Auren Katin Kasa Part 3 Complete Hausa Novel
Reading file: Auren Katin Kasa Book 3.docx
Chapter 38 of 52
Chapter 142
Update
Unedited
Mikewa ammah tayi fuskanta dauke da lausansan murmushi dake nuna tana cikin farin ciki sosai “Akwai abunda kikeson ci?”
Sauke kanta tayi qasa tana mai jin kunyar ammah ayanxu sosai, “ah ah”
“Daughter ki ajiye kunyan nan fah, yanxu ba lokacin kunya bane ba kinji ko, ba abun jin kunya bane abun farin ciki ne”
Da kyar ta iya bude Bakinta ta amsa ammah “tohm ammah”
“Bari na barki ki shirya saiki sauko qasan ko”
Ammah na kaiwa nan ta fuce daga cikin dakin fuskanta dauke da murmushi, tana gab sauka qasa saiga Amar ya fito daga part dinta Ganin bata ciki, kallonshi tayi fuskanta dauke da murmushi da fara’a, “son Har ka Tashi”
“Yes ammah na shiga naga bakya nan” ya amsata anatse yana me karasowa inda take “naje wajen daughter ne” ta amsashi kai tsaye tana murmushin jin dadi
“Good Morning, ya karfin jiki” ya fada fuskanshi asaka yana kokarin maida wayar hannunshi cikin aljihun gajeran wandon jikinshi don daga gym yake., “morning son, jiki kam Ay ya gama sauqi Alhamdulillah, muje ciki daman inason muyi wata magana”,
Cikin part dinta suka wuce Har zuwa sitting room dinta, zama tayi akan doguwar 3 seater kafin tayi mashi nuni da gefenta akan yazo ya zauna, takowa yayi ya zauna gefenta ya tattara duka natsuwarshi gareta, “yaushe zaka koma uae?”
Dan shuru yayi yana nazari kafin ya soma magana “Duk ayyukan da zanyi na gama yinsu, anytime from now za a iya nemana a office don na rigada na gama tura duka report din ayyukan danayi anan so anytime from now Zan koma”
Nunfasawa ammah tayi, jikinta yayi sanyi sosai, harga Allah tafison ya hakura da aykin na chan don ya samu ya kuka da dukiyarsa, saidai bazata taba hanashi yin abunda yafi so ba don wannan burin shi tun yana karami na zama babban soja, don haka ta dan nunfasa tace “matar Ka fah?”
Sunkuyar da kanshi yayi yama rasa abunda zai ce, “ya zakayi da ita? Zaka tafi da ita ne?”
Ammah ta sake tambayarshi
“Zan barta anan, Zan dunga zuwa every month”
Shuru ammah tayi kafin tace “okay!”
Da mamaki ya dago din baiyi tsammanin zata amince ba cikin sauqi don yanda yaga gana ji da ita cikin kwanakin nan ko shi bata bashi attention kamar haka,
“Inason Ka gyara gidan Ka na larrics, a refurnishing din gidan”
Ba tare da ya tambayi dalili ba yace “Insha Allah!!” Dukda yasan dalilin hakan.
“Allah yayi albarka ya Kara arziki da lafiya,” ammah ta sake fada tana murmushi
“Ameen” ya amsa ta anatse cikin kamewa, mikewa yayi tsaye ya nufi hanyar futa “Zan dan futa Zan kai dare”
“Allah ya kiyaye, yauwa kaje Ka duba daughter bata jin dadi”
Anatse ya amsa ta “Okay”
Yana futa ammah ta mike tana hamdala ta wuce bathroom.
Tun bayan fitan ammah amra ta kasa mikewa tana nan zaune, lost in her thoughts completely, tunanin abun takeyi kamar a mafarki, maganganun ammah sun tsaya mata sosai, “I’m pregnant???” Ta tambayi kanta in a confusing way, samun kanta tayi da taba tummy dinta dake a shafe kamar babu komi, dan matsawa tayi kadan taji tauri, sai alokacin ta tabbatar da wannan ma yana cikin changes din datake gani a tattare da ita cikin kwanaki,dan matsawan nan da tayi taji abu nayin zillo a cikinta, a rude ta miqe tsaye cikin firgici, is not like bata san komai
Game da ciki ba saidai Har Yanxu ta kasa yarda da abunda ammah ta fada mata, tabbas sunje asibiti kuma doctor ya tabbatar bata da ciki, Toh ya haka kenan? Boye wa cikin yayi komenene? Gaba daya ta gama daburcewa she’s so confused, tana nan tsaye tana kallon cikinta Amar yayi knocking harya shugo dakin kai tsaye bata sani ba, tundaga bakin kofa ya tsaya ya kura mata idanu, towel ne kawai a jikinta sai gashi ta data baza a kafadarta, kallonta yayi daga sama zuwa kasa, ta dan rame kadan a fuskanta zuwa wuyanta, saidai kwata kwata ranar batayi affecting structure dinta ba da dirinta, idanunshi ne ya sauka akan inda yake kallo, bai gane dalilinta na kallon cikin nata ba don haka ya soma takowa Har inda take, ahankali ta soma jin daddadan turarenshi na shiga hancinta, da sauri ta dago idanunta ta sauke a cikin nashi dake yi kyalli, zuba mashi idanu tayi ta kasa daukewa don yau kusan sati guda kenan rabonta dashi, ya dan chanza ba kamar lokacin da suke jigilar zuwa asibiti ba, ya Kara kyau da kwarjini, bata ankare ba ganshi a gabanta ya zuba hannayenshi cikin aljihun wandonshi, Gyaran murya yayi ya dan kauda kanshi gefe “meke damunki?”
Ba zato ba tsammani taji tambayar nashi, gabanta ne yadan fadi Tayi saurin kauda zancen ta hanyar cewa “Ina kwana”
“Morning how are you feeling?” Ya tambayeta daga nan tsaye ya kame
“Alhamdulillah da sauqi” ta bashi amsa
Sake tambayarta yayi fuskanshi na nan yanda take a kame “meke damunki?”
