Aindo Part One Complete Hausa Novel
Reading file: Aindo Tantagariyar Yar Aiki Part One Complete Hausa Novel.txt
Chapter 30 of 44
*Page -59-60*
Masha Allah bayan kowa ya watse daga ita sai husseina, murmushi husseina tayi tace"to amarya ,yanzu an shigo sahun mu,zaki dandana, kema😉."
Yaye marufin kanta A'indo tayi takai ma Husseina duka cik'in wasa,tare da fadin "ke kin raina ni ko?
ni ba yayar ki bace😒"
To naji su yaya manya,ni zanyi tafiyata Kar ango yazo ya rutsa ni,au na manta kinga ba yan mata ya kamata na amshi kudin siyan baki.🤣
"Au gori zakiyi min ,ai kinsan ni na ki fada ma kowa ko."
"Eh naji dai."
Cewar Husseina,suna cik'in magana sai ga Bashir dashi da wani abokin sa,sunsha manyan kaya,Bashir yayi bala'in yin kyau,dama A'indo najin salamar su tayi mazan maida lulubin ta saman kai suka shigo.
Abokin Bash mai suna Salman ya dan tsokani amarya,sanan akayi salatin Annabi (S.A.W),tare da musu fatan Alherie,bayan sun gama Salman ya bada kudin budar baki, akayi dan wasa da dariya ,sanan yayi musu Salama Bashir ya raka sa,anan itama Husseina Idrissa yazo d'aukan ta Inda suka gaisa da Bashir Husseina tayi ma A'INDO salama,harda yar kwalar su da zasu rabu.
Bayan ta tafi ne Bashir ya dawo ya rurufe ko ina,sanan ya shigo da salamar sa,har d'akin,bisa gado ya zauna tare da yaye ma A'indo mayafin ta ,sanan yace"Masha Allah Alhamdulillah Allah shine abin godiya ,yau Allah ya nuna mana wanan ranar mai cik'e da farin ciki,Amarya sai ki tashi muje muyi Sallah mu gode Allah."
Murmushi A'indo tayi ,sanan sukaje sukayi Alwalla sukayi Sallah ,bayan sun gama ya d'auko plat ya ciyar dasu naman kaji,duk da ita bata wani sake taci ba,saboda fargaba da tsoro .yanayi yana kallon ta,ganin kyan da ta kara masa,ji yayi kamar ya hade ta dan so.
Bayan sun gama ya fita yaje d'akin sa yayi wanka,itama tashi tayi tayi wanka,ta shafe jikinta da mai da turaruka masu kamshi,tazo tasa wata doguwar rigar barci,sanan ta kwanta,tuni barci ya fara d'aukan ta.
Shima bash bayan ya gama wankan sa yasa kayan barci,tare da feshe jikin sa da turaren sa Mai sanyin dadi,ya rufe d'akin sa ya nufi nata,iskewa yayi har ta fara barci, murmushi yayi,ya rage hasken wuta,sanan shima ya kwanta saman gadon tare da jawota jikin sa.
baiyi wata wata ba ya jawota jikin sa,ya fara shafar ta,jin haka yasa A'indo bud'e idanu,saurin rufewa tayi gam cik'e da tsoro,bai wani damu ba,dan shide yanzu Kam a bukace yake,wasa ya dan fara da jikinta sanan ya hade bakin su wuri daya,tuni A'INDO ta fara wutsil wutsil da k'afafu,tana neman raba jikin ta da nashi."
"Haba Aisha! meye haka mufa ba yara bane,dan haka ki bari muyi abinda kowa keyi mana."
Bashir ya fada dan ransa ya dan fara baci da abinda take yin.
