Aindo Part One Complete Hausa Novel
Reading file: Aindo Tantagariyar Yar Aiki Part One Complete Hausa Novel.txt
Chapter 24 of 44
*Page -47-48*
Murmushi husseina tayi ita sai taga ma yanzu A'indo har tafi ta tsiwa,zama tayi kusa da A'INDO ta dafa ta,tace"haba sis meye haka,a gani na ai gaskiya ya fada,meye a ciki,kiyi kawai abinda ya umarce ki ,idan ba haka ba kuma zan iya cewa har yanzu kina son ya Al'Hassan."
Jin haka yasa A'indo zurmut ta tashi,ta cire hijabi kawai ta sa wani,tana zumbure zumbren baki tabar d'akin,Husseina na mata dariya,domin yanzu ta gano lagwonta.
Komawa tayi da salama ta shiga,sai a lokacin ya juyo shima ya amsa salamar tata, cik'in murmushi,kallon sa tayi,ita kanta saida taji wani iri,yanda taji gabanta ya fadi,haka kawai taji gaban ta ya fadi ta kuma rasa meye silar faduwar gaban,domin kuwa kyan nasa har tsoro ya bata,"zauna ko"
Yace da ita cik'e da murmushi,zama tayi itakam sai ya zamana tamkar itace bakuwar bashi ba, gaba-daya ta rasa sukunin ta,haka kawai take jin kamar da akoi wani abu a tatare dashi.
"Yauwa my princess da fatan dai kina lfy ko?
Kuma na same ku lfy,Masha Allah yau dai ga bashir din ki ya bayyana."
Murmushin yake tayi, sanan tace"naga bashir,ashe k'yakyawa ne shi yasa ka boye min kanka."
Murmushi yayi sanan yace"yauwa Aïsha nifa ba wasa ya kawoni ba,kamar yanda kika sani kika sani na kuma fadama mahaifan ki to yanzu ma zan baki cikak'en tarihi na,nan ya fada mata kamar yanda ya fada ma su Hajiya da Alhaji.
Murmushi tayi,sanan tace"Masha Allah
Allah zaba mana abinda yafi Alherie."
Ameen yace,sanan yaci gaba da janta da zance tun bata biye masa sosai har ta saki jiki suka sha fira,anan ne taji ya kuma shiga ranta,anma ta rasa me yasa sam ya kasa kwanta mata sosai,anma kuma tasan cewar tabar ta aure sa tayi dace,dan haka indai su hajiya sun amince dashi zata yarda ta aure sa.
Sunyi awa biyu suna tadi,sanan yayi salama ya tafi tare da aje mata tsaraba ,kin amsa taso Yi saida ya nuna mata bacin ransa tukon ta amshi kayan...
Direct yana tafiya tayi b'angaren su hajiya da kayan,wanan karon hajiya kadai ke falo .
A'indo ta shigo da salama Hajiya ta amsa Mata tana murmushi,A'indo tazo ta zauna kusa da Hajiya tare da dan rungume ta tace"Hajiya na kina hutawa."
"☺ina hutawa ya ta,yaya har kun gama tadin,Kai a gaskiya yaron ya kwanta min Allah yasa siriki na ne."
Sunne kai A'indo tayi cik'e da jin kumya sanan taba hajiya leda ,tace"gashi wai tsaraba ce."
Amsa Hajiya tayi tana murmushi,su turaruka ne manya masu kamshi,da mayuka masu tsada.
Hajiya ta yaba,nan A'indo ta diba musu ita da Alhaji duk da na Mata ne,Hajiya taji dadi sosai.
Sanan tayi salama ta tashi ta koma b'angaren su,Husseina ma tayi murna,sanan ta kara bata shawara akan ta amince ma Bashir kawai,itama kuma tayi na'am da shawarar.
*Bayan sati daya*
A yau ne Alhassan ya shigo jirgi Dan zuwa K'asar sa ta haihuwa,a inda yake tafe da bacin rai,Zuciyar sa na masa wasi-wasi akan matar sa Mina ,hakan ko ta faru ne dalilin fadan da sukayi jiya,na cewar tun kusan sati biyu saura zasu bar kasar yace da Mina ta shirya,sanan akoi auren kannin sa,bata basa amsa ba,saida a gobe zasu tafi yace da ita su shirya su tafi,tace ita ba inda zata yai tafiyar sa,me zatayi a wani Niger,ita ba inda zata a takura mata,ransa yayi bala'in bacewa,sanan yace matsawar bataje wanan auren ba to wallahi zai iya rabuwa da ita,yana gama fadar haka ya gama shirin sa,washe gari k'arfe takwas na safe yayi Shirin sa shi kadai aka kaisa yajirgi ya daga dasu zuwa Niger.
a wanan lokacin kuma soyaya A'indo da Bashir ta bunkasa a zukatan su ,dan a yanda suke son juna abin baya faduwa,wata irin shakuwa ce sukayi,suna ji da juna ,koda yaushe suna like da waya suna fira,idan A'indo zata fita shi ke zuwa ya kaita a cewar sa baya son ana kalle masa mata,in yayi hakan sai yaba A'indo dariya ,tare da cewar "har na ma zama Matar taka kenan."
Sai yace sosai ma.
Ba abinda ke kashe A'indo kamar dimple dinsa.