Saurin sauke kanta kasa tayi tana jin yanda kirjinta ke yin lugude, pat pat, Bakinta na karkarwa ta soma magana “ciwon kai da zazzabi”
Juyawa yayi ya nufi hanyar fuce “get ready muje asibiti”
Cikin sauri ta katse shi tunawa da maganar ammah “noo basai naje asibiti ba, ammah ta bani magani I’m okay now”
Ba tare da ya damu ba yace “okay”
Yana kaiwa nan ya fuce daga dakin, saurin dafe kirjinta tayi ta zauna saboda wani jiri jiri daya soma dibanta, saida ta dauka kusan minti ashirin a zaune saiga salima ta shugo da tray a hannu da ammah ta aikota dashi don tasan amra ba lallai ta sauko ba saboda yanayin jikinta, plates da bowl biyu ne akan tray din daya pepper soup din gizzard da liver ne a ciki sai kuma fruits da ammah tasa salima ta yanka mata,
Da sallama salima ta shigo “oh yau ashe za ayi ruwan sama da kankara kin Tashi da wuri adda Wai, nikam adda Anya wannna barcin naki na lafiya ne kuwa? Kodai zamuje asibiti”
Banza amra tayi mata don ba surutun ta ne agabanta ba yanxu, confusion din dake kanta ma ya isheta don gaba daya ta kasa gane yanda akayi ciki ya zauna a jikinta bayan doctor yace babu shi.
Ajiye tray din salima tayi a gefenta tace “gashi ammah tace na kawo maki, wannan special treatment dun da ammah ke baki yana bani mamaki” ta karashe tana kama habar Bakinta, dafe kai amra tayi ba tare da ta kalleta ba tace “dan Allah salima kije kawai, ni ciwon kai surutunki ke sani Wallahi, Ki tafi da wannan abun ma banason cin fruit kawai zaki barmin” ta karashe tana nuna mata plate din gizzard. Da mamaki salima ke kallonta, kafin ta tabe baki “uhm Toh shikenan,“
Daukan plate din salima tayi ta bar mata bowl din fruit ta fuce daga dakin tana mamakin yanda gaba daya amra ta sauya kamar ba ita ba.
Salima na futa ta janyo plate din fruit ta fara ci tana tunani harta cinye tass ba tare da saninta ba, gaba daya jin tayi tana son karasa don haka ta zari hijab dinta ta sauko kasan, yau kusan sati kenan rabonta da saukowa kasan kullum tana kunshe a daki, anatse take tafiya harta shugo kitchen din, ammah ce sai salima a tsaye suna Dora lunch, da mamaki duka suka juyo suka kalleta, ammah ce Tayi saurin cewa “shugo daughter ya kika tsaya”
Karasowa amra tayi kanta a kasa “ammah ke da kan a kitchen?”
“Ay naji sauqi sosai daughter, dole na sauko Kar ayki yayi ma anty salima yawa” dariya ammah tayi tana kallon salima, amra ma dan murmusawa tayi don ta gane dalilin kiranta da anty da tayi, kallon bowl din hannunta ammah tayi Ganin ta shanye tace “ Masha Allah, kina buqatan wani abun? Ko a sake yanka maki wani fruit din”
Girgiza mata kai amra tayi tace “Zan yanka”
“Ah ah bazaki yanka ba, kije ki kwanta ki huta, salima zata kawo maki yanxu”
Kallonsu kawai salima keyi tana kallon ikon Allah, tabe baki tayi ashagwabe tace “ni gaskia ammah wannan nuna kulawa da kikeyi ma adda yayi yawa Wallahi ni kwata kwata ba a yimin haka”
Dariya ammah tayi ta wuce gaban fridge ta zaro bunch of different fruits ta ajiye akan island “haba mutuniyar, bakiga addan taki bata jin dadi bane?”
Karban wukan da ammah ta dauko salima tayi tace “Bari na yanka bana son kina son wahala, Amma dai gaskia ammah nima adunga kula dani haka I’m jealous”
Rankwashi amra takai mata tare da hararta, da sauri ta kauce tana mata gwalo, dariya ammah ta dunga yi masu kafin ta tsagaita “oh Allah kuma kuna yin yar saqo da saquwa kenan, yanxu dai daughter ki wuce sama karki biye mata ta wahalar dake”
Sunkuyar dakai amra tayi cikin jin kunya tace “Toh ammah” kafin ta juya ta nufi hanyar futa daga kitchen din, kallonta ammah tayi harta fuce daga kitchen din kafin wani tunani yazo mata, “daughter!! Daughter!!! Zo”
Salima ce ta ajiye wuqar ta nufi hanyar futa kitchen ta tsaya daga bakin kofar tace “addaaa kizo ammah na kira” tana kaiwa nan ta juya cikin kitchen din ta cigaba da yankan fruits.
jiki a mace amra ta juyo don Har takai stairs, dan saukowan nan datayi da tsayuwar datayi gaba daya taji ta fara galabaicewa jikinta ya fara mutuwa, daman tana jin haka sai barci gaba daya tama manta da maganar ciki da ammah tayi mata akan shike sata barcin don yabi jikinta,
Da sallama ta sake shugowa kitchen din, ammah na ganinta ta soma magana anatse “sorry dear Har kin gaji ko? Ungo wannnan ki kaima Muhammad, na manta tun dazu ya buqaci akai mashi”
“Ah ah ban gajiba bari nakai mashi” amra ta amsata tana Karban mug din da ammah ke miqa mata tayi da yake turiri sosai kafin ta juya ta fuce daga Kitchen din, harta fuce ammah na kallonta tana karantar yanayin ta sosai saboda bayanin da zatayi ma doctor insunje asibiti akan yanayi ta, kana ganinta kasan she’s so excited, fara’ar fuskarta taqi yankewa kwata kwata, babu abunda take sai godiya ga Allah da kuma fatan abunda take tunani ya tabbata insunje asibiti dukda ta tabbatar da hakan a nata hasashen.
Anatse take tafiya harta shugo part dinshi, kamshin parlor ne ya bugeta don parlor ya dau sanyi sasai wanda taji lokaci guda cikinta ya hautsina, saurin toshe hancinta tayi ta wuce bedroom dinshi cikin sassarfa, tana bude kofar ta shige ta sauke wata nauyayyan ajiyar zuciya saboda kamshinsa daya bugeta wanda ya sata jin cikinta ya lafa, Har wani dadi taji ya ziyarceta aranta, tana bala’I son kamshin musamman a yanxu.
