Bawan Allah Part 1 Compleete Complete Hausa Novel
Reading file: Bawan Allah Part 1 Compleete Hausa Novel.txt
Chapter 11 of 15
*Page*3⃣3⃣
Kwanci tashi ba wuya yanzun su Ummi suna Hutu Wanda da zarar sun koma zasu 200level , ba laifi tad'an saki jiki da Aminullah amma duk da haka bata tab'a bari suyi fira , sai dai Hafsa ce k'awarshi.
*Umar*
Umar kuwa ko da mahaifiyar shi taga yana D'an samun rufin asiri tace lallai sai dai ya fara Neman aure , da taga bashi da niyya sai ta had'a shi da Malam , nan Malam ya kirashi yayi mai nasiha sannan ya amince , zai yi auren amma D'an k'ara mishi lokaci domin ya d'anyi shiri, mahaifiyar tace ta amince .
Wannan kenan
Ummi da Hafsa kuwa yanzun ankoma makaranta karatun su suke tuk'uru basuda matsalar komai , Aminullah shi yake kula da al'amuran su na makaranta , lokuta da ma shi yakan maida su gida duk da Ummi bata son hakan amma idan Aminullah ya nace mata da magiya dole take binshi su tafi.
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
Yau shekara biyar kenan da b'atan Abdallah , Wanda ko me kama dashi ba'ace angani ba tun ana zuba idon ganin shi har an hak'ura da wannan *RUTACCEN ALAMARI* sun fawwalawa Allah komai .
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
To masu karatu bari na lek'a birnin London Dan ganin meke faruwa .
*W*asu kyawawan matasa ne na hango d'aya akwance d'aya kuma yana tsaye gaban wardrobe yana ta cillo kaya sama Dan k'areren gadon dake d'akin sai da ya d'ibi mai isarsa sannan ya rufe wardrobe d'in ya hau kitsa kayan shi awani kyakkyau sky blue d'in trolley , yana gama wa ya juya ya kalli na kwancen da keta faman lumshe idanuwan shi yace
"Friend Kodai bayau zaka bar k'asarnan bane?
Wanda aka Kira da Friend ya mik'e zaune tare da jingina da bango yace " Saif wallah bana jin tafiyar nan bansan mai yasa duk lokacin da naji sunan 9ja gabana ke fad'uwa ba , amma kuma wani b'arin na zuciya ta yana son koma wa ta bansan mai yasa hakan ke faruwa ba"
Ajiyar zuciya Saifullah yayi domin ya fahimci abokin nashi Dan tunda yake dashi be tab'a jin yayi hirar Nigeria ba ko wani relative nashi sai yai yana ganin kamar akwai wani *B'OYAYYEN AL-AMARI*da abokin nashi yake b'oye mai .
Cikin sanyi ya taka zuwa kusa da abokin nashi ya dafa shi tare da fad'in " ka kwantar da hankalin ka abokana mai yuwa wani alkhairi ne shiyasa zuciyarka ta aminta da komawar"
Cikin yanayin damu wa Abdallah ya d'aga k'ana nan idanuwan shi ya kalli abokin nashi kallon ban fahimta ba amma kuma sai bai ce komai ba .
Cikin tausasawa da lallashi Saifullah ya kwantar ma da Abdallah hankali yaryaji yana son tafiyar , nan ya mik'e suka cigaba da shirin su Kasan cewar yau zasu koma kuma flight di k'are hudu zasu bi .
Cikin dare suka sauka a Abuja Dr Ahmad da kanshi yaje taryar D'an nashi cikin sauri ya k'arasa ya rungume Abdallah yana fad'in "welcome to Nigeria son "
Da murmushi ya amsa masa sannan suka rungume juna .
Saif kuwa dama agida yace karsu zo tarbar shi su bari sai gobe sabo rashin kyawun hanyar .
Cike da fara'a Dr ya jawo Saifullah yana mishi sannu da zuwa .
Daga nan ya jasu zuwa gurin motar shi suka Shiga suka wuce gidan shi dake maitama.
Kusan raba dare suka yi suna hira Wanda Kasan firar Dr ne da Saifullah suke yi Abdallah ko jefi-jefi yake sa musu baki da ga baya dai ya gaji ya mik'e ya Shiga toilet ya d'auro alwala ya fara jero nafilfili , idan da sabo Saifullah ya saba da ganin hakan wannan d'abi'ar Abdallah Wanda shima yake k'ok'arin koyi da kyawawan halaye irin nashi .
Bayan Dr yayi musu sallama ya koma d'akin shi tunanin Abdallah ne suka addabe shi Wanda ba tun yau ba yake jin hakan , yanzun kam dole ya nemi mafita don baya son hak'k'in 'yan uwan shi ya kama shi wata k'ila ma yana da mata da yara idan ko hakane ya zama azzalumi kenan , da irin wad'an nan tunanin yayi barci Wanda sun zame mai jiki duk in yazo kwanciya sai ya yisu , .
*DA SAFE*
Bayan sunyi wanka sun shirya sukayi break 9:30 suka d'auki hanya bayan Saifullah ya kira mahaifin shi ya sanar masa da Dad d'in abokinshi zai dawo dashi .
Saifullah ne ya k'arb'i tukun suna tafe suna hira cikin nishad'i tun lokacin da suka doshi Zaria Abdallah yake ganin hotunan wasu abubu a idon shi sunan mai flashing tamkar video black white rutse idonuwan shi , duk wani moving d'in shi Dr yana gani sai bai kula shi ba Dan yana ganin wannan wani sign ne da Abdallah zai fara sanin koshi waye .
Ko da suka Shigo Zaria Abdallah duk ya gama zaucewa musamman ma da suka biyo ta kasuwar tudun Wanda Kasan cewar Saifullah D'an cikin tudun wada ne abun da k'ara d'aga mai hankali bai wuce da yaga shagon ogan Umar ba nan kam gaba d'aya durkushewa yayi a waje nan take zufar da yake yi ta k'ara yawaita , shi kanshi Dr abin ya bashi tsoro matuk'a , janyo shi yayi jikin shi yana shafa bayan shi.
Motsin da Saifullah yaji ana yi ne yasa shi kallon su tajikin mirror , yaga yadda abdallah jikinshi ke wani irin b'ari afirgice ya ce "Dr lafiya"
Shi kanshi Dr ya firgita kawai sai cewa yayi su wuce asibiti, mik'e titi yayi street *SHIKA* yake son kaisu domin nan ne yake ganin za'a ba abokin shi kyakyawan kulawa.
Kasan cewar basu had'u da cinkoson ababen hawa ba yasa acikin minti ashirin da biyar suka isa asibitin emergency aka kab'e shi aka wuce dashi wani private room nan likitoci suka duk'ufa akanshi .