Cik'e da mamaki A'indo ta dago kai taga wai Bashir ne ya fara mata tsawa daren farko ko kuwa?.
bai damu ba,ya cire mata riga nan yaga na shanunta tsaitsaye,dasu gwanin sha'awa da kyau,ya kama su ya fara matsa,sanan ya saka baki yana tsotsa kai kace jariri,kasa juriyar ci gaba da wasan yayi,dan a matse yake,dan haka ya tashi ya bubud'e k'afafun ta,tuni A'indo ta fara kuka na tsoro,ko akan sa kokarin sa mata zandariyar sa yake,wace take karama, Addou'a yayi ya fara kokarin tura mata ita,ihu A'INDO tayi saboda radadin da taji a kasan ta,da k'yar ya samu ya shige ta,yana gama shigar ta,ya fara nishi,nan ya fara zura mata yana fitarwa, yana lasar baki,itakam A'indo ihu take tana kuka ,tare da rokon sa ya bari,abun mamaki ko minti biyar bai d'auka ba yayi realising,sanan ya sauka kanta,Yana maida numfashi,ya juya mata baya,ba'a jima ba sai jiyo munsharin sa tayi alamun har ya fara barci,kuka take kasa kasa,ranta a matukar bace,tana son ta tashi anma ta kasa,niko nayi dariya nace yarinya ai bakiji maza ba ma .
Da k'yar ta tashi ta nufi b'andaki ta kunna ruwan zafi ta shiga ciki,tana dan ihu ihu da k'yar ta d'aure ta zauna,saida ta gasa jikinta da kyau
Sanan ta fito daga ciki tayi wankan tsarki,fitowa tayi ta sake wasu kayan barcin ,tazo dan ta kwanta anma taga jini,dan haka ta shimfida salaya kasa ta kwanta a saman ta.
Alhassan a yan kwanakin nan kullum cik'in faduwar gaba yake,shi yasa yayi ya gama abinda yake ya baro garin ya dawo gida.
Bayan ya dawo nbaya ganin A'indo shine ya yanke shawarar tambayar Hajiya, murmushi Hajiya tayi tace"ai ya ta A'indo jiya aka kaita gidan miji.
Waro idanu Alhassan yayi cik'e da zanzana,tare da jin wani irin bala'i a zuciyar sa , murmushi yayi cik'in dakewa yace"Hajiya tsohuwar matata fa nake miki magana."
"To Soja na, na sani mana baka ji nace maka tayi aure ba jiya aka kaita,bai gama Jin maganar ba idanuwan sa suka rufe ruf, sai gashi ya fadi sumame da sauri Hajiya ta kwala ihu tare da neman agaji,domin Alhaji baya Nan,ya tafi K'asar waje yau da asuba saboda harkokin kasuwancin sa.
Ihu Hajiya keyi,sai ga gards nasa sunzo,tace su kama mata shi,kama sa sukayi, aka sasa a mota, aka kaisa asibitin idrissa,nan hajiya ta Kira idrissa tare da fada masa gasu bisa hanyar asibitin sa,yayi sauri yazo.
Kusan a tatare suka isa,da su Hajiya da idrissa, urgency aka kaisa aka shiga dashi,aka fara kokowar ceton ransa, gaba-daya abun nasa ya lalace,sosai ake iya kokari wajen ceton ransa,a inda su kansu likitocin abun ya fara basu tsoro.
Hajiya sai kuka take tana zuwa da dawowa.
An d'auki awa biyu a kansa ,da k'yar aka samu numfashin sa,anma kuma ba dai-dai ba,dan saida aka sa masa oxygen.
Shi kansa idrissa yana zufa ya fito,Hajiya hankali a tashe ta nufi wajen idrissa tana tambayar sa,ganin yanda hankalin Mahaifiyar tasu ya tashi dan haka ya boye damuwar sa,yace"Mom ya farfado,kuma da sauki,mun masa alurar barci ne,karki damu,mun shawo kan matsalar."
Sai a lokacin hankalin Hajiya yadan kwanta,nan take fada ma idrissa dalilin faduwar Alhassan,sauke ajiyar zuciya idrissa yayi tare da cewa dankari.
Domin kuwa ya gano dan uwan sa jinin sa ya hau sosai.
Bayan wasu awanni Alhassan ya tashi,nan ya fara sabatu yana yan surutai marar kan gado,,tare da kiran sunan A'indo,kowa saida ya tausaya masa,alurar barci aka kuma yi masa..