Bin dakin nashi tayi da kallo, it’s been long ta inda ta tako da kafarta ta shugo tun bayan last day din da suka dawo tare daga asibiti bayan yayi mata korar kare Inda tayi alqawarin bazata sake takowa ba tazo Inda yake harya daukota ya kawo ta, babu abunda ya sauya adakin, it’s still so clean kamar yanda yake, ko’ina fess fess gwanin ban shaawa, baya cikin dakin ta tako gefen bedside ta ajiye mashi mug din, saukan ruwa ta ji a kunnenta nan ta gane yana cikin toilet kenan m, har zata fuce daga dakin ta dawo bakin gado ta zauna tana jiran fitowa shi dinta bashi sakon ammah, tana nan zaune Har kusan minti goma bai fito ba, ga wani irin barci dake fusgarta sosai, zungudawa tayi kadan tayi kwanciyarta nan take barci ya kwasheta anan kan gadonshi,ba tare da sanin ta ba.
After like 10mins da kwanciyarta ya bude kofar bathroom, ya futo anatse kamar basarake, wani irin kamshi ne ke fita daga jikinshi mai kamshi dadi sosai at the same time ga tururin ruwan zafin da yayi wanka dashi, towel ne kawai a kugunshi, sai dan hand towel daya rike a hannunshi yana goge qirjinshi daya mummurde sosai, kwata kwata bai Lura da ita ba ya wuce gaban dresser ya fara Yan shafe shafen shi cikin class kamar wani mace, shafa chan goga chan, saidaya gama kafin ya nufi gadonshi don yana son yadan kwanta kona 2 hours ne don baiyi barcin safe ba tun bayan sallar asuba daya dawo daga masjid ya wuce gym.
Gaban switch na dakin ya wuce ya kashe ya rage bedside lamb kawai, dakin yayi duhu sosai don da hadari aka Tashi a garin daman abuja badai ruwan sama ba kullum cikin hadari ake ko ruwa haka garin zai hade sosai.
Juyowa yayi ya tako bakin gadon idanunshi a lumshe yana hamma.
Chak ya tsaya don saura kiris ya afka kan gadon saboda baiyi expecting dinta ba, don Yama manta when last ta shugo dakinshi da kafafunta, da fuskanta ya fara cin karo, da mamaki yake kallon yanda take barci hankali kwance, samun kanshi yayi da kallon fuskanta, Har lokacin he’s surprised, ta kwanta ta tattare hijab dinta sama don harya harde mata wuyanta, kana Ganin ta kasan kwanciyar baiyi mata dadi ba but she’s sleeping peacefully kamar wadda tasha wani abu, shuru ya danyi yana mamakin wannan wani irin barci ne haka? Bai kawo komai aranshi ba don haka ya dan harde hannayenshi a kirjinshi ya soma magana “Aisha!!! Aisha!!””
Tsit kake ji kamar da kanshi yake magana, sai fidda nunfashi takeyi akai akai kamar wadda aka shake, ganin nunfashinta na sama sama still tana barci yasa ya matso inda take kwance, Bakinta ta soma bude tana blabbering, Har lokacin barci na idanunta don ta rufe idanun gam, wajen wuyanta ta kama jiki a mace ta fara Jan hijab din “wayyo mamii.. wu..ya..na”
Ahankali take furtawa don kwata kwata bai ji abunda take cewa ba saidai bin Bakinta yayi da kallo harya gane abunda yake cewa, cikin hanzari ya karaso bakin gadon ya sake kiranta “Aisha aisha!!” Inaaa, bata jin shi, barcin ta kawai take tana surutai, Ganin tana kokari janye hijab din daga wuyanta ya gane damunta yake don haka ya zura hannunshi cikin hijab din da hannu daya Dayan kuma ya tallabo kanta gaba daya ya janye hijab din daga jikinta, yana cire wa ya sauke mata kanta ahanakli kan gado ya zame hijab din kasa, wani irin nunfashi ta sauke alamun samun relieve kafin ta gyara kwanciyarta tayi rub da ciki, dan yatsine baki tayi ta juya gefe saboda ta takura cikinta, Duk wannan juye juyen da takeyi akan idanunshi, gaba daya mamakin yanayin ta ya gama dabaibayeshi, wannan barcin baba lafiya bane ya fada aranshi, karshe dai tabe baki yayi ya maida idanunshi kan fuskanta, wani siririn hawaye ne ke sauko a fuskanta kamar tana mafarki, lokaci guda kuma yaji yana tausayin ta babu dalili, tana kashe mashi zuciya sosai ba tare da saninshi ba, yanxu ya gama yarda ya bata special gurbi a zuciyarshi, tayi mashi abunda bazai manta da ita ba, yanda ta nuna jajirce wajen ceto mahaifiyarshi bazai taba mantawa da wannan ba, saidai Har yanxu he’s struggling akan karbanta a matsayin matar shi,he just feel like idan ya amince kamar ya cuceta ne, ko kuma he’s being selfish saboda baya haihuwa,cause she’s so young, tana da rayuwa anan gaba, idan ta zauna dashi a haka she will miserable ba kowa ne zai iya zaman auren da babu haihuwa ba,dalilin da yasa yaqi amincewa kenan da auren shiyasa tun farko da ya tabbatar babu cikinshi a jikinsa yaso ya saketa taje tayi aurenta tunda ita bata da matsalar komai.
Saurin dafe kanshi yayi yana tausaya mata haka kawai, yayi kokarin ya nunama ammmah manufarshi na qin karban auren ta amma ta kasa gane wa, saurin dafe kanshi yayi yana jin wani irin, dago da kanshi yayi da jajayen idanunshi ya kalleta kamar wani mai jin tsoro haka ya miqa hannayenshi ya fara gyara mata kwanciyanta zuwa jikinshi, ahankali yake matso da ita kamar kwai don baya son ta Tashi kafin ya janyo masu duvet ya rufa masu, tana jin kamshinsa na shiga hancinta cikin barci kuwa ta damkoshi sosai “uhm ina….shon..wannan..” ta furta tana turo dan bakinta ahankali kamar mai rada cikin barcinta.
