Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: KUYANGA part 1 cmplt-1-1-4-1.txt
Chapter 23 of 23
" Allah nagode maka.cewar *KUYANGA*
Zulaihat tace "Ga magunguna can inji Iya Sha,awa tace kada kiyi sake da kowanne masu kyaune akwai nasha da nono dakuma nasha da Zuma anjima zata kawo miki na tsugunno
*KUYANGA* takama baki " oh maganin mata kuma tun yanzun?
Zulaihat tace "Eh aishine daidai hakan kinga abin xaifi kamaki Sosai
" Hhhmmm Allah dai yasa ba daci
Zulaita tace "koma me gareshi haka zakisha tunda kinsan Halin tsoffin nan insuka bada Abu ba,ashaba fada zasuyi suce suna mana gata muna gocewa
*KUYANGA* Tayi murmushi tadauki magungunan tafara hada wa xatasha
******
Yarima yadauki wayarsa yalalubo nambar abokinsa SAHABI da suka Dade basuyi wayaba
Acan bangaren SAHABI yana ganin kiran Yariman yayi murmushi yadaga yana fadin" Dama kana da nambata kamance dani
Yarima yace "inada ita mana fushi nayi dakai na abinda kayimin amma yanzu na huce Dan haka Ina gayyatarka Aurena karshen wata
SAHABI yayi murmushi yace " Allah yasanya Alkairi nima Auren zanyi nanda sati mezuwa kafin nakama
Yarima yace "Shegen kaya wato banda nakira bazanjiba kenan ?lallai na yarda karikeni aranka SAHABI
SAHABI yace " ba haka bane yarima Aurenne ba Wanda nakeso ba Hadani akai da yarinyar diyar kanin mahaifina ce ita ke sona
Dariya yarima yabushe masa yace "sunmin daidai walh domin insun kyaleka " yar talakawa zaka dauko musu banza me sakaran ra,ayi
Sahabi yace "kai " yar INA zaka aura?
Yarima yabashi labarin Hindu da yanda suka hadu a Airport a England
SAHABI yace "Hhhmmm to bagiringirin ba dai tayi mai
Yarima yace " oho dai nafika tunda ni Auran Soyayya zamuyi
"Nima bawai kinta nakeba tunda yar 'uwa tace
Ina Zeenatu naji ance abinda ta Haifa yarasu
Yarima yace " Eh, Sunkusa Aure da LAMIDO...
SAHABI yakatseshi da sauri "ya akai hakan dama soyayya sukeyi?
Nan yarima yazayyane masa komai
SAHABI yace " Gud ammafa naji dadi LAMIDO yaburgeni Allah yasanya Alheri
Yarima baikulaba yai masa sallama
Acan kasan ransa soyayyar Zeenatu na nan baxai mantawa
******
Anata shirye shiryen biki akowane bangaren
Shi yarima agidansa na cikin gari zai zauna baiyda ra,ayin zama acikin gidansu wai kada atakura masa shida amaryarsa
Shiko LAMIDO sashi guda aka gyara masa agidan me dauke da dakuna agidan gidan yasha gyara babbane dama ba kowa ciki
Aka zuba komai na alfarma agidan
Lefe yazo daga Dubai akwatuna goma Sha biyu cike fal da kaya tsadaddu
Komai dozinne ciki koina acikin gidan da wajen gidan zancen kayan lefensa akeyi domin sunhadu sunburge kowa
Saida aka kaiwa takawa yagani yace sunyi yasa albarka kana mata suka hadu suka dauka bayan Su MAMAH DA FAATU sun gani aka kaiwa KUYANGA
Tsoffinsu sunsaka albarka sunyaba Angyagije Zeenatu anfiddata kunya dukda sunsan arina
Shiko Yarima karya yahada ackn kayan duk don ace nashi sunfi na LAMIDO
Harda key din mota yasaka akan lefen mahaifiyarsa ta saka takardun gida duk akan lefen gudummawarta duk don mutane suga na LAMIDO lami ne sannan su burge mutan Kaduna
Amarya anata rawar kai anatashan magungunan karin Ni,IMA da tsukewa sbd gurin anshigeshi
Tun fara karatunta a Abroad tayi soyayya da wani Anwar yamaisheta tamkar mata ta amince masa daga baya ya yaudareta yana gama karatu yakoma kasarsu yamance da ita
Shiyasa data hadu da yarima takasa ta tsare saida taga natsaida lokacin Aure sannan hankalinta yakwanta
Duk kashe kudin da akai alefenta baisa sunyi rawar jiki ko an yababa tunda su ba farin shigar komai bane ita kanta motocinta biyu na hawa tanada gidaje kuma
Aiko dai yan kawo kaya suka koma jiki asanyaye danma anbasu tukuici me tsoka
Rana bata karya saidai uwar diya taji kunya
Allah yakawomu wannan rana
Ranar Asabar takama ranar daurin Auren da nadin sarautar
Ancika agdn sarki anata kade kade da bushe Bushe da algaita LAMIDO yasha kwalliyar sarakai
Yayinda yarima yai tashi ta angwaye daidai misali ba yabo ba fallasa yasha tsadaddiyar shadda babbar Riga d yar ciki
Saida akayi nadi LAMIDO yazama sarki sannan aka daura auransa da KUYANGA kana akayi shagulgula sannan wasu suka dunguma da angoma Yarima suka tafi daurin Aurensa Kaduna
Andauro Aure antaho da Amarya a ranar domin sai dare suka iso aka ajiyeta a gidansa dake GRA
Itako KUYANGA data tashi daga wannan suna daga yau ta tare ackn gidan sarkin A gidan mijinta LAMIDO daya zamo sarki ayau
To fans saimu Tara a page din gaba *GIMBIYA ZEENATU* Cigaban KUYANGA
Wanda zakuji badaqala da cakwakiya ackn Wanda nake muku zaton yafi wannan Dan haka kada kubari abaku labari
Taku har kullum Auntyn Sayyada da Shahida
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.