Nagode"
Duk yadda suka so amma fir yaki, haka suka gama suka bar gidan.
.... Karfe biyar na yammacin na farka sannan na nufi ban daki nayi wanka, sannan na fita na nayi sallah, ina sallah naji shigowar shi. Bayan na idar na kulle kofar, haka nayi ta zaman daki ga yunwa ga zazzaɓin da ana magarib nake fara shi dai gari ya waye, nake samun sauki.
 Cikin dare na farka nayi ta buga kofar dakin, na kasa bude kofar, karshe balle kofar kayi, suka kai ni asibiti. Anan na kwana.
***
Washi gari.
Ya shiga gaishe da Hajiya Latifah, tana zaune. Abun duniya ya dame ta, sunkuyar da kai yayi sannan yace mata.
"Ammyn ki yafe min"
"Zan yafe maka amma sai ka min alƙawarin ba zaka tab'a dawo da Maimunari rayuwar ka ba, idan kayi min haka wallahi na yafe maka."
    Da sauri ya d'ago kai yana kallonta, kafin ya sunkuyar da kanshi.
"Naji"
"Alhamdulillahi! Allah yayi maka Albarka ka tafi Maiduguri akwai Yar Kawata ka nimo aurenta."
"Toh"
Ya fada mata, haka ya fita ya nufi shashin mahaifin shi ya gaya mishi, yadda suka yi.
"Toh Allah ya kyauta"
"Amin amma kafin nace ina son zuwa naga Nahnah naji ance min bata da lafiya."
"Karka sake ka gaya mata kome ka barta Allah ya bata lafiya."
"Toh insha Allah."
  Haka ya shirya ya tafi Agadaz babu shiri. Duk da ya samu jikinta da sauki, amma sai da ta mishi maganar Maimunari, yake yayi mata.
"Zata zo Insha Allah"
"Akwai labarin da zan baka, naji labarin abinda ya sami Mamman Nasir, gaskiya ce babu bincika karya ba. Amma kuma ai Nasir ya rike shi da Amana.
Shekaru saba'in da wani abu baya.
Duk wanda ya xaga Afrika yasan bayan wasu kabilun babu kabilar da ta kai Fulani yaÉ—uwa a nahiyar Afirka"
Ajiyar zuciya ta sauke nauyin kafin tace mishi.
"Karka damu, idan ka shirya kazo kai da iyayenka ka iyayen yarinya, zamu yi magana da kai. Akwai abinda na gani a tattare da Yarinyar. Kayi min fatar na samu lafiya zan gaya maka yadda kome yake har ita yarinyar ta san waye Mahaifinka, sannan itama uwarka ta san waye Mahaifinka."
Ba haka yaso ba, amma haka ya bar gidan bayan ya cika ta da Alkhairi, sannan tayi mishi addu'o'in ya tafi.
***
Bayan wata uku.
Cikina ya shiga na huÉ—u, ina kwance bana shiga harkan su, amma yau da ya kasance juma'a ina lura da yadda suka ki kallo har wayata dauketa Abie yayi,Ni kuwa ba magana nake mishi ba, Innah tayi fadar tayi rarrashin har ta gaji, shi kuwa zuba min ido yayi.
Kuma ban da sakarci naso na kuma guduwa, amma wallahi haka na gama shiryawa, nayi ta yawo a cikin gidan ban fita ba. Haka ya zuba min ido,domin idan yace zai yi magana tabbas zai dake ni, domin zaman da nayi da shi a yanzun wallahi yana da mugun zafin rai, gashi idan yayi magana kamar saukar aya. Bana mishi musu kuma bana mishi taurin kai.
Amma kuma bana magana dashi, Mohan shi yake zuwa ya kai ni asibiti, amma shima na lura wani dauke min kai yake,haka ya sani jin na tsane su baki daya.
   Ina ganin Abie ya shirya zai fita.
"Hammah Sama'ila ina zaka?"
"Zan tafi Maiduguri ne daurin auren MOHAN"
Dama na fito daga cikin kitchen kenan rike da bowl na y'ay'an itacce. Ban san yadda aka yi na yanki jiki na zube ba, jini me mugun yawa ya shiga zuba min kamar an bude fanfo.
  Tashin hankali,daukata yayi tare da nufar waje dani. Asibitin aka nufa dani, Allah da ikon shi Muka hadu da Khausar. Ita ta amshi ni, shi kuma Abie ya kira Mommy ya gaya mata.
.... Washi gari tazo, ita da su Benazir. Abun dariya bata kula Abie a gaban yaran su kuwa dake Abie yana zuwa duba su, Yaran suka makale mishi, ganin halin da nake ciki tacewa Innah.
"Ina ga ko zamu fita da ita ne, na gaji da Nijar din nan!"
Juyawa nayi tare da cewa.
"Babu inda xan bi ki, idan ma fitarwan ne sai dai Baba Mari da Innah su bini, amma ke wallahi ba zaki bini ba" marin cinyata Innah tayi.
"Barta Aminatu, shikenan za a kawo miki Baba Mari! Sai ku tafi Zurich."
   Kin amsa mishi nayi tare da dauke kaina ina kuka.
"Mommy Adda Munah sai kace baby. Ta bude baki tana kuka, sai na gayawa Hammah Mohan ya ga kukar ki"
  "Innah kin ga dake Ita yar Aure ce tana min ab..." Marin bakina tayi.