Akan idanunshi tayi haka wanda yasashi Saurin runtse idanunshi yanajin yanayin shi na sauyawa, gaba daya komai ya tsaya mashi chak, baiyi wata wata ba yakai bakinshi kan nata ya dan bata slow peck kafin ya zare bakin shi “mai bakin rashin kunya” ya karashe yana sauke wani lausasan murmushi wanda ya Kara ma fuskanshi mahaukacin kyau sosai kamar bashi ba, lumshe idanunshi yayi har barci ya sauke shi mai dadi sosai.
Salima na gama yankan fruit ta wuce sama don takai mata, tana hawa sama taga wayam, bakin toilet dinta ta tsaya tace “adda??? Kina toilet ne? Ga fruits din”
Jin shuru yasa ta cewa “adda!” Still babu response, da sauri ta Bude kofar nan ma wayam, haka nan ta juya ta sauko kasa ta wuce kitchen, ammah dake sauke tukunya tana ganin ta shugo hannunta dauke da bowl din fruit din data futa dashi tace “ah ah ya kika dawo dashi ko bata so ne?”
“Ammah naje ban ganta ba, na duba ko’ina”
Dan shuru ammah tayi kafin ta dan murmusa tace “ajiye mata a fridge zata sha anjima”
Gaban fridge salima ta bude ta saka bowl din don itama sai a lokacin ta tuna taje wajen ya Muhammad, dariyar keta ta danyi kafun ta dan basar saboda ammah na wajen.
Suna cikin shirya abuncin warmer Aman ya shugo kitchen din yana hamma, da sallama ya karaso ya gaishe da ammah kafun yace “ammah!!! meysa kika shugo kitchen ya kamata ace kina hutawa ne saboda baki gama recovering ba”
Murmusa ammah tayi ta kalleshi cikin kulawa tace “son na samu sauki fah, kuna shagaltani da yawa shiyasa naqi biye muku kaida son, Ay gwara na fito saboda na dunga exercising jikina, bayan wannan ma my baby tana buqatar helping hand tunda ku bakwa taimaka mata”
Ta karashe tana kallon salima dake smiling kamar mimi kafin ta kalleshi ta watsa amshi harara, shima hararar ta yayi, ammah na kallonsu tana murmushin jin dadi sosai, “wannan mara kunyan babu wanda zai taimaka mata”
Ya fada yana kallon salima yana zabga mata harara
Turo baki salima tayi ta rike kugu ta kalleshi “niba Mara kunya bace yaushe nayi maka rashin kunya ?”
“Bani kika yima ba, baby na kikayima” wani irin maqoqon baqin ciki ne ya turnike ta Har batasan lokacin datace “ah ba baby ba Ka manta feeder ce”
Kallonsu ammah tayi kamar tohm and jerry yanda suke ma junansu, “nidai aurar daku zanyi na huta inkunje chan saiku karata ba a gida ba”
Tabe baki Aman yayi ya bude fridge ya dauko ruwa yana shirin balle karfin yace “chapp ammah dawa zaki hadani? Wannan ? Badai niba ni inada wadda Zan aura”
A harzuke salima ta kalleshi da idanunta da suka kawo ruwa tace “nima inada wanda nake so,”
“Toh ya isa haka nan, kowa Zan bashi wanda yakeso tunda bakwa son juna,”
Ammah ta fada fuskanta na nuni da she’s serious, kallonta Aman yayi kafin ya dan sauke murya yace “nifa ba Yanxu zanyi auren bafa ammah”
“Meysa ba yanzu ba ga dan uwana nan da matanshi, kaima aurar dakai zanyi very soon acikin shekarar nan ka fadama babyn taka anytime za a turo”
Dan jim yayi kafin ya dan dago idanunshi nan take ammah ta kashe mashi ido daya,nan ya hasko abunda take shirin yi, dan murmusawa yayi ya soma magana trying to go along, “Toh shikenan ammah Zan mata magana, sai aje ayi tambaya ma kawai” ya karashe ba tare da ya kalli inda salima ke tsaye ba,
Salima dai kafafunta gagarar daukanta sukayi don haka Tayi saurin fucewa tana hawayen takaici.
Tana futa amma ta kalleshi, “ son!! Kaifa yanxu ba yaro bane, basai an fada maka yanda yarinyar kirki ke sonka ba, man up and stop all this childish act Ka daina wahalar min da yarinya, seat her down and talk to her in a cool manner, okay??””
Kanshi a kasa ya amsata “Insha Allah ammah na”
“Masha Allah, Allah yyi maku albarka baki daya”
“Ameen” ya yi saurin amsata kafun ya taimaka mata suka fito da warmers zuwa dining.
Salima na hawa sama tasha kukanta tana dana sanin shegen Jan aji data dunga yi mashi gashi yanxu ya kubce mata, son da take mashi bata jin yayi mata irin shi, “Wallahi yaya bazaka auri kowa ba saini” ta fada tana hawayen takaici.
Bangaren su amra Basu farka ba sai wajen karfe uku na rana, shine ya fara bude idanunshi ya sauke su akanta, gaba daya ta nannadoshi kamar mage ta kudundune shi, saida ya dauka kusan minti biyar yana kallonta, kumatunta daya kara zama fluffy yajaa kadan kafun ya kauda kanshi ya soma kokarin zame jikin shi daga nata ahankali.
Kokarin riko towel dinshi yayi saidai yanda ta kwanta a jikinshi dole saidai ya bar towel din, haka kuwa yayi ya akai towel sun don baya son tashin ta,juyawa yayi ya dan tsaya yayi miqa jikinshi na murdewa sosai, ahankali ya soma tafiya majestically, daidai nan ta bude idanunta da sukayi luhu luhu karaf ta sauke su akan naked bodynshi daga bayanshi zuwa ga structure dinshi, da sauri ta runtse idanunta don batayi expecting Ganin haka ba daga tashinta daga barci, kamar munafuka haka ta soma bude idanunta akaro na biyu ta sauke akanshi lokacin har yakai wajen kofar bathroom zai shige, kasa sauke idanunta tayi daga kallon jikinshi, he’s so hot, skin dinshi fari tass babu tabo, ga kirarshi so sexy, saida ya shige bathroom ya dawo hayyacinta ta sauke ijiyar zuciya kafin Tayi saurin mikewa ta gyara towel dinta dake neman zamewa ta janyo hijab dinta ta zura shi ta fuce daga dakin cikin sassarfa don wata irin yunwa ce ta tashe ta daga barcin.
