Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt
Chapter 9 of 27
*PAGE 9*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
_Ga masu buƙatar sayan littafin Nakasa ba kasawa bace, turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276. Ko kuma ka/kiyi min transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ka/ki turo screenshort na shaidar ka/kin biya_
~Wannan shafi nakune mutanen Group É—in Nakasa ba kasawa bace fans two ina al'fahari daku~
Free page
Tsurawa fuskokinsu ido cikin hikima yake nazartan zantukan da sukeyi,
wanda ya rasa madosar zancen,
mik'ewa yayi a hankali ya fara nad'e gammon da yake sawa a kanshi kafin ya aza kwalin omon,
yana mai ci gaba da nazartan kalaman wanda aka kira da Alhaji Sani yana cewa.
"Nan da wata biyu zasu rufe sararwan,
dan haka muyi k'ok'ari mu samu mu sari koda kad'an-kad'an ne,
Company ya talla ta mana ne dan sanin mune manyan costumes d'insu na nan jihar Gombe,
sun kuma bani tabbacin tabbas nanda wata hud'u Maggi zaiyi tsada sosai kusan ninka kud'inshi zaiyi,
domin ya bani misalai da dama,
sun kuma ce wannan damace da aka bawa kuduncin Nigeria, to shiyasa suma musulmanmu suka nemi da a bawa arewacin Nigeria samun wannan garab'asar dan sanin arzik'in musulmi yanada fa'idoji da dama."
d'aya daga cikin sunne ya kuma cewa.
"Ni kam in sha Allah zan k'ok'arta in samu koda kad'an ne."
gyara zama Alhaji Kabiru yayi tare da zaro kud'i yana mik'awa Saifuddeen yayinda hankalinshi ke kan abo kan nashi,
cikin nitsuwarsa yace.
"To zanyi k'ok'ari inga ko zan samu wasu 'yan kud'ad'e na da nike bin bashi sai in sa hannu a ciki."
cikin farin ciki sukace.
"Alhamdulillahi to Allah yasa ka samesu."
Amin Amin yace tare da kallon Saifuddeen da ya juya ya fita zuciyarshi cike da sak'e-sak'e haka kawai yake son yaji tushen zancen.
Su kuwa bayan sun gama tattauna yadda abin zai wakana.
Nan suka sallami Alhaji Kabiru suka tafi.
Saifuddeen kuwa yana fita yaci gaba da zageyenshi na tallan omo da kayan sanyin nashi,
bai fito kasuwarba har k'arfe shida na yamma dan tunda azumi ya wuce suka dawo kamar da sai bayan sallan isha suke komawa.
Yana fitowa yayi al'wala yayi sallan magrib yana fitowa ya samu Salisu na jiranshi,
daga nan bakin Al'kasim suka tsaya nan suka d'anci abinda ya sauwak'a sannan suka wuce Dukku.
Bayan kwana uku da zuwan su Alhaji Sani wurin Alhaji kabiru suka kuma zuwa,
kan su jaddada da mishi batun kadafa ya d'auki abun a shirme ya dai ce musu yana nan yana tabin wad'anda yake bin kud'in.
Iya bukku kuwa ,tun randa suka koma ko mai sunan Saifuddeen taji an kira sai gabanta ya faÉ—i.
A cewarta ba ita ba dukku har gaban abadan, dannan wannan kurman matashin daya zubda mata haƙora biyu a karonsu na forko. Tofa tabbas in antayi artabu dashi a karo na biyu kanta zai sare ya bata a tafin hannunta, Goggo Ummi kuwa da Bappan ta sunji daɗin hakan a ransu, kuma sunada niyar sake ziyartarsu.
Yau tunda Saifuddeen ya gama raba ledanshi kana ya yawata da tallanshi har la'asar bayan anyi salla ne ya nufi gidansu Ishaq dan sunyi dashi zaije su Ahmad da Saminu da Mudassir ma duk sunyi dasu zasuje dan sun kwana biyu basu had'uba,
Hud'u dai-dai duk suna had'e a d'akin Ishaq yayinda gari yayi duhu sabida tasowan hadari,
Mama kuwa tuni tai ta musu hidima dan dama sun ce mata danbun zogale sukeso,
nan suka zube suna hira sunaci,
Ahmad ne ya kalli Saifuddeen da yayi shiru alamun nazari had'iye abincin bakinshi yayi sannan ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Saifuddeen kaci dambun mana."
Kai ya jujjuya mishi alamun bazai cima,
cikin kula yace mishi.
"Meyasa bazaka ciba?."
Mudassir ne ya d'auki ledan pure water ya b'ula kana yashanye fiye da rabi sannan ya kalli Ahmad tare da cewa.
"Ka manna Saifuddeen da zab'en abinci ai baicin dambu."
jin haka yasa Ishaq mik'ewa tare da cewa.
