Aindo Part One Complete Hausa Novel
Reading file: Aindo Tantagariyar Yar Aiki Part One Complete Hausa Novel.txt
Chapter 22 of 44
*Page - 43-44*
Zama yayi dabas tare da dafe kai ,"ya Salam ,nikam abinda na auro ma kaina kenan,mai yasa na tafka wanan kuskuren,ai duk da ina son wayewa ba irin wanan ba,ya Allah."
A gaskiya badan daddy yayi min gargadi ba,da Yi min Allah ya Isa matsawar na saketa to da yau ba abinda zai hanani sakin Mina."
Gaba-daya Alhassan ya rasa abinda ke masa dadi.
Mina kam tana shiga d'akin ta tasa key,ta fida kayanta tsirara ,tare da d'aukan wayar ta ,ta kunna videos call da ita da wani saurayin ta johne tsirara,yana ganin surar jikin ta,shima ya tube yayi tsirara ,tare da nuno mata jijiyar sa da take tsaye yana wasa da ita yana lumshe idanu,ya salam itama Mina gwale cinya tayi ta nuna masa kasanta tana murzawa tana lumshe idanu,kawai suna iskanci tsantsa,ba ko tsoron Allah,bayan sun kawo duka,sanan sukayi salama,ta shiga b'andaki cik'e da nishadi,tana ayyana jijiyar johne,dole ma ta dandana ta,dan girman ta yayi mata,zataso taji ta a kasan ta.
Wanka tayi ta fito,tasa rigar barci ,ta sauko kasa ta gansa zaune wanda har yanzu yana nan ya daskare wuri daya,yana mamakin yanda Mina ta iya fada masa magana haka, yarinyar da take bin bayan sa tana son sa,yanzu itace ke masa wanan wulak'anci tab.
abincin ta taci ta k'oshi, sanan ta dawo ta zauna kusan sa,kamar ba abinda ya faru tace"my Man nace,ya kamata mu fara shirye-shiryen bikin mu ko,tunda kaga dai ba Wanda yasan da auren nan,nikam inada burin hada baban party,wanda kasashe zasu dinga maganar dinner na auren mu ya kagani,ya kamata a fara shirye-shiryen tunda kazo."
Ji yayi kamar ya shaketa saboda wani irin haushin ta da yakeji.
"Mtsss"
Tsaki ya buga ya tashi ya bar mata gurin ,saboda wani irin takaicin ta da yakeji,shi kansa yaso yayi dinner,anma yanzu duk auren ma ya fice masa a rayuwa.
Tabe baki Mina tayi tace"kanka akeji,nikam Babu ubanda ya isa ya hanani shanawa ta wallahi."
Shikam Alhassan d'aki ya shiga gaba-daya kansa yayi zafi,ya fara dana sanin auren Mina.
A Nigeria,Hajiya ce zaune ita da A'indo,inda take bata takardar sakin ta,cewar ta cika Alkawarin ta,dan haka itama tayi mata Alkawarin ci gaba da karatun ta,sanan bata son iyayen ta suji wanan sakin,ta rufe abun har Allah ya kawo mata miji na gari.farin ciki sosai A'indo tayi ,tare da gode ma Hajiya,ji take kamar an rabata da kaya,yanzu kam zatayi shigar ta ta Yan mata dama can tunanin akoi auren wani akanta yasa bata shigar da take so ,anma yanzu kam sai tayi yanda taga dama. Tashi tayi ta koma b'angaren su.
Anty ce tazo gidan gaba-daya a firgice,part din Hajiya ta nufa,abinda Hajiya taji a bakin Antyn su A'indo ya firgita ta,a rikice ta zari mayafin ta,suka nufi part din su A'indo yau weekend dan haka suna nan, dukansu.
Gaba-daya Idanun Hajiya sunyi jawur,daga ka gansu ita da Anty kasan suna cik'in tashin hankali,yayin da A'indo da Husseina dama tun jiya dadare gabansu ke faduwa.
Hajiya tace susa hijabin su zasuje asibiti,basu tambayi ko lfy ba,suka sa hijabin suka fito dreba ya jasu sai hospital, gaba-daya daga A'indo har Husseina sun kasa magana,saboda yanda gaban su ke faduwa,jikin su yayi sanyi.
Har suka isa suna isa
Anty ta fara Fitowa itace gaba,har d'akin da ake kai wa'inda suka kone,wato wa'inda wuta ta kone su.
