Complete Hausa Novels

Baroroji Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Baroroji Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 2 of 64

BABI NA UKU.
Wata tafiyar.

Sake baki Salihu Muhmuda yayi tare da Amadu.
"Amma zamu haÉ—u" suka fada mishi,.mik'ewa yayi cikin rashin tsoro yace musu.
"Idan muka hadu abinda kuka bani ku hanani" ya faÉ—a yana fita daga kujeran,
"Mara mutunci"
"Lokacin da aka zo rabon shi bana nan"
"Mugu"
"Eh gadon shi nayi"
"Dan iska kawai"
"A'a sai dai guguwa"
Ya fada tare da barin tabirin su, kamar zasu fasa jarabawar, karshe haka suka mike zasu kai, sai a lokacin Amadu ya kai idanun shi kasar tabirin su ya lura da rubutun da Almamoon yayi ya ajiye musu. Da sauri suka dauka. Murna kuwa baki yaki rufuwa.

Koda suka gama, fitowa suka yi. Tare da samun shi a kasar bishiya ya zauna yana ta rubutu, idan ka ga hancin shi har baki, daga gefen fuskar shi kuwa saje ce ya kwanta gwanin ban sha'awa.
"Kai mara mutunci" banza yayi musu.
"Mun gode"
" Da aka yi me?"
"Da bamu amsar da kayi"
Kallon su yayi sannan yace musu.
"Ai ina mamakin yadda Uwayen ku suke kashewa jakuna kudin makaranta." Ya fada tare da mik'ewa.
"Wawa kawai dan baki duna"
"Eh toh ta yiwu ni bakin ne, amma kuma ina takaicin haduwa da katon jaki" ya faÉ—a tare da nufar hanyar ajin su.
"Almamoon dan me gadi"
Cak ya tsaya tare da juyawa ya sake murmushi, kafin tace mishi.
"Eh toh dukda haka yafi cirani" da Yaron ya ji abinda ya gaya mishi fasa ihu yayi tare da burgima, an zage mishi uba an can dan cirani.

      Haka yayi ta kuka har Malamin su ya shigo tare da tambayar su meye ya haɗa su.
"Zagina yayi na bashi hakuri" inji Almamoon,
" Karya yake cewa yayi Ubana dan cirani"
Tsaki malamin yayi sannan yayi musu fada.
... Bayan sun gama jarabawar suna nufi hanyar gida, yau ya shirya musu tsiya shi yasa bai kula su ba.
"Yau idan muka je gida zan samu anyi mana abinci me dad'i?" Suna son yayi magana amma dake yayi shiru basu kuma takalo shi ba.
 
Haduwa da wasu yan samarin unguwar su, suka tsaya tare da make su, amma ban da Almamoon, wuce su yayi. Sai da suka bar gurin.
"Mamoon kai wani irin mugun mutum ne ka ga sun tsare mu ba tsaya ba."
"Me ya faru daku?" Ya tambaye su, kamar bai ga abinda ya faru ba.
"A'a babu"
"Nima naga alama" ya ga musu tare da wuce su, matasan nan ba kome yasa suka make su Amadu Bukar da Salihu Muhmuda ba, sai dan tsokanar su da suka yi, kuma akan idanun shi suka tsokane su. Shi kuma baya tab'a bin bayan karya.

  Haka suka isa gida idan suka gaya mishi maganar banza ya gaya musu wacce tafi tasu muni.
"Dan banza munafuki wanda baya yarda yayi wanka a gaban mutane." Wannan maganar tayi mishi zafi, da gaske ne baya tab'a wanka a gaban mutane, kuka kamar yadda babba zai shiga ban daki yayi wanka, haka shima yake. Rasa amsar basu yayi har suka isa cikin gidan, zasu nufi dakunan iyayen su yacewa Salihu..
"Ka tambayi Iyakar me yasa bata wanka a waje"
Ya gaya mishi sannan ya shiga dakin su. Samun Innar shi yayi tana ta daman cura fura da aka kawo mata aikin shi take.
"Sannun Innata"
"Sannun D'an albarka, dauki abincin ka yau Allah ya taimaka malam ya samu dan albashi ya sayo maka shinkafa aka dafa, duba ka gani har da nama."

Kallonta yayi sannan yace mata.
"Innah hala ko cin namar baki yi ba daga ke har Baba." Ya fada idanun shi na cika da kwalla.
"Mun ci mana"
Ta faɗa tare da maida hankalinta kan aikinta, bude kwanon yayi ya ga Bama kusan ya lullube abincin,  sai ganye da aka zuba a saman namar, ture abincin yayi tare da cewa.
"Ba zan ci ba"
"Yi hakuri Bawan Allah, sanyin idaniyar Innar, Dan da aka haifa tsiya na barci, Kasan yadda nake kokarin kyautata maka, toh maza ci sai ba baka labarin wani mafarkin da na jima ina yi akanka"
"Wallahi ba zan ci ba sai dai muce tare"
Shafa kanshi yayi tare da cire mishi hular kanshi, gashin kanshi irinta Bororoji yana nan daga tsakiyar kanshi anyi Mishi wata irin kitso me hawa biyu, doka sai wasu kanana da aka saka musu wuri wato braid, gashin nan baki suddin har gadon bayan shi, wuyar shi a daure yake da guru da azurfa,   murmushi yayi sannan yace mata.
"Gobe za a fara shadi a rugar Baima, zamu je don Allah Innah ki bar ni naje" kura mishi ido tayi cike da tsoro.
"A'a ba zaka je ba"
"Don Allah nace Innata..."
"Iyar Mamoon! Wallahi nakawo miki dokaciya, kiyiwa Mamoon fada da irin maganar da yake zarowa nan."
"Toh Allah yayi min baƙi bari nayi shiru kar kayi Magana"
Rufe mishi baki Innar shi tayi.
"Kiyi hakuri Iyar Salihu."
"Ina dalili yaro sai kace mace gurin zaro magana, na kara jin yacewa Salihu me yasa bana wanka a gaban su."
"Toh ai dalilin da nasa nima bana wanka a gaban jama'a kenan" ya faÉ—a tare da kallon Innar shi, kamar zai yi kuka.
"Iyar Mamoon"
"Toh kiyi hakuri" ya faÉ—a tare da kallon Iyar shi.
"Kiyi hakuri iyar Salihu," ta juya tana cigaba da sababinta, dariya yayi sannan yace mata.
"Zama da mutane sai ka koyi halin su"
"Almamoon ka duba girman Allah ka daina harba mutane da magana marasa Dad'i,irin wannan halin shine ya faru shekaru goma sha daya, harbin wuni da bakin magana, karka jefa rayuwata cikin ukuba mana."

"Shi kenan" ya faɗa tare da tura mata kwanon, haka bata so sai da taci yankar naman daya, sannan ya fara cin abincin. Abu biyu yaƙe dauke da Almamoon yanayin shi na Uwar shi ce da kamanin ta, bakin fatar shi na Hamma Sama'ila ne, domin har yafi Uban baki ma.

Shekarun baya bata yarda cewa yaron zai kai haka ba, domin kuwa bayan ya shekara daya yayi fama da rashin lafiya, irin su bakon dauro, tamowa, da kuma laulayi irinta yara kananu, sai da ta kai ko abincin da zasu ci gagagrar su take, a lokacin gidan da suke suka sakota a gaba sabida rashin bawa Yaron nono da kuma bata mishi wanka a gaban jama'a. Suka yi ta gulmar su da kananun magana.. haka bai saka ya tab'a ko d'aga kai tayi magana ba.

   Dole Sanda ya fita niman aikin yi, domin ba zai iya rayuwa da iyalin shi babu abinda zasu taimakawa kansu ba, sabida yanayin da suke ci ko surfen an daina bata. Sun sha wahala da yaron, domin rashin nonon uwa yasa ya rasa lafiyar shi, sai da suka hada da na gargajiya, irin wanda suka sani da kansu. Suka hada mishi magani. Da yayi wayo kuwa idan basu samu wadataccen abinci ba, wanda suka samu suke hakura su bashi, su kuma su kwana haka.

   Allah cikin ikon shi Sanda ya samu gadin kasuwa, abinda ya rufa musu asiri kenan, duk  da haka suke biyan kudin haya, tare da abin da zasu ci, tunda likita ya gaya musu, yana bukatar kayan gina jiki, suke wannan kokarin ki basu ci nama ba zasu saya mishi, a zuba mishi akan abinci. Madara kuwa, kullum idan zai dawo da safe zai sayo mishi  ta gora ya kawo mishi.

    Wani irin kaunar yaron suke kamar su bada rayuwar su domin fansar nashi.

   ---
"Innata na gama gaya min mafarkin da kika yi?" ya tambaye ta,
" Wai na ganka ne tare da wasu manyan mutane, kuma ka zama babban mutum, sai farin ciki kake"
"Daga karshe kuma kika tashi a barci ko?" Ya katse mata labarin. Girgiza kai tayi tana cewa.
"Allah ya shirya min kai!"
Tana murmushi, domin karfafa mishi haka take.

Kiran sallah ne ya sashi mik'ewa yayi alola sannan ta dawo dakin yayi Sallah, kafin ya zauna yana kallon Innar shi.
"Inna mun gama jarabawar mu yau, Allah yasa ki biya min kudin Makarantar sakandari" ya faÉ—a yana tararradi yadda zata dauki maganar.
"Idan kayi min alƙawarin zaka yi karatu domin Allah da kuma tsayawa da kafarka me zai saka na ki biya maka" ta faɗa tana jan wani akwatin katako ta bude cikin shi. Kudine babu iyaka. Suka zauna aka yi lissafin su tsaf.
"Innah har zai rage ma ai kuÉ—in."

"So nake na cigaba da tarawa, dan ba zaka yi karatu a makarantar gwamanti da babu kulawa ba, kai ma makarantan kudi zaka tafi." Murmushi yayi sannan yace mata.
"Insha Allah"

     ***
Haka suka share wata biyu sannan sakamakon su ya fito, haka Aminatu ta fasa asusun aka biya mishi kusan makudan kudade na makaranta, ranar da zai fara zuwa. Suka zauna dashi aka mishi nasiha, tare da mishi gargadi.
"Karka sake kayi wasa da karatunka, kayi hakuri da mutanen da zaku hadu makarantar yaran masu kudi ne dan haka karka bari a Kama ka da laifin da zai dame mu.