Da safe Bashir ne ya fara tashi, yaje yayi wanka ya tsarkake jikin sa ,yazo yayi Sallah,ya shirya cik'in farar jalabiya fara,ganin A'indo yayi can kwance a kasa, murmushi yayi ,yaje ya dadaba ta,tashi tayi,ta bud'e Idanun ta,kallon ta yayi tare da yin murmushi,yace"princess ki tashi kiyi wanka,ki wanke wanan zanin gadon da Kika bata, kidan samar mana breakfast dan yunwa nake ji."
Cik'in ran A'indo tace"tab dankari,daga aure sai fara girki,tashi tayi da k'yar,duk da zazabin da ya fara zubo mata taje ta tatare shimfidar,zata tafi ya kama hannun ta,ta juyo,yace"thanks princess.🥰"
Tasan me ma'anar thanks din,anma a zahirin gaskiya badan taji dadin abinda yayi mata ba,ai ko zawara aka kawo masa sai haka,bata mantawa,yar uwar ta harda kyauta aka mata,sanan tasan irin tatalin da miji yayi Mata,anma ita nata ko in kula,sai thanks kawai da yace mata,wai anya Bash dinta ne kuwa?
B'andakin ta shiga ta wanke zanin gadon ta shanya,sanan tayi wanka ta kara gasa jikin ta,fitowa tayi,ta shafa mai a lokacin ya fita daga d'akin ,mai ta shafa,sanan ta dan shafa pwoder da kwali,ta shafa turare lungu da sako,taje ta bud'e wadrop ta fido kaya, tasa kayan ta riga da zani na atamfa,kayan sunyi bala'in dacewa da jikin ta tayi kyau,ta Fido wani zanin shimfida ta shimfida,sanan tazo tasa sarka da yan kunne,ta gyara d'akin ta ta kunna turaren kamshi ya game d'akin, wani baban mayafi ta d'auka ta lulube jikinta Jin da tayi anata salama a waje tana lekowa ta k'ofar falon inda Allah ya taimake ,ta tarar da Husseina ta aiko dreba ya kawo masu breakfast ba karamin dadi taji ba,har tukwici taba dreban ya tafi.juyowar da zatayi ta gano Bashir tsaye bayan ta Rai a matukar bace,yayi kicin-kicin da fuska,kallon ta yayi rai a bace yace"wane irin wulak'anci ne Aisha,kinada hankali kuwa? zakizo kina magana da Kato kuma haka,look! wanan iskancin da kikeyi kowane namiji na ganin tsiraicin ki ni bazan lamunce shi a gida na ba,in ba kin raina ni ba duba dan gyalen da kika yafa,dashi kika leka waje,kuma har kina magana da wani katon da ba muharamin ki ba,duba yanda kike kamshi."
Kallon kanta A'indo tayi taga katon gyale ta yafa lokacin da taji salama ta fito,kuma iyakar fuskar ta da hannunta kawai dreban ya gani,anma meye na wani zagi kuma.
Dakewa tayi tace"Allah ya baka hakuri,wallahi baiga jiki na ba,iya fuska ne da hannu,kuma Husseina ce ta aiko Mana da breakfast."
"Mtsss ina ruwana da wa ya aiko wani breakfast nidai na fada miki wanan shine na farko kuma na k'arshe."
Yana gama fadar haka ya juya ya koma saman table nacin abinci yana huci .
Sakaka da baki A'indo tayi tana bala'in mamakin canzawar Bashir lokaci guda.
Jiki a sanyaye ta juya ta nufi table da abincin.
*Bayan sati daya*
Masha Allah jikin Alhassan ya danyi sauki anma har yanzu dai Zuciyar sa sai a hankali,kullum sai yayi kuka,Mina ko dama tun bayan bikin Idrissa ta koma Paris a cewarta bazata iya zaman Niger ba .
Bayan an salamo su,da kwana daya yana falo zaune Hajiya tana basa fruits Yana sha
Sai ga kanwar sa Halissa kamar daga sama mai aure a Niamey.da kuka ta jefar da jakar kayan ta isa wajen Hajiya ta rungume ta, tana kuka Hajiya tace"ya Salam Halissa meye haka kuma,wai daga Niamey kike ne ko kuwa?