Cikin sassarfa ta hau sama don bata son amah ta ganta, saida ta shiga cikin daki ta sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya tana haki kamar wadda za a kama, toilet ta wuce direct ta dauro alwala don an kira sallar la’asar.
Bangaren salima saida ta shaqi kukanta son ranta kafin tayi wanka, tana futowa agurguje ta sauya kaya tayi sallah ta fito kasan jiki a mace, idanunta sun kumbura sosai alamun kukan datayi sosai,
Kasa ta sauko ahankali tana tafiya tunaninta ya gushe harta shiga kitchen , ganin ko’ina tsaf yasa taji wani iri don tama manta aiki sukeyi ita da amah ta gudu sama saboda takaicin aman, fridge ta bude ta janyo pack daya na hollandia bata ma san shi ta dauka ba don tunaninta ya gushe, damuwar da soyayyar aman na burkita mata lissafi harta fito daga kitchen din ba tareda tana kallon gabanta ba, hanyar stair ta nufa tana tafiya kanta a kasa, buge kafarta tayi da karfen handrail, da sauri tayi baya ‘’wash allah na’’ ta furta ahankali, dan dukawa tayi tana kokarin duban kafar tata,
‘’dan allah ayi min Magana da hajiya’’ labaran dake zaune tun bayan saukowanta ya hangota daga nesa harta shige kitchen ta fito, daman ya dade a zaune yana jiran wanda zai sauko dan yayi fada ma hajiya yazo, har cikin kwanyarta taji muryarshi, anatse ta soma dagowa, tana shirin waigawa inda taji muryar aman ya sha gabanta, yanda ta ganshi a gabanta ba zato ba tsammani yasa gabanta faduwa cikin tsiwa tace ‘’meye haka kuma,’’
Yanda suka saba cikin kwanakin idan suka hada hanya yawanci harara ce ke biyo baya saidai yanxu taga akasin haka don murmushi yake mata, sauke kanta kasa tayi tana tausayin kanta don ya maidata as a joke, don haka ta nemi giftawa ta gefenshi, hannunta ya rike in a calming tone ya soma Magana ‘’sorry for what I said earlia idan ya bata maki rai’’
Dan dagowa tayi ganin yanda ya marairaice, kauda kanta ta sakeyi tare da zame hannayenta tace ‘’bakayi min komai ba’’
Hannun nata ya sake kamawa ya bude tafin hannunta ya dora mata leda akai kafin ya juya ya wuce dakinshi, kallon ledar tayi kafin ta wuce sama itama, labaran dake zaune yana kallon ikon allah harsuka bar wajen.
Salima na haurowa sama har zata wuce daki ta tuna da maganar mutumin dake zaune a kasa, dakin amah ta wuce ta sanar mata da wani yazo yana kasa kafin ta futo ta wuce dakinta ta bude ledar daya bata, bunch of chocolate ne a cikin ladar hade da apology card a ciki, dukda taji dadin kyautar hakan baisa ta tabe baki ba tana tausaya ma kanta.
Saukowa kasan amah tayi cikin mutunci, anatse ta karaso har cikin sitting room din ‘’lale maraba, malam labaran sannu da zuwa’’
Zama tayi kan kujera tana fuskantarshi, yana zaune akasa ya dukar da kanshi ‘’ina wuni hajiya, ya karfin jiki, ashe bakiji dadi ba, nazo shekaran jiya ay baba mai gadi yake fada min, allah yasa kaffara ne’’
‘’ameen ya allah malam labaran, ay naji sauqi sosai, ya noma? Kwana biyu baka zoba’’ amah ta fada tana kallonshi
‘’wallahi nayi rashin lafiya ne tsawon wata guda hajiya shiyasa na kwana biyu ban zo ba’’ malam labaran ya fada cikin girmamawa
‘’subhanallahi shine baka kira ka fad aba labaran’’ amah ta fada in a concerning way.
‘’ay naji sauqi sosai hajiya, allah ya kara arziki da lafiya’’
‘’ameen ya allah’’ amah ta amsashi
‘’kun gaisa da mutan gidan kuwa?’’ amah ta tambayeshi tana kallon gefensa
‘’eh mun gaisa da yallabai na dubai,don tare mukayi sallah a masallaci ma, dan uwansa ne dai bai lura dani ba lokacin daya shugo’’
Malam labaran ya karashe yana sunnar dakai
‘’madallah, ay kwanaki inataso na fada maka yayi aure ma’’ amah ta fada tana murmsuhi
Cikin fara a malam labaran yace ‘’masha allah , allah ya sanya albarka, ya kade fitina’’
‘’ameen ya allah ya aikin gona’’ amah ta tambayehsu anatse
‘’ay sai godiyar allah hajiya, tun shekaran jiya naso na kawo kwasar wannan shekarar, an samu buhu talatin na shinkafa, buhu ashirin na masara’’
‘’ahhh madallah, allah yasa albarka, akai kasuwa kawai’’
‘’toh shiknan hajiya’’
Sun danyi hira kafin yayi mata sallama ya wuce bayan ya kara yi mata godiya akan abubuwan datayi mashi.
The next day…
Da sassafe amah ta wuce dakin amra don ta shigo da asuba ta sanar mata da wuri zasuje asubiti don bata son amar ya sani saboda zai iya suspecting wani abun ko yace zai bisu don haka ta shaida mata da wuri zasu fita.
