Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: KUYANGA part 1 cmplt-1-1-4-1.txt
Chapter 20 of 23
Yaxabura yakusa yarda Yaron don furgici
Tayi saurin taro D'an ta
Eyeeee😅🙄🙄😳😳Zeenatu Ashe dama kina sonsa
Yanunata da yatsa " Baki isaba wannan suna baiminba niya cancanta inzaba bake ba Nike da iko danhaka maza kikoma kice SAFWAN za,a saka masa ba Wani sunan BAWA ba
Tayi murmushi tace masa "aika makaro aikin gama yagama mai martaba yakarba tuni Dan haka banzamo meraina nagaba daniba da zanje masa da canxa magana
Tana gama fadin hakan ta juya ta tafi abinta
Yabita da kallo yana kwafa
Da bakin ciki yakwana Tirkeken ragon daya ware zaikai don ayankawa jaririn saiya fasa bayarwa domin ba sunan dayakeso za,a sakaba bazai iya xuwar wa sarki da canjin sunan ba domin kallon arxiki ma baya samu inyaje gaidashi
Yanajin wata irin kaunar jaririn domin sonta ma yafara raguwa yadawo kan Yaron kyan Yaron yatafi dashi tabbas zaiyi fashion dashi agun abokai
Da Sassafe gida yakacame da taron suna dama tun asuba a masallaci da suka idar da sallah aka radawa yaro suna da MAHBUB
Raguna biyu manya mai martaba ya aika fadawa suka kai bangaren Bayi aka yanka amatsayin Hakika
Tabbas kowa ya aminta agidan yaro dan gatan sarkine tunda gashi sunga abubuwa da dama na soyayya daga sarkin
Ita kanta *KUYANGA* taji Dadin hakan saikuma tasake akoina tunda da ace Dan bai karbuba agidan da tuni anata tsangwamarsu
Aranar kwana tayi rumgume da d'anta tanajin wata kaunarsa na shigarta ayau da yaron ya amsa sunan Masoyinta taji kaunarsa tashiga jikinta tabbas tana masa so sosai Albarkacin son da tayiwa margayi MAHBUB
A Bangaren UMMAH Jakadiya takawo mata tsegumin yanda Sarki yakai abin yanka manya manya na hakika
UMMAH ta quta cikin Takaici tace "Lallai Ashe har soyayya aka shiryi nunawa Dan shege kenan nifa har yanzun jakadiya banyarda da jaririn nan Jinina bane tabbas akwai meshi awaje
Jakadiya kamar ta furta " Duk kamar da sukai 🙄😆
Saitaja bakinta tayi tsit sbd tsaro kada UMMAH Taji haushinta
UMMAH tace mata "kinajina ko agobe nakeso aikinki yafara akowane lokaci kika sami dama ki shaqe min Yaron yamutu shine kadai burina da farin cikina mutuwarsa inhar kika aikata hakan Alkawarukanki sunanan zanbakisu
Jakadiya tace " angama uwar dakina yanzuma can zantafi inshiga cikinsu inzauna ayi komai dani kafin gobe in aikata aikinki........
Tofa muje zuwa fans
Auntyn Sayyada da Shahida ce 👌🏻
[8/8, 10:02 AM] Ummi Tandama: 📿 *KUYANGA...* 📿
*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION_*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*Nabilancy Luv* 💘
(Auntyn S&S)
85-90
*KUYANGA* takurawa junior MAHBUB idanu tana karewa irin kyan Da Allah yabashi sai ayau taji ta kara kaunar Yaron dayaci sunan MAHBUB
Ta rumgumeshi sosai ajikinta tamkar Wanda za,a kwace matashi tana Adduar Allah yasa yagado hali da ilimi na me sunan sa
Yanata baccinsa dama yarone me hakuri inyasha nonon dare baya farkawa saisafiya
Sallar ishsha,i akayi inba,aci sa'a ba shida tashima sai safiyar
Zulaihat bata dakin nata taje sashen Inna Dije takarbo abincinta
Kafin ta dawo bacci yafara daukanta tana rungume dashi akan kirjinta
Can ta motsa da sauri da taji motsi ana shigowa tayi tsammanin ko zulaihat CE
Saitaji sanda can kuma taji tsit
Da taji dai shiru ba,a shigo dakinba saita dire junior tafuto tana kiran zulaihat saitaga bakowa atsakar gidan
Ta dau buta tashige bandaki abinta dama fitsari takeji ga cikinta yana murdawa tunsafe dama take Dan shiga toilet din tana ba haya
Acan waje kofar gida Yarimane yazo gunta yanata Neman Wanda zai aika yaji shiru tsit babu gilmin mutane sbd whether ta sanyice da wuri ake shigewa akwanta
Yananan tsaye dai dayaga zai tsayu agun saiyayi kokarin yacusa kansa kawai domin dama sallama yazo yi mata yaga dansa kafin gobe yatafi Turai abinsa
Adaidai sadda yazo saka kai cikin gidan alokacin ne Yaga fitowar mace aguje tayo waje daga ciki afurgije ba gaskiya atare da ita ta bangajeshi tazura da gudu
Baiyi kasa aguiwaba yabi bayanta yazage karfinsa yacimmata acan nesa da gidan yadamqeta
Wa zai gani inba Jakadiya ba
Tana ganinsa tasan yaganta sai jikinta yayi sanyi tunda tasan asirinta yagama tonuwa ayau
Yace mata "jakadiya kece dama?meya kaiki bangaren bayi awannan Daren meyasaki uban gudunnan ?
