Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: KUYANGA part 1 cmplt-1-1-4-1.txt
Chapter 7 of 23
Takoma daki abinta
Basu fitoba sai karfe 11 daya suka fito tana rike dashi ajikinta
Tare suka ciyar da juna tana bashi abaki yana bata
Rihannah kyakykyawar baturiyace wacce itace mace kadai dayafi so tafi kuma gamsar dashi
Tasan salo salo da luggar gamsar da namiji
Macece me tsananin kishin tsiya saita kashe mutum akan kishi
Tunda suka fuce basu dawo ba sai dare daga yawon su
Yatarta da *KUYANGA* adakinta tana bacci
Yabubbuga mata kafa ta farka afurgice ta tashizaune tana mitstsika idanu
Yace mata "nazone don inja miki kunne akan kada ki sake kiringa futowa alokacin da kikasan bakuwata na nan banason taganki zamu iya samun matsala da ita.
Tayi saurin gyada masa kai
Yajuya yafuta yana waiwayenta domin tayi masa kyau ga surarta tar wacce yake tsananin kwadayi ckn wasu kananan kaya
******
Duk yadda yake gudun RIHANNAH kada taga kuyanga saida aka sami akasi taganta domin kwananta uku agidan akai kicibus a falo
Tafito tabaroshi adakin xatayi kallo ita kuma *KUYANGA* Tafito Zata dauki Abinta akicin kuma dole saita sada kanta ta falon tunda dakinta atsakiyar falon yake yana kallon nashi
Kallon kallo aka hauyi
Ita *KUYANGA* Ba damar yin magana gashi gabanta na dukan uku uku tana ganin tasab'a doka gashi Ba turanci take jiba balle tagaidata ckn harshen turancin
RIHANNAH Tayo kanta tana fadin " _hey girl what Are you Doing here_
*KUYANGA* Tasadda kanta kasa jikinta na kyarma
RIHANNAH takarewa kuyanga kallo taga yanda yarinyar tahadu ga kayan jikinta ya amsheta wandone pensil da riga b'igil me siririm hannu ajikinta kanta ba kallabi gashinta yakwanto agadan bayanta
RIHANNAH Ta fuxgota Tana ihu kamar zata cinyeta don kishi " _When are you coming This house_?
*KUYANGA* takara furgita ta kankame jikinta takasa magana tunda bata fuskanci mema takece mataba balle tabata amsa
RIHANNAH ta gaura mata mari tana fadin " _are you mad_? _If you talk me Rubbish i will kill you now_ ganin *KUYANGA* Batada niyyar magana yasa taga kamar raina mata hankali takeyi
Tashakota ta hadata da bango
Ihu da kakarin da *KUYANGA* Keyi yasa YARIMA dake can dakinsa kwance yasa yafito aguje
Yana ganin abinda ke faruwa yayo kansu aguje yakwaci *KUYANGA* Ahannun RIHANNAH yatura *KUYANGA* Gefe yana fadin taje maza dakinta
RIHANNAH ta cakumeshi tana masa ihu akan saiya gaya mata wacece tagani agidansa
Yazabga mata mari saida taga taurari
Agigice ta sakeshi tana rike da gurin taji marin har kwanyarta tahau kuka tana tumami agurin
Yawuce ta afusace yayi dakinsa
Ta tashi tabishi tana cewa saiya kori yarinyar kokuma ita tabar masa gidan
Tasan yana sonta sosai shiyasa take fadin hakan
Amma agun yarima wannan ba abune dazai yiyuba yama xa.ai yakori *KUYANGA* To inya ma koreta ina zataje itada batasan kowa akasar ba shine dalilin xuwanta ai inhar yabiyewa son zcyr yabi zabinta tabbas zai aikata kure domin sai ya fuskanci bacin rai gun mahaifinsa inyaji toko mahaifiyarsa da bata son bacin ransa itanma ai baxata barshi ba
Dayagaji da hargowar tata saiya zare belt yaringa dukanta ko ta kyaleshi
Ranta yabaci da irin hukuncin da yayi mata wanda bata xataba
Kwana tayi tana faranta masa rai domin sau biyar yahauta kafin wayewar gari domin ita din jurauce itace tayi masa sabo da ZAZU 😅
"Oh!SU Rihanna yau ga karshenki sai akara gaba 😛
Itadai *KUYANGA* tana jiyo ihunta ana dukanta saita kara cika da tsoro taji kuma baiburgeta ba domin shine yajawa kansa dabaya dauko mata da bazasuzo suyi masa hauka agidaba.
RIHANNAH bata kwana agidanba tuni ta fuce da ita da komatsanta tayi fushi dashi sukayi baran baran aranar ………
*Hhhhh muje zuwa*
Auntyn Sayyada da Shahida ce👌🏼
[7/25, 3:33 PM] Ummi Tandama: 📿 *KUYANGA* 📿
*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*SHARHI*....