Da sallama amah ta bude dakin, a kwance take cikin shiri don saida tayi wanka ta shirya barcin nata yazo mata, takowa har inda tae amah tayi tana murmushi, ‘’wannan jika nawa akwai barci’’ amah ta fada tana murmsuhi,
Dafata amah tayi ‘’daughter, tashi muje ko’’
Bude jajayen idanunta tayi ta sauke su akan amah kafin ta miqe da kyar ‘’good morning amah, harkin futo’’
‘’yes dear muje kar muyi latti’’
Atare suka sauko amah naga ba amra na biye da ita, sanye suke da abaya gaba dayansu, tasha stone tundaga sama har kasa, sai colors din daya banbanta, amah na rike da wata haddaiyar handbag mai shegen tsada ta manyan mata, fuskanta da farin glass mai kara kwarin idanu tayi masifar kyau, hausawa sunce lafiya uwar jiki kana ganinta kasan ta samu sauyi sosai a rayuwarta compare to lokacin da take yawan rashin lafiya, ramar datayi ma kara mata kyau tayi sosai, inka ganta bazakace ta haifi amar ba kwata kwata, skin dinta sai glowing yake daman ga haske ga kyau duk ta hada don a jikinta amar yayi gadon komai, amra dake gefenta ma tayi kyau sosai dukda gama daya kana ganinta kasan tana jin jiki.
Inka gansu yanda suka fito atare cikin abaya zaka dauka sisters ne saboda amra nada jikin girma sosai fuskanta ne kawai ke nuna kankantar shekarunta, sai kuma amah in ka kalli fuskanta ta zaka ga ta manyanta dukda manyancen nata bai futo sosai ba, she’s looking so beautiful and young kamar ba ammah ba, bata da damuwar komai ayanxu sai ta iyalinta don yanxu ita kadai ta rage masu gaba dayansu.
Duban agogon dake maqale a hannun ta tayi ganin kusan bakwai da rabi yasa tace ‘’daughter ay bazamu jira driver bama ni zanyi driving dinmu’’
Murmushi amra tayi tace ‘’toh ammah’’ kafin tabi bayanta har suka karaso inda motoci suke, da sauri baba mai gadi yazo ya gaishesu gaba daya kafin amah ta bada umarnin ya cire car cover din motarta don it has been long tayi driving tun bayan rashin lafiya data farayi,
Baba mai gadi na bude cover motar amah saida na kalla na sake kalla, wata bugaggiyar range rover ce rr2023 white color, fadin irin haduwar motar bata lokaci ne da alamu ma sabuwa don kamar ba a shiganta,
Motar ma gaba daya smart car ce, don bata danna key din motar ba kofar ta bude ta, amra dake biye da ita ma tana tsayuwa motar ta bude da kanta, anatse ta shige gaban motar ta zauna.
Saida amah tayi warming motar kafin tayi revarse ta juya, nan securities suka bude gate suma suna kwasar gaisuwa kafun su fuce daga gidan.
International specialist hospital…
Daidai wani haddadden asibiti amah tayi parking, amra na kwance tana barci batama san sun iso basaida amah ta tasheta, bin asibitin ta sma yi da kallo, ya hadu sosai har yafi wanda aka kwantar da amah.
Atare suka fito amah ta taimaka mata wajen rike mata hannu don she looks pale and weak,har suka shiga cikin asibitin .
Suna shiga amah ta barta anan reception ta wuce wajen receptionist ta bude mata file, cikin yan mintuna kalilan ta gama yi mata komai har tayi booking appointment.
Tana gamawa ta dawo ta taimaka mata ta mike suka wuce wajen vips don anan zataga doctor, idan lokacin appointment dinsu yayi daman by 8am dctor zaizo.
Zama suka danyi har doctor yazo, nan ma saida amah ta taimaka mata suka shiga har office din doctor, fadin irin haduwar wajen ma bata lokaci ne don ya fita daban a cikin asibiti, don ana kiran wajen da presidential root lol, zama sukayi inda doctor yayi welcoming dinsu kafin amah ta soma mashi bayani, a bayanin da amah tayi mashi saida ya tsaya y agama sauraron ta kafin ya soma Magana ‘’well hajiya ance komai na allah ne inda rai akwai rabo, we have a lot of patients muma anan nigerai waenda sukeda ospermia kamar aynda kikayi explain mujinta nadashi, kuma cikin ikon allah zakiga basu da kwayayan haihuwar cikin ikon allah zakiga allah ya akwo wata hikima allah ya basu haihuwar, yanxu ayanda kikayi bayanin yanayinta it obvious shes preg, but zamu mata blood test baya daukan 10mins result ke fitowa don munyi upgrading facilities dinmu na nan, sannan zanyi mata scanning yanxu so that we can know how far she has gone then after that sai muyi tunanin wani irin medication zamu daurata.
Murmushi amah tayi tace ‘’okay tohm’’
Kiran wata nurse doctor yayi don ita zata taimaka mashi tana shugowa office din ta ajiye abubuwa test data dauko daga mini lap dinshi dake cikin office din, nuni yayi mata da amra yace ‘’overall blood test za ayi mata yanxu but ina buqatan pregnancy test immidiately’’
‘’okay sir, it will be ready in 5 mins;’’
‘’okay thank’’ ya amsa nurse din, gaban amra ta karasa ta soma diban jininta tana gamawa ta ta wuce general vip lap don tayi running test din daya buqata, cikin mintuna biyar saigata da result har biyu, karba doctor yayi, tunda doctor yak araba gaban amra ya soma bugawa pat pat, ammh kuwa babu abunda take sai murmushii tana godema allah don tasan ma mai zai buyo baya, bayan doctor ya gama karantawa ya kalli amah fuskanshi dauke da murmushi yace ‘’hajiya congratulations, shes 5 months and 3weeks pregnant, by next week zata shiga 6months zata fara zuwa antenatal, sannan akwai magungunan da ya kamata ta dunga sha don jininta is very low shiyasa take zama weak,’’
Tunda ya fara Magana amra kebin bakinshi da kallo gabanta na faduwa, yanxu itane ake cewa tana da ciki? Cikin ya muhammd?
Bangaren ammah kuwa Fadin irin murna da farin cikin da take ciki a wannan lokacin bata lokaci ne karshe ma bude Jakarta tayi ta zaro bundle din kudi yan dudu dubu guda uku ta ajiye akan table din doc tace ‘’wannan tukwicinka ne for this good news, I’m sure idanda agaban mijinta kayi breaking wannan news din abunda zai baka saiyafi wannan ma, but ayi managing wannan’’
‘’no hajiya ia cant take it’’
Kaste amah tayi ‘’I insist,’’
ta karshe tana hamdala, hannun amra ta rike tana kallonta ta fara zabgo mata albarka,’’allah ya shi maki albarka daughter, allah ya saukeki lafiya, allah ya biyaki da gidan duniya kin gama yimana komai, youre a blessing to us dear thank you so much’’ hawaye ne suka soma zubowa akan fuskan amah itama kukan takeyi sosai tana rungume amah, saida sukayi mai isarsu shiko doctor don farin ciki shima yak washi kudin da aka bashi ya ajiye a locker shi.