Haka suka gama mishi fada, sannan zai fita Malam Sanda tace mishi.
"Kin gaya mishi gaskiya akan" kallon shi tayi tare da cewa.
"Wannan sirrin shi ne, karka manta wata rana zai fahimci dalilin haka, kai dai ka hana shi mu'amala da maza da mata,"

        Kallon su yayi kafin yace musu.
"Wani sirrin kuke boye min?"
"Babu wani sirrin da a ke boye maka"
"Toh shi kenan," ya faÉ—a tare da barin d'akin, shi da Baban shi.
A iya yanzun haka kawai take jin kamar sun tauye mishi hakkin shi da kuma yancin shi, sai dai kamar yadda Mijinta ya faÉ—a haka ne, baya son tarihi ta maimaita kanta ne akan shi, shi yasa ya zab'i hakan a matsayin babban al'amari akan.

Amma kuma tana ganin kamar haka ba hujja bane, kamar tauye hakkin shi ne, kai toh idan wani abu ya same shi fa? Gwara kawai a tafi a haka. Toh gaba kuma aka dawo aka samu akasi fa?  Lallai bari malam ya dawo zasu yi magana domin ba zai tab'a yiwa ba, ka sayi kura da daddare da safe ka samu kare ne, haka ba zai tab'a yiwa ba..amma shi yaron ai bai san hujjar su na maida kome haka ba.

      ..... Bayan malam ya dawo ne ta kalle shi kafin tace mishi.
"Malam anya bamu so kan mu ba? Taya zamu bari har zuwa lokacin da."
"Ki bar kome a hannun, idan ta fara girma zamu fahimtar dashi kome, sannan zamu sauya mishi gari domin kar a samu matsala, karki yarda wani yasan wannan sirrin. Ya zauna a tsakanin mu."

Had'iye yawun tayi sannan tace mishi.
" Sai nake ganin kamar da cutarwa, a bar shi haka ba a gaya mishi dalilin da yasa yake raye a haka ba, sannan kuma. "
"Karki karaya mana, tsoron abinda ya faru shekaru goma sha daya nake kara ada Yaron nan ba wai dan wata manufa bane, kawai ki tayani boye maganar shi nan bana son kamar yadda iyayen shi suka mishi, shima ace ya fuskanci haka.

      Duk da muna namu Allah yana shine gaskiya."

"Ko a ina Sama'ila yake oho?" Ta faÉ—a cikin sanyin murya, me ban tausayi. A hankali yake kwalla suka zubo mata, tana kallon kasa. Ya tafi ya manta da gida, ya tafi bai kuma waiwayar baya ba, me yasa ya tafi shima? Me yasa ya gaza tsayuwa ya fuskanci rayuwar abinda ya bari, babu kome, Allah yana nan zata rike yaron ta kuma boye mishi waye shi. Domin samun goben shi.

Amma Tabbas akwai sirri me girma ga rayuwar Almamoon.

****
Asalin labarin.
Fulanin Wodaadabe Bororo.
Wato sune Fulanin da basu zama kuma basu da mazauni daya, idan suka shekara anan yau gobe zasu kara shekara a wani garin. Sannan Allah yayi musu baiwar ilimin addinin Muslunci, musamman Alkur'ani.

   Zunzurutun baiwar da Allah yayi musu kasancewar su bakakken Fulani masu jajjen shanu, yasa zaka sami yaro karami an daura shi a saman saniya yana tafe yana karatun Alqur'ani, kuma ya tafi da saniyar har wata tafiya.

Yanayin shigar su ba kamar na sauran Fulanin bane, domin suna sanye da wata hafaffera, riga ce Armless, har gwiwar su rigar take, sai wandon yadi ce baka kowa wata kala, suna saka hular malafa akan su,  matan su, suna tara gashi a gaban goshin su, me shegen yawa kuma suna saka bakakken kaya har kasa kamar riga da zabi ko doguwar riga.

   Suna shigowa gari da matan su, tallar maganin mata ko maganin gashi,  suna bin gida gida suna tallar shi, zaku gan su dogaye ne matan. Kyakyawa bakakke...

    Duk da ana samun fararren su, amma bakakken sunfi yawa, suna da Albarka na dabbobi, sannan kuma suna da matukar kyakyamin abinda ya shigo musu, musamman abinda ya kasance sabon abu.

BOROROJI suna da wata muguwar dabi'a wacce take salwantar da rayukan mata da yan mata, mace kome girman mata idan har tsautsayi ya faÉ—a akanki shikenan.

Ismail Mohammed Wodaadabe.
Shine cikakken sunan Sama'ila, yana da kanwa daya tal a duniya Aminatu.

       Dayawa abokan shi sun sha mishi barazana zasu dauke Kanwar shi, amma bai tab'a damuwa da haka ba, sabida yasan abinda ya shiryawa, wani mugun hali da yake dashi. Shine yawancin matasan bororo suna zuwa mishi yayi musu aiki, kuma idan yayi kamar yankar wuka taci.

         Umar sanda shine cikakken sunan abokin shi saurayin Kanwar shi Aminatu. Zaune suke a kasar bishiya.
"Ila, shin da gaske zaka babu kanwarka dan naga baku da dangi ko daya a wannan rigar kace suna can mali"

Mik'ewa yayi bayan ya kad'e jikin shi ya rufe Alqur'anin shi. Yana faÉ—in.
"Duk cikin abokaina kai ne kawai kace min kana son auren Aminatu sauran kuwa cewa suke zasu yi *CIRENTA*  shi yasa na amince ka nemi aurenta kai ma ai ba dangin ne da kai ba."

"Toh meye na bakar magana? Daga tambaya sai bakar magana ta biyo baya." Kallon shi yayi da wutsiyar ido, yace mishi.
"Ba bakar magana ba ce farar magana ce."
"Ai kaji ka mutumin banza kawai"
"Idan ni mutumin banza ne toh Sannun na Allah" ya faÉ—a yana kad'a kan shanun shi.
"Ban da ina girmama Aminatu da ba zan tab'a yarda na bi ka ba"
"Idan baka bini ba sai na fadi na mutu dan ka ki bina"

"Wai kan Ila bakinka baya mutuwa ne?"
"Sai ranar da kasa ta rufe min ido" ya faÉ—a abin shi haka bai dame shi ba, sai ma kara hada kan dabbobin shi yake suka bar gurin kiwon, ba tare da ya gayawa Sanda ba, ranar juma'a, Sanda ya shiga gari juma'a aka daura auren Aminatu,
8/19/21, 12:42 PM - My Mtn Number: 🐂🐂BOROROJI🫀🫀 
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
Littafi na D'aya...

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Idris
I'm on Instagram as @s.square_fashion_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=gorfmwut2x22&utm_content=cgl6gfx
     ```Zaku iya samun kayan mu daga turaren zamani na wuta, shu'umar humra, dambun nama na mata, tsumin. Da sauran su kayan mu ba irin nasu bane sai an gwada akan san na kwarai..... Akwai haɗin kayan amare da na uwargida...🗣️🗣️Friday  Promo!!! Buy 13pcs @15k only : Turaren wuta 5pcs, humra 3pcs, Turaren tsugunno, shu'umar humra, mopping and toilet perfume, curtains and carpet parfume &kasko💃🏻💃🏻```

Zuciyar Mutum..!
BABI NA HUDU

Koda Sanda ya dawo aka bashi labari, mamaki ya bashi yadda aka daura.
"Nagode sosai Abokina" duk ya rasa yadda zai mishi godiya, sai ga kuka.
"Ji sakarai."

Ya fada yana murmushi,
"Nagode"
"Abinda nake so ka rike min ita da Amana, shine abinda zaka min tsakani na da kai"

"Insha Allah zan rike ta, da amana Insha Allah ba zaka tab'a samu na da laifi ba."
Ba iya shi ba hatta sauran abokan su, sunyi matukar mamaki da abinda Ila yayi, sai ma dai kawai matsalar da aka samu wani abokin su da ya tab'a niman Aminatu har suka sami matsala da Sama'ila, shine kawai yayi barazanar dauke ta.

    Dan haka shima Sama'ila da ta shi, bai tsaya ba dan ya san halin su na Fulani da aikata abinda suka fada, sai yayi maza ya kad'a hankalin mutumin yayi gaba, haka ya saka suka zauna lafiya.

   Bayan shekara daya da auren su, Ado wani abokin Sama'ila ya gayyaci Sama'ila bikin shad'i na wani abokin shi a rugar Alu, suka tafi tare, dan sun  tafiya da Sanda yace ba zai sami zuwa ba.

   **
Malam Hamza Ja'e Bugaje, babban malami ne a cikin rugar kowa yasan shi da mutunci da kamala, dattijon arziki. Haka yasa ake daraja shi. Kuma abin burgewa Ardo Mustapha babban Aminin shine dan har sunyi baikon yaran su, Zainab Abuh da Kabiru Almustapha, sai dai Zainab tana karatun ta na sankadire, kasancewar Malam Ja'e yayi cuɗanya da mutane, yasa ya saka yar shi karama  a makarantar boko, duk da ana ganin kamar yazo da bidi'a amma haka bai saka ya fasa abinda yayi niyya ba.

       Tsakanin Kabiru da Zainab akwai soyayya mai karfi sosai, wanda ya saka kowa yake ganin kamar bai zama dole su mallaki juna ba, amma sun dauki haka a matsayin kaunar suce. Zainab tana kai kindirmo cikin gari, kuma a duk lokacin da ta tafi makarantar boko take tafiya da nonon, idan ta ajiye a Office din shugaban makarantar, sai ta wuce aji ana tashi zata dauki kayan ta ta nufi Asibitin Aminci da yake cikin garin Maradi. Ana take sayar da nonon.

Dr Khalid.

Matashi ne dan kabilar Buzaye, kyakyawa ne, ajin farko dogo me cikar halittar jiki. Idan ka ganshi zaka Fahimci namiji ne, mutum ne mai yawan fara'a da barkwace, haka haduwar shi da Zainab, da zolaya ya fara cewa yau yaga Yar Fulani da unifoam. Kamar da wasa aka fara.

Wata uku yana dakon sonta, bai gaya mata ba, sai ana gobe zata daina kawo nono sun gama makaranta, tana da shekara goma sha bakwai.
"Dr daga yau na daina kawo nono, sabida zanyi aure kuma."
"Kamar Ya? Wallahi ina sonki na kasa gaya miki ne, toh Allah ya sanya Alkhairi, amma Allah ya gani ina kaunarki da aure."

   Murmushi tayi sannan tace mishi.
"Kayi hakuri koda baka gaya min ba, ina da mijin da zan aura shi yasa na gaya maka ma yanzun Nagode da kaunar da kayi min."