Iya k'ololuwar tashin hankali Saifullah ya Shiga mostly yana ganin Abdallah a irin wannan halin amma nayau yafi gigitashi , ringing d'in wayarshi ce ta katse mai tunani da ya keyi ahankali ya zaro wayar cikin pocket d'in shi sunan da yagani ajikin screen d'in wayar ya fad'i a hankali "DAD?"
A nutse ya d'aga wayar gamida sallama bayan Anas sallamar maifin ke tambayar shi lafiya shiru har yanzun basu iso ba?
Cikin natsuwa Saifullah yake sanar ma dad d'in shi abunda ke faruwa .
Cikin mamaki dad d'in yace gashinan zuwa,
[1/13, 8:00 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
*Wannan shafin rankatakaf naku ne masoya Bawan Allah na mallaka muku shi aduk inda kuke fad'in k'asar nan Allah yabar zumunci da k'aunar juna Amin â¤🤞*
*Dedicated to Faty Axland🤪*
3⃣4⃣
Banda *SAFA DA MARWA* babu abunda Dr da Saifullah suke yi , sun d'ibi kusan minti arba'in a haka sai ga Dadyn Saifullah ya Iso cikin girmamawa suka gaisa da Dr sannan yayi masa ya mai jiki sai wurin ya d'auki shiru , chan Dr ya juyo ya kalle Saifullah yace "Saif kaje gida ka huta mana "
Cikin sanyi yace " no Dr bazan iya zuwa ko ina ba har sai nasan halin da abokina yake"
Dadyn Saifullah yace "gaskiya ne bari mu tsaya muga jikin nashi "
Ana cikin haka k'ofar d'akin da aka kwantar da Abdallah ta bud'e wani Dr ne ya fito daga cikin ta cikin ta ya k'araso kusa dasu yace " ina Baban Abdallah?" Dr yace" gashinan "
"Ina son ganin ka"
Cikin sanyin jiki Dr Ahmad ya bi bayan shi suka D'an tab'a tafiya kad'an sannan suka k'arasa office d'in shi bayan sun Shiga sun zauna Dr ya fara yima Dr Ahmad tambayoyi akan rashin lafiyar Abdallah ,
Ba tare da b'ata lokaci ba ya sanar masa da duk abunda ya faru har zuwa yanzun ,
Ajiyar zuciya Dr yayi yace "this is serious, but Dr meyasa baka yi k'ok'arin dawo masa da tunanin sa ba kuma ka k'asa sashi cikin wata rayuwar rud'ani ? Wannan serious case ne amma da tun farko ne da yanzun memory d'inshi ya dad'e da dawo wa "
Shi dai Dr Ahmad shiru yayi Dan duk abinda zai fad'a ya gama fad'i ,
Dr ya sake cewa "kuma abinciken da mukayi muna da tabbacin yana da connection da garin nan , Dan haka indai ka shirya nema masa lafiya to lallai sai dai ka barshi a nan zuwa wani D'an lokaci"
Bayan guntun nazarin da Dr Ahmad yayi yace" shikenan ba damuwa indai zai samu lafiya komai me sauk'i ne"
Dr yace "akwai yuwuwan hakan insha Allah"
"Zan iya zuwa na gashi ?"
"No har yanzun likitoci basu gama aikin suba ku k'ara musu lokaci"
Nan dai suka k'ara tattaunawa akan matsalar sannan suka rabu , alokacin da Dr Ahmad ya koma wajen Saifullah shi kad'ai ya tarar a wajen nan yake tambayar shi "Saifullah ina Baban naka?"
Saif cikin yanayin damu wa yace " yayi bak'i ne agida "
"OK muje muyi sallah Gashi har la'asar tayi ba muyi azahar ba "
Sai da suka d'anyi tafiya sannan suka fara tambayar inda masallaci yake akayi musu kwatance ,
Bayan sun fito daga masallaci ne ya Ciro wayarshi ya fara kiran wata number da aka rubuta "Bro" ajikin ta , acikin ringing na biyu aka d'aga kiran ,
Murmushi yayi sannan ya amsa sallamar da aka mai , bayan shiru da yayi na kimanin minti d'aya sai yace " duk naji k'orafin ka kafin nabaka amsa , kana school ne ?"
Shiru yayi domin sauraran me za'a ce mishi sannan yace "to ina ina cikin hospital naku ka sama mana abinci mare nauyi na mutum uku "
Nan d'in ma shiru yayi sannan daga baya yace "no don't worry ba ni bane friend d'ina na , kayi sauri fa na fara jin yunwa " kitt ya kashe wayar Dan yasan halin k'anin nashi ba k'i ma yatafi siyan abincin da wayar akunnen shi suna hira ba
Bayan sun aje wayar ne Dr Ahmad yace "AI da ka bari ma akwai restaurant anan waje da sai muci achan kawai "
"Wallah Sam bana son Barin cikin hospital d'in nan sai naga kamar wani Abu zai faru da Abdallah"
Dafa kafad'arshi Dr yayi yace "babu abunda zai faru dashi a hirar ma da mukayi da Dr yace yaji sauk'i yanzun ma bacci yake yi "
Ajiyar zuciya Saifullah yayi sannan yace " Alhamdulillah"
Suna tafe suna hira jefi jefi har suka k'arasa bakin d'akin da aka kwantar da Abdallah suka zauna a d'aya daga cikin kujerun dake aje wurin.
Bayan kimanin minti ashirin wayar Saifullah ta hau ringing ya d'aga tare da karawa akunne , k'anin nasa ya tambaye shi a inda suke , shi kuma ya mai kwatance , ba'afi minti Biyar ba sai gashi ya bayyana awajen .
(Ni mai d'aukan rahoto Wanda Nagani wajen saida alk'alami na ya fad'i k'asa saboda mamaki Saifullah ne ya mik'a min tare da fad'in " yes he's my brother " 🤪 AI ba shiri na cigaba da d'aukan rahoto Dan kar ayi show bani)
Aminullah ya k'arasa cikin sauri gami da ajiye ledar abincin kan d'aya daga cikin kujerun ya rungume D'an uwan sa cikin shauk'in bege yace " I miss you sweet bro "
"I miss you too little bro"
Sannan suka saki juna suna murmusawa .
Ahankali ya kai Cuban shi ga Dr cikin girmamawa ya gisheshi
Dr ya amsa tare da murmushi afuskarshi
"Bros ga abincin nan fa kuci "
Cin abincin suke amma kowa da abinda yake sak'awa a ranshi.
Wasu doctor's ne guda biyu suka fito daga d'akin , d'aya daga cikin su ya ce musu ya farka zasu iya zuwa su Ganshi , cikin sauri suka Shiga d'akin shiko Aminullah mamaki ne fal acikin shi yanda yaga har riga-rigen Shiga suke yi AI shima sai ya bisu abaya.
