Complete Hausa Novels

Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: KUYANGA part 1 cmplt-1-1-4-1.txt

Chapter 10 of 23

Kayanki kaf bayardasu xanyi bazaki kara sakasuba domin kwata kwata babu na arxiki ack

Yanzu zanfita zansayo miki Dogayen riguna kala uku natabbatar baxa,a dara kwana uku biza bata samuba sannan zantaho miki da magani sbd ciwon kan naki zantaho miki da abinci ma kada kisawa kanki damuwa baxan cutar kiba ba halin na daya da yarima ba domin ni ina zuwa kasar nan ne don hutawa ba wai don lalata da mata ko yin mummunar dabi,a ba dai kiyi hkr da abinda yayi miki haka kaddarar ki take kijure kixama me tawakkali Zeenatu watarana sai labari zanje baxan dadeba

Tace ahankali "Nagode

Yace "ba damuwa kigodewa Allanki.

Yajuya xaitafi kenan tace masa "Dan Allah kada kanuna masa muna tare ina tsoron abinda xai faru tunda shike da iko da ni da kuma.…

SAHABI yakatseta da Cewa "kwantar da hankalinki nasan kina cikin tsoro kuma kina neman taimako bazan bari yasan kina guna ba zankoma gidan ma yanzun gun me gadi inja masa kunne akan kada yagaya masa

Tayi ajiyar zcy tareda kakaro murmushi tace

"To saika dawo.

Yasa kai yafice

Kai tsaye Gidan Abinci ya wuce yasiyo mata me tsadar gaske

Kana yashiga pharmacy yasiya mata magunguna hardana ciwon jiki dana zazzabi da ciwon kan

Sannan yawuce gidan Yarima yai sa,ar kuwa Baidawoba

Yakebe da Me gadin yabayyana masa komai tareda bashi kudi cinhanci

Me gadin musulmine dan kasar cameroon ne yanajin hausa sosai

Yahau gyada kai yace "bazan fadaba insha Allahu domin natausaya mata yarinyar tanada kirki tun zuwanta nadaina zama da yunwa wannan Yaro bashida kirki sam, baya ganin karama ce Amma dai kaima kayi taimako Allah yabiyaka.

SAHABI yaji dadi yayi murmushi yace "Amin ngd.suka karayin musabiha yatafi

******
Abangare guda da YARIMA ANwar yadawo gidan bai neme inda takeba ko kusa ko alama domin cikin fushi yake da ita

Kwana yayi yana tuna yanda takasance atsakaninsu domin ta bashi haushi sosai wato don yana jin dadi ajikinta shine tasami hanyar rainashi har tana iya musanta masa da sa,insa dashi lallai dolene yayi maganinta domin bazai zauna da *KUYANGAR* Da bata ganin darajar saba zai gyara mata zama

Abu daya yake masa yawo akwanyarsa Baiwarta da YANDA take wajen ni,ima tabbas awannan fage yasan ta ciri tuta ba karya yarinyar tacika mace baitabajin macen daya kusanta yajita zam -zam kamar taba

Aikoda zaiyi fushi da ita na lokaci kalilan ne bazai iya rabuwa da itaba tunda ya dan daneta yaji wani abu aransa akanta yazaune masa kamar super glu aransa

Yakwana yana tuno Dadin dayaji ajikin *KUYANGA*

Da Gari yawaye sai yashirya zaifuta gidan wani abokinsa zasu je wani shoping har ya futa kuma yai tunanin yacancanta yaganota tunda baiji motsin taba ko batada lafiya

Yana kuma son dai yaganta domin shap dinta na burgeshi da cikar kirjinta

Yana shiga abin mamaki baiganta ba baikuma ji motsinta a toilet ba har lekawa yayi

Saiyaja yatsaya a tsakiyar dakin yana tambayar kansa "to shin ina wannan yarinyar taje ne?

Yai sauri yafuta yaleka kicin namma bata nan

Yazaga bayan gidan shine har lambu yagama zagayensa yana neme nemensa amma shiru ba bayaninta balle ma wata alamar ko tana gidan

Nan kuma jikinsa yafara sanyi kada dai guduwa tayi? Yatambayi kansa

Gabansa yafadi alokaci guda

Domin yasan inhar ta gudu ba iya kai kanta gida xatayiba tunda batada kudin jirgi balle wata hanya agarin da xata iya guduwa gida

Yatafi da saurinsa yatambayi me gadi yace masa shin ko yaga fitowar Zeenatun?

Me gadin yahau girgixa kai yana nuna tu,ajjibinsa azahiri yana fadin "bangantaba tun jiya rabona da insata a ido

Yarima yace "azamanka nayau aget kamatsa na awa nawa ko minti nawa?