   Haka suka rabu ita kam bata ji kome ba, sabida zuciyar ta yana ga mijin da zata aura....
***
Tunda aka fara shirin bikin nan kowa yake murna, dan haka zasu fita bikin shad'i idan aka yi kuma, zasu saka abu a fuskar su, tafi ta ta nuna musu mijinta a cikin su. Dan haka aka gayyace matasan fulani daga rugagge masu yawa.

    Kafin a fara wasan sun fita da yan mata, bakin wata rijiya suka zauna, suna hira shiru tayi tana kallon su.
"Abuh meke damunki tun jiya"
Murmushi tayi sannan tace musu.
"Babu kome kawai ina kewar kune" murmushi suka yi. Matasa ne samari suka nufi gindin rigiyar zasu sha ruwa, watsewa yan matan suka yi, ya rage sai ita. Su dake suna zaman gida sun san su waye matasan, shi yasa suka gudu Ita kuwa bata ma tab'a jin ko labarin su ba, tana dai kallon su, suka gama shan ruwa, sau daya ta d'ago kai ta kalli Sama'ila, bata kuma kara kallon shi ba, har ya juya zai tafi yace mata.
"Baki ga yan uwanki sun gudu bane ke gaki yar taurin kai?"
Sauke numfashi tayi sannan tace mishi.
"Toh meye zan guduwa? Ko mutuwa ai ba a gudunta, dan haka kuyi tafiyar ku, anan kuka same ni."

Tab'e baki yayi tare da bin abokan shi suka tafi, dayawa abokan shi,sun san yana taimaka musu gurin samun mata, amma basu tab'a jin yace yana son wata mace ba, duk da kuwa yan mata dayawa suna kawo mishi kansu ya aura Amma yake ki. Dan ce musu yake matar da zai zauna da ita yana son wacce take tankawa ne ba wacce take tsoron shi ba.

Haka yasa yake nan shirgegen tuzuru, shi baya ma niman yan matan, sau dari idan zai hadu da su dauke kanshi yaƙe, sabida baya son damuwa. Yana ganin yadda abokan shi suke kawo karan matayen su.

    "Ila yarinyar tayi maka ne?"
"Ta cika kyau da farin fata".kuma haka ne, duk cikin rugar Alu babu ta biyun Zainabu kyakyawa ce fara kuma me kyau, doguwar ma'abociyar gashi da cikar kamala, kamar mahaifinta. Mahaifiyar ta tabiyo dan bafulatanar Libya ce ko nace balarabiyar Libya, haka take fara kal da ita.

       Shi yasa duk cikin rugar aka musu lakabi da, Fulanijo. Sabida basu yi kama da Fulanin asali ba.

    Dan haka yana tafiya gizo take mishi, itace mace ta farko da ya fara gani kuma tayi mishi, dan haka yana tafiya be amma bawai yana cikin nutsuwar shi bane. Bai kuma shiga dimuwa ba, sai da aka fara wasan ya ganta itace zata zab'i Kabiru kai tsaye bai iya boye abu a ranshi ba yace mata.
"Bai dace dake ba, zan shiga shaÉ—in ni na dace dake"

        "Allah yayi min tsari, koda mazan rugar Alu sun kare wallahi na fi karfin zuwa a matsayin matar ka, balle ka duba da kyau ka ganshi, mijin aurena ne a can"
"Lallai ina sonki da aure ki hakura dashi a daura auren da ni"
"Ba zan tab'a koda ana mutuwa a dawo." Ta faÉ—a tare da juyawa ta zab'i mijinta a gurin, tana zaban shi ta gaya mishi abinda Sama'ila yake gaya mata, ai kuwa fada ya rikice a tsakanin su, dakyar aka tashi taron dan sabida faÉ—ar da aka yi,
---
Tunda ya koma gida, yake sintiri a dakin shi, yana huci sabida tsirta mishi yawu da tayi a fuskar shi. Takaici ne ya kama shi ya ciro kayan shi ya fara aikin shi da sunanta. Sai yaga haske me ƙarfi ya lalata nashi aikin. Karshe haka ya fita ya yanka tunkiyar shi ya fara aikin da ita, bai kai ga idarwa ba, yaga nashi aikin ya rufe na hasken. Har goshin asuba, kafin ya kammala. Yana idar da sallah bai tsaya ba sai rugar Alu, yana isa ana daura auren Zainab Hamza Bugaje da Kabiru Almustapha Bugaje.  Yana zuwa bai kai ga musu magana ba ya shiga cikin gidan Malam Hamza Ja'e ya dauko amarya a gaba yayi tafiyar shi da ita, sai da ya bar gurin aka samu damar ihu ko kafin abi bayan shi sun b'ata babu shi babu ita.

Koda ya dauko ta daure musu hanya yayi yadda bazasu sake su nime shi ba, ya nufi Mali da ita.

  Tunda ya tafi da ita suka yi tafiyar kwanaki kusan goma, sannan suka isa inda garin su yake, cikin wani ƙauye can, anan ya ajiye ta. Bawan Allah nan bai d'aga mata kafa ba, sai da ya rabata da kimarta, sannan ya cigaba da azabarta da ita, duk da tana kallon shi amma bata tab'a tunanin meye ya haɗa da shi ba, tana zaune dashi ne har tsawon wata biyar, sannan ya daukota ya dawo da ita, rugar Bako.

Bayan tafiyar shi iyayen ta, sun tafi har rugar. Suka samu bayanan bai ma zo garin ba ita ba, abinda ya ya saka mahaifinta komawa kenan, duk bayan sati daya sai yazo, jin labarin ko sun dawo mishi da iya. Babu su babu labarin su.

Har kusan wata biyar sannan ta dawo da ita. Ranar da ya dawo da ita, aka yi ta rigima da shi a rugar Bako. Ya kafe akan matar shi ce har itama yasa ta cewa mijinta ne, koda iyayenta suka zo yarinyar nan taki yarda akan iyayen tane, haka suka tafi suna kuka. Kuma abinka da jini sai sun tafi tayi ta kuka tana da nasani.

A wannan yanayin ta samu ciki, haka tayi ta wahala, gashi mutanen garin sun tsangwame ta, shima yayi mata wulakancin. 

Mahaifinta duk da abin ya dame shi bai fasa niyyar shi ba, dan sai da yayi kokarin lalata abinda yayi mata, yana b'oyewa ne amma tun ranar da abin ya faru, mahaifin Kabiru ya kawo mishi takardan sakin, abinda tun daga lokacin ya fara kokarin ganin ya bar garin sabida abin kunyar da ya faru da diyar shi. Bai kuma gigita ba sai da Mahaifiyar Zainab ta je yaga halin da take ciki na laulayi, wannan dalilin yasa ka suka tattara suka tafi abun su, Kabiru ne yayi taurin kai yazo ya samu Sama'ila akan lallai ya sake mata matar shi. Shi kuma ya dake shi a kanshi karshe a anan aka sami gawar shi kuma babu wanda ya isa yayiwa Sama'ila magana, suma iyayen Kabiru sun bar garin da suke, rugar ta watsa babu kowa.  Lokacin da Zainab ta ji labarin tayi bakin ciki amma bata iya magana ba, domin tana buɗe bakinta zata ji wani abu ya tsaya mata a wuya. Gashi duk abinda yayi da izza yake gaya mata, dan so yana matukar kaunar ta, amma matsalar idan ya tuna yadda ta wulakantashi a gaban jama'a, abin zafi yake mishi, shi yasa koda abokan shi suka zuga shi bai hakura ba sai da ya dauke ta ranar aurenta, da mijin. Wannan kawai ya saka shi ya Huce takaicin shi. Amma kuma lokacin da yaga cikin shi na d'agawa daga maranta ya daura musu kaunar duniyar nan ita da abin cikin domin har ya daina hulda da ita burin shi idan ta haihu a warware wancan auran a daura dashi.   Sau dayawa yana ganin k'iyayyar shi a kwayar idanun ta, bai tab'a zaton zata girma haka ba.

    Tsawon Wata goma sha biyar ana wannan yanayin, har ranar da ta haifi abin cikin ta, wanda ko fuskar shi bata kalla ba, tayi tafiyar ta, wannan abin yayi masifar mishi ciwo, yasan muguwar al'adun sun na cire mace daga gidan mijinta a tafi da ita shi ya lalata mishi kome na shi. Tunda ta tafi ya kasa koda fahimtar kanshi da zuciyar shi,  yasan ita yake so, amma bai san yadda aka yi ya iya cutar da ita da soyayyar shi ba.

       Yayi kuka yayi danasanin, ya ji a ranshi ya zalince ta, musamman abinda ya haifa, wannan abin ya saka shi jin tsanar kanshi da kanshi, meye matsayin Yaron? Meye zai gayawa Yaron? A yanzun ina uwar Yaron take, ya cuci kanshi da duniyar shi ya kore farin cikin shi da kanshi, har yayi nadaman zuwa bikin ranar. Kafin ya gudu yakan zaga yaje bayan bukkar Aminatu ya zauna yana jin shashekar kukan Yaron, zama yake yaji duniyar tayi mishi zafi da kunci shi yasa matukar zai cigaba da ganin halin da jaririn yake ciki zai iya sanya shi zuciyar shi ta buga yasa shi tafiya ya bar Aminatu da D'an shi ba wai ya gudu dan ya tsani Yaron ba, ya gudu sabida abin kunyar da ya janyo wa yaron, ya gudu domin barwa Kanwan shi da abokin shi yaron tunda Allah bai basu ba haihuwa ba, yasa shi ya bar musu shi. Kuma yayi alƙawarin ba zai tab'a dawowa ba, ya hakura da su, har da Aminatu da jinjirin. Yayi tafiya inda shima bai san zai tsaya ba shi yasa yace karta nime shi.

***
Dawo labari....
--
A hankali ta goge kwallar da ya zubo mata, tare da cewa.
"Iya wannan kawai ya isa ya tarwatsa mishi farin cikin shi....
8/19/21, 12:42 PM - My Mtn Number: *🐂🐂BOROROJI🫀🫀*
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
BOOK ONE

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Idris
I'm on Instagram as @s.square_fashion_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=gorfmwut2x22&utm_content=cgl6gfx

_Tambaya suna yawa! Wasu ina iya amsa su, wasu kuma ina kallon su na wuce su basu da Amsar a lokacin.... Kuyi hakuri labarin nan dauke yake da Zanen kaddara wanda alkalamin ƙaddara ta rubutashi ba labarin soyayya bace da za a ci soyayya akwai a soyayya labari ne wanda zaka samu yana tafiya da asalin rayuwa ban ce labarin ya faru da gaske ba, sai dai labarin iya iya tafiya kamar yadda yake faruwa a wani kaulin, zaku yi hakuri dani nima kuma zanyi hakuri da ku, idan uzurina ya shigo zan jingine nayi sabgar gabana, idan kuma na sami sarari zan baku sama da yadda kuke tsammani! Banyi alƙawarin kyautatawa ba, amma nayi alƙawarin farantawa ban yi alkawarin zai yi dadi ba, amma nayiwa kai na alƙawarin zai badda yadda zai tafi, idan kuka duba taken labarin Journey of Destiny! Wato Tafiyar ƙaddara... Dan haka idan nayi kuskuren ku min Uzuri sabida nima Yar Adam ce! Idan nayi dai-dai ku tuna da kalaman ku da tunatarwa! Kuyi hakuri dan labarin Yanzun muke Littafi ba Ɗaya fatan Alkhairi 👏_

Harshen ka...
BABI NA BIYAR.