"Amma baki da hankali ko? Ciki ne a jikinki kike tozarta iyayen ki? Haba Maimunari Haba Maimunari" aikuwa na kuma buÉ—e baki na fashe da kuka. Shigowar Hammah Mohan, a hargitse. Abie yace mishi.
"Fita kar na kuma ganin ka, mara hankali kawai. Wallahi ka bani mamaki. Idan ka yi wasa WALLAHI sai na haramta maka Maimunari har abada, dan hauka ka sake yarinya ko gidanka bata shiga ba! Sannan nayiwa Mahaifinka magana yace ba zai maka dole ba"
  "Ai Abie na zame maka dole, domin dai Maimunari uwar dana ne kuma sau dari idan aka sani niman aure sai ka auro su ba sake su."
"Mahaukata kawai."
  Karasowa yai bakin gadon yana me rike hannuna,.na kuwa fashe da kuka.
"Dan ka cuce shi shine kawai zaka zo min jeka ta cinye ka." Takaici ya ishe Abie, dan dole ya kore Mohan, amma dan bakar jaraba yana kofar d'akin.
  Da yamma haka Hajiya Lateefah ta biyo ni har asibitin taci zarafin mu, babu wanda ya tanka mata, sai dai bayan tafiyarta ne, dake tace min Ni da Mohan sai a lahira idan ana zaman aure mayi. Shine na fara aman jini.
Dan haka Abie ya tafi Maradi ya dauko Baba Mari, ya kaita gida dake Innah da Mommy suna kaina, itama kanta wannan karon Mommy tayi kokari, ta saka an daure mahaifar, ita tayi ta shige da ficce, har gurin Primer minister, wanda al'umma suka hana shi barin aiki. Ta nime ya saka hannun, sannan sun tattauna dashi, ya fahimce ta sosai ta koka mishi a matsayin ta na uwa da kuma halin da Yarta take ciki. Kuma ya gamsu.
  Dan haka tana dawowa lokacin, Abie ya kawo Baba Mari, suka haɗu da Mommy, ta gaishe ta a fisge kasancewar suna tattauwana da wasu likitocin, aka kuma amince da kome sannan ta dawo dakin, kallon juna suka yi, cikin wani irin ta shin hankali Mommy ta rungume Baba Mari.
Kuka suke baki daya, kafin suka nutsu. "Ikon Allah! Munyi gudun abin kunya, yau gani na rike abin kunya da hannuna. Gudun abin kunya bayan mun tafi Allah yayiwa Malam rasuwa, tare da fatan zaki nime mu, amma bayan na gama takaba, na dawo Nijar . Naje gidan su Khalid baya na karshe na samu labarin yayi aure sun koma kasar waje da matar, bayan wani lokaci na koma aka ce min sun zo sun. Koma Mahaifiyar shi ta rasu.
Ban kuma komawa ba, na barwa Allah duk inda kike zai dawo min dake, shine wata rana ina yawon niman mafaka, Malam Ansar ya buge ni, karshe da yaga bani da matsuguni ya bani matsuguni a gidan shi, har Allah ya kawo min Almamoon, lokacin tana mata maza!"
Sun sha kuka sannan suka zauna suka tsara yadda tafiyar zata kasance, tunda su Yumnah sun samu hutu a tafi dasu. Ita kuma Mommy ta zauna a nan ita da Innah tayi tsalle tace bata zama, bakin aikin ta zata koma.
Haka kuwa akayi. Suka tattara suka tafi. Ko Mohan bai san inda suka tafi ba, karshe itama Mommy tafiya Saudiya tayi.
*
Kuka take kamar ranta zai fita idan ta ga yadda Hanan ta koma, sai ta ji zucuyarta yayi nauyi sai ta ga bayan Hajiya Lateefah, Mohan, Maimunari, sam Hanan ta koma kamar wacce ta shekara dari tana jinya, duk inda suka shiga sai ace su koma wanda suka yi niyyar tab'awa ne ya dawo musu da kayan su.
Yau ma sun gama wahalar duba inda za a saka mata jini, yaki samuwa, can kuma ta kama amai kore shar, kafin tace.
"Aniyata ta zata koma kaina" daga haka bata kuma magana ba, sai warin da ya cika d'akin. Koda aka duba kayan cikinta ne ta kasaye shi, abin tausayi haka Yarinyar nan ta mutu, hauka tuburan uwarta tayi, tana cewa.
"Sai na kashe su, sai na kashe su"
Itama rufe ta aka yi a daki...
(Ramin karya kurarre ne inji bahaushe)
**
"Mohan wai ya zan maka ne? Sake ta kayi fa!" Inji Hajiya Latifah,
"Toh Ammyn ki kuma nima min wata"
"Anya yarinyar nan ba mayya bace? Ya daga kawai an gaya maka ta fadi zaka sake yar mutane..... *KAINA NA MUGUN CIWO A SAKA NI ADDU'A 😓🤮*
_KU FAHIMTA MANA SHUGABAN KASA FA AKA BINCIKO LABARIN SHI AKAN SHIMA KAMAR MAIMUNARI CE DAN HAKA A DAINA RUDEWA PLEASE IDAN KUKA YI HKURI ZAKU JI KOMEðŸ¤_
#Mai_Dambu
8/19/21, 6:54 PM - My Mtn Number: ðŸ‚ðŸ‚BOROROJI🫀🫀
~The Journey of Destiny💔~
Mai_Dambu
Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.