Akwance suka same shi hannun shi d'aya an samai drip tashi d'aya har yad'an fad'a kad'an ,
Cikin kulawa suka fara tambayar shi yajin nashi , kai kawai ya d'aga alamar da sauk'i , sannan ya kalli Saifullah yace.
"Saif baka tafi gida ba?"
Saif ya D'an harare shi yace " why should I go home when you are here"
Murmushi yayi ya kawai sannan ya juya kalli Aminullah kallon Neman k'arin bayani akan shi ,
Said ya janyo Aminullah kusa dashi yace " Aminullah da nake baka labarin shi, "
Sannan ya juya ya kalli Aminullah yace " Abdallah nasan ka gane shi "
Aminullah ya rab'a ta gefen Saifullah ya k'arasa kusa da Abdallah sannan yayi mishi ya jiki , suna d'an fira jefi-jefi dai-dai nan wayar Aminullah ta hau ringing sunan da yagani jikin wayar yad'an murmusa , Saifullah na kallon shi ya sakar masa dundu tare da fad'in
"D'an iska dariyar me kake "
"Ba komai sister na ce ta kira "
Zuwa lokacin kiran har ya katse D'an haka shi sai ya k'ara kira ,
Alokacin da aka amsa kiran yaji ance " haba Aminullah ka ce mujiraka kuma kayi shiru gashi har Aunty Ummi ta gaji ta tafi "
Dafe kanshi yayi tare da fad'in "ya subhannallah yan ke kina ina?"
"Ina inda ka barni "
"OK gani nan zuwa".
Ya juya ya kalli Saifullah yace "bros bari naje na dowa , kuna buk'atar wani Abu ne "
"Ah ah ka gaida k'anwar tawa"
Yamik'e tare da Sosa k'eya yayi musu sallAma har ya kai bakin k'ofa Dr yace " Aminullah kawuce da Saifullah gida ya D'an huta "
Saif zaiyi magana Dr ya dakatar dashi ta hanyar nuna masa yaje kawai ba wata damu wa,
Sai da suka Shiga mota sannan Aminullah ya juya ya kalli D'an uwansa yace "bafa gida direct zan wuce ba kuma kaga yamma tayi "
D'an tsaki yaja yace "muje"
Cikin makaranta suka koma , Hafsat na hango motar Aminullah ta taso ganin wani kyakkyawan saurayi cikin motar sai da yasa numfashin ta d'aukewa na wucin gadi , da k'yar ta iya Jan k'afafun ta zuwa kusa da motar , baya ta bud'e ta Shiga bayan ta rude motar sai nan ta gaida Saifullah a dak'ile ya amsa mata ya juyar da kanshi kan titi gami da d'aure fuska
Tunani yake yi wannan wace yarinya ce take tare da k'aninshi? Meye dangan takar su , yana cikin maganar ya tsikayi muryar abokin shi yana cewa "Hafsa nakira wayar Aunty Ummi bata d'aga ba ko tayi fushi ne?"
Sai da tayi dariya sannan tace " idan munje kaji"
"Is that what you said?"
Dariya kawai tayi domin tasan yanzun zai birkice Dan baya son ganin fushin Ummi Sam
*sorry for this one
[1/15, 1:55 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
*Readers bansan da me zan saka muku ba har kullum bakwa gajiyawa wajen sambad'o addu'oin fatan alkhairi agareni wallah har cikin raini ina ji daku ina k'aunarku Allah ya k'ara had'a tsakaninmu ya karemu daga sharrin dukkan abin k'i*ðŸ™Â
*This page dedicated to you dearies*
*k'awalli*
*Maman hanan*
*Nafi khan*
*Fareeda*
*Ameenah*
*Mrs Abdulwahab*
*Rahma Isma'il*
*sa'adiya illa*
*Calz me nuccy*
*Maman Mimi*
*Umulkhairi Jibril*
*Ummulkhairi GJ*
*kai wallahi kuna da yawa you're uncountable amma kusani ni d'in taku ce har gaban Abadan*â¤😘ðŸ˜Â
3⃣5⃣
Shikam Saifullah ta kaici Duk ya cika shi , tun kafin su k'arasa aka fara kiran sallar magrib , dan haka suna k'arasawa Aminullah ya gyara parking dai dai k'ofar gidan su Hafsa , ta na fitowa tayi musu godiya had'e da sallama ,
Aminullah ya kalli yayan shi yace "bros ga masallaci chan muje muyi sallah "
D'an tsaki yaja sannan ya fito daga motar tare da fad'in " dama akan wannan abar ka b'ata min lokaci?"
Murmushi yayi yace "uhum bros ba zaka gane bane amana tace dole na kula da su "
Wata harara ya sakar mai sannan suka wuce masallaci .
Ummi kuwa tana shigowa unguwar su madadin ta wuce gidan su Hafsa sai ta wuce gidan su sai dai ta aika k'aninta da jakar makarantar ta , sai da ta yi sallar magrib sannan tayi sallama da gida tafito.
Dai dai lokacin su Aminullah suka dawo daga masallaci , yana ganinta yaja ya tsaya shiko sai tuni ya kame acikin motar
Takaici ne duk ya isheta bata so suka had'u ba tasan yanzun zai dameta da surutun shi , tamau ta had'e ranta sannan ta k'araso wurin ,
Hannun shi biyu ya had'a alamun banhak'uri sannan ya marai-raice yace " ayya Aunty Ummi Ki gafarce ni "
Dariya ne yakusa kufce mata dan yadda yayi maganar dole ne ma yabaka dariya,
"Is OK sai da safe " tana k'ok'arin shigewa gida ya tsayar da ita tare da fad'in
"Ga bros d'ina ku gaisa "
D'an lek'awa tayi ta window motar k'yarrr suka had'a ido dashi yana waya , d'agowa tayi tace ma Aminullah "ka gaishe shi nina tafi sai gobe "
Tana kaiwa nan ta shige gida , shi kuma ya bi bayanta da kallo yana murmushi
Yana Shiga mota Saifullah ya tallabe mai kai yana fad'in " D'an iska arasa gane wace ce budurwar taka aciki"
Tallabe k'eyarshi yayi yana cewa "wallah bro amana nane"
Ahaka dai yaja motar suka tafi suna hirar yaushe gamo
******************
Wasa-wasa dai Abdallah yau kwanan shi biyar a asibiti yana samun kulawa sosai wajen su Dr Ahmad da Saifullah , Aminullah ma ba baya ba idan ya samu chance yana k'araso wa su sha fira , Abdallah har ya gaji da nacin asallameshi dan shi babu inda yake mai ciwo sai uban gwaje gwaje da ake mai da tare tambayoyi wad'anda suke k'ok'arin birkita mai tunani,
Saifullah kuwa har yanzun baisan hak'ik'anin abinda yake damun abokin shi ba domin Dr Ahmad ya sakaye zancan daga shi sai likitoci suke aikin su,
Tun lokacin da Saifullah yaga Ummi Sam hankalin shi ya kasa kwanciya fuskarta sai gizo take mishi duk iya k'ok'arin shi ya daure amma ya kasa , sai kawai ya yanke shawarar ya nemi k'anin shi suyi magana , bayan ya dawo asibiti da daddare ya nufi part d'inshi wanka yayi ya ci abinci sannan ya nufi part d'in Aminullah a kwance ya sameshi yana game d'in criminal case a tab d'inshi da alama yana jin dad'in game d'in , motsin da yaji ne abayan shi ya sashi juyawa Saifullah yagani tsaye bakin k'ofa ya jinga ya zuba mishi k'ananun idanuwan shi da suke alumshe kamar mai jin baccin , dama idan ka Ganshi cikin wannan yanayin to akwai abunda ke damun shi .