Goge kwallar tayi tare da kurawa hatsin da aka kawo mata surfe, yau kimanin shekaru goma sha daya zuwa sha biyu, babu wanda ya tab'a ganin ta tayi fada da mutane, Allah ya zuba mata baiwar hakuri da juriya, ta kuma jure halin dan rikon su. Shi yasa yaron ya tashi da mugun kaunar su.
B'ata tab'a daga hannu da sunan dukan shi dan yayi mata laifi ba, sai Addu'a, da fatan shirya shi yasa mutanen gidan da suke, wasu ke jin haushinta, ga Mamoon da mugun sakalci, bai san yayiwa kanshi wani abu ba sai an mishi. shi yasa ya tashi a sakalce, duk abinda akewa yara masu gata shi ake mishi, kai ko takalmi Mamoon baya saka me cinyayyen kasa. Kai rigar shi ce ta yage ba zai kuma sakawa ba sai wata.

Gashi dai iyayen rikon shi talakawa ne futtik, amma bai taso da yanayin talauci ba, sai gata kamar jinin gwamna. Haka ta mike tare da shiga cikin gidan ta dauko langa ta dibo ruwa ta wanke mishi tufaffen shi, wanda duk bayan wata biyu sai an dinka mishi riga da wando, kala biyu koda su basu saka ba shi zai saka. Wani irin kauna suke mishi wanda shima Yaron yasan da haka shi yasa ya taso babu ruwan shi da kowa.

Kai zunzurutun bakin hali inji mutanen gidan dan sukan ce bai gaji halin Aminatu da Malam Sanda ba, ya dauko mugun hali a wani gurin can, ko dakin mutane baya shi, yana bakin kofar shi, gashi da farin jini yara cika suke a dakin su. Idan ya kwanta ya mike kafa yace kar ayi magana babu me tari a dakin. Idan kuwa yace a fita dan Uban Yaro ko kaho ne akan Ubanka sai ka fita wannan yasa Yara dayawa suke tsoron shi. Bai da fada amma iya maganar fatan baki ya isheka bakin cikin wani guda....

<<>>
Tunda aka nuna mishi ajin shi baban shi yayi mishi fada kafin ya ciro kudin tara ya bashi.
"Bana kudin nan yayi yawa" ya faÉ—a yana juya kuÉ—in.
"Yaron arziki kenan, bai yi yawa ba. Ka rike shi kaji karka yi faÉ—a kaji na san ka baka da abokin fada kayi karatu kaji yaron baba."
Cogewa yayi yana kifi kifi da ido.
"Almamoon meke damunka?" Duk ya rud'e.
"Baba kazo ka É—auke ni, a keken ka" murmushi yayi sannan yace mishi.
"Insha Allah zan zo da kaina, na dauke ka yayi maka?" Ya tambaye shi gyada kai yayi, sannan ya kuma raka shi bakin aji, yayiwa malamin sallama, sannan ya ce.
"Maza shiga dan Baba." Haka ta shiga bai kalli inda malamin yake ba, ya juya yana kallon Baban shi.
"Baba idan kaje gida kaci abinci kaji"
"Insha Allah dan Baba"
Sake baki suka yi suna kallon ikon Allah, wannan irin soyayyar fa, ko makarantar Firamare da ya gama basu yi wannan dirama ba, gyara jakar shi yayi yana kallon ajin kafin ya hango wani kujera babu kowa. Ya zauna.
"Meye sunanka?" Malam min ya tambaye shi.
"Almamoon Isma'il Wodaadabe" ya faÉ—a a sanyayye,
"Zauna"
Ya zauna yana kallon allon, duk da makarantar kudi ne, haka bai hana shi fahimtar yadda ake koyarwa ba, kasancewar wanda ya gama ma, na kudin ne. Ana tashi tara ya ya dauki jakar shi ya fita.
Dariya yan ajin suka mishi. Murmushi yayi musu tare da kallon su. Haka ya fita yayi break da aka dawo aji aka cigaba da karatu.

Karshe daya Baban shi ya zo da keken shi ya dauke shi a gaba, a hanyar komawar su gida ne suka bi kasuwa, baban ya saya musu kayan abincin da za ayi na dare. Sannan ya dauke shi suka tafi. Har zasu tafi wani abokin aikin Malam na rana shima buzu ne yace mishi.
"Malam Umaru, idan ka dawo ina son magana da kai" dan haka ya kawo Mamoon gida ya koma, zama yayi kusa da Mutumin yace mishi.
"Malam Nasiru gani"
"Kayi hakuri idanuna idan suka ga abu bakina baya shiru, musamman kai da muke tare da kai." Shiru yayi yana kallon ƙasa kafin yace mishi.
"Idan ka tafi ka bashi wannan zoben ya saka a hannun shi duk da kana boye mishi abu akan shi. Kayi hakuri gaskiya rayuwar shi ce akwai daukaka akwai faduwa, bayan nan ban san meye Allah ya ƙaddara ba, amma gaskiya na tausaya mishi domin wata irin ƙaddara da zata sanya shi bayyana kanshi itace ƙaddarar da zata sanya shi kuka.

Bana duba ko buga kasa, amma tabbas na hango abubuwa dayawa da yasa ba zan yaga maka ba, lokaci zai bayyana kanshi" murmushi yayi sannan yace.
"Kuyi ta mishi addu'a Ubangiji ya shiga lamarin shi. Indai har zai jarabce shi ya jarrabce shi da abin da zuciyar shi zata iya daukar shi.". Jikin Malam yayi mugun sanyi sosai.
"Karka cigaba da boye shi, domin zai fidda kan shi, wani lokacin muna son farin ciki amma sai kaga akasin ƙaddara ko tafiyar ƙaddara ta shigo mana, haka zamu yi hakuri da abinda Allah ya bamu, ba tare da mun katse wanda muke ba, idan ka duba ƙaddaran wasu sai ka zata laifi suka yiwa Allah ne yake jarabtar su.

Wani lokaci kuma kaga kamar Allah ya fison wasu shine ya basu duniya da abinda yake cikinta, Ya Allah ka jarabce mu da abinda zamu iya, karka jarabce musu da abinda na zamu iya ba. Kayi hakuri na saka ka damuwa karka yarda maganata ta sanya ka damuwa, kayi hakuri don Allah."

"Nagode sosai malam Nasiru."

Malam Nasiru irin mutnen nan ne da Allah yayi musu baiwar ilimin addinin musulunci, musamman litattafan addinin musulunci, matsalar da aka samu yana da tab'in ƙwaƙwalwa ne, domin sabida ilimin shi aka jife shi, shi yasa yake abu kamar mahaukaci, amma kuma a haka Allah yayi mishi ido, idan ya fadi abu da ya gani tabbas Allah yana tabbatar da alkhairin, sai dai idan haukar ta motsa toh kome zai fada a surdudu zai fada. Dan haka Malam yana tashi ya koma shagon malam Bukar. A kasuwar nake yana sayar da shayi, shi ya nimawa Malam Umaru gadin kasuwa, nan ya kalli Malam Umaru yace mishi.
"Naga Nasiru hoge ya kiraka, toh karka yarda da abinda zai fada dan kai ma kasan ba lafiyar kwakwala gare shi ba, dan haka ka watsar da batun da ya gaya maka shiririta ne kawai da haukar shi da ta MOTSA."

Ajiyar zuciya malam ya sauke, duk da yasha ganin idan ya fadi abu yana tabbata, haka ya saka shi watsar da batun.

***
Yana ajiye shi a kofar gida da cefene, ya juya yana faÉ—in.
"Maza shiga gida Dan Baba" haka ya shiga, tare da sallama kamar wani babban mutum, matan da suke tsakar gidan basu amsa mishi ba sai Innar shi ta fito tana amsawa.
"Barka da dawowa Dan Inna" wani irin murmushi yayi tare da kallonta yana faÉ—in.
"Yawwa Innata" ya sa kai zai shiga Dakin kai Salihu yace mishi.
"Almamoon wai da gaske ka fara zuwa boko?"
Kallon kayan jikin shi yayi, sannan yace.
"A'a ban fara ba ina jiran ranar da Iyarka zata biya min kudin ne"
" Ba dai iyata ba sai dai Iyarka"
"Eh gata nan jikin garka ta gode" ya nuna uwar Yaron da take bakin kofa zaune, ya shige da sauri dakin su. Matar me suna Murjanatu ta mike tsaye tare da cewa.
"Wallahi sai na ci Ubanka dan banza me kama da yan daudu. Me mugun hali kawai" zuba mishi ido Innar shi tayi.
"Me yasa ka cika rigima ne?"
"Kiyi hakuri" ya faÉ—a tare da gyara zaman rigar shi, yana kallon jerin gwanon kwanonin da aka shirya na abincin shi da na Baban shi. Zama yayi tare da fara cin abincin shi.
"Ya karatun kana Fahimta?" Gyada kai yayi ya a kwasar tuwon gero miyar kuka.
"Ina fahimta, sai dai yaran ajin mu ne zan koya musu Yaren da zasu Fahimta."
"Bana son damuwa, kayi hakuri mutane baka sauya musu halin su. Haka zaka gansu ka Barsu?"
"Innah?" Kallon shi tayi, sai kuma ya share maganar.
Lokacin islamiyyan na yi yaran gidan suka shirya baki daya, suka nufi islamiyyan.
***
Zaune yake yana kallon matar shi, bayan ya gama cikin abincin rana, ya labarta mata abinda suka yi yau a kasuwa, kallon shi tayi na wasu dakikai. Kafin ta sauke ajiyar zuciya.
"Me yasa ka tsaya kana sauraron shi ? Irin wadannan mutane basu da aiki sai na haddasa rikici a tsakanin zukatar al'umma insha Allah babu abinda zai sami Almamoon dina aniyar moÉ—a tabi Randa sannan ka mai da mishi zoben shi ba zai saka ba."