Me gadi yahau sosa keya yace

"Eh to dayake dai yau natashi da bacewar ciki inata shiga toilet shiyasa bana ce ko sau nawa ma nabar get ba kuma nakan dade kafin nadawo.

Yarima yadafe kai yace "Shikenan ta gudu! Nashiga uku.

Me gadi yazabura yace "ta gudu? Zeenatun innalillahi wa innailaihirrajiun.

To yanzu ina za.aje aganta wata sani a kasar nan?

Yarima yaharareshi yace "koma wata sani ko bata sanin ba ai kana da hannu aciki tunda kana wasa da aikinka baka rufe gidan yadda yakamata.

Yajuya yabar Megadi da atsaye saroro

Aifa aranar yarima yarasa tsugum yanata Faman xaryar gun jami,an tsaron garin yana basu bayanin B'atan *KUYANGA* waiko Allah zaisa aganta ahanya

Kwana biyu sukai suna checking akanta amma shiru dole yahakura yakira gida yana tambayar mahaifiyarsa

Koda UMMAH taji abinda yake faruwa daga bakinsa ta kidime tahau yi masa fada

"Yarima kodai akwai abinda kake matane?ko takura mata kayi da ayyuka da fadanka?

Yarima yace "To UMMAH inma nayi mata fadan saita gudu? Banida ikon dazan matane?kawai dai yawon bude ido nakejin ta tafi tunda idonta yabude dama bakiga yanda take shigar kananan kayaba tana son tafuta gari nahanata ashe dai xata shammaceni tagudu

Jin Hakan yasa UMMAH ta yarda tahau fada tana cewa "to ai da ba guduwa yakamata tayiba saita fada maka maza take bukata saika dawo da ita gida ayi mata Aure yanzu kaga hakan ai sharri zata jawo maka ace kai ka koreta ko cutarta kakeyi yasa ta gudu gani da mahassada ackn gida (kishiyoyi)

Kuma dole kasan TAKAWA zaiyi fada amma kabarni dashi zansan mezan fada masa

Yarima yahau godiya yanajin dadi aransa

******
Akwana na ukunta agidan SAHABI bizarta ta samu itadashi

Suka kamo hanyar dawowa Nigeria

Dayake tasaki jikinta dashi tunda taga ba cutarta xaiyiba sai suketa hirarsu ajirgi tana ta masa godiya da nuna masa farin cikinta azahiri

Shikam bakomai yake ce mata ba sai "nikam bazan daina gaya miki ina sonkiba kirike alkawari

Ta lumshe idanunta tabbas inda wanda zataso to abayan SAHABI yake amma ina yau data nufi kasarta ji take wata kaunar MAHBUB ta dawo mata sabuwa

Dayaga tashiga tunani saiyace mata "Zeenatu kada fa kisawa kanki damuwa kicire komai aranki domin ni da Aure nake sonki kuma bazan ringa miki kallon abinda yarima yai miki ba kimance da komai yadda nima zanmanta da komai haka kuma kija bakinki kiyi tsit kada kifadawa kowa abinda yasa kika dawo ko abinda yarima ke miki kimarki zata ragu agun mutane sannan za,aita yawo da maganar agidan.

Tagyada kanta tagamsu itanma ai zataso asirinta yarufu domin kada masoyinta yaji bazaiji dadiba sannan ga "yan uwanta KUYANGU abin xai iya zama abin surutu ayi mata wani kallo

Da dare suka diro kasar Nigeria bayan Ishsha'i

Har gidan sarki Abdallah yarima yadauki shatar mota aka kaisu amma shi bai bari anganshiba

Ita kadai aka sauke akodar gidan sarki aka tafi dashi zuwa hotel din dazai kama yakwana ingari yawaye ya wuce Daura garinsu

Kafin su rabu tun amota yabata waya karama kirar Tecno domin yace yana son yaringa jin muryarta akoyaushe sannan in tanada Damuwa ta sanar masa zai mata maganin damuwar

Tabbas SAHABI yagama mata komai

Shigarta gidan tun daga kofa aka fara mamakin dawowarta tunda ansan da Ita da yarima suka tafi kuma basuda labarin dawowar yariman

Kai tsaye bangarensu ta zarce bata bari kowa yagabta ba

Adakinsu mutum biyune basuyi bacci ba Zulaihat idonta biyu kawarta

Da zulaihat taganta kirji ta dafe tana fadin "wa nk gani kamar Zeenatu? Dama yau kuna tafe amma banji sanarwar ackn gidan ba

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.