Cike da kulawa Aminullah ya aje tab d'inshi sannan yace "what's up bro?"
D'aga kafad'un shi yayi alamar babu sannan ya k'arasa shigowa d'akin ya zauna kan kujera ya sake zubamai ido
Tasowa yayi yazo ya zauna kusa da shi yace " Bros wai meke damunka dan Allah ka sanar da ni idan zan iya taimaka maka idan ba zan iya ba kuma ko shawara na baka"
Ba tare da b'ata lokaci ba Saifullah ya sanar ma Aminullah da k'udurin shi akan Ummi daga k'arshe kuma ya nemi shawarar shi
Duk da Cewar Aminullah yaji wani iri akan maganar amma sai ya dake domin yana son ganin farincikin D'an uwansa , shima bai b'oye mishi komai ba game da wace ce Ummi ,
Tausayinta ne k'arara a fuskar Saifullah ya d'ago idanuwan sa da suka k'ara k'ank'ancewa yace "kana nufin har yanzun ba'a ga mijin nata ba ?"
"Had yanzun ba'aga Wanda yaga me kama dashi bama"
Jinjina kai yayi yace "gobe zaka rakani wajen mahaifin ta"
D'an zaro ido Aminullah yayi yace" me zakayi?".
With compidence yace "auren ta zan nema"
"Bro haramun ne fa Neman aure akan aure "
"Sam wannan auren nata bashida amfani kawai yarinya k'arama ana k'ok'arin d'aura mata wahala , yanzun haka ma wayasan inda yake ? Ko yana da rai ko bashida da rai oho?"
"Tab mai da wuk'ar , but you have to control your anger "
Bai cemai komai ba ya fita a d'akin , daren da k'ar ya samu yayi barci tunanin Ummi kawai yake yi dan yanzun wani tsananin sonta ke k'ara shigar shi duk ya k'agara gari ya waye
Kasan cewar yau Saturday ne ba makaranta dan haka da wuri suka shirya suka je gidan Malam kasan cewar safiya ce sun same shi yana ta koyar da almajiran shi wuri suka samu gefe suka zauna saida Malam ya sallami almajiran sannan ya kalli Aminullah yace " Amintacce bawa Kaine da sanyin safiyar nan ?"
Murmushi yayi yace "nine Malam"
Cikin girmama juna suka gaisai sannan Aminullah ya gabatar da D'an uwanshi Saifullah awajen Malam
Shikuwa Saifullah ya gabatar da k'udurinshi na son auran Ummi a wajen Malam
Shiru Malam yayi kamar ba zaiyi magana ba Dan maganar tazo mishi a bazata
Ya fara magana kamar haka , " kamar yadda D'an uwanka yayi maka bayani Ummi dai da aure a akanta sannan kuma bamu da ikon daura wani aure har sai an warware wanchan dan haka kayi hakuri duk yadda muka shawarta zan nemeka"
Godiya sukayi suka tafi duk da cewar sa Saifullah baiji dad'i ba Kasan cewar bai samu k'wak'waran tabbaci daga Malam ba haka ya koma gida cikin zullumi
Ranar wata talata ne wurin k'arfe biyar Ummi ta gama lectures d'in ta Hafsa kam bata samu zuwa va sakamakon wani irin ciwon kai da ta tashi dashi , hakan yasa yau ita kad'ai Aminullah zai mayar gida , bayan sun Shiga motar ya Tayar kenen wayarshi ta hau ringing Saifullah ne ya kirashi , bayan ya d'aga wayar yana sauraron me zaice bayan ya gama kawai sai ya ce "OK "ya kashe wayar
Juyawa yayi yace ma Ummi "Aunty Ummi kimin hak'uri kad'an zan amshi sak'o wajen bro acikin hospital "
Ta D'an b'ata rai tace "to"
Suna isa asibintin yayi parking inda ake parker motoci sannan yace "D'an Allah muje Ki gaida yaya na yana da mutumcin shi be cika d'aure fuska irin na Saifullah ba"
"Uhum muje"
Haka suka taka sunan jera wa kowa ya gansu sai ya sake kallon saboda tsabar marching da sukayi
Sai da sukayi tafiya me d'an nisa sannan suka k'arasa d'akin
Ummi kuwa nan take taji zuciyar ta na bugawa kamar zatayi tsalle ta fad'o k'asa
Tare da sallama ya bud'e k'ofar Kasan cewar gadon yana kallon k'ofar ya saya direct kana Shiga zaka hangi na kwance akan gadon yana baccin
K'iiii taja wani dogon birki sakamakon arba da tayi da wata fuska da ta dad'e tana marmarin gani duk da dai sauyin da ta gani hakan bai hanata gaskata ko wa ta gani ba
Aminullah ne ya juyo da niyar yi mata magana ita kuma alokacin ta juya ta kwasa aguje
"Ummi! Ummi!! Ummi!!!?" Haka yayi ta kwad'a mata kira amma bata waiwayo ba haka yasa shima ya kwasa aguje yabi bayan ta
â¤â¤
[1/17, 3:57 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
3⃣6⃣
Tun da ta runtuma bata tsaya ba mutane sai kallonta suke , duk iya k'ok'arin Aminullah ya tsaida Ummi ya kasa , aiko yana ganin sun kai wurin wani kwararo da ba mutane ya figo hijab d'inta ta dawo baya , kamar zata bangaje shi ,
Ganin yadda take kuka harda majina gashi sai wani tittirjewa take kamar sabuwar 'yar bori ya sashi daka mata tsawa " ke Zainab!!"
K'ara firgita tayi zata sake gudu sai ya sassauta muryarshi yafara magana cikin sanyi " Ummi Ki natsu mene ne ?, me ya faru ?, wani Abu aka miki,?"