Wajen wani gado sukaje,inda aka rufe wata mata da farin kyale duka jikin ta kanta kadai ke bud'e, yayin da take shaida sama sama.A'indo ce ta fara ganin ta ta dafe gabanta,ta rugo da gudu ta rungume Matar tare da fadin" Umma!! Da k'arfi wanda ya janyo hankalin Husseina itama da gudu ta karaso gurin tace "Umma, innalillahi wa'ina illaihi Raju'un,Umma me ya same ki haka?😭😭😭ina baba,hawaye ne suka sauko a idanun kuluwa mahaifiyar su A'indo, dak'yar ta iya bud'e bakin ta, cik'e da wani farin ciki duk da halin ciwo da take ciki,tace"Masha Allah kamar yanda nake fata Allah ya nuna min yara na cik'in nutsuwa da kwanciyar hankali,Wanda a kullum fatana bai huce yarana su shiryu ba,su samu tarbiya Mai kyau da ilimi ingantace ba,gashi kuma Allah ya amshi Addou'a na,Allah na gode ma da ka shirya min su,ku tsaya kuji yarana zan muku Nasiha wace nake so kuyi amfani da ita ko bayan ba Rai na,dan nasan tawa ta kare,ku zamo masu son junan ku,ku zamo masu taimakon Al'umma,ku taimaki na kasa daku,kuyi ilimi ingantace wanda zai amfani duniya,ku zamo masu yafiya da hakuri da juriya,ku rike Addinin ku,ku zamo masu bin mazajen ku a gidan auren ku,Mahaifin ku har ya cika maganar sa guda ne Allah ya muku Albarka Allah ya shiryar daku,kuyi kokarin sa mu farin ciki yayin da muke gidan mu na gaskiya."
Rungumeta sukayi suna kuka,itako tana murmushi,sanan ta yafito Hajiya da take tsaye tana kuka itama,tace"Hajiya ke mace ce ta Allah,mai halin yan Aljanna,hakika kinyi abinda na kasa yi,kin saita min yara na kin basu ilimi, ubangiji Allah ya biyaki da gidan Aljanna,ga yarana na baki amanar su,kece uwa kece uba,domin su yanzu marayu ne,dake da yar uwata na baku amanar yaran nan,nagode matuka,Allh saka miki da gidan Aljanna, Alhamdulillah ko a yanzu na cika buri na ya cika,yarana ku rike Hajiya da Antyn ku,ku rike Hajiya tamkar uwa da ta haife ku kuyi mata biyaya,idan kuka yarda kuka saba Mata ko kuka bijire mata, akan abinda ta zaba muku Allah ya isa ban yafe muku ba,Hajiya ga yaran ki nan Amana,nikam yanzu tawa tazo k'arshe zan bi baban ku."
Nan ta fara shakuwa,tare da fara kalmar shahada,inda Hajiya ke maimaitawa,itama tanayi har tazo k'arshe,tayi wani jan dogon numfashi Alamun rai yayi halin sa.
Kai daga A'indo har Husseina kusan karamin hauka sukayi, A'indo ke fadin Umma ki tashi karki barmu,ya zaku barmu a wanan duniyar dake da aban mu."
Su kansu su hajiya kuka suke matuka.
Hakan ta faru ne ne da gobarar da akayi a gidan Ado Mahaifin su A'indo,lfy lau suka kwanta,a cik'in rumfar gidan ta kara, inda Kuluwa bayan ta gama abinci sai bata kashe wutar ba,to bayan sunci abinci da yake suna mura ne,Ado ya biyo musu da maganin mura mai sa barci,hakan yasa suna Sha barci ya kwashe su a wajen, kasancewar rumfar irin ta kara ce,da zana ,a lulube take ruf,harda marufi,suna barci ikon Allah wutar iska ya kado ta zanar ta fara ci da wuta,Allah bai basu ikon ji ba,har wutar ta kama gaba-daya Nan ta fara cin su😭 a jiki,anan take Ado mai saida kifi rai yayi halin sa,Kulu ce ta samu ta fito wuta na cin jikin ta,tana ihu makwabta sukazo suka zuba mata ruwa,inda gaba-daya jikin ta wuta ta ci kanta kadai ne,Nan aka kwashe ta sai asibiti,ado kam ya kame saboda wuta kumus ta cinye sa ."
Husseina Kam har suma tayi,inda A'indo tabar kuka da taji cewar mahaifan ta sun rasu duka,wuri daya ta k'ank'ame,tana raraba idanu tsabar shok.
Hajiya ta kira Alhaji tana kuka ta fada masa, shima yaji mutuwar
Tare da fadin gashinan zuwa.,nan aka basu gawar kuluwa a ranar akaje kauye acan aka binne ta,jama'a gari sunji mutuwar sosai,saboda Ado mutumin kirki ne,ga hakuri bashida abokin fada,yayyin da kuluwa duk da tanada masifa,to tanada bala'in kirki,bata gulmar kowa,ko gulma ka kawo mata yanzu zata futuntuke ka ta kora ka,itadai barta da masifa,anma matar kirki ce.
