Complete Hausa Novels

Bawan Allah Part 1 Compleete Complete Hausa Novel

Reading file: Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel.txt

Chapter 13 of 15

*page* 4⃣1⃣

Wani bak'in ciki ne ya tokare Saifullah amma sai ya dake ya ce " zo muje D'an k'anina musa contains kar Madam tayi mana dariya"

Nok'e kafad'a Aminullah yayi yace "nak'i wayon "

"Haba my little bro my best friend ever "

Da k'yar ya lallab'eshi suka matsa gefe kad'an .

Ita dai Ummi tana gefe tana cin dariya

Can sai taji Aminullah ya na cewa " asshhh da zafi fa " ko da ta juya ta kalleso sai taga suna ta dariya har da rungumar juna , nan suka canja salon hirar tasu .

Sai da sukayi sallar la'asar sannan suka Shiga lectures .

Ba su duka Shiga gida ba sai k'arfe 7:30 , ga wahala ga yunwa agurguje sukayi sallah sannan kowa ta mik'e awurin don jiran sallar isha Ummi kuwa wani wahalallen bacci ne yayi awon gaba da ita Hafsa da taga tayi bacci saita fita ta tafi d'akin Mama , tana d'akin Abdallah ya shigo yana shigowa bayan sun gaisa yace ma Hafsa

"Ke kira min Ummi"

"Tayi bacci "

"Baccin gaske ko baccin k'arya ?"

"Wallahi tayi bacci tun d'azun "

"Go and call her for me my Friend!"

Sumi sumi ta mik'e ta fita , Ummi na bacci taji ana jijjigata ana kiran sunan ta , tana bud'e ido taga Hafsa ce taja wani wawan tsaki ,

Hafsa abun ya bata haushi tace "oh ga marainiyar wayaunki ko , to bani ke kiran Ki mijin Ki ke kiranki "

Cikin muryar bacci tace "baki ce mai ina bacci bane ?"

"Na gaya miki Malama Ki tashi kije kafin ya gaya wa mutane a matse yake dan naga yana gab"

"Bafa inda zanje idan kinga na tashi awajen nan to Tara tayi "

Baki a sake Hafsa tace " eyyeh haka kika ce , ni 'yar sak'oce , kar ya huce a kaina "

Hafsa ta fita taje d'akin Mama baya nan sai ta tafi d'akin su sallama tayi ak'ofar d'akin sai da ya amsa sannan yace "ya akayi kuma ?"

Kai tsaye tace " tace ba zata zo ba"

Shiru yayi sannan yace "tana da waya?"

"Eh"

"Bani number ta"

Nan da nan ta rattafo mishi numbers din sannan yace mata "jeki " ta tafi tana sauke wani nannauyan ajiyan zuciya,.

Tana kwance taji wayarta na ringing da kamar ba zata d'auka ba sai da kiran ya kusa katsewa sannan ta d'aga tare da sallama ,

Amsa sallamar kawai yayi sannan yace " kizo Ki sameni ad'aki ina jiranki minti biyar kawai na baki" k'itt ya kashe wayar ,

Wata zuciyar tana cemata taje wata zuciyar tana cemata kije ya sake rik'e Ki irin na jiya Ki kwashi abun kunya da safe shi ba ruwan shi🤷‍♀

Can kuma dai me tatuna oho sai ta mik'e ta fita , tana zuwa bak'in k'ofar tayi ta jero sallama bai amsa ba sai da ya mula ya mulmule sannan ya amsa be ce mata ta Shiga ba ita ma kuma bata Shiga ba takai kusan minti biyar awajen sannan ya ce

"Idan baki gaji ba to kiyi ta tsayuwa " ba shiri ta banko labulen ta shigo ta nemi gefe ta rakub'e kamar wata bak'uwa,

Juyawa yayi ya kalleta cikin tsare gidan shi yace mata " Ummi na lura Sam bakya murna da dawowa ta "

Cikin sauri ta d'aga ido ta kalleshi kallo me tattare da alamar tambaya

Shima kallonta yayi yace "yes da kin damu dani da zaki nuna farin cikinki gareni amma dayake ba damu wa da ni kikayi ba sai wa wasan b'oyo mukeyi "

Ita dai ta kasa magana Wanda tasan har ga Allah ko mahaifiyashi da wiya ta kaita zumud'in ganin shi , tana cikin tunani taji muryar shi yana cewa " shikenan tunda ni ba bazaki iya magana ba kije kawai "

Ba tare da tayi tunanin komai ba tayi waje abinta .