Ta faÉ—a tana jin kamar ta rufe mutumin da duka, ina ma da zata ganshi da ta zabga mishi mari, kwafa take a kai akai.
"Ayya Kabo kiyi hakuri mana."
"Assalamun Alaikum, Barka da gida" sallamar Almamoon ya katse musu, abinda suke fada.
"Waalaikumun Salam, shigo Babban mutum" inji Baban shi.
Yana shigowa ya ajiye allon shi yana tab'e baki.

"Yau na gaji, kai ka rantse da Allah nayi abin arziki" ya faÉ—a yana kwanciya a jikin Innar shi.
"Ai karatun ai abin arziki ne, sannun kaji tashi kasha dawwo" da sauri ya tashi ta mika mishi kofin silver, yana sha yana murmushi. Sabida yadda yaji sugar kamar zai tsinke mishi kunne.
"Innah hala baku sha ba?" Ya tambaya, mikawa Baban yayi yana faÉ—in.
"Nasha itama tasha kai ne muka ragewa"
"Allah ya kara muku budi, ya kuma raya ni, nayi muku abinda kuka min na zama me tausayi a gare ku iyaye na"
Kallon juna suka yi kafin suka ce.
"Amin Ya ALLAH"
"Toh ni dai zan tafi Almamoon ban da rigima ko;"
"Ubangiji ya kiyayye ya dawo da kai lafiya."

Haka suka mishi addu'o'in, sannan ya fita, bayan fitar shi ne suka shiga hira har ta fita tayi musu abincin dare, Alhamdulillahi suna ci sau uku a rana haka ba karamin arziki bane.

Kullum idan zai tafi makaranta Baban shi ke kai shi makarantar, haka ya mugun kawo renin hankalin a tsakanin yan ajin su, har ana mishi kallon abubuwan da yawa, akwai wani yaro me suna Abdul Hadi, kato ne ashe gurin zaman shi Almamoon ya zauna sunyi tafiya, ranar da ya dawo washi gari ya dawo makarantar, shine yazo ya ga Almamoon a kujeran shi, dama an kai mishi gulma.

Yana zuwa ya daki kujeran, zunzurutun karfin kai bai saka Almamoon d'ago kai ya kalle shi ba.
"Kai tashi min a gurin zama"
"Daga gidanku kazo dashi?" Ya tambaye shi,
"A'a daga gidan me kawo ka a keke"
"Gaskiya kan shi yasa na ganka haka ashe abinda ake fada akan ka gaskiya ne" ya faÉ—a tare da mai da hankalinsa kan Littafin gaban shi.
"Kai meye kake nufi?"
"Yo ina zan gaya maka tunda baka gane bakwai da sha bakwai, wuce kawai tukekke" ya faÉ—a tare da bashi guri ya zauna.
"Kai ba zaka zauna ba. Domin zaka shafa min bakin ka ne"
"Ni kuma zan zauna domin zaka da irinka arziki ne, zan gaya maka abin da ake fada a kan a cikin ajin"
Take yaron ya zaro idanu, kafin ya matsawa Almamoon, ya zauna . Yayi ta Bin shi ya gaya mishi me suke fada akan shi, fir yaki kashe idan ya dame shi da tambaya ya caka mishi bakar magana, haka yasa shi jan bakin shi yayi shiru, dan ya fahimci Almamoon ruwan sanyi ne dafa moda.

Haka suka ci-gaba da zama a tare da juna, har zuwa lokacin da suka saba da juna.

Dukda bai shiga harkan yan aji da mutanen makaranta, amma kuma, ilimin shi da kyawun dabi'ar shi ta janyo mishi soyayyar malamai, ta kai ko gasa aka saka shi yakewa makarantar su na daya, haka yasa malamai da dalibai ji dashi.

A hankali ya zamewa makarantar su, tauraro duk inda aka shiga makarantar ne ke gaba, har sai da shugaban makarantar ya bincika suwaye iyayen shi, daga karshe ganin yadda suke iya daukar nauyin shi dukda faffutikar rayuwa suke, yasa shi dauke musu nauyin biyan kudin Makarantar, haka ba karamin dad'i yayi musu ba, domin kuwa basu zata zai zame musu Alkhairi ba, lokaci guda ya sauya musu ƙaddarar su.

**
Lokacin da suka shiga aji uku, a lokacin ne suka tashi a gidan da suke, sakamakon sayar da gidan duk suka watse, suma suka koma wata unguwa kusa da makarantar su. A lokacin Almamoon yana da shekara goma sha biyar.

Ya zama matashin saurayi, me tashe da kanshi. A lokacin kan shi yana masifar ja ga kuma Yan mata da suke mugun rigima akan shi idan yazo har hidima suke mishi, wasa wasa yaran masu kudi suka shiga mishi barin kudi, hidima suke mishi. Idan aka yi break haka zasu mishi sayayya kayan abinci har fada ake akan shi, bai tab'a d'ago kai ya kalle su ba.

A lokacin daga Aminatu da Sanda, hankalin su yana kan shi kome yake suna kallon shi, ga Addu'a, da ake bashi na rubutu da na kariya saboda kambun baka da kambun ido, sai da ta kai baki daya basu da nutsuwa domin duk wata saiwa da itacce haka ake sassaka mishi ana bashi yana sha.

Ba sai ga Almamoon ya fara gane gane ba, ranar da ta fara ganin abu, kwana suka yi akan shi. Domin kuwa hana su runtsawa yayi. Haka suka kwana akan shi, sai goshin asuba ya samu barci.

A ranar bai je makaranta ba, sai da aka kwana biyu, sannan ya koma makaranta, sai da takai zoben da yake gurin Malam Umaru shi ya saka mishi a hannu, shine ya sami saukin abinda yake gani, sai suka kai ta kokarin rufe mishi ido, tunda garin niman gira an rasa ido baki daya.

Karshe dai da yaga suna damuwa da halin da yake ciki sai ya daina gaya musu, amma yana tsorata sosai, dan ma yana da taurin zuciya ne.

Haka suka yi jarabawar su ba gama aji uku. Suka shiga aji huÉ—u. Abu daya yake damun shi yadda abokan shi suke mishi tsaya da me muryan mata. Haka ba karamin d'aga mishi hankali yayi ba, yazo gida yana gayawa Iyayen shi. Rarrashin sa suka yi tare da gaya mishi kar ya sake ya biye musu, dan ba abokan kwarai bane. Ya fita hanyar su.

Sai ya ji maganar ya fita hanyar su, har ya fara maida hankali a abinda yake gaban shi, aka dawo da wata Daliba makarantar, me suna Salimah Dawood, kamar da wasa yarinyar ya makale mishi. Kullum sai anyi dambe da ita da wata tsuhuwar budurwan shi,(😛🙄 Maryam Mimi ayi a hankali dan baki yayi kasuwa dambe ake akan shi)

Haka zai zauna yana murmushi cikin jin dadi, ana dambe akan shi idan kaga yadda ake abin zaka fahimci yarinta ke damun su baki daya. Idan shugaban makaranta ya kira shi shaida murmushi yake sannan yace mishi.
"Yallabai ban me yasa suke dambe a kaina ba, sai dai kawai naji ana kiran suna na, Ni uwayena karatu suka turo ni ba soyayya ba, dan haka duk wacce take ganin zata iya tayi abinta, dama ta samu "

Abin yayi matukar bawa kowa mamaki, domin tunda ake dashi bai tab'a magana kan ana dambe akan shi ba, sai yau. Haka suka fito bayan anyiwa yaran fada. Tare shi Salimah Dawood tayi tana kallon shi.
"Ka kyauta abinda kayi?"
"Meye ya faru!" Ya tambaye ta,
"Toh kenan baka san meye kayi ba?"
"Ina zan sani, tunda ba ofishin yan kai kara bane ni" ya faÉ—a zai wuce.
"Wai meye ka taka ne?"
Murmushi yayi tare da ce mata.
"Abinda kike bi, abinda kika gaza gani a kan sauran mazan makarantar." Ya taka gabanta tare da kallon cikin idanunta,
"Suna kike bi, abin da nake ji dashi kike bi, shi yasa baku gaba na karatu nazo yi"

"Dan matsiyata kawai dan an damu da kai"
Murmushi yayi sannan yace mata.
"Sabida kudin Ubanki kika gaza mai da hankali akan karatun ki, kina bin malamai Office suna kara miki maki, shi yasa aka cire ki a can aka kawo ki nan, toh ki duba nan baki daya sansani na ne, kika sake na kuma kamaki kina dambe da Daya daga cikin yan matan makarantar nan sai na zane ki a gaban jama'a mata, Ni matsiya ci ne, amma kuma me tsaye akan kafarshi me bin maganar iyayen shi, bake da baki jin batun iyayen ki ba."

Haka ya yab'a mata bakar magana sannan ya barta a tsaye a gurin, tana kuka.

"Ai dama bata san waye shi bane, shi Sarkin mu ne, gashi talaka da babban zuciya, shi ba irin sakarkarun makarantar nan bane." Suka tafi suna mata dariyar renin hankali, tuni ta fara kuka me ƙarfi.

Almamoon ba yawa ba dad'i, idan yayi yawa ma sai kayi kuka da kanka
8/19/21, 12:42 PM - My Mtn Number: *🐂🐂BOROROJI🫀🫀*
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
BOOK ONE

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Idris
I'm on Instagram as @s.square_fashion_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=gorfmwut2x22&utm_content=cgl6gfx

_Real integrity is doing the right thing, knowing that nobody’s going to know whether you did it or not._

Tafiyar ƙaddara..
BABI NA SHIDA
Rayuwar da aka gina shi domin Allah tafiya yake cike da Yardan Allah, duk wata nasara tana tafe da wanda Allah ya baka, wannan shine adadin farin cikin da Almamoon wanda yayi saukar Alqur'ani wanda yayi daidai da kammala makaranta shi na Sakandiri, kuma Allah cikin ikon shi ya samu tallafin karatun jami'ar Maryam Abatcha dake garin Maradi...

Duk wani ƙaddara ta fara ne daga wannan yankin, duk wani tafiya daga nan ta fara, sai gashi cikin Ikon Allah tafiyar ta kuma canzawa izuwa Maradin.

Bayan kwashe watanni suna jiran sakamakon, yana fitowa shi da iyayen shi suka kuma dawowa Maradi domin su abinda zasu iya mishi, Allah cikin ikon shi ya kuma basu tallafin wasu mutane, suka taimaka musu har aka kammala cuku-cukun makarantar, sannan suka dawo dashi gida, aka shiga fadi tashi yadda zasu sami damar nima mishi dakin makaranta domin nauyin karatun shi aka dauka su kuma zasu biya kudin daki da na littafai, abin tausayi wannan karon ma akwatin asusun ta kuma fasawa aka samu kudi me yawa, sannan ta bawa Malam suka dawo Maradi da Almamoon aka kuma biyan kudin makaranta. Sannan suka koma.