Anan kauye akayi jana'izar su,aka kaisu mak'wancin su na gaskiya .
Nan su A'indo suka zauna su ke k'arban gaisuwa duk da basa cik'in hayacin su,Momy ita ta zauna tare dasu,Koda Lokacin tafiya France yayi domin hada taron da za'ayi ma su Alhassan,Alhaji da Idrissa kawai sukaje,shima idrissa yaje gaisuwa.
Dashi da Alhaji sukaje wajen taron Karin girman Alhassan,ko kadan Alhassan baiji dadi ba da yaji mahaifiyar sa bazata zo ba,jin cewar ta tsaya ne a dalilin A'indo yaji ya kara tsanar A'indo,so take ta raba sa da mahaifiyar sa,wanan taro da yake Mai mahinmanci a tatare dashi shine ta hana mahaifiyar sa zuwa."
Alhaji gaba-daya basu yaba da halin Mina ba,da yanda ta tarbe su,kayan jikin ta ma kumya ya basu,basu wani tsaya ba sukaje masaukin su dan bazasu iya wanan kayan kunyar ba.
Taro ne akayi na kasa da kasa ,a inda aka Kara ma Al'Hassan girma,dashi da Abass,da dayan.masha Allah taro ya kayatar ,inda suka samu baban yabo da kyaututuka daban daban,Mina sai lake ma Alhassan take ba kumya ,duk da shi yana mata fadan ta daina masa hakan anma bata ji."
*Bayan shekara daya*
Gidan Alhassan na leko muku A inda Mina ta shako kwalar rigar sa tana zazaga masa masifa,tace"ai wallahi baka isa ba ,kayi kadan yau wata daya rabon ka da ka bani hakki na,wanda kuma ba haka kake a da ba,yanzu ka kirkiro min da wanan banzan wulak'anci."
"Mina Ina matsayin mijin ki kike Kama min kwalar riga,kinsan da babu Wanda ya taba yimin irin makamancin haka,namiji ko mace,anma ke dan salon raini ni zaki shaka,idan so kike na baki hakkin ki, ki daina abinda kikeyi,Mina ace kina mace anma kullum kina club,babu ranar da zatazo baki fita ba ko zuwa party,bayan haka na hanaki fita da kananan kaya anma kina ci gaba dayi,na miki fada kinki ji,kina matsayin ki na yar musulmi,kuma bahaushiya."?
Ki sakeni, idan ba haka ba wallahi na lahira sai ya fi ki jin dadi."
"Me ka isa kayi"?
Buge mata hannu yayi,tare da marin ta,nan ya fara ball da ita,tana ihu,saida yayi mata jina jina,tukon ya barta nan kwance,nuna ta da yatsa yayi yace"gobe ma zaki kara."
Yana gama fadar haka yayi gurin aikin sa,taji jiki sosai ,da kafa taja jikin ta har ta iso gun wayar ta ,ta d'auka kira tayi bansan me tace ba,can sai ga wasu mutane su uku ,duk Mata nan aka shigo da su falon,Mina ta kalle su tace"kunga abinda mijina yayi min,inason a fida min hakki na,saboda doka ce,da french take musu wanan maganar,wato Humain right,yan tambayoyi suka mata ta basu amsa,duk karya,wajen aikin sa ta fada musu,sukaje."
A barack kafin su shiga suka nuna katin su,sanan suka fadi wanda suke nema,tafiya akayi aka shaida ma Alhassan,yace a shigo dasu,bayan sun shigo ne,sukace "sa ankai Mana karar ka ne,na taushe hakkin Matar ka,sanan kana dukan ta ,kuma munga shaida."
Sakaka da baki Al'Hassan yayi yace"ni kuma,wace Matar tawa"?
Wace ka bari a gida bayan ka duke ta ,sa muna umartar ka da ka bi mu ba tare da musu ba,."
"Wane irin hauka ne,dan an fada muku shirme sai ku hau ku zauna."
Alhassan ya fada a matukar hasale.
"Sa kayi hakuri,bama son abun yakai ga kowa yaji ,domin zai iya shafar aikin ka,kazo muje."
shiru yayi na dan wani lokaci,tabas yasan aikin su ,ba ruwan su da matsayin ka,idan doka ta hau kanka dole zakayi taka tsantsan a rabu Lfy."
Tashi yayi yace su shiga gaba,tunani ne ya fara barkatai,yanzu ace kamar shi akazo kamu ,akasa a gaba kamar wani barawo,lalai Mina tayi nisa,shikam ya auro ma kansa jangwom.