Duk ya gama jero tambayoyin shi amma kawai da ido tabishi
Azuciyar ta ko fad'i take ina ma tana da halin amsa masa wad'an nan tambayoyi data amsa su
Shi kuma ganin shirun da tayi ga hawaye yana ta sintiri a fuskarta sai ya fara tunanin anya Ummi kam kanta k'alau ? Bai sake cewa komai ba yaja hannun ta har gurin motar shi sannan yace mata ta Shiga , tana Shiga ya rufe sannan ya zagaya shima ya Shiga , sannan ya tada motar har a lokacin kuka take shak'a ,
Haka yayi ta tuk'i amma Sam zuciyarshi bata mishi dad'i saboda yadda yake jin kukan Ummi a zuciyarshi kamar ana d'iga mishi tafasasshen ruwa.
Suna isa k'ofar gidan su ta hangame murfin motar ta fito ko tsayawa ta rufe batayi ba ta fad'a gidan su Hafsa , shi dai Aminullah kanshi duk ya d'aure ya rasa gane meke damun Ummi ayyah batada junnu, nan ya coge a k'ofar gidan.
Ummi kuwa tun da tasa kanta a zauren gidan ta fara k'wala ma Mama kira
Mama na d'aki abin da bata tab'a ji ba kenan afirgice ta fito tana "Ummi mene ne ?"
Amma ina zubewa tayi ta dasa sabon kuka , Mama duk ta kid'ime ,
Hafsa dake d'aki tana fama da kanta tafito ganin yadda Ummi ke kuka bilhak'i da gaskiya sai jikin ta ya k'ara sanyi domin duk runanin ta wani mummunan abun ne ya faru .
Duk suka rud'e da tambayoyi amma Sam Ummi tak'i magana sai kuka , cikin k'unci Hafsa ta koma d'aki ta d'auko hijab d'in ta ta fice , yanayin tashin hankalin da take ciki shi yasa bata lura da Aminullah dake zaune kan dakali ya zabga uban tagumi ba , shima kuma bai kula ta ba .
Direct gidan su Ummi ta fad'a ba'afi minti biyar ba sai gashi sun fito tare da Malam.
Malam ya ga Aminullah zaune turus ya zabga tagumi , shi kanshi Malam d'in sai da gaban Shi ya fad'i , cikin sanyi ya ce " Amintacce meke faruwa ne ?"
Aminullah ya kalli Malam cikin damuwa sannan ya labarta mishi sukkan abubuwan da suka faru d'azun ,
Bai yi wata wata ba yace ma Aminullah zo muje , suna suga gidan Malam ya hau fad'a yana tambayar ta me ya faru ? Ko tayi hauka ne duk ta tayar wa da mutane hankali,
Murya na rawa kamar ta mai koyon magana tace "Baba na...na..Ganshi"
"Wa kika gani?"
Zata k'ara wani kukan Malam ya yi jan ido yace takuma sai ya lallasa ta
Da k'yar tace " *ABDALLAH* "
Maman kam dab'as ta zauna a k'asa tayi zaman 'yan bori , tana tunanin to kodai mafarkin ta na jiya ya zama gaskiya ne?
Hafsa ma sai da ta Zabura,
Aminullah gaba d'aya ya firgice domin bai gane inda zancen ya dosa ba .
Malam ma kanshi duk ya d'aure ya kalli Ummi da keta wik'i-wik'i da ido dan yanzun kukan ya tsaya ya ce "Ummi kinsan me kike fad'a kuwa?".
With confidence ta d'aga kanta tare da fad'in "ku tambayi Aminullah AI shi ya kaini inda yake "
Nan fa kallo ya koma kan Amintacce wanda duk sun k'ara birkita shi , Malam ya kalli Aminullah yace " Amintacce mene ne hak'ik'anin wannan zancen?"
Cikin muryar rud'u Aminullah yace "kamar yadda na gaya maka a waje , abokin yaya na ne bai da lafiya shine yaya na yakirani na je na karb'i kaya na wuce mai dasu gida , shine na rok'i Ummi ta raka ni lafiya lau muka shigo asibitin amma tunda muka Shiga d'akin duk ta birkice kuma ni bata cemin komai ba shine na kwaso ta na dawo da ita"
Malam ya kalli Ummi cikin takaici zai magana tayi sauri ta ce "wallahi tallahi Baba naga yayan Hafsa indan kuma baka yarda ba kuje dashi ka gani idan bashi ba wallahi na yarda daga yau na zama bazawara" ta k'arike maganar da wani kuka me tsuma zuciyar me saurare.
Kowa awurin sai da ta bashi tausayi , Mama da k'ar ta tattaro natsuwar ta tace " Malam aje a duba ko Allah yasa za'a dace"
"To"kawai yace ya fice Aminullah ya bi bayan shi , suna fita ya juyo ya kalli Aminullah yace " ka tsaya muyi sallar magrib anan sai muje ka kaini" jiki a sanyaye yace "to"
Shikam Bawan Allah duk wainar da ake toyawa bai sani ba sharar baccin shi kawai yake yi sabo allurar da aka mai
Saifullah kuwa tun da su Aminullah suka fita yabi bayan su amma cikin rashin sa'a ya sa bai gansu ba , tun lokacin ya ke kiran wayar Aminullah amma bai d'aga ba hankalishi duk ya tashi gashi shi kad'ai ne awajen Abdallah ballantana yabi bayan su .
Sai 7:30 sannan Dr Ahmad ya dawo ganin Saifullah cikin rud'ani yasa shi tambayar meke damunshi amma ya rasa amsar da zai bashi kawai sai yace mai "ba komai "
Bayan minti goma Abdallah ya farka gami da mik'a da salati , duk suka yi mishi sannu jiki a mace yakalli agogon da ke mak'ale a bangon d'akin zumbur ya mik'e ya fad'a toilet domin d'auro alwala , shigarsa bayin kenan Aminullah ya bud'e k'ofar d'akin tare da sallama suka shigo da Malam
Cike da girma-mawa suka gaggaisa Malam yayi musu ya mai jiki , Saifullah ya kalli Aminullah domin Neman k'arin bayani suna had'a ido yayi sauri yuyar da kanshi ,
Murfin k'ofar bayin aka bud'in tun da Malam yayi arba da wannan fuskar gaban shi yayi mummunan fad'uwa ya tabbatar da ba'a zaune yake ba da sai ya fad'i k'asa warwars lallai Ummi tayi namijin k'ok'ari
😂😂😂😂😂😂😂😂
Da k'ar Malam ya had'o miyon bakin shi yace " *BAWAN ALLAH?*"
Sosai sunan ya daki k'ok'on zuciyar Abdallah amma Sam Brain d'in shi ta kasa functioning ,
D'aga idanun shi yayi ya d'orasu kan Malam take tsigar jikin shi ya tashi , brain d'in d'in shi ta fara mishi flash back nan take ya runtse ido , Dr Ahmad na ganin haka ya danna k'ararrawar kiran likita zame wa yayi zai fad'i sukayi sauri suka tare shi.