"Yes haka nefa kaga ni nama mance bari inje in gayawa Mama tayi mishi d'anwake dan na lura yana son abincin mata."
dariya sukayi baki d'aya sannan ya fita,
Saminu kuwa gyatsa ya d'anyi tare da cewa.
"Au ashe dama d'an wake cimar matane?."
kai Saifuddeen ya jujjuya mishi alamun a a kam.
fitan Ishaq ba jimawa sai gashi ya dawo nan sukaci gaba da hira.
Bayan kamar awa d'aya da rabi sai ga Imran ya shigo da tire,
kai tsaye gaban Saifuddeen ya ajiye,
sannan ya juya ya fita,
shi kuwa Saifuddeen tiren ya jawo wanda aka cika d'an madaidaicin pilet da d"anwake sai dafaffan kwai guda uku a sama sai mai da magi da yaji,
nan ya fara ci sosai yaji dad'in d'anwaken,
Mudassir ne ya kalleshi tare da cewa.
"Oga ba tayine?."
hararanshi ya d'anyi tare da nuna mishi kulan dambun cikin mishi alamun kunci nabanku.
Ahmad kuma tab'e baki yayi tare da cewa.
"Ahab barshi da d'anwake ko rabi nai bazai ciba zaice ya k'oshi, sai dai ka ganshi yana ture pilet d'in."
ana cikin haka Allah ya sako iska mai sanyi wanda yake nuni da hadarin ya watse lokaci d'aya gari ya washe.
Shi kuwa Saifuddeen baici rabinba ya ture pilet d'in kana ya mik'e ya shiga bathroom,
nan sukayi ta mishi tsiya wai yana nan kamar kifi,
wonka yayi yana fitowa ya bud'e durowan Ishaq ya canza kaya sannan ya kallesu tare da musu alamun shi zai tafi,
sai ya kuma kamo hannun ishaq tare da mishi alamun ya tafi,
nan suka mik'e duk suka fita daga nan duk suka salami juna.
K'arfe 11:15 pm Saifuddeen ya mik'e tsaye tare da ninke sallayan da yayi sallan shafa'i da wutiri, a kanshi
bakin katifarshi ya zauna tare da yin addu'a ya shafa a jikinshi sannan ya kwanta ta b'arin dama.
Can misalin k'arfe biyu dai-dai ya farka bakinshi d'auke da addu'a,
a hankali ya bud'e idanunshi yana mai tuno mafarkin da yayi,
salati ya kumayi ya sanarwa mahaliccinshi,
jingina yayi da jikin pillow sai ya kuma lumshe idanunshi tare da son nazartan mafarkin nashi,
sai ya kumayi saurin bud'e idanun nashi dan ganin abin ya dawo mishi tamkar yana ganinshi a majigi,
a hankali ya mik'e ya fito tsakar gidan nasu inda ya samu ashe anyi musu ruwan sama kamar da bakin gwarya,
cikin nitsuwa ya wuce bandaki fitsarin da ya matseshi yayi sannan ya fito bakin barandan k'ofan d'akinshi ya tsuguna yayi al'wala sannan ya mik'e ya shiga d'akin kana yayi ta nafilfilinshi.
Washe garin da rana irin rana tayi fed'e-fed'e d'innan lokacin gari ya d'anyi zafi sai inuwan gajimare kad'an-kad'an,
sosai ya saida kayan sanyin koda ya gama kafa na uku, sai ya wuce shagon su Jabeer nan sukayi ta hira har aka kira salla bayan sunyi salla kuma sai ya wuce shagon Alhaji Kabiru yana isa ya samu yaran shagon duk sunata hidiman jera kayayyakinsu bisa dukkan alamu sarin da sukayi ne ya iso,
shi kuwa Alhaji Kabiru yana cikin shagon bisa alamu lissafi yakeyi,
ganin haka sai Saifuddeen ya tsallaka ya shiga ciki can kusa da shi ya zauna cikin body language ya gaida Alhaji Kabiru da tuni ya gama lissafin ya had'a takardun wuri d'aya,
cikin mutuntaka da dattaku ya amsa gaisuwar Saifuddeen,
sai ya kuma kalleshi ganin yana mishi alamun tambyar ina woyarshi,
murmushi yayi tare da cewa.
"Wayata gata a aljihuna."
kai ya jinjina mishi kana ya mishi alamun ya fitar da ita zasuyi mgna,
gane hakan ya sashi zaro woyar,
daga nan ya suka fara mgna ta inbox nasu suna musanyan text messages,
sosai Alhaji Kabiru ya nitsu yana kallon text d'in da Saifuddeen ya tura mishi inda yake cewa.
"Assalamu alaikum, Alhaji ya gida ya kasuwa,
Allah ya taimaka."
sai ya rubuta mishi amsa da.