Take tarasa ta cewa ta diririce tafara kuka tana fadin " karufamin asiri kamar yadda narufa maka
Yanuna kansa "kika rufa min kamar Yaya?
Tace " Eh Ai inada wani sirrinka da bakowa yasaniba sai ni da mutanenka dakasa aikin
Yarima ya mamakantu da maganar jakadiya ya nuna kansa yace "Sirri kuma?ni nasaka aiki ?to akan me nayi aikin dahar kika Sani?
Tayi wata dariya kana tace " kasani cewa akan kunne na naji kabada Umarnin aje akashe Bawa MAHBUN kawai don son rai da kishin da kake dashi nasan komai yarima ayanzuma daka ganni nima akan aiki nake
Yace "wanne aiki kikaje gidansu Zeenatu awannan Daren ?
Jakadiya tace " aikin kisan kai...
Dasauri yawatsa mata Tambaya "wa kika kashe ?kada dai Zeenatun?
Ta girgiza kai babu tsoro atare da ita don tasan me ta taka " Dan Zeenatu nakashe amma mahaifiyar kace tasani hakan
Yadafe kansa "wa,iyaxubillah D'an nawa kika kashe?
Tace " kayi hkr banida laifi
Yaharxuko kanta "Kinfi kowa laifi kuma saina hukuntaki bazan kyale kiba
Tace " idan har katonamin asiri tokamar mahaifiyarka katonawa sannan nima saina tona naka asirin nabaya
Tana gama fadin haka ta tawuce abinta tabarshi da tarin bakin ciki
Kai yadafe yana fidda hawaye
Jakadiya ta cuceshi yana matuqar son Yaron nan SBD shi yazo gidan tabbas mahaifiyarsa ce taja masa komai Ashe dama ba kaunar jininsa takeba
Ihu da hargowa yajiyo ta cikin gidan Su Zeenatu itada Zulaihat ne suke kuka da karfi da neman dauki ganin anzo ankashe yaro hargida
Dayake ta bayan gidan yake tuni yai saurin barin gurin kada wani yaganshi yashiga zargi
******
Kuka sosai sukeyi gidan yacika da mutane anata jajanta mata narasuwar jaririn ta Wanda akashigo hargida aka kasheshi
Kowa mamakin wannan Abu yakeyi anata fadin lallai duk yanda akai makashin yana ckn gidan kafin tashiga bandakin haka bayan makashin yafito zulaihat ta shigo gidan
Da filo akai amfani wajen danne shi harya mutu
Saida safe aka sallaceshi aka kaishi
Da yarima aka kashi aka binne yanaji yana gani dole yai shiru bai iya bayyana wacce takashe yaronsa abin sonsaba
Ranar dama fushi yayi da mahaifiyarsa bayan adaren yaje yai mata bore da kuka akan ta aika ankashe abin sonsa jinin jikin sa
Mai martaba ma yaji mutuwar Yaron dakansa yataka yaje yaiwa *KUYANGA* Ta,aziyya domin yana son Yarinyar aransa domin Nutsuwarta
Kwana tayi tana kuka tana tuno fuskar yaronta
Aranta kuwa tanajin bazata taba yafewa Wanda yai mata wannan abuba don ancuceta saida akaga tafara kaunar yaron aka rabata dashi
UMMAH kuwa ranta fes ta cikawa jakadiya alkawarinta na abubuwan datace zata bata
Ammafa agun yarima bata jin ta dadi shiga daya shiga biyu saiya gaya mata magana tamkar ba mahaifiyarsa ba
"Kinji dadi kinraba Dan tahaliki da duniya kunji Dadin hakan Kuda Allah kuncuceni kunrabani da farincikina.
😏kunjishifa kaika manta daka sa aka raba bawan Allah da duniya Ashe abun ba dadi
Kwana uku da faruwar hakan LAMIDO yazo yi mata gaisuwa
Tafito cikin hijab har kasa
Yakura mata ido harta iso gareshi tagaidashi ckn ladabi
Ya amsa yana kallon Dan karamin bakinta mekamada alawar lollipop
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.