Abdallah kam bak'in ciki ne ya isheshi wato ma ba zata iya zama kusa dashi ba me take nufi ? Irin wannan tunanin yayi tayi har dare ya raba sannan ya fita ya d'auro alwala .

Ummi kuwa d'akin Hafsa ta koma ta k'udun dune cikin hijab d'in ta tana ta kuka azuciyarta tana fad'in " ina ma ace zan iya fad'a maka sirrin zuciyata , ina ma ace zan iya fad'a ma irin kewarka da nayi ina ma ace zan iya fad'a maka irin farin cikin da nashiga lokacin da ka bayyana agareni amma bazan iya ba dan duk sun wuce gaban kwatance sai dai a aikace mijina "

Irin wad'an nan kalaman tai ta fad'i cikin mayan shauk'in soyayya har Hafsa ta dawo daga d'akin Mama ta same ta wajen tana kuka ,

A hankali Hafsa ta zauna gefen Ummi tace " Aunty Ummi lafiya ?, me ya faru?"

Kamar jira take dama akulata sai ta zauna ta dasa sabon kuka , da k'yar Hafsa ta lallesata sannan ta sake tambayarta me ya faru cikin kuka take sanar da ita yadda sukayi da Abdallah .

Hafsa ko mai zatayi inba dariya ba Ummi kam had'e rai tayi tace " saboda wulak'anci kice na gaya miki damuwata madadin Ki bani shawara sai tsaya kina yi min dariya ?"

Cikin dariya Hafsa tace " yo Aunty Ummi AI ke d'in ce sai a hankali"

"Da nayi me fa?"

Murmushi tayi tace "Aunty Ummi yaya Abdallah kulawar Ki yake nema kin kasa ganewa yanzun haka ma k'ila ko D'an welcome kiss d'in nan baki mishi ba , au ko dayake bari nayi shiru naga jiya kun kwana d'aki d'aya " ta k'arasa maganar tana dariyar mugunta .

Ummi kam abin ya k'uleta ta d'auki pillow ta makawa Hafsa tare da fad'in " wallahi baby bakiyi ba"

Duk suka kwashe da dariya daganan Ummi ta mik'e ta d'auro alwalar sallar isha da batayi ba sai da tayi sannan 'yan hanjinta suka fara Neman agaji , ba shiri ta nufi kitchen shinkafa da miya ta tarar miyar taji soyayyen nama sai buga k'amshi take nan tazubo taci sannan ta koma ta kwanta.

*DA SAFE*

Kamar yadda Umar yake yi yanzun kafin ya tafi kasuwa sai yazo sunsha hira da Abdallah sannan ya wuce , yauma suna tsaka da fira sai Umar yace

"Aboki nima fa na kusa Shiga daga ciki "

Cikin sauri Abdallah yace " Allah mutumi na "

"Wallahi kuwa , yau saura sati biyu"

Had'e fuska Abdallah yayi sannan yace " amma gaskiya bana kyauta min ba sai yanzun kake gaya min"

"Kayi hak'uri abokina na bari ka samu natsuwa ne sai muyi maganar "

Ajiyar zuciya yayi sannan yace " shikenan Allah ya Santa alkhairi , a ina ka samu matar?"

"A funtua 'yar k'anwar Mama ce"

"Hakan yayi kyau , to ya maganar kayan aure an had'a ?"

"Eh an gama komai "

"Masha Allah na tayaka murna sosai , a ina zaku zauna?"

"A nan d'aki na mana "

"To ai kaji matsalar guy haya zaka nema idan ba haka ba ina mai tabbatar maka ba zaka mori amarcin ka ba"

Umar ya kalleshi ya kwashe da dariya yace "ahankali dai abokina yanzun kam dole mu zauna a nan dan duk basira ta ta k'are Mama kanta bataso mu zauna wuri d'aya amma insha Allah ba da jimawa ba zan nemi hayar"

"Tashi muje Umar "

"Ina zamu? nifa kasuwa zanje "

"Shikenan kaje amma kasani gobe ba inda zaka je "

"Allah ya kaimu"

Nan sukayi sallama
[2/6, 10:54 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*

*MRS NN ONE💋*

® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*

_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com

*dedicated to you readers ina alfahari daku*

*BAwan Allah fans much luv dearies Allah ya barmu tare*❤

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.