Shirye shiryen biki ake ba k'ak'autawa,Hajiya ta d'auko mai gyaran jiki ana ma Husseina,itama A'indo ana mata, jikin su yayi luwai luwai yayi kyau ,duk sun raba ma yan Makarantar su katin gayata,dan harda dynner za'ayi, za'ayi shagalilika sosai,dan sai anyi fulani day,indiya day,dadai sauran su,abin ba'a cewa komai,domin A'indo da
Kawayen su na school suke shirye-shirye ba kama hannun yaro,kusan kulum yanzu sai kawayen su sunzo gidan an cika gida ,ayita wasa da raha.
Husseina da A'indo har wani fresh suke abin gwanin sha'awa,sun ciciko sunyi wani irin kyau.
K'arfe hudu jirgin su Alhassan ya sauka ,bai huce gida ba saida ya biya company dinsu,yayi wasu abubuwa,bayan sallah magariba,gards dinsa suka rako sa zuwa gida,shiga sukayi,direct wajen su hajiya ya huce,tarbon sa akayi sosai cik'e da murna,kowa yayi murnar ganin sa,anan akaci abinci,su A'indo dama tunda kawayen su suka fara zuwa wasu hardaga wani gari,sai suka koma cin abinci a b'angaren su.
Dan haka suna b'angaren su tare da kawayen su na school da suka fara zuwa Mimi ,Salma ,da Safna,kawayen su ne yan Niamey,sun shaku matuka hakan yasa suma sukazo bikin,anko ko kusan kala biyar kawayen amarya sukayi,itama A'indo kusan kayan su iri daya dana husseina Saidai banbancin kalla.
Bayan anyi fira sosai wajen k'arfe goma su hajiya suka shiga barci itada Alhaji,yayyin da husseina suke b'angaren falon baki suke tadin su,Alhassan ne zaune a falon baki sanye yake da t-shirt ,da wondo na sojawa iya gwiwa,sunyi bala'in yi masa kyau,fatar sa da ka ganta kasan cik'in hutu yake ,yayi fresh yayi bala'in kyau ,kafa daya kan daya,yana danna computer ,yana shan juis sanye yake da farin gilashi.aiki kawai yake a cumputer.
Salma ce ta kalli A'indo tace "sis dan Allah ki d'auko min waya ta,inajin wallahi mun barta a b'angaren su hajiya dazu,kinsan da mukazo aiki anan nasa caji kuma kinga yanzu inason Kiran Mom."
Murmushi A'indo tayi,sanye take da riga da wondo na kayan barci masu sulbi sunyi bala'in yi mata kyau,sanin cewar a yanzu Hajiya da Alhaji basa falo suna d'aki ita da Alhaji shi yasa kawai ta fita da kayan barcin dake jikin ta da kuma hulla,ta gashi kasancewar lokacin sanyi ne,kayan sunada dan kauri,tasa takalma masu gashi , daga sama, gaba-daya sai tayi bala'in kyau.
Kai kamar wata ba'indiya fitowa tayi ta iso falon su hajiya da siririya salamar ta,ko kadan hankalin ta bai kai a gunsa ba,ganin tayi tunda ta shigo bara ta huce ta aza tea Tasha,shikam tun kafin shigowar ta ya jiyo wani bala'in kamshi mai sanyaya zuciya da ruhi,wanan dalilin yasa ya aje aikin da yake ya zuba ma k'ofa idanu,har ta shigo wani irin dum gabansa ya bada,ganin wanan k'yakyawar halitar a cewar sa,har ta nufi kichen tana shirin shiga Hajiya ta sauko da yake taga A'indo ,tace"a'a A'indo lafiya dai na ganki."
Da murmushi A'indo ta juyo wanda ya kara ma face dinta kyau,tace "là Hajiya kin fito,wallahi Salma ce ta manta wayar ta a caji dazu,kuma abubuwa suka d'auke mana hankali,shine tace nazo na d'auko mata,shine nima nake son hada tea nasha."
"Ayya to yi ki hada,kije kice ma idrissa yabar Husseina yaje b'angaren su,dan in ba haka nayi bazasu iya rabuwa ba har asuba."
" To hajiya ." A'INDO tace tare da shiga kitchen
Sai a yanzu Hajiya ta lura da Alhassan zaune,Wanda ya saki baki cik'e da shagala Yana kallon A'indo wanda Jin an ambaci A'indo gaban sa yaji Yana faduwa,dan kuwa gami daya yaji yarinyar nan ta shiga ransa."
Murmushi Hajiya tayi tace"Ashe kana nan."
"Eh Mom,wacece wanan"?
Ya fada Yana nuna hanyar da A'indo tabi,
"Au wai A'indo kake nufi,ai A'indo ce tsohuwar Matar ka baka gane ta ba"?......."
Aci gaba da gashi🍇
Maimou love😘
[20/10 à 19:40] MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE: https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*A'INDO*
_(Tantagariyar Yar Aiki_)
✨✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨
✨✨✨✨
✨✨✨
✨✨
✨
*NA*
*MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE AM*💋
*🤝🏻ANA TARE WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*
_(We are the best Writers Among All writers_)📚
*DAGA AKALAMIN MARUBUCIYAR*
👇
*YA MACE KOWACE DA IRIN NI'IMAR TA*,
*LABARIN MAIMOUNATOU*,
*KAICONA*,
*HASSADA GA MAI RABO*,
*YAN MATAN ZAMANI*,
*INA MATSALAR TAKE MAZAN KO MATAN*,
*MAKIRCI*,
*LATIFA*,
*CANJIN RUHI*,
*WACECE NI KAMRINA*,
*SO NE SILAR FARUWAN HAKAN*,
_and Now_👇
*LATIFA SABON SALO*,
*A'INDO (Tantagariyar Yar Aiki)*
_DEDICATED TO SADJIDA & UMMY ONTOP_
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.