Complete Hausa Novels

Bawan Allah Part 1 Compleete Complete Hausa Novel

Reading file: Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel.txt

Chapter 2 of 15

Page 2⃣

WAYE ABDALLAH

Abdallah d'ane ga Abdallah asalin mahaifin shi D'an wani k'auye ne ahanyar jos ya baro gida sakamakon rasuwar iyayen shi kuma shi kad'ai iyayen shi suka Haifa , alokacin da ya baro gida yana da matar aure me suna Hindatu itama auren zumunci akayi musu da ita , Abdallah ya tattara yan k'wandalolin da ya ke dasu ya taho garin zazzau domin Neman kudi , yasamu wani D'an k'aramin gida yasiya suka zauna shi da matarshi Wanda har zuwa wannan lokacin bata da ciki , yakan fita kullum ko zai samu abin yi amma babu rannan kawai sai ya yanke shawarar bari yaje bakin kasuwa ko dako yayi , to ahaka yake samu yana ciyar da matar sa duk da ba kullum ake samu ba,

Kasan ce warsa shida matarshi basu da hayaniya yasa suka zauna lafiya da mutanen unguwar , gidan da ke kallon gidan Abdallah gidan wani malami ne mai suna Malam Kabiru mai almajirai wani lokacin idan Abdallah ya dawo k'adugo yakan zauna yayi karatu awajen shi Kasan cewar shi mutum mai son karatu , akwana a atashi ba wuya sherar su Abdallah biyar agarin Zaria , suna rayuwar su yau samu gobe rashi , Akwai wani mak'ocin Abdallah wani tsanin gidan shi Dana mak'ocin gida biyar ne sunan sa Jafar shima dai rufin asirine kawai gareshi shiyasa abotar su tazo d'aya da Abdallah ,

Wata rana sai suka yanke shawarar suje su nemi aiki gidan bulo ko ruwa ne surunk'a d'ebowa , aiko basu sha wahala ba tunda sunsan me gidan bulo d'in ,

Kwanci tashi ba wiya har suma aka koya musu yadda Zasu had'a bulo wata ,

Wata rana Hindatu ta tashi da zazzab'i ciwon kai da jiri sai ranar sanyi take , akwai wani PHC asaman layin su nan ya kaita gwanjin farko aka tabbatar mai da tana da ciki murna kuwa ba'a fad'uwa tunda ga lokacin ya koma bata kulawa na musamman Dan duk wani aikin gidan shi yake yi

Alokacin da cikin Hindatu yakai wata takwas ya shigo mata da wani madai-daicin rago tayi murna sosai tare da godiya , bayan sati biyu Abdallah yaje gurin aikin shi sai man injin d'in ya k'are be jira kowa ba ya d'auko mai ya shiga d'urawa yana cikin haka ne wani noti ta k'asan injin d'in ya fita yana gama d'ura man ya cire rigarshi ya kwanta ta k'asa saida ya lek'a ya ga Ashe ma notin ba d'aya bane kafin ya gama tunanin da zai yi injin d'in ya fad'o masa a k'irji bai sake sanin inda kanshi yake ba sai dai ya farka ya ganshi gaban Hindatu ta na ta faman kuka k'irjin shi duk an d'aura mai su da farin bandeji da k'yar ya iya d'aga hannu ya bubbuga mata bayan ta , sai sannan ne ta juyo tace mishi sannu Malam d'aga mata kai yayi dan ya kasa magana k'irjin shi ya mishi nauyi sosai , tunda ga ranar baya iya komai idan ya fara tari haka yake fitar da jini guda guda , ranar wata juma'a kuwa Abdallah ya rasu , Allahu Akbar mutane sunji mutuwar shi sosai musamman ma abokan shi guda biyu Malam Jafar da Malam Kabiru,

Bayan rasuwar Abdallah da sati d'aya Hindatu ta haihu tare da taimakon matan Malam Kabiru da Jafar , matar Jafar lokacin tana da goyon yaron ta Umar D'an wata biyar ,

Hindatu ta haifi d'anta namiji yaro sak kamar shi da Baban shi dangin ta da suka zo sunso su maida ta gida amma fir ta k'i hakan yasa suka hak'ura suka barta mak'otan nan nata su ke ciyar da ita , ranar bakwai yaro yaci suna Abdallah .

Haka rayuwa ta cigaba da garama Hindatu idan mak'otanta sun samo su bata randa basu samu ba kuma kowa ya sha ruwa ya kwanta ,

Lokacin da Abdallah ya kai shekara bakwai Malam Jafar ya had'a shi da Umar ya sasu amakaran tar boko ta gwamnati ,

Abdallah da Umar sun taso cikin son junan su da tausayin iyayen su wani lokacin da Kansu suke zuwa bakin kasuwa suyi dako su sami 'yan kud'i su kaima iyayen mata sukuwa suyi ta sa musu albarka

Tun suna k'anana suke zuwa d'aukar karatu wajen Malam Kabiru har suka sauke bayan sun sauke sai ya sa musu littafai

Suna SS3 mahaifin Umar ya rasu anan karatun su na boko ya tsaya ,

Abdallah da Umar suna iyakar bakin k'ok'arin su wajen ganin sun ciyar da iyayen su amma abin yana fin k'arfin su wataran gwanda ma Umar mahaifin shi da aka raba gado Maman shi ta fara sana'ar k'ulla-k'ulle dashi suke rufa ma Kansu asiri

Lokuta da yawa Malam Kabiru yana musu nasiha akan suji tsoron Allah kada talauci ya sa su rasa imanin su da irin wad'an nan nasihohin kullum Malam ke musu

Da temakon Malam suka samu koyar wa a wata islamiya da ke wata unguwa babbar makaranta ce sai dai albashin ta mai K'aranci ne baya isarsu d'awai niyar su

Wannan shine BAWAN ALLAH kamar yadda mahaifiyar shi me kiran shi dan bats fad'in sunan sakamakon sunan mijin ta kuma sunan d'anta na fari

For comments
08165728746
[12/13/2017, 5:36 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*

*MRS NN ONE💋*

*I dedicated this page to you , masoyana a koda yaushe ina jin dad'in yadda kuke k'arfafamin gwaiwa na Gode Allah ya bar k'auna AMEERT Nd FATIMA (K'awwali)❤*

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.