Cikin kewar shi suke kallon shi.
"Kasan waye kai? Ka kuma san dalilin ka na zama a gurin nan, akwai al'amarin da zamu gaya maka amma a yanzun shekarunka basu kai nauyin É—aukar abinda zamu gaya maka ba.

Jami'a ba kamar Sakandiri bane, a can gidan Yanci ne. Ba gidan da zaka zauna kayi laifi wani ya fito yayi maka fada bane, guri ne na kowa kanshi ya sani, dan Allah ka dubi girman Allah karka samu kuka, kamar yadda kace zaka sanya mu, farin ciki ka cika mana burin mu, mun san ba iyawar mu bane yasa kake kare kanka Allah ne yake kare ka, zaka shiga inda babu kunya ko tsoron Allah, don Allah karka watsa mana kasa a idanu, ka taimaka kayi abinda muka turaka Allah ya tsare maka imanin ka."

Kallon su yayi yaga yadda suke share kwalla, sai yaji a ranshi akwai abubuwan da ya dace ya tambaye su. Amma kuma,
"Babana me yasa kuke son na rayu a haka? Bayan akwai matsala idan wata rana."

Rufe baki Innar shi tayi tana kuka tace.
"Ban da karatun nan bamu muna biya ba, wallahi da ka fasa, tsoron goben ka muke ji, shi yasa muka lullube farin cikin ka, kayi hakuri kayi wannan tafiyar shima kamar tafiyar ƙaddara ce, babu wanda yasan me zaka taras a gaba, don Allah karka yarda wani ya yaudare ka, kaga kai ɗaya muka mallaka, don Allah ka rufa min asiri."

Kallonsu yayi yana son tambayar su, amma a yadda yake hango firgici da tsoro ya saka shi had'iye tambayar, ya haÉ—a kayan shi da wanda yake daya sakamakon dan kudin da iyayen shi suke bashi dukda ba wani samu suke ba, dan Tun lokacin da yace musu yana son fara aiki a kasuwa suka daina barin shi yana niman abubuwan bukata, wani lokacin har kuka yake me yasa ba zai tafi kasuwa ba. Haka suke kokarin faranta mishi amma sabida sun hana shi sake yasa shi hakura.

Yadda ake kaf-kaf dashi wallahi ko mace sai haka, akwai ranar da ya faɗa ai yana da yan mata, a makarantar boko, ranar sai da Innar shi tayi zazzaɓi, idan ta kalle shi sai ya fashe da kuka, tun yana daukar abin wasa har ya shiga tashin hankali, shi yasa ya daina subul da baka, domin yana tsoron abinda zai sami iyayen shi.

Ranar Lahadi suka saka shi a mota har da kayan abincin shi, bayan an mishi fada. Kamar kullum. Basu bar tashar ba sai da motar ta bar gaban su, suka bar tashan.

Haka suka koma gida cike da kewar dan su, me cike da al'ajabi. Karfe hudu tayi musu a garin Maradi.

Daga nan makaranta ya wuce inda ya nufi can dakin kwanan dalibai, ya nufi dakin su. Ya samu dakin akwai matasa biyu shine na uku, bai musu magana ba, ya dauki kayan shi ya shiga cikin dakin, ya shirya tsaf, sannan ya bude yar robar da yazo da shi na Abinci yaci sannan ya koshi. Sannan ya wanke shi, ya fita bayan ya gyara kayan shi ya rufe ruf ya nufi kasuwa, ya sayo abubuwan da zai bukata, sannan ya dawo dakin su.

Babu ruwan shi da kowa haka suma babu ruwan su dashi, washi gari ya riga su tashi dan haka har yayi wanka bayan yayi idar da sallah, ya zauna ya dama garin kunu yasha da yar kulin da Innar shi tasa wata makociyata tayi mishi. Yana ci yana kewar Innar tashi, bayan ya gama zuwa karfe bakwai. Ya fita abin shi har ya kai bakin kofar daya daga cikin yan dakin yace Mishi.
"Malam Almamoon! Yana da kyau idan ka shigo guri kayiwa mutanen da ka samu magana koda ba zasu kula ka ba, suna na Mubarak Habib, wannan kuma Rabilu Adam, ga dan mukulin dakin guda uku ne ni daya kai É—aya shi daya, idan muka kasance bamu na daya nan idan kuma tsautsayi yasa ya fadi toh sai ka rike wannan, haka dai dukkan mu zamu kasance, dan haka ina maka fatan Alkhairi, Allah ya bada sa'a."

Duk sai kunya ta kama shi, ya fita tare da cewa.
"Nagode"

...... Haka suka kasance, duk da babu wata mu'amalar arziki a tsakaninsu amma kuma dukda haka suna gaisawa da tambayar karatu.

Bayan wata hudu lokacin da aka yi jarabawar zangon farko na karatun su dan lauya ya zab'a, sai da ya kasance dalibi mafi yawan maki a tsangayyar su, domin sunan shi ne na farko da A1 da maki 4.8, sai gashi ana niman shi ido rufe, wanda bai san shi ba so yake ya ganshi.
(Abinda yasa na ke kokarin d'aga Darajar Almamoon ba kome bane dayawa yaran da suka kasance irin wannan a cikin al'umma zaka samu Allah yayi musu baiwar ilimin da daukaka na rayuwa, gasu nan dai basu da wata wata kyakyawan nasana, amma sai ka samu irin su Allah yana taimakawa rayuwar, idan kaga irin su sun lalace toh daga marikan sune, ko iyayen su. Ko uwa ko Uba, sun kashe musu sa ransu a gaban idanun su, irin wadannan Yaran idan ka tsaya musu da addu'a, ka basu ilimin addinin, ka nuna musu muhimmancin rayuwa da girman ƙaddara, sannan ka nuna musu ai suma mutane ne masu yanci wallahi sai su maka abinda dan Sunnah bai maka ba, su din kamar kowa ne, idan da zaka bincika su, zasu gaya maka suna jin kunyar amsa sunan suna na masu yanci, karka sarewa irin su gwiwa, show dem suma suna da Yancin irin na me Uba... Zasu rayu cikin farin ciki, amma idan society's suka fara kyamar su. Dayawa sai su fada halin banza da aikata abinda iyayen su suka aikata koda yake wannan hukuncin malam bahaushe ne, idan namiji ne za boye mishi asalin shi musamman idan yana da kudi idan kuma mace ce har karshen rayuwar ta, tana girban laifin da ba nata ba, don Allah al'ummar Hausawa mu sauya tsarin rayuwar mu, wallahi dayawa wasu nason fadan halin da suke ciki mune bamu basu kwarin gwiwa da fahimtar su. Abin tausayi...)

Haka aka yi ta niman shi, shi kuma yana can wajen makarantar yana zaune, yana kallon yadda dalibai ke shiga ke fita, musamman idan suka leka sakamakon su, bai yi kyau ba. Abinda ya hana shi zuwa gurin kenan duk da akwai cunkoso mutane.
"Kai ba kai bane Almamoon?"
D'ago kai yayi ya zubawa mutumin da yake tsaye ido, malamin sune, mik'ewa yayi sa sannan yace mishi.
"Eh nine"
"Toh ka shiga makarantar ina taya ka murnan ka cinye jarabawar ka baki daya."
Rufe bakin shi yayi yana murmushi, sannan tacewa malamin.
"Nagode sosai" kura mishi ido malamin yayi, tunda yake bai tab'a ganin abinda ya burge shi sama da wannan dalibi nashi ba, murmushi yayi tare da cewa.
"Toh a kara himma"
"Nagode Insha Allah" haka ta shiga makarantar, malamin ba bin shi da ido, wani irin bugu zuciyar shi yaƙe, har sai da ya dafe kirjin shi, yana bin Almamoon da idanun.

D'aga motar din shi yayi yabi bayan shi har inda ake kallon sakamakon, sannan ya juya. Bayan sunyi hutu.

Sai da yayi ta damuwa da yaron ya dawo. Domin kawai yana jin yayi ta kallon yaron burge shi yake.
Malam Ansar Yusuf Alhgabit, shine cikakken sunan shi, fari ne daidai ba me yawa ba, yana da matsanancin jiki me kyau, kyakyawa ne, kamar yadda ya kasance shi din Bazabarmen ne, daga garin Zinder. Dan kimanin shekaru talatin da shida, bai tab'a aure ba.

Yana da kane da Mahaifiyar su, tana can, duk karshen wata yana zuwa gida, ya yi kwana biyu. Wannan hutun ba karamin gajiya yayi ba da gida, dan Allah ya jarabce shi da son ganin Almamoon.

Hutun sati Uku suka yi, amma Almamoon bai dawo a satin farko ba, sai a na biyu. Ya dawo ya bar Baban shi babu lafiya, kamar na zai dawo ba. Haka suka sashi a gaba ya dawo. Bai da walwala duk da malam Ansar Yusuf yayi ta tambayar shi bai gaya mishi abinda yake damun shi ba. Ranar juma'a aka tafiya masallatai Jumma'a, ya nufi tasha sai Damagaram, Alhamdulillahi ya dawo ya sami jikin baban da sauki sosai.

Rike kunnen shi suka yi tare da cewa.
"Shi mutum mara jin magana Allah ya shirya mana shi, sai mun fara zane ka da girmanka"
Cikin shagwaɓa yace musu.
"Wallahi satin nan ban san meye na karanta ba, tab mahaifina bai da lafiya ina Ni ina karatu, wallahi gudowa nayi naga halin da Ubana yake ciki laifine?"
Wannan kulawar da yake nuna musu yana masifar musu dad'i, dan haka suka ce mishi.
"Babu laifi tunda kana shan nono ai shikenan." Dariya yayi ta musu Kawai. Ranar Asabar suka saka shi a mota ya dawo Makarantar.

**
Ranar Lahadi ya fito zai tafi kasuwa ya hadu da Malam ANSAR.
"Ina zaka Almamoon?"
"Kasuwa zani!" Ya bashi amsa,
"Shigo na kai ka"
"Laa Nagode" ya faÉ—a tare da wuce motar, kura mishi ido Ansar Yusuf yayi ya kuma bin shi da mota.
"Shigo nace" yadda yayi maganar a dake yasa shi shiga motar cikin jin babu dad'i, ya zauna suka nufi kasauwa duk da babu wanda yayiwa wani magana amma kuma haka yayi matukar sanya Malam Ansar farin ciki, koda suka isa yayi sayayya karshe Malam Ansar ya biya kuÉ—in. Lokaci guda abin ya daurewa Almamoon kai.
"Malam wannan abun kamar bai dace ba, kuma idan ba zaka damu ba don Allah kayi hakuri karka kuma wallahi iyayena zasu min faÉ—a."