*sorry for this one wayata tana hucking*🤪👈
.
[1/21, 12:18 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
*This page dedicated to you Bawan Allah fans , nagode da addu'oin fatan alkhairi da kuke agareni lallai Ku k'awayen arzik'i ne nagode Allah ya barmu tare ya sadamu aljannatul firdau*â¤
*k'awa*🤪
3⃣7⃣
Gaba d'aya Abdallah ya birkice wasu irin hotuna yake gani black and white wa D'an da bai San inda suka samo asali ba .
Ko da likita yazo tambayoyi ya runk'a mai amma yace bai San komai ba , haka suka sake masa allurar bacci ya koma .
Har zuwa wannan lokacin Malam yana asibin mamaki duk ya cika shi .
.
Dr Ahmad ya maida duban shi ga Malam yace " Malam dama ka sanshi ne?"
Murmushin takaici Malam yayi yace "Abdallah haihuwar shi ce kawai banyi ba , kuma har yau bana bamban tashi da 'ya'yan da na Haifa da ciki na"
Shiru d'akin yayi Malam ne kawai da Dr Ahmad suka san mai suke cewa amma Saifullah da Aminullah gaba d'aya Kansu s juye yake .
Malam ya kalli Aminullah tare da nuna Abdallah dake kwance yace "wannan shine mijin Ummi da ya b'ata shekara biyar da suka wuce "
Wayyo Allah zo kuga tashin Hankali a idon Saifullah gaba d'aya yaji maganar ne tamkar saukar aradu , tabbas da za'a gwada jininshi alokacin da ansha mamaki , domin bai taba zato ba balle tsammani,
Cikin murya mai cike da firgici yace " Malam mai kake nufi ne wai ?"
Malam bai ce komai ba domin baisan kuma ya zaiyi ya fahimtar dashi ba .
Dr Ahmad yace "Saifullah ka kwantar da hankalinkA gobe insha Allah za kaji komai yanzun dare yayi "
Sannan ya juya ya ce "Aminullah ka maida Malam gida gobe zamu je gidan dukan mu in Allah ya kaimu"
Nan suka mik'e Malam yaje wajen kan Abdallah ya tofa masa addu'oi sananan sukayi sallama amota kuwa Aminullah ne ya damu Malam da tambayoyi domin shi duk ya k'agu yaji gaskiyar al'amari, amma Malam yak'i Sam suyi magana .
A can gida kuwa su Ummi sun kasa sun tsare , har da Umar ma da ya shigo gidan bayan fitar su Aminullah da Malam , tun suna tsaye har suka gaji suka zauna amma babu su babu labarin su, har 10:30am .
Mama ta kalli Umar tace "Umar kaje gida mana kaga dare yayi "
" Mama ko naje gida bazan iya yin bacci ba"
Mama zatayi magana kenan sai sukaji k'arar tsayuwar mota , Umar yace "Mama Bari na duba nagani"
Ummi kuwa zuciyarta sai k'ara bugu takeyi.
Umar na fita Aminullah har ya ta tada motar shi yayi gaba Malam kuma ya d'auki hanyar k'ofar gidan shi, cikin sassarfa Umar ya k'arasa gurin Malam yana fad'in "sannu Malam"
"Yauwa Umar "
"Malam Abdallah ne kuka gani ko?"
Murmushi Malam yayi sannan ya dafa kafad'ar Umar yace " ka kwantar da hankalinka gobe insha Allah zasu zo sai muji koma wane ne"
Ajiyar zuciya ya sauke sannan sukayi sallama , shikuma Umar ya koma gidan su Hafsa dan sanar dasu yadda sukayi da Malam,
Ranar dai kowa kwanan zullumi yayi musamman ma Ummi da take ganin ga k'oshi ga kwanan yunwa.
*Da safe*
Misalin k'arfe Tara na safe Abdallah ya fito wanka ya shirya cikin shigarshi ta k'ananan kaya maroon din T-shirt ce ajikinshi sa navy blue d'in jeans kalar yayi matuk'ar amsar jikinshi Kasan cewar shi faran saurayi kan kujerar robar da aka tanada dan masu dubiya ya zauna tare d'aukar wayarshi ya fara dannawa .
Aminullah ne ya bud'e k'ofa ya Shiga tare da sallama , batare da ya juyo ba ya amsa sallamar ,
"Bros Dr yace mu same shi awaje " cewar Aminullah yana kallon Abdallah da ya kyab'e fuska
"Ina zamu je ne?"
Aminullah zai yi magana kenan wayar Abdallah ta fara ringing , cikin sanyi ya d'aga wayar gami da sallama , bayan D'an shiru kuma sai ya mik'e ya kashe wayar ba tare da yace komai ba , Aminullah ne ya d'auki wata 'yar k'aramar traveling bag dake gefen gadon suka fita
A parking space na cikin asibitin suka tarar da Dr Ahmad da Saifullah suna jiran su Saifullah ya Shiga mazaunin driver , Abdallah ya Shiga b'arayin me zaman banza , yayin da Dr da Aminullah suka Shiga baya .
Tunda suka d'auki hanya Abdallah ya tattare hankalin shi da natsuwar shi yaba titi amana, runtse idanun shi yake yi yayinda wasu hotuna keta masa yawo a kwanyar shi wasu kalamai suna ta mashi yawo a dodon kunan shi , hannu ya sa ya toshe kunan shi idon shi kuwa runtse shi yayi kamar k'aramin yaro , duk suna lura dashi amma Sam Dr ya hana su tab'a shi sai dai suka bishi da fuskar tausayi , har suka iso k'ofar gidan bai ma San sunzo ba , sai da Saifullah yayi mishi magana sannan d'ago jajayen idanuwan shi ya kalle shi
"Mun iso fa" cewar sai ya bud'e murfin motar zai fita , shima murfin ya bud'e ya fita k'ofar gidan su ya ci karo dashi take wasu abubuwa daban daban suka runk'a yi mishi yawa akai gaba d'aya ya daina ganin zahiri sai bad'ini
Malam dake ta karatu da almajirai ba shiri ya sallame su suka tafi sannan ya k'araso fuska d'auke da farinciki
Umar ya fito daga cikin gidan su Hafsa sakamakon tsayiwar motar da yaji yana fitowa yayi arba da Abdallah jingine jikin mota aiko da gudu yaje ya k'wak'wu-meshi , shi dai Abdallah ji kawai yayi an rungume shi , shikam Umar ji yake kamar in yasaki Abdallah bazai sake ganinshi ba , rungumar da Umar ya ma Abdallah sai da yajiyo bugun zuciyar shi domin yi take zamar zata fasa k'irjin ta fito
Cikin dauriya Abdallah ya b'amb'are Umar daga jikinshi , kallon juna suke ido cikin ido , da k'yar Abdallah ya k'ak'alo wani murmushi ya jefa asaman fuskarshi , Umar ya kalli Abdallah cikin kewa yace "nayi kewarka aboki na , kai kam ko nema na baka yi "
Shikam Abdallah bubbuga kafad'ar Umar kawai yayi amma Sam bai ma San koshi waye be .