Saida komai yadan lafa doctor yace ‘’yanxu scan zamuyi ko? At this time zaku iya sanin gender of the baby ma’’
‘’no doctor, bazamuyi ma allah shishigi ba kuyi scanning din kawai it’s a gift from allah so we want to keep it basai munsan komai ba ta hanyar yima allah shishigi’’
Dariya doctor yayi yace ‘’toh shikenan hajiya, zan duba lafiyan babyn kawai’’
Mikewa yayi ya nuna ma amra kan gadon da zata zauna anan office din nashi kafin ya janyo scanning machine, anatse ya soma observing cikin nata saida ya dauka kusan minti goma kafin ya mike ya dawo saet dinshi, amra ma mikewa tayi dakyar don tana jin kamar karta tashi ta kwanta tayi barcinta.
yan rubuce rubuce yayi a laptop ammah dai na zaune tana kallonshi, saida ya gama ya dago a kallesu su duka,’’she is having a healthy baby, the breathings are nomal, babyn yana inda ya kamata,’’
‘’toh likita banga bumps ba? Kuma naji kace ta kusa wata shida’’ amah ta tambaya
‘’yes that is not a problem yanayin jikinta Kenan, baya nuna bumps din, mostly matan yanxu haka suka fi so saboda basa son suyi teba da stretvh marks but intakai 8 months definitely she will be very very heavy saboda cikin’’
‘’alhamdullah alhamdullah’’ abunda amah ke fada Kenan har doctor ya rubuta masu magungunan da zata buqata ayanxu da allurai.
Godiya amah tayi ma doctor suka futo tana rike da hannun amra dake ta faman sunnar dakai, ta kasa believing cewa wai ciki ne da ita cikin ya muhammd, shes so emotional right now, bata san me zatayi ba farin ciki ko akasin haka, shi uban dan ma ba sonta yake ba,saidai ganin yanda amah ke farin ciki yasa hankalinta ya dan kwanta, yanxu koba komai ta sakama amah da yanda ta rike yan uwanta ta zama gatansu kuma ta riksu amana.
Cikin awa guda aka gama yima amra komai aka bata magunguna akayi mata allura, ba laifi tunda akayi mata alluran nan taji wani dadi a jikinta da kuzari, nan nurse ta bata shawaran ta dunga shan ruwa sosai da lots of milk, godiya sosai amah tayi mata kafun su fuce daga asibitin, yanda amah ke lallabata kamar kwai abun har kunya ke saka ta don koda ska karaso wajen mota da kanta ta bude mata ta shiga cikin motar ta zauna kafin ta zagayo ta kunna motar, ‘’daughter me kike son ci?, please ki fada min kinji? Ko zakici cake naga kinason kayan zaqi’’
Ganin yanda ta damu sosai yasa amra ta dan murmusa tace ‘’zanci cake din ammah’’
Cikin murna amah tace ‘’yauwa my dear, bari na kaiki wani cake shop, akwai different varieties saiki zaba
wanda kike so’’
Tada motar amah tayi ta juya akalar motar suka bara harabar asibitin, wayanta dake ruri ta daga tana ganin sunan amar ta ajiye a gefe yanxu batashi take ba ta amra take.
Koda suka iso cakemeaway shop, amra bata shiga ba saboda tana jin jiri amah ce ta sayo mata different types, flavors and toppings of cake kusan guda goma, haka aka biyota da ledoji har cikin mota kafin subar wajen.
Suna kan hanya ammah taga mai agwaluma, da data, nan ma saida ta tsaya ta saya mata kafin su bar wajen, har lokacin amar waya yake mata yayi mata missed call yafi talatin hankalinshi duk y agama tashi, karshe ma message tayi mashi ‘’son were fine, please stop calling’’
Horn din motar amah ne ya karade gidan, securities ne suka bude gate, amar dake safa da marwa a parlor yana jin horn yayi saurin futowa tsakar gidan, sanye yake da shorts sai vest gaba daya bashida natsuwa tun bayan daya tashi saida yaji horn din motar amah.
Amah na parking yazo gaban mazaunin driver, bude kofar amah tayi tana murmushi, babu zato ba tsammani ta rungumeshi, da mamaki ya tsaya shima ya rungumeta, ‘’alhamdullah alhamdullah son, im so happy today’’ ta kaarshe tana dariya, amra ce ta fito daga motar tdan deba kayan da suka shigo dashi zata wuce amah tace ‘’noo noo kawo nan, muhammd zai dauka, ay shine da wannan bake ba diyata’’
Kallonshi amma ta sakeyi tace ‘’karba kayan chan ka wuce mata dashi dakinta,’’
Kallon inda amra ke tsaye tayi tace ‘’zaki iya kuwa daughter ko ya daukeki kema ya kaiki saman’’
sauke kanta kasa tayi tana jin kunya sosai, amar dai baki sake ya tsaya yaan kallon yanda amah ke cikin farinciki da annushuwanda bait aba gani a tattare da it aba, ‘’ammah whats the news? Why are you so happy’’
lakatar kumatunshi amah tayi tace ‘’it’s a secret’’
tana kaiwa nan ta shige ta barsu tsaye shida amra, karasowa yayi ahankali yazo gabanta, kamar baa mar bay a miqa mata hannunshi don ta bashi ledojin, dan dagowa tayi ta kalleshi nan ta shagala harta fada tunani, ‘’ya Muhammad is the father of my baby? Hes going to be a father, allah sarki ashe yana da rabon ganin danshi shima,’’ saida ya dan gyara murya ya daga mata gira daya ta ankare da kallonshi da takeyi, saurin sauke kanta kasa tayi tana tausayin kanta, ayanxu data tsaya agabanshi sai taji wani irin dadi sosai koba komai zata saka mashi da alkairin da yayi ma yan uwanta ta hanyar protecting dinsu ya kula dasu ya basu ci da sha, badan shiba qila da sun salwanta saidai tausayin kanta take ayanxu kuma, don ta rigada tasan bazai tabasonta ba bazaitaba kallonta a matsayin mace ba. Fatanta allah yasa taci albarkacin abunda ke cikin ta ta samu kwanciyar hankali a cikin aurensu da soyayyarsa.