Ya fada kamar zai yi kuka.yadda yake maganar yayi matuƙar burge malam Ansar,
"Kai dube ka sai kace mace, amma yayunka mata ne ko?" Bai san ya tura baki ba, sai da yace mishi.
"Kaga abinda nake fada ba, amma kai ne auta a gidanku ko? Da alamu kai mata na biyo"

Sake fuska yayi tare da nuna mishi ya gode amma don Allah kar ya kuma wallahi karatu yazo yi ba kananun magana na,, haka suka dawo makarantar.

-- a hankali kome yake tafiya. Farin jinin shi da nutsuwar shi yasa an kuma zaɓen shi mataimakin shugaban dalibai na makaranta, duk da ko shekara bai yi ba a makarantar, a bangaren addinin sun zo bashi wani matsayi aka hada musamman masu jin haushinsa suka ce ai dan daudu ne, hatta maganar shi ta mata ce, sannan akwai wata alaƙa tsakaninsu da malam Ansar, abin da yayi mugun b'ata mishi rai kenan, ya fita hanyar malam Ansar.

A haka har suka gama aji daya suka shiga na biyu, a lokacin ma makin shi ya dara na kowa, lokacin da suka tafi hutu suka dawo, shakuwar shi da Malam Ansar tayi yawa, duk da akwai malaman da suma suke tare da Almamoon, musamman a ta bangaren addini, har tsoron shi ake idan yana karatun Alqur'an ko idan aka tambaye shi akan hukunce hukuncen addini, idan yana bayani sai ka zata babban shehin malami ne. Nan kuwa dan shekara goma sha takwas ne da ƙwaƙwalwar gigaby.

A hankali malam Ansar ya wani gari ya mutu a kaunar Almamoon, dan sau dari idan ya saka shi a gaba, da idanun shi yake sauya mishi fasali daga Namiji zuwa mace, har gani yake idan Mamoon yasha kwalliya a matsayin mace ya maza zasu yi. Dan yana girma bakin fatar shi tana kara wani irin yanayi har wani Golden Golden yake idan ya shiga rana.

Haka kawai abokan Wani dalibi da yaso a bashi mataimakin shugaban dalibai, suka nufi dakin su Almamoon suka mishi mugun duka, tare da watsa mishi kayan shi a waje, haka ya sa. Aka sami wani dalibi ya kira Malam Ansar yazo, ya dauke shi da kayan shi bayan sun rubuta Report da kome akan É—aliban. Sannan suka nufi gidajen malamai.
"Sannun ga dakin nan ka zauna kayi wanka an jima na kai ka asibiti a duba maka jiki ko kayi rauni."

"A'a ba sai mun je ba, da sauki sosai." Tunda ya shiga dakin ya rufe kofar zama yayi yaci kuka sosai. Idan kaga yadda yake kuka sai ka tausaya mishi, bayan yayi wanka ya kwanta dan jikin shi ciwo yake. Dake ya gaji yana kwanciya barci yayi gaba dashi.

Bai farka ba sai da asuba, yayi Sallah sannan ya kwanta, karfe bakwai ya tashi domin yana jin ana shara a falon, yana fitowa ya samu wata dattijuwar bafulatana ce. Kallon juna suka yi sannan tace mishi.
"Akwai abinci a cikin dakin girki inji malam idan ka tashi kaci ga magani na baka," murmushi yayi mata sannan yace Mata.
"Nagode" kara kallon shi tayi a karo na biyu, yaron ya shiga ranta"
"Meye sunaka?" Murmushi yayi mata sannan yace mata.
"Mamoon" ya zauna yana cin abinci shi a nutse, kallon shi tayi sannan ta nufi kitchen ta dibo mishi ruwan zafin da maganin ta ajiye mishi, shigowar malam Ansar ya sashi mik'ewa yana faÉ—in..
"Ina kwana malam?"
"Lafiya ya jikin naka?"
"Da sauki sosai"
"Idan ka gama kazo ka wuce makarantar ana niman ka"
"Toh" ya faɗa bayan ya sha maganin ya nufi dakin ya saka kayan shi. Sannan ya fito. Suka nufi Makaranta,. Duk wanda yaga yadda Malam Ansar ya damu da Mamoon sai da suka yi magana domin kuwa wata mahaukaciyar soyayya yakewa dalibin shi, har ta kai sai da aka yi maganar a gurin ai kuwa nan Almamoon ya gaya musu cewa babu wannan tunanin a ranshi, yasan malamin shine, bai taɓa mishi wannan abu na rashin ɗa'a ba, dan haka sune suke tunanin haka.

Kuma batu na gaskiya Almamoon bai tab'a jin wani abu na burgewa....
8/19/21, 12:42 PM - My Mtn Number: *🐂🐂BOROROJI🫀🫀*
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
BOOK ONE

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Idris
I'm on Instagram as @s.square_fashion_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=gorfmwut2x22&utm_content=cgl6gfx

_Alhamdulillahi books dina baki daya wanda nayi su na kuÉ—i suna Okada akwai masu cewa suna bukata basu da Whatsp toh ga dama ta samu ku garzaya Okada na akwai su baki daya a can da sunan RamlatArManga_

_🙄🙆🏾‍♂�? Yanzun batun mata maza ya kare an koma Malam Ansar daga Taimako 😭 sai ya zama Shayyi 🙄😏_

*Assalamun Alaikum Jama'a, Ina iyayen da suke nimawa Yaransu malaman Lesson a cikin garin Kano! Dayawa basu da lokacin da zasu zauna sunyiwa yaran su extra lesson a gida toh shakurumin ku! Akwai dalibai mata shin ke Uwa ce? Indai har haka ne toh kin tab'a tunanin akan yaranki ko? Toh indai haka ne Mommy akwai Yan matan da suka kware a fanin computer, Islamic Studies! English da sauran darusa. Karki manta Yan matan nan dalibai ne, dan haka suke niman hanyar tsayawa da kafar su. Idan kika basu karki yi tunanin kome kisaka Allah a cikin lamarin zai tsaya mana Save our ladies please ku Basu damar koyar da Yaranku insha Allah zaki ji dadin haka, hausawa sunce a rashin tayi akan bar araha! Za a samu wannan damar ce idan kana garin kano a tuntube wannan Number 08147787720 mun gode only Kano sai an gwada akan san na kwarai,*

Sirrin Zuciya...
BABI NA BAKWAI.
Sai da Almamoon yayi musu bayani da irin taimakon da Malam Ansar yayi mishi, sannan ya daura da cewa.
"Bana tunanin kome akan malamina, sannan idan ma za ayi magana ne sai dai ace shi din Kamar Yaya yaƙe min, don Allah ku daina Yaɗa labarin karya akan mu.

   Wallahi Billahi azim, malam bai tab'a min kome ba, asalima Alkhairi ne a tsakanin mu, idan nace zan fadi Alkhairin shi yawa ne dashi, dan haka kuyi hakuri. Shima Malam Ansar yayi hakuri. Da bai shiga lamarina ba, haka ba zai faru ba, su kuma masu jin ba dad'i a kaina suyi hakuri." Ya fada tare da sunkuyar da kanshi.

          Hannun shi ya had'a a fuskar shi yana kallon yaron, idan ya nutsu yana magana a yangance wallahi sai ka dauka irin yan matan nan ne, Yayi imani da Allah da zai samu hutu fatarshi sai tafi haka kyau da haduwa. Balle kuma ya haɗa sabulai da mayukan shafawa.

   Kawai hango Almamoon yake cikin riga doguwa, kamar wanda aka buge kanshi ya girgiza kai yana kallon yaron da kyau. Malamai da sauran mutanen cikin dakin taron suka bashi hakuri, da kuma tambayar shi idan bai yafe ba a dauki mataki.
"A'a ni kam na yafe"
Ya fada tare da niman izinin zai fita, babu wanda ya hana shi, anan malam Ansar yayi magana me kama hankali, tare da nuna musu muhimmancin Almamoon a cikin makarantar idan har suka sake wani abu ya same shi tabbas za ayi ta.

     A kasar bishiyar lim ya same shi yayi nisa cikin tunani, dafa kafad'ar shi yayi da sauri ta cire hannun, yana karamin murmushi.
"Yallabai"
"Kaine Yallabai, me yasa ka yafe musu?" 
Murmushi yayi sannan yace mishi.
"Suna jin babu dadi ne sabida ni ba kowa bane, kuma ina zuwa aka bani Matsayin da suka jima suna so, ko ni aka yiwa haka zan ji babu dad'i balle kuma su da suke tsofin dalibai na makaranta."

"Na zata kayi hakuri ne dan kawai an baka"  dariya ce ya subuce mishi a dan karamin bakin shi. Yace,
"Wai ni din banza? Ni din wofi akwai mutane dai da su din wasu ne, na hakura ne dan bana son tashin hankali, kome ya wuce A bar zancen" ya faÉ—a bayan ya mike daga kujeran, yace.
"Na gode da taimako, zan koma dakin kwanan mu"
"A'a ban yi niyyar ka koma dakin ku ba, idan kuma kana zargina da abinda aka fada ne toh shi kenan ka bar gidan."

   Duk sai yaji babu dad'i, tare kawai baya son takura kanshi kuma baya son takura wani, dan haka kai a kasa yace.
"Nagode"
"Toh ka jirani na kai ka gida tunda nima  na gama" ya faɗa tare da tsare shi da idanu, diriricewa yayi ya rasa inda zai saka kanshi tunda yake babu namijin da ya tab'a mishi haka, sai ya saka Mishi jin nauyin Malam Ansar sosai.
"A'a yallabai zan biya ta dakin karatu na."
"Bana son gardama" kasa yayi da ido, baki daya ya rasa me ke Mishi dad'i.
"Toh shi kenan" ya faÉ—a tare da komawa gefe ya zauna, kanshi a sunkuye. Juyawa Malam Ansar yayi zuwa cikin ofishin su na malamai yaji gulmar shi da ake yi.
"Ni nafi zargin yana bin yaron nan kawai sabida ilmin shi ba wai yadda ake tsammani ba, bayan haka bana da wata manufa akan alakar su."

"Tab! A yadda duniya ta lalace nan ne zaka yi tsammanin haka? Shima munafikin yaro yasan abinda suke kulluwa, ban da haka meye zai dauki yaron jiya ya maida shi gidan shi da babu kowa sai su? Idan mai magana wawa ne majiyin shi ba wawa bane" inji wani malami,

"Zato zunubi! Kuma tunda kuka fara wannan maganar ban saka muku baki ba, amma yana da kyau duk inda kuka ga musulmai ku kyautatta musu zato, domin babu wanda yasan daidai sai Allah, tayi mu da muke fada akan abinda bamu da tabbas mune akan b'ata basu ba, wallahi mu daina kashe wutar gaban mu muna hura na wasu sam Ansar bai da mugun nufi akan Yaron, da yana da shi da tuni ya gwada akan yaran makarantar, kuma duk  idan hazikin dalibi yake kowa zai so mu'amala da shi, musamman wannan yaron da muke mishi kallon dan baiwa, don Allah mu wanke zuciyar mu kafin mu fadi Sharrin wasu mu."

"Allahu Akbar, yanzun dama ka iya wannan nasihar kake zaune anan? Baka tafi masalaci ko kasuwa ba? Toh bari na gaya maka ba zan daina yiwa Ansar kallon mutumin banza ba, akan me zai dauke hankalin yaro karami yana jan shi a jiki, yaron nan ko magana kake mishi bai tab'a baka hankalin shi sai idan Ansar yayi mishi magana zaka ga jikin shi na rawa, dan haka akwai abinda suke kullawa wanda babu wanda ya sani sai Allah."

      Shigowar Malam Ansar yasa duk suka yi tsuru tsuru, murmushi yayi sannan ya nufi inda ya ajiye kayansa ya dauka, sannan ya juya abinci.
"Ansar Yusuf"
"La karka damu ban ji kome ba" ya faÉ—a yana lashe bakin shi, sannan ya saka kai ya fita daga ofishin, abin yayi masa zafi, kirjin sa sai zafi take kamar an cinna mata wuta,haka ya nufi gurin Almamoon. Tare da mishi alama ya taso su tafi, kura mishi ido yayi yaga yadda yake tafiya a hankali tare da dafe gefen cikin shi, lura yayi da yadda fuskar shi yake hade kamar baya jin dadi ne. A dame yace mishi..
"Meke damunka?"
Murmushi yayi sannan yace mishi.
"Kasan jiya sun dake ni a cikina, idan na zauna sosai yana mugun min ciwo, nafi son kwanciya"
Ya fada bayan ya bude bayan motar ya kwanta. Malam Ansar ya rufe motar.
"Toh mu wuce asibiti mana"
"Da wa?" Ya tambaye shi a birkice yana zare fararren idanun shi nan,
"Akwai wani bayan kai ne? Ko akwai wani a nan ne ban sani ba?"
Ya tambaye shi yana tsuke fuska, "a'a wallahi bani zuwa su min allura, kawai ka kaini gida idan na kwanta rub da ciki zai dai na min ciwo"
"Bana son shashancin,. asibiti zamu tafi"
"Toh wallahi" yadda ya zuba mishi ido ne yasa shi kasa da kai, kamar wani yaro karami ya fashe da kuka,  yana mita.
"Ni nace ba zanje ba ka matsa min lallai naje uwar me zasu min? Ni wallahi ma barin gidanka zanyi na dawo makaranta."
"Toh Allah ya baka hakuri, sai kayi ta zama da ciwo tunda baka son kulawar da za a baka." Shiru yayi yana jin shi amma yaki magana, har suka isa gida. Babu wanda ya kuma magana da d'an uwan shi, yana shiga dakin shi ya saka key tare da kwanciya a saman katifar shi da ya dawo dashi gidan, yayi rub da ciki, kwance. Har dare babu wanda ya kuma jin duriyar dan uwanshi.
Sai washi gari. Ya fito tare da kallon Malam Ansar da yake zaune ya gama shiryawa yace mishi.
"Ina kwana? Ina da test dan haka zan fita yanzun sai an jima" ya faÉ—a da sauri yana barin gidan.
"Wannan yaron ko aljanu ne suke damun shi, baki daya ya kasa nutsuwa, kana mishi magana zai fita da sauri." Murmushi Baba Mari tayi sannan tace mishi.
"Yaron kuwa bai da matsala idan ka cire rashin maganar shi, amma babu wani abu na aibu a tare dashi,yanayin shi da maganar shi yana min É—ibi da na wata wacce na sani wallahi."

"Ayya! Yawwa Baba Mari kika ce min wata kika zo nima a cikin Maradi, shin kin gane inda take?". Shiru tayi sannan tace mishi.
"Har yau ban same ta ba, sai dai na kasa cire rai da ita, domin ina Ni a jikina zamu hadu, kawai abinda na sani naje inda nake tsammanin tana nan sunce min basu nan, kimanin shekaru goma sha kenan da rasuwar matar, yaron matar ma baya nan shi da matar shi. Ina cikin halin kewa da KaÉ—aitaka, amma ganin wannan yaron ya sani jin kamar ina Da sauran dangi a duniya."

    Cikin jimami da tausayawa yace mata.
"Kiyi hakuri, Insha Allah zasu bayyana. Na tausaya miki wallahi. Kuma Yar uwanki ce ko?"
Share kwalla tayi tare da kallon kasa.
"A'a Ƴata ce karamar Ƴata ce, kamar wannan Yaron, har da tsayin da yanayin su, kawai shi bakin fata ne ya rabasu kamar yadda kagannin haka take jajjur da ita..wancan tsinannen dabi'ar tasu yasa na rasa ta har abada, nayi kokarin komawa inda suke amma shima aka ce basu nan, na yarda da Allah kuma na yarda da ƙaddara shi yasa na amshi abin hannu bibbiyu, ina kuma mata fatan Alkhairi Allah ya bayyana min ita, dangina kan sunyi min nisa sai dai nasan akwai wasu a iyakar kasar nan."
Ta faÉ—a tare da zubda kwalla, kamar ba yanzun take murmushi ba.
"Insha Allah, Ubangiji zai kawo miki mafita, shin wacce irin dabi'a ce haka?" Kallon shi tayi kafin ta zauna tayi mishi bayani, jinjina kai yayi tare da hango tsagoron rashin imani domin ban da rashin imani akan me zaka aikata haka. Hakuri ya bata sannan yayi mata sallama. Tare da barin gidan.

Yana isa makaranta, ya hango mutumin nashi dalibai sun zagaye shi, yana musu bayani. Zama yayi a cikin motar, yana kallon yadda dan karamin bakin yake motsi hannun yana bayani da ita, fuskar me dauke da dan karamin gashin baki yayi mishi cass, wani irin farin ciki ne ya kama shi, ya kara zuba mishi ido, lokacin da daliban suka shiga mishi tafi, yana murmushi.
"Ya Allah! Kai ka sanya min kaunar Yaron nan Ubangiji ka sauya min da wata ban da wannan namijin dan haukacewa zanyi." Ya fada a zauce. Kai ina ba zai iya boye sirrin zuciyar shi ba , zai gaya mishi koma yayya ne.

Daga nesa yayi mishi horn. D'ago darara daran idanun shi yayi ya zuba a kan malam Ansar, a hankali ya mikawa wata abokiyar karatun shi littafan shi. Ya nufi motar, yana zuwa ya isa inda Malam Ansar yake zaune ya kalle shi.
"Baka da aji ne Malam?" Murmushi yayi sannan yace mishi.
"Ina da shi mana, kawai ina son nayi maka magana ne, sai kuma nake ganin kamar na haukace."
"Ka haukace? Kamar ya? Bayan gaka a zaune anan din? Toh meke damun ka?"

"Shigo sai na gaya maka"
Shiga yayi yana kallon malam Ansar.
"Ka tab'a ganin mahaukaci ido da ido?"
"Eh mana, na sha ganin su,"
"Toh amma baka tab'a ganin wanda ya kai ni hauka ba?" Kallon mamaki yayi mishi sannan yace.
"Subhanallahi, me yasa kake jifan kanka da miyagun kalamai?"
"Sabida na zare?"
"Kamar Ya?"
"Sirrin Zuciya tace, zan ajiye shi har karshen rayuwata, Don Allah kar ka manta da kayi ta saka zararren malamin ka a cikin addu'ar ka, ba mamaki ko nasani saukin haukar da nake shirin farawa."

   "Toh amma ai naga lafiyar ka lau, sannan kuma babu abinda yake damunka" inji Almamoon,
"Eh mana akan idanun ka nake lafiyayye, amma a zahirin gaskiya zararre nake, idan kana jin ana zararre ni ne lamba daya. Don Allah ka sanya ni cikin addu'a ba mamaki nayi katarin samun lafiya amma na haukace sosai."

Dariya Abin ya bawa Almamoon, yayi dariya yayi dariya, shima shagala yayi da kallon yadda yake kyalkyalewa da dariya bai san lokacin da da ya tsinci kanshi da dariya ba, suka tabbata mahaukatan a cikin motar, domin daga Almamoon har Malam Ansar an rasa wanda zai dakatar da wani.....

_#girmamawa.... Zaku yi min hakuri da Uzuri na kwanaki biyar Insha Allah, zan kammala Aliyu Asadullah ne Insha Allah don Allah ku gafarce ni, na san zan saka ku jiran amma Insha Allah idan na kammala, zan baku dogon page ina muku fatan Alkhairi 👏 And wallahi naga comments din Wattpad da vote yayi kasa, Insha Allah idan na dawo toh wallahi zan muku irin na zanen ƙaddara ta ne Yanxun haka yana Okada 700�? zaka saya da shi da sauran books dina na kuɗi zaku iya samun shi a Okada, so ku motsa idan ba haka ba nima next zan bada a WhatsApp, kuma idan kika biyo ni daga Wattpad wallahi saya zaki yi shi yasa nake baku a free, idan ya koma WhatsApp toh wallahi ina gama book 1 Insha ALLAH zan kai Okada 2 ma haka. So ku karanta kafin na kai inda zan jin karan kuɗi 🤣🤸😛😜🤣😂_
8/19/21, 12:42 PM - My Mtn Number: *🐂🐂BOROROJI🫀🫀*
                   
~The Journey of Destiny💔~
  Mai_Dambu
BOOK ONE

Sadaukarwa ga
  Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Idris
I'm on Instagram as @s.square_fashion_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=gorfmwut2x22&utm_content=cgl6gfx

_Alhamdulillahi books dina baki daya wanda nayi su na kuÉ—i suna Okada akwai masu cewa suna bukata basu da Whatsp toh ga dama ta samu ku garzaya Okada na akwai su baki daya a can da sunan RamlatArManga_

Sauyin Yanayi...

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.