Motar sa ya shiga ,har offishin su suka isa,an karama sa,nan shugabar su ta fito,ta zauna tace"Alhassan ko dama mun kawo ka wanan wurin ne saboda mu ja maka kunne,mu babu ruwan mu da matsayin ka,da ko kai waye,idan doka ta biyo ta kanka dole zamu hukunta ka har zuwa inda k'arfin mu ya kare,dan haka ka kiyaye,ka bar ma matar ka yancin ta,Kar ka kara kokarin dukan ta,ka san wanan tsarin daga yanzu zamu zuba ido a gidan ka,ka kiyaye domin idan bakayi wasa ba har aikin ka zai iya samun matsala."
Murmushi Alhassan yayi wanda baikai ciki ba,daga gani kasan wanan abu yayi matukar bata ransa,anma ya ya iya dole yabi doka, salamar sa sukayi,kasa komawa wurin aikin yayi ya dawo gida,isketa yayi tana cin abinci,ji yayi kamar ya mangare ta,tsaki tayi ,a hasale ya tashi zai doke ta,ta daga hannu tace "kull kar ka kara ,ka sansu sarai wallahi na kara kiran su na fada musu,to wallahi wanan kakin da kake takama dashi sai ka tashi babu shi dan haka ka kiyaye."
Jimke hannu yayi ya dunkule waje daya tare da bugun bango,da sauri yabar wajen,itakam Mina dariya ta kece da ita.
Tace"dan rainin hankali gobe ma ka kara mugu kawai,kuma sex Kar kayi dani mana, inada dubun ka wa'inda idan na fita zasu biya min bukatana,muyita zama a haka."
Alhassan shigar sa d'aki,duk abinda ya gani ya fara farfasawa tare da sakin ihu ,saida yayi ma d'akin kaca kaca,sanan ya zauna ya kunna taba ya fara sha ba k'ak'autawa, ba abunda yake tunawa irin kashedin da aka Masa,ace kamar shi yanda duniya ke son sa da Alfahari dashi,shine yau aka tozarta,"Mina na tsane ki,nayi dana sanin auren ki,tabas na gane kuskuren zabi na,ya Allah."
*Bayan shekara uku*
A yau ne aka ba su A'indo sakamokon jarabawar su ta k'arshe,a inda suka gama secondry dinsu cik'e da nasarori daban daban,wanda su ke cin na daya a jarabawa.
A yau akayi bikin murnar kamala secondry dinsu,a inda akayi musu kyaututuka,a yanzu ne kuma su A'indo suka zama cikakun yan mata,wa'inda ake ji dasu,da kyansu,wa'inda duk namijin da ya d'aura Ido a kansu bayada wani buri illa yaji sun zama malakin sa .
Idan kana neman wayewa ,ilimi,kyau , kamala kazo kansu ka tsaya,a yanzu shi kansa Rabi'u idan sun fito kirari yake musu.
A zuwa lokacin kuma Alhassan ya ladaptu domin kuwa a yanzu idan akoi abinda Mina ta raina to bayan sa yake,cik'in sa ma ta zubda wajen sau uku.a cewar ta bata tashi haihuwa ba,tun yanzu ya gaji da rayawar nan,kasar sa yake son komawa,da ya nemi transfer akace a'a ya taimaka ya zauna suna bukatar sa,sun dai ce zasu basa hutun shekara daya,hakan ya masa dadi domin yanzu ba abinda yake bukata kamar zuwa gidan su cik'in yan uwan sa,da suka dawo gida,ba kamar kanwar sa da yafi so.
A cik'in wanan yanayi ne kuma aka sa ranar auren Husseina da Idrissa,wata daya,bayan an gane so da kauna da suke ma juna a inda Hajiya ta tashi ta zake ta fara gyaran husseina........
[16/10 à 12:44] MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE: https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*A'INDO*
_(Tantagariyar Yar Aiki_)
✨✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨
✨✨✨✨
✨✨✨
✨✨
✨
*NA*
*MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE AM*💋
*🤝🏻ANA TARE WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*
_(We are the best Writers Among All writers_)📚
*DAGA AKALAMIN MARUBUCIYAR*
👇
*YA MACE KOWACE DA IRIN NI'IMAR TA*,
*LABARIN MAIMOUNATOU*,
*KAICONA*,
*HASSADA GA MAI RABO*,
*YAN MATAN ZAMANI*,
*INA MATSALAR TAKE MAZAN KO MATAN*,
*MAKIRCI*,
*LATIFA*,
*CANJIN RUHI*,
*WACECE NI KAMRINA*,
*SO NE SILAR FARUWAN HAKAN*,
_and Now_👇
*LATIFA SABON SALO*,
*A'INDO (Tantagariyar Yar Aiki)*
_DEDICATED TO SADJIDA & UMMY ONTOP_
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.