Malam ne ya katsesu da cewa " mu Shiga daga ciki ".
Hafsa da tafito ta basu izinin Shiga sai kallon Abdallah take kamar taga sabon hallita , suna had'a ido dashi ya balla mata harara azuciyar ta tace"bari na kama kaina tun kafin ya jizga ni dan naga ya k'aro wulak'anci"
Juyawa tayi sukuma suna binta abaya tana tafe tana tuntub'e , shiko Aminullah sai dariya yake kwasa aranshi yace ya samu na tsokana
[1/22, 5:11 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
38
Hafsa na k'arasa Shiga gida ta runtuma aguje sai d'akin Ummi ko sallama bata tsaya yi ba ta yaye labule ta afka , Ummi dake ta cikiniyar sa kaya Wanda da alama yanzun ta fito wanka ta kalli Hafsa tace "ke dai banga ranar da zaki girma ba ke kullum aguje kamar y'ar gudun hijira "
Hafsa ta had'a girar sama da ta k'asa tafara magana cikin hasala "ke fa gaba d'aya ba'a miki gwaninta daga zuwa yi miki albishir sai Ki hau gwasale mutum , to ni kinga tafiya ta nama fasa fad'a " ashagwab'e ta k'arasa maganar
Cikin marai-raice murya Ummi tace "ayya *k'walli* ta yi hak'uri zo Ki fad'a min "
Hafsa ta had'e rai tace " a nawa ?,"
Ummi tayi dariyar mugunta tace "a arba'in"
Du Kansu suka kwashe da dariya .
*Bawan Allah* kuwa tunda suka shigo gidan ya k'ara birkicewa musamman ma da yayi arba da Mama tana shimfid'a tabarma k'uri ya k'ura mata ido tamkar mai son ya fahimci wani Abu amma Sam ya kasa
Saifullah ne ya jashi ya zaunar dashi, har wannan lokacin idonshi yana kan Mama , ko da Mama ta juyo suka had'a ido sai da taji gaban ta ya fad'i , azuciyarta tace "tabbas wannan bawan Allah ne"
Bayan 'yan gaishe-gaishe Mama ta mik'e taje ta kira su Ummi domin ayi komai a gaban su ,
Ummi ce agaba Hafsa tana binta a baya ahankali take takun ta kamar me tsoron kar ta taka wani abun , dai dai lokacin Abdallah ya juyar da fuskarsa b'angaren , tundaga k'afafuwan ta yake kallon ta har sai da ya dire idanuwan shi cikin Nata Sam yakasa daina kallon ta wani Abu yake ji tamkar magnet yana fizgarshi zuwa gareta badan ya danne zuciyarshi ba to tabbas zai iya mik'e wa zuwa gareta , cikin natsuwa tagaishe sannan ta nemi wuri chan gefe ta rakub'e
Malam ya kalli Aminullah da yayi shiru amma idanuwan shi k'yar akan Ummi yayi murmushi kawai ya maida duban shi ga Saifullah da kawai pretending yayi amma zuciyar shi Sam bata mishi dad'i ,
Malam ya Kali Dr Ahmad yace " Alhaji zamuso muji ya akayi ka had'u da Abdallah?"
Cike da fahinta Dr Ahmad yafara magana sai alokacin Abdallah ya maida dubanshi wurin, Dr yace" akwai wata rana ina hanyata ta dawowa kano daga Kaduna Kasan cewar tafiyar asuba nayi k'arfe shida da Rabi nakusa Shiga kano ina daf da shiga gari sai naga cincirundon jama'a a gefen titi har zan wuce kuma sai naji zuciyata tana fizgata akan naje wajen koda na fita nayi parking mota ta a gefen titi na tsallaka abunda nagani ba k'aramin tayar min da hakali yayi mutane ne kwance kamar matattu cikin gaggawa na kira motar asibitin my nan da nan sai gasu sunzo akwashe su sai asibitin aminu kano , to nikam tunda na mik'asu cikin saurin likitoci ban k'ara bi ta Kansu ba domin ba b'arayi na bane , bayan yan kwanaki sai aka kirani ake sanar dani cewar mutanen nan duk 'yan uwansu sun gansu amma banda mutum biyu dan d'ayan ma bai farfad'oba likitoce nata aiki akanshi shikam d'ayan ya farka , tunda naji hakan na garzayo nazo asibitin , abunda na gani ba k'aramin rud'ani nashiga ba amma na dake duk dan kar agane , fuskar Abdallah iri d'ayace da fuskar d'ana Abdallah da yarasu shekara bakwai kenan da ace yana Raye to tabbas za'a kirasu da identical twince wannan dalilin ne yasa naji ina son taimaka masa"
Tunda ga nan Dr Ahmad ya cigaba da bada labari har yau da suke tare .
Malam yayi ajiyar zuciya yace "lallai Allah mai girma wato Abdallah Allah bainifi zakayi ilimi har ka zama wani abuba sai da basirarka ta gushi lallai Allah mai girma ne , Alhaji babu abunda zamu ce maka sai dai mu bika da godiya gami da fatan alkhairi Allah yasaka maka da mafificin alkhairi , Allah ya jik'an Abdallah"
Nan dai Malam yayita kwararo addu'oi suna amsawa da Amin,
Daganan Dr Ahmad ya buk'aci yasan wane ne Abdallah , tiryan tiryan Malam ya runk'a bashi labarin tundaga haihuwar Abdallah har zuwa ranar da suka rabu dashi da sunan zuwa kano saro kaya , maikaratu idan ya had'a da labarin Dr zai bashi cikkaken taruhin Abdallah,
Ko da Malam ya gama bada labari gaba d'ayan su kowa da hawaye a idonshi musamman ma Saifullah da baitab'a tsamanin Abdallah zaiyi irin wannan rayuwar ba tsantsar tausayin abokinshi ne ya kamashi matuk'a .
Shikam Abdallah kuka yake kamar yaro dan sai yau duk abubuwan da yake gani suka fayyace mishi gaba d'aya ya rasa bakin magana sai hawaye dayake ta faman yi .
Ummi kuwa abad'aya farinciki ne ya mamaye mata zuciyarta Rana ji kamar taje ta rungume mijinta dan murna da jin dad'i .
Duk dauriyar da Mama taso yi amma hakan ya gagara sai hawaye ya sub'uce mata .