*ZUWA GAREKU MAKARANTAN LITTAFIN KUYANGA INASO INYI MUKU WANI DAN TSOKACI MUSAMMAN MASU YAWAN KAWO NASU RA,AYIN AKAN KUYANGA TOKU SANI BAWAI INA KUSHE GA BATUNKU BA INASO KUBARNI DA NAWA RA,AYIN NAYANDA NA DAUKO ABUNA, AKWAI MASU CEWA KIYI KAZA GURI KAZA!KADA KIBARI YAYI MATA KAZA!KYANTA DAMA KISAKA TAYI KAZA KO YAZAMO MEYIN KAZA!!! TO DUK INASO KUZUBA IDO KUGA KARSHENSA WANDA YAGA ABIN HAUSHI MA YACE ABIN BAI MASA BA ZAIDAINA KARANTAWA INBAN YI KAZABA DON BAI DACE BA TO FALILLAHI HAMDI NI DAMA BANYI DAN INMUKU DOLE BA DOMIN INHAR NABI TA BAKIN WASU TO LITTAFINA ZAIYI KWANA NE YATAFI LABARIN WATA MARUBUCIYAR TONIKUMA BANA FATAN INYI SATAR FASAHA YANDA NA DAUKO LABARINA ABARMIN AHAKA DOMIN DIRECTOCIN INDIA DANA KASAR MU NIGERIA DA SUKE HAUSA FILM BA DAYA SUKE DANA INDIYA BA AKWAI BAMBANCIN FASAHA KARYAR MUTUM YAGANO YANDA FILM DIN INDIYA ZAI KASANCE AKARSHE TO NIMA KADA ACANXAN RA,AYI INA KARA FADA WACCE TAGA NOVEL DINA YABATA HAUSHI AKAN STAR MACE KO NAMIJI ANYI ABINDA RANTA BAISOBA TABAR ABIN ARANTA BASAITA FURTA MARA DAD'IBA INA K'ARA JADDADA MUKU BABU FA DOLE.DOMIN KUYANGA YASAMI DAUKAKAR DA BAZAI FADUBA, KALAS*!!!! _tank you fans inayinku yanda kuke yina Allah yabar kauna_💋💘
*Nabilancy Luv*💘
(Auntyn S&S)
30-35
Da daddare *KUYANGA* Tana kwance taji shigowarsa dakin nata
Tayi saurin tashi tana masa Barka da dawowa
Ya xauna bakin gadon nata yana mata murmushi tare da Amsawa
Tayi mamaki domin bata xaci zataga fara,arsa ba ma tunda tasan ta karya masa doka tafuta alokacin dayace kada tasake tafuto in RIHANNAR tana nana gashi harsun sami sabani adalilinta tsorone ma yadarsu aranta tana tsammanin ko fada yazo yi mata
Ta takure jikinta agefen gadon
Daya fahimci atsorace take dashi sai yasha mur yace "meye kike wani matse jikinki wato kina ganin ko wani abu nazo miki ne? Ko a hotel kyaleki nayi bawai hkr nayiba yanzu kuma ba zuwa nayi na taba kiba tunda kinyi sanadin barin me debe min kewa gidan dole yazamo kece zakici gaba da deben kewar tunda dama dan hakan nataho dake bawai donki dafan girki koki gyaramin daki nake zaune dakeba don inji dadin rayuwa ta dakene dan haka kizama cikin shiri zuwa daren gobe yau ba,a gidan xan kwana ba inada Dinner din wani abokina till down kwana zamuyi acan.
Yana gama fadar hakan ya mike yafuce yabarta da fargaba aranta
Zancensa ke mata yawo akwanya tome yake nufi?
Nufinsa kenan zai maidata farkarsa innalillahi wainnailaihirrajiin Allah kayimin tsari da aikata zina.
Tarintse idonta wasu zafafan hawaye suka hau mata xarya akuncinta
MAHBUB ne yafado mata aranta domin akullum insun zauna a inda suka saba zama aikinsa ne yi mata Nasiha da wa,azi akan kamun kai ga mace dakuma tsare mutuncinta
Yanzu kenan yana nufin agoben zai santa a "ya mace ? Batada tsumi bata da dabara domin ita baiwace agareshi dolene tayi masa biyayya fatanta dai Allah yatseratar mata da mutuncinta kawai kada yayi sa.ar abinda yake da kuduri akanta
Da safiyar Allah Ta tashi da Zazzabi fargaba ce da tsoron abinda xai faru da ita yasanya mata zazzabin
Bata iya futowaba sai shadaya na safe ta mike dakyar ta nufi kicin don neman abinda zatasaka abakinta
Dafe take da kanta bari guda na mata ciwo ga jikinta zafi rau kashinta kamar ana kwankwatsarsu
Wani jiri ne yakwasheta ya yarda ita afalon bata san inda kanta yakeba ashe suma tayi ma 😳🙄
Allah cikin ikonsa sai ga SAHABI abokin Yarima yazo nemansa gidan
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.