Facala Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Facala Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 26 of 26
*page 50*
🔚🔚🔚🔚🔚🔚
****************
Tun da ga wannan lokacin wata shak'uwa da k'arin zumunci ya karfafa tsakanin Sakeena da Su'ada, har ta kai Sakeena ta hana Su'ada bawa me raino rikon Muklees, ko yaushe wajan ta take barinshi,ita zata shiryashi ta bashi abinci, don daman shi ba mai kulafacin nono bane don haka ta yaye shi.
*Bayan wasu shekaru*
Abubuwa da yawa sun faru,na dad'i da akasin hakan,ciki kuwa harda k'arin haihuwa da Su'ada tai,wanda zuwa lokacin take da Yaya bakwai,autanta me sunan Yaya Muktar ma a lokacin shekarsa takwas, sai sakeena da ta k'ara haifar y'an biyu duk mata.
Zuwa lokacin Abba yana da shekaru talatin a duniya,kuma yana can k'asar Niger inda yake safarar waken suya, yayi karatun degree dinsa a fannin kasuwanci,lalurar ciwon suga da ta zaunar da Mahaifinsa waje guda ya sa shi ke d'auke da wani sashi na nauyin gidansu,yayin da Khaleelee ke d'auke da kaso mafi yawa na dawainiyar tasu.
Su'ada da Khaleelee a yanzu ba sa kano, suna zaune a Kaduna, kasancewar tuni Khaleelee ya bar d'inki, ya sami aiki a karkashin hukumar costume.yanayin karatu ya sa basu tafi da Nusrat da Muklees can ba,suna zaune gun Sakeena,sai sauran ne tare da su.
Fannin gida kuwa suna dai wannan gidan,sai dai Khaleelee ya rusheshi duka kowanne ya mai sabon gini sama da k'asa, babu wanda zai ce Wannan gidan na su ne,in sun zo hutu nan su ke yada zango.duk karatun y'ay'an yaya Muktar da na shi shine d'aukan nauyi.
___________________
Hajiya Su'ada zaune tana wayarta don nemo number Hajiya Sakeena,Jim kad'an da shigar kiran ta d'aga, daga b'angaran Hajiya Sakeena tace "Hajjaju yanzu na ke shirin kiranki fa,da gaske yaronki ya matsa number ba ba za'a d'aga mishi biki ba,wai dole ayi kamar ya da aka sa."
Dariyar kamilallun manyan mata Hajiya Su'ada tai kafin tace "To daman ai Kune da son kai,in ba haka ba ansa biki lokaci ya k'arato kawai yarinya ta bullo da wani batu Ku kuma Ku biye mata,tabbas da Nusrat kusa da ni take zata sha bugu,to kin sata a gaba tana yin yanda taso,don haka fatana Allah ya dawo da Abba gida lfy,sati guda da dawoqarsa za'a fara biki."
Cikin mirmishi Hajiya Sakeena tace "To an fi karfinmu dai ni da y'ata, shi kenan Allah ya kaimu lokacin."
"Ameen Ameen."
Hajiya Su'ada ta amsa.
Bayan sun yi sallama ta kashe wayar tana bin labulayen da su kaiwa falon k'awanya,wani tunanin take a ranta na shekaru ashirin da su ka wuce.
Tana tuno rayuwarsu da Sakeena tun farkon aurenta har zuwa yau,wato har kullum tana k'ara tabbatar da cewa FACALA ba abokiyar ga da fad'a bace,FACALA y'ar uwace,zuwa yanzu gashi zumuncin da ke tsakanin ta da Sakeena har za su had'a yayansu na fari aure,wato Abba da Nusrat.
Wani mirmishi ta k'ara saki tana fad'in *ALHAMDULILLAH*
_*Anan na kawo k'arshen Wannan littafi nawa na FACALA, ina godiya ga sarkin da ya bani ikon rubuta shi, abunda nai dai dai Allah ya ban ladan,abunda na kuskure Allah ya gafarta min*_
_Masoya da su kai jimirin bina cikin labarin ina godiya matuk'a da gaske, Allah ya bar zumunci_
*Sharhi ko shawara*👇
*07067270055*
_Layuza kabir Adam_🥰😍🙋♀🙋♀🙋♀
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.