"Wa alaikassalam lfy lau Saifuddeen, Amin Amin. Naga kamar muhimmiyar mgna kakeson muyi, kada ka damu ka d'aukeni kamar mahaifinka ni ina ina jinka tamkar Isma'il d'ina."
Sosai Saifuddeen yaji dad'i mgnar hakan ya sashi murmusawa tare da rubuta mishi.
"Ngd matuk'a Alhaji." sai ya kuma yi shiru bai kuma rubuta komaiba ya rasa ta ina zai faro zancen gane haka yasa Alhaji Kabiru dafa kafad'unshi cikin bashi k'arfin guiwa yace.
"Ina jinka."
shi kuwa rusunar da kai yayi tare da rubuta mishi.
"Kayi hak'uri Alhaji ka gafarceni ranan asabar d'in da ya gabata, ka kirani na kawo maka ruwan sanyi, inda nazo na sameka da bak'i to nayi laifin fahimtar maganganunku, sai dai kuma naji ina sha'awar sanin kasuwancin da suke tallata maka,
in akwai damar da nima zan iya sa hannuna a ciki nima zanyi."
yana tura text d'in sai ya sunkuyar da kanshi,
shi kuwa Alhaji Kabiru murmushi yayi bayan ya gama karantawa cikin kekyawan fahimta ya dafa kafad'un Saifuddeen wanda ya sashi d'ago kai ya zuba mishi ido alamun jin na bakinshi.
Gyara zama yayi tare da zuba mishi idanu cikin sanyin sauti alamun yana son su sirranta zancen yace.
"Me zai hana zaka iya mana, ai duk abinda mai ji zai iya na kasuwanci in sha Allah zaka iya,
sai dai kuma fa wannan al'amarin da kamar wuya."
da sauri Saifuddeen ya gyara zama tare da fuskantarshi yana mai kallon motsin bakinshi ta yadda zai fahimceshi da kyau shi kuwa Alhaji Kabiru cikin tsarkakan zuciya ya fara mishi bayanin kasuwancin.
"Company Maggi ne suka kawo mana tallan Maggi a sirrance a matsayinmu na manyan dilolin maggi,
sun tallatama mana ne dan suna mana sha'awar ci gaba,
sun bamu sirrin company cewa nanda wata biyar magi zaiyi tsadan da bai tab'a yiba,
sun k'ara da ce mana mu fito da kud'ad'enmu mu sari maggin mu ajiye sun sanar damu cikin wata biyar zuwa bakwai company zai k'ara tsadan magi sun bamu tabbacin in sha Allah babu batun fad'uwa sai dai cin riba,
in dai bamuci riba ba toko bazamuyi asaraba."
sai ya kuma d'an tsagaita tare da kallon kekyawan fuskar Saifuddeen kana cikin tausayawa yace.
"Tabbas nasan akwai riba dan yar daddunmu ne suka sanar mana dan son ci gaban junanmu,
to matsalar uku daga cikinmu duk last week mukayi sari bamu da kud'i a k'asa asalima kaga sai yau kayan ya isomu,
sannan masu zuwa sari su zo su sara wanda yawanci bayan wata d'aya suke dawo da kud'in.
To da fari company wata biyu suka bada k'a'idar rufe sarin dan kamar bonanza ne zasuyi mana to sai kuma suka maida k'a'idar wata d'aya.
to shi kanshi uban gidanmu Alhaji Sani wata uku da suka gabata ne ya gama ginin sabon gidanshi inda ya k'aura ya koma yanzu,
to bashi da kud'i sosai a k'asa da zai ranta mana."
ganin yayi shirune yasa Saifuddeen gyara zamanshi tare rubuta mishi.
"To magin kuma kamar na k'asa da nawa zasu bada sarin?."
Numfashi Alhaji Kabiru ya furzar tare da cewa.
"To ai anan gizo ke sak'a domin sun san in sukace kad'an-kad'anne da yawa zasu iya sara,
so sai suka d'an saka hikimar da suma zasu samu wani abu,
sun bada tabbacin cewa mafi k'arancin sarin da zasu bada shine na 2 million,
tofa shisa duk jikinmu yayi sanyi da abun."
cikin d'imuwa Saifuddeen ya maimaita 2 million to shi tunda aka haifeshi yazo duniya baima tab'a ganin dubu dari biyar cikakku bama,
kai ya rink'a jujjuyawa da a zatonshi ko irin d'an sarin 100k ne zuwa 200k nan zai iya zaton zai samesu in ya fasa asusunshi,
tab'ashi da Alhaji Kabiru yayine ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya tafi kai ya rink'a jujjuyawa jin tambayar da Alhaji Kabirun ya masa cewa.
"Kanada kud'in sari ne?."
ganin yanata jujjuya mishi kaine yace.