Me akayi me ya faru."
Hankalin Hajiya a tashe,shi kansa Al'Hassan hankalin sa a tashe da ganin kanwar sa na kuka ,domin Allah ya mugun jarabtar sa da son kanansa.
Fida katon bakin gilashin dake Idanun ta Halissa tayi,sai ga tabon duka nan gefe-gefen Idanun ta.
"Ya Salam Hajiya tace ,ganin kumburin Idanun halissa ,da kuma sayun duka duk a jikin ta.
Halissa na kuka tace"Mom wallahi bana son wanan auren a raba sa,bazan iya ba,yau kimanin shekaru uku kenan kusan kullum Latif sai ya dake ni,abinda baikai bai kawo ba sai duka,ni bazan iya ba, wallahi yanzu ma daga asibiti ne na gudo na shigo jirgi na tafo,ni ba jaka bace,bazan iya ba😭😭😭."
Lumshe idanu Alhassan yayi tare da fadin "Ya Salam ,Allah na tuba,idan hukunta ni ne kake,ya Allah ka sasauta ma zuciya ta....!
Hum akoi sauran rina a kaba,muje dai zuwa......
Aci gaba da gashi🍇
Maimou love😘
[28/10 à 17:22] MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE: https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*A'INDO*
_(Tantagariyar Yar Aiki_)
✨✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨
✨✨✨✨
✨✨✨
✨✨
✨
*NA*
*MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE AM*💋
*🤝🏻ANA TARE WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*
_(We are the best Writers Among All writers_)📚
*DAGA ALKALAMIN MARUBUCIYAR*
👇
*YA MACE KOWACE DA IRIN NI'IMAR TA*,
*LABARIN MAIMOUNATOU*,
*KAICONA*,
*HASSADA GA MAI RABO*,
*YAN MATAN ZAMANI*,
*INA MATSALAR TAKE MAZAN KO MATAN*,
*MAKIRCI*,
*LATIFA*,
*CANJIN RUHI*,
*WACECE NI KAMRINA*,
*SO NE SILAR FARUWAN HAKAN*,
_and Now_👇
*LATIFA SABON SALO*,
*A'INDO (Tantagariyar Yar Aiki)*
_DEDICATED TO SADJIDA & UMMY ONTOP_
_Assalamu Aleykum,a gaskiya idan Kuna min irin haka sai na hakura na daina typing din_ _kwata-kwata haba dan Allah,ya zaku dinga yi min haka,ni nake rubuta book dina tun kar na fara nasan me zan rubuta,na tsara kayana,to dan me kuke so na bi ra'ayin wasu na canza labari na,ga masu cewa wai inason A'indo ta koma ma Al'Hassan shi yasa na kirkiri bata Bashir,da_ _masu cewar wai ya kamata A'indo taji dadin aure yanzu,kuna manta cewar kowane dan Adam da irin jarabawar da Allah ke hadasa da ita,ai ba wai sai A'indo tana laifi ba zata dinga haduwa da mazan da zasu_ _wulakanta ta ba,a'a ko bata laifi Allah zai iya jarabtar ta ,ta ko wane b'angare ubangijin mu yakan iya jaraba mu yaga zamu iya cinye jarabawar ko kuwa,misali na zauna da wata kawata wace saida tayi aure daya,daya har guda hudu anma Allah bai hadata da miji na gari ba,saida tayi na biyar sannan ta dace ,kuma dukan mazan da ta aura babu wanda zaice ga laifin da tayi masa, wallahi saide su yabi halin ta na gari bayan sun rabu da ita,to sanin kanku ana irin wanan abubuwan da dama kuma abinda muke fuskanta kenan,anma wai sai ana bina Pc ana cemin ga yanda ya kamata nayi,wasu kuma da bakaken maganganu suke bina,plz duk wace tasan bazata iya hakuri ba ta bini taga yanda Labari zai tafi ban matsa ma kowa ba ya karanta litafi Wanda yaga hakan bai masa ba,za'a iya barin sa a inda yake🙏_
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.