Umar , Saifullah tare da Aminullah su kaita rarrashin Abdallah
*gareku readers shin me kuke tunanin dai Kasan ce bayan nan ? Shin Dr zai bar Abdallah hakanan duk da cewar ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar shi ? Shin ya alak'arshi da Ummi zata kasance , maiye makomar soyayyar Saifullah ga Ummi? Wannan da ma sauran wasu tambayoyi suna cikin page na gaba*
Taku ce Maman Muhammad💓
@08165728746
[1/24, 4:46 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
*Wannan page d'in na sadaukar da shi ga dukkanin masoya labarin bawan Allah , tare da duk mai suna Zainab*💓
*Fatan alkhairi*â¤
*Edited by Mum Mussadiq*ðŸ˜Â
3⃣9⃣
Bayan natsuwa gami da gamsuwa ta ratsa zukatan su sannan Malam ya maida hankalinshi kan Abdallah yace " to Abdallah yanzun ka gane ko kai waye ko ?"
Sai da ya ajiye wata nan nauyar ajiyar zuciya sannan yace "na gane Malam"
Murmushi Malam yayi sannan yace " to wace ce waccen?" Ya nuna Mama
Kallonta yayi tana ta sharar k'walla yaja gwuiwoyin shi ya tafi kusa da ita tare da rik'e hannuwan ta yana fad'in " Ki yafe min Mamana na saki kuka insha Allah ba zaki k'ara kuka ba daga yau"
Dafa kanshi tayi tana Sosa gashin kanshi da ya kwanta yayi luf tamkar D'an India tama kasa magana tsabar farinciki ,
Dr Ahmad yayi gyaran murya yace " Allah ne k'addara zumunci tsakanin mu shiya sa bai bani ikon Neman danginka ba tunda farko kuma zumuncin mu ba zai tsaya anan ba "
Rarrafawa ya sake yi yakoma gaban Dr Ahmad yana mai share k'walla yace " thank you soo much Dad bansan da bakin da zan godemaka ba hak'ika kai wani haske ne acikin rayuwata, ka bani ilimin da ina rayuwar zahiri banyishi ba sai gashi na samu alokacin da iyayena da dangi na suka cire tsammani da rayuwata, nagode Allah ya saka maka da mafificin alkhairi Allah ya jik'an d'an uwana Abdallah yayi mishi Rahama"
Duka suka amsa da "Amin"
Kusa da Umar ya koma tare da rik'e hannun shi yace "ina cikin kewar d'an uwana wani lokacin nakanji zuciyata tayi min baki Ashe rashin abokin arzik'i ine irin ka"
Murmushi kawai Umar yayi
Dai dai kusa da Aminullah ya koma ya saiti kunnanshi yace " thanks for taking care of my wife I really appreciate you are indeed a real hero"
Aminullah yace " you deserve it"
Banza yayi da Saifullah kamar bai ganshi ba , Ashe shikuma abin ya bashi haushi sai ya mik'e afusace zai bar gurin , cikin sauri Abdallah ya rik'o hannunshi " where do you think you're going? ka kwantar da hankalinka ba sai na ambace ka ba you're always and ever in my heart"
Nan duk suka kwashe da dariya haka sukayita hira har lokacin azahar yayi ,
Awaje haka mutane keta tururuwar zuwa ganin D'an gayu Abdallah wasu ma sai sun tab'a shi sunji .
Mama kuwa haka mak'ota suka ta zuwa mata barka da taya murnar dawowar tilon d'anta cikin lafiya da aminci
Bayan tafiyar su massalaci sai ga yara daga gidan su ummi d'aya Leda ce ahanunshi bak'a d'ayan kuma d'irkeken zakara ne anyanka shi an fige sukace gashi inji Malam , nan da nan suka fara aikin su ,
K'arfe 2:30 suka dawo massalaci , suko su Ummi har sun gama dafa jalof d'in shinkafa da wake ga naman k'aza k'amshi sai tashi yake , su jera kan tabarma .
Bayan sun ci abinci sun k'oshi Dr Ahmad yace musu dama yau yake San komawa kano , Abdallah yaso ya bishi amma k'emadagas Dr yak'i yace ya zauna sai ya huta agida sunaji suna gani yayi musu sallama yatafi bayan ya yima Mama da Malam alkhair
Nan fa suka zauna shida abokanshi suna ta hira Mama na gefe yana kallon D'an nata zuciyarta k'all.
Ummi kuwa duk haushi ne da takaici ya cikata wato yasan da zaman kowa amma banda ita? lallai ma meyake nufi ? badai jiran banza tayi ba?
Haka taita jero tambayoyi har Hafsa tazo ta sameta Cikin tsokana ta fara magana "Amarya angon naki ya dawo madadin na ganki cikin fara'a amma naga sai cin magani kike "
Wani kallon shatara shatakwas ta aika mata dashi , tsabar takaici ma ta rasa me zata ce.
Abdallah , Saifullah , Aminullah, tare da Umar suna tare har k'arfe Tara sannan Aminullah yayi hamma gami da salati yace "jama'a Bakujin bacci ne?"
"Subhanallah" cewar Saifullah yayin da ya kalli agogon hannun shi
Mik'e wa sukayi dukan su Mama na d'aki ta jiyosu ta lek'o cikin barkwanci tace " Amintacce inace pillows kawai zan mik'o muku".
Dariya kawai sukayi sai da suka rakasu har bakin mota sannan suka Shiga suka tada ita suka tafi , yarage daga Abdallah sai Umar .
Abdallah yace" kaima badai guduwar zakayi ba ko?"
Kallon shi yayi da idanuwanshi da sukayi fici-fici saboda tsabar bacci yace " jiyafa saboda tsabar k'osawa da nayi inganka Sam nakasa yin bacci"
Dariyar mugunta Abdallah yayi sannan yace " ayyah abokina "
Umar tsaki yaja ya k'ara gaba yana cewa" ajedai a rungumi pillow" gaba ya abinshi
Shikam dariya kawai yake yi ahaka ya Shiga gida .
Ummi kuwa tunda magrib tayi ta fara kwasan kayan da zata buk'ata adare ta maidasu d'akin Hafsa dan chan take so taje ta kwana .
Dai dai k'ofar d'aki taci karo dashi shikuma zai Shigo cikin hanzari ta fad'a d'akin Ummi kamar an wurgo ta , shikam abin ma dariya ya bashi d'akin ya nufa direct , yana ta k'are mai kallo komai nanan yadda yake da ba tarkace jakar kayanshi da Aminullah ya kawo mai ya tuna dashi fita yayi ya nufi d'akin Mama wadda har ta fara bacci a hankali ya d'auki jakar tare da sakayo mata k'ofa Kasan cewar yanayin sanyi ne , komawa yayi d'akin ya rage kayan jikinshi , sannan ya fito ya tunjumi ruwa arijiya ya nufi bayi ,
*kuyi hak'uri da wannan readers ina fama da ciwon kai*🤦â€Â♀ðŸ™Â
[1/26, 4:53 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ÊÂųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ É– ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.