"Shiyasa nace abin da wuya ni du'du du yanzu dubu d'ari biyar nake dashi,
in samu wanda zamu had'a hannu muyi sarinma abin ya gagara ya rigada yanzu cinikaiya ta d'anyi k'asa, amman kaje kayi shawara in kanada yadda zaka samu 500k d'in kamar nawa sai mu had'a in sha Allah zan samu su Alhaji Sani sai mu had'a da wasu in an samu."
Cikin rauni da sanyi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai tare rubuta mishi.
"Kud'in sunfi k'arfina bani da hanyarsu ko dalilinsu.
Ngd matuk'a da bani kulawa da shawara naji dad'in yadda kamin kekyawar fahimta."
Cikin kula ya kalleshi ganin yana shirin aza kwalin omonshi a kai alamun zai tafi murya a tausashe yace.
"Ba komai Saifuddeen wlh ni ina jinka tamkar d'ana na cikina,
na kuma yarda da amincinka,
muyi ta Addu'a Allah ya bamu sa'a."
A saman labb'anshi ya amsa da Amin Amin kana ya juya ya fita shagon.
Daga nan yaci gaba da tallanci yanayi cikin nasara,
randa yayi kwana biyu da zuwa wurin Alhaji Kabiru, da dare ya sake yin wani mafarki ma kamacin wanda yayi ranan,
sosai abin ya d'aure mishi kai al'wala yayi sannan yayi ta karatun Qur'an washe gari, ana fitowa sallan asuba yaga Sabir k'anin Saminu yazo gaban Bappa Ali inda ya shaida mishi wai babanshine ya aikeshi kan yazo ya gaya mishi yana son ganinshi anjima shida Saifuddeen.
jin haka bai wani damu Bappa Ali ba dan akwai alak'ar zumunci a tsaka ninsu in abi ya shafi na addini to ana nemanshi.
Sai dai da yaji yace shida Saifuddeen shiyasa ya hana Saifuddeen tafiya cikin gombe yace Salisu yaje kawai shi Saifuddeen yau bazai jeba sai gobe in Allah ya kaimu da haka Salisu ya tafi.
K'arfe tare dai-dai na safe Saifudddeen da Bappa Ali suka isa fadan masarautan Dukku.
Bayan anyi musu iso suka isa har cikin masauk'in bak'i.
Cikin mutuntaka suka gaisa da mai martaba da Wazirinshi da sauran wad'anda ke wurin,
daga bisani Sarkin ya gyara zama tareda murza rawanin kanshi cikin salon mgnar sarakuna yace.
Malam Ali kunga na aika a kira minku da sanyin safi ko?."
kai Bappa Alin ya gyad'a tare da cewa.
"Eh shine ma dalilin zuwanmu domin amsa kiranka."
kai ya jinjina cikin salon adalcin sarauta yaci gaba da cewa.
"To batun dai filin nan naku na Dugge ne da filin yayanka na nan bakin kasuwa shine dai dililin kiran naku yau ma,
in baka mantaba kwanaki nayi maka mgnar cewar akwai masu son filin walau saya walau haya shi filinku na Dugge d'in sunce su ko haya ne a basu, to da nayima mgna kace min baka da hurumin saida filin domin filin nakune kai da d'an uwanka ne Bello mahaifinsu Saifuddeen ka shaida min cewa yanzu filin na magada ne yaran shi kenan da kai.
To kuma company layin waya na mtn suna tayi mana zirya a gari sabida sun tabbatar mana da cewa, sun samu igiyoyin services a cikin filin naku koda na sanar musu bani da hurumin saida musu filin sabida na magadane to sun kuma dawowa kan cewa ko hayane a basu filin duk shekara zasu rink'a biya,
nanma na kuma jaddada musu bani da hurimin filin, to sunci gaba da duddubawa cikin garin dukku amman Allah baisa sun samu wani wurinba da zasu samu su kafa na'u'rarsu ta services,
to shiyasa suka kuma dawowa gareni da neman al'farman a basu hayan filin zasu rink'a biyan kud'i mai tsoko cikin ko wanne shekara,
to ganin sun dameni nace bari in kuma kiranka kaida Saifuddeen d'in in sanar muku sannan kuyi shawara da juna."
ya k'arishe mgnar cikin son jin ta bakinsu,
shi kuwa Saifuddeen numfashi ya d'an fesar a hankali kana ya zubawa bappa Ali idanu cikin alamun nuna mishi duk hukuncin da ya yanke yayi dai-dai.
gane hakan yasa bappa Ali yin mgna cikin mutuntaka yace.
"To ba matsala in sha Allah zamuje gida muyi shawara da mahaifiyarsu Saifuddeen d'in da kuma yayarshi Rahma da k'anneneshi dan jin ta bakinsu tunda suma sunada hak'k'i a ciki."
cikin mutuntaka yace.
"To ba laifi, sai naji shawarar da kuka yanