Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Yankan Kauna By Autar Manya.txt
Chapter 26 of 31
Tana nuna masa inda zai yi da yatsanta har suka ƙarasa bakin asibitin yayi parking Ɗin Motar tashi Ita ta soma fita sannan yabi bayanta a reciption suka haɗu da Aunty murja wadda take zaune Ummi ta tsaya a wajan Aunty Murja shi kuma ya wuce Cikin ɗakin data nuna masa wanda saadah ke kwance acikinsa.
Jikinsa a matiƙar sanyaye ya buɗe Ƙofar ɗakin ya shiga ɗan ƙaramin ɗakine mai ɗauke da gado guda ɗaya sai toilet.
Cikin Nutsuwa ya ƙarasa bakin gadon data ke kwance ruwan ma ya ƙare an cire mata bacci take sosai sai dai Ganin yadda Fuskarta ta kumbura ne yaɗan sosa ranshi a hankali ya tsaya akanta ya Jingina da bango wanda hakan yayi daidai da sanda ta Motsa tana Buɗe idanunta a hankali ta sauke su acikin nashi wata irin firgita tayi da sauri ta tashi ba shiri take Ƙoƙarin dira daga saman Gadon.........
*YANKAN ƘAUNA...I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*
*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*
*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*
_A WANI ÆANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ÆANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*
*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*
*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO
*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*19*
Ya zuba mata ido yana kallonta na wani Lokaci, kafin ya kawar da idanun nashi daga kanta, Lokacin har ta sami damar sauka daga saman gadon tana Ƙoƙarin Fita daga cikin ɗakin ma.
"Zo nan ki zauna"
Ya faɗa mata cikin ƙaramin sauti kamar mai yi mata raɗa.
Maƙe ƙafaɗa tayi kamar wata ƙaramar yarinya idanunta na kawo ruwan hawaye! shaaaa.
"Subuhanallahi, To kukan na menene?"
Ya faɗa mata cikin ƙureta da mayen kallon shi.
Shuru tayi masa shima bai ƙara yi mata magana ba, haka suka kasance yana tsaye ajikin bango ita kuma tana tsaye a bakin Ƙofa ita bata fita ba ita bata shigo ɗakin ba, Ƙirjinta sai faman harbawa yake fat! fat! sabida tsananin Tsoro tambayar kanta take yaushe yazo waye ya kawo shi inda take.
Numfashinta ne ya tsaya na wucin gadi sanda taji ƙamshin turarenshi acikin hancinta a hankali take ɗago ƙwayar idanunta tana ƙare masa kallo yana tsaye akanta gab da ita sosai kamar zai Rungumeta.
Baya ta dinga ja harta kai Jikin Ƙofa ta maƙure tana Sauke Numfashi.
A hankali ya kuma ƙarasowa gabanta dab da ita kamar zasu haɗe, Maƙure kanta ta kuma yi ajikin Ƙofa tana ƙoƙawa da Numfashinta.
"Muje ki zauna"
Taji muryarshi acikin kunnenta, Turo baki tayi gaba kafin tace.
"Ni dai ka tafi"
Ya ɗan zaro ido kaɗan wanda hakan ya ƙarawa idanunshi Girma wani sahihin kyau ya bayyana a tare dashi.
"To zan tafi amman Muje kiji"
Ya wani ja kijin da É—an tsayi.
Raɓe shi tayi ta Nufi bakin gadon ta zauna sai dai yadda tai zaman ne in ka kalleta sai kai dariya sabida kamar kace mata Ket! ne ta zura aguje.
Da sassarfa ya ƙarasa wajanta ya tsugunna a gabanta tare da kama Gefen gadon ya zuba mata ido Jin kaifin idanunshi na yawo a dukkan sassan Jikinta yasa ta ƙara shiga wani Irin yanayi na kasala da Mutuwar Jiki.
"Sai kallo kamar ƙuda"
Ta faɗa a hankali tana Ƙunƙuni.
"Ni ay nafi Ƙuda ma komai da Komai"
Ya faÉ—a ashe yaji, Toshe bakinta tayi da hannunta tana zare ido.
"Me yake damunki? Jiya naga lafiya lau Muka rabu"
Kamar Jira take yayi magana sai ta rushe da kuka! bai hanata Yin Kukan ba kuma bai daina kallonta ba, Kai jama'a Anwar ƙarshe ne wajan Miskilanci sai da tai Kukan mai isarta sannan ta tsagaita dan kanta.
Ya ciro Hanky ya miƙa mata Ƙin amsa tayi tare da juya masa baya ta turo mai Ƙeyarta.
Murmushi yayi mai sauti yana hango tarin Ƙuruciyarta.
"Please accept and wipe away your tears" ya faɗa yana kuma miƙa mata.
Ƙin amsa tayi ta cigaba da yin ƙaramin Kuka wanda sautin shi ke tashi a hankali.
"Mami so kike nima nayi kukan?"
Taji sautin Muryarshi cikin wani irin yanayi.
Mamaki furucin nashi ya bata.
"Wannan kukan naki yana damuna Dan Allah ki bari"
Ta kuma jin furucin sa.
Ajiyar zuciya ta sauke jin tayi shurun yasan shi tashi ya dawo Kusa da ita ya zauna ƙafaɗun su na jeruwa dana Juna.
Da sauri ta matsa a hankali sautin Muryarshi ke tashi.
"Bana jin zan tsaya yi Miki Æoye Æoye sabida iya Æ™wayar idanuna kaÉ—ai Kika kalla kinsan yadda nake ji game dake, Bazan takura miki akan sai naji dalilin kwanciyar ki anan ba amman ina roÆ™on ki da Ki daina Kuka wannan Kukan naki yana Æ™ara KiÉ—imani Please zaki Aure Ni?"
Gabanta ne yayi wata Mummunar faɗuwa wani irin kuka mai ƙarfi ya tawo mata Furucinsa na ƙarshe ya tsorata ta ya Kiɗimata.
A wahalce ta É—ago tana Binshi da kallo still hawaye na kwarara acikin Idanunta Shima idanunshi yana kanta sai dai bai Kuma ce mata komai ba.
"Bayan abin da kayi Min Jiya yau ma Biyoni kayi ka Ƙara tarwatsa Min sauran Farin cikina? yaudarar taka ta Koma aure na domin ka cimma Burinka Mummuna akaina?"
Tsira mata ido yayi tunda ya ganta bata taɓa yin doguwar magana dashi kamar haka ba zaƙin Muryarta ne ya ƙara Jefa shi Cikin wani yanayi bai san me zece mata ba sai ya zuba mata ido ya wani rafka tagumi yana cigaba da kallonta.
"Nidai zan aure ki sabida Allah After this I don't know what to say"
Ya faÉ—i har Lokacin idanunshi yana Kanta wayar shi ta shiga Ringing! a hankali ya É—auka yana magana wadda ba zata ce ga abin da yake faÉ—a ba.
Lokacin Nurse ta shigo ɗakin ya tashi ya fita yana cigaba da wayar Bayan ya gama wayar ya shiga wajan Likita suka ɗanyi abun da zasu yi ya Biya Kuɗin komai aka basu sallama da tarkacen magunguna ɗakin ya koma Lokacin su Ummi sun shiga wajanta yaɗan Dubi Aunty Murja wadda take gaishe dashi ya amsa a taƙaice yana ce wa zasu iya tashi ya aje su agida sabida an basu sallama yana faɗin haka ya fita wajan Mota.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.