Ganin batada niyar bashi yasa ya karba daga hannunta kawai yace ‘’muje ciki’’ sata yayi agaba yabi bayanta.
Suna shiga ciki suka tadda ammah ta tara su salima dasu aman da salim tana masu kyautar kudi, yaudai kowa ya shaida ammah na cikin farin ciki dukda sunyi sunyi ta fada amsu taki.
Amra dai sama ta wuce amar ya bita da kayanda ammah tace nata ne, yana shiga yaso ya tambayeta inda sukaje saidai kuma wata zuciyar ta haneshi da hakan don haka ya fito daga dakin ba tareda yace mata qala ba yana futa tabi lafiyar gado itama.
Monday morning…
Yau su salima zasu koma school don by next week zasu fara waec da neco don already bandasu yan ss3 za ayi exam din school sais u salim dake ss1 going to 2.
Haka suka jera kwanaki suna zuwa school kullum ita da salim, ta maida hankali sosai kan revision da practice exams da akeyi masu saboda preparing dinsu akeyi for waec da neco.
Amra dai kullum tana kwance, ammah na kula da ita sosai har lokacin babu wanda yasan abunda suke ciki, ammah bata yarda ta fada ma amar ba don tace sai when the right time comes.
Shima bai damu ba don bai tambaya ba, haka ya dunga harkokinshi, yanxu kokari yake y agama komai don ya samu ya wuce bakin aikinsa.
Gyaran da ammah tace yayi bai fasa ba, yasa anyi refurninshi gidan gab daya an saka furnitures din da sukaci uban nada, fadin irin yanda gidan ya chanza ya kaar kyau ma bata lokaci ne don komai yaji zam zam, ko a kasar waje sai haka.
After 3weeks….
Yau saura sati guda salima su gama neco don already sun gama waec, gaba daya ta rame sosai sai karatu takeyi kullum tana daki, salim kuwa ya gama school exam, kullum yana zaune yana games dinshi sai salima ne ke zuwa school itama in a week zata gama, gaba daya ta fidda tunanin aman aranta saina karatunta , shima ya bata space sosai don baya son ya takura mata saidai duk sanda suka hadu koda a wajen dining ne nan suke aika ma knsu kallon love wanda kowa ya shaida soyayya mai karfi ce a tsakaninsu…
Amra ta shiga 6month harda sati biyu, har lokacin cikinta bai fito ba don bazaka taba cewa tana dashi ba inka kalleta saidai wanda yasan ainihin ciki ko yayi experianceing zai gane dashi ajikinta. duk ranar Wednesday ammah ke kaita antenatal babu wanda ya sani a gidan amar ne kawai ke yawan tambayr inda suke zuwa,shima lokaci guda ta taka mashi burki don tasan zai iya yin buncike don haka ta shaida mashi bata san shishigi, he should behave him self, nan take kuwa ya shiga taitayin shi bai sake tambay aba kuma baiyi gigin yin bunciken ba.
Friday morning..
Tunda amra ta tashi yau ta tashi da son cin yalo, avocado, gurjiya da agwaluma gaba daya at the same time, haka ta dunga zarya adaki harda kukanta ta rasa yanda zatayi, cravings din kamar zai saka ta hauka, babu shiri ta daura hijab dinta akan towel dinta don yanxu dashi take wuni idan tayi wanka bata son saka kaya kwata kwata, ta na fiowa ta wuce dakin ammah direct, da sallama tashiga dakin harda hawayenta, ammah na ganinta ta mike ‘’daughter lafiya? Akwai abunda ke maki ciwo ne?’’
Karasowa amrat tayi kanta akasa ‘’ammah dan allah inason yalo da data, da gurjiya, da avocado da dayan banma don sunanshi ba but kinsaya min lokacin da mukaje asibiti’’
Murmuhsi ammah tayi ta rike hannunta, ‘’haba daughter yanxu saboda wannan kike kuka? Share hawayenki bari na kira muhammda yaje ya nemo maki, yanxu kuwa kiji,’’ ammah na kaiwa nan ta dauki wayarta, amar dake shirin futa don harya riko keysa dinshi ya nufi inda motarshi take wayar ammah ta shugo mashi, saurin dauka yayi yasa a kunneshi ‘’muhammad kana ina’’ ammah ta fada tana sauraronshi
Daga chan ya amsa ‘’yanxu zan fita, inzo ne?’’
‘’no basai kazoo ba, daughter na son cin yalo da data da avocado da agwaluma da gurjiya da dinya’’
Zaro idanu yayi waje don tunda ta fara Magana baima gane abunda take nufi ba ‘’sorry come again ammah’’
Ya fada surprisingly
‘’nace maka my daughter nason cin yalo da data da agwaluma da dinya da gurjiya sai avocado, ianson kabar duk abunda kake kaje ka nemo mata’’
‘’what!! Ammah, menene wannan din, kuma….’’
Saurin katseshi ammah tayi ‘’look babu wani kuma, kaje duk inda zakaje nab aka nan da 1hours’’ amra ce ta katseta yayin da ta fashe da kuka, 1hour ina bazata iya jira ba, ammah na ganin haka ta gane don haka tace ‘’kaii nabaka 30mins, ka nemo su duka duk nda zakaje kaje ka nemo su yauwa’’
Tana kaiwa nan ta kasha wayar dipp ta juyo gaban amra ‘’daugter, ki kwantar da hankalinki kinji, zai akwo aynxu yanxun nan, bari na yanko maki avocado ki fara dashi don naga akwai anan kitchen kafin ya kawo sauran’’
Ashagwabe amra tace ‘’thank you ammah’’
‘’ki kwanta ma anan ki huta yanxu zan dawo my dear’’ ammah ta fada tana mikewa
‘’amra kuwa janye hijabin tayi ta kwanta abunta nan take barci ya kwasheta………….
***Auren katin kasa***
Romantic love story
written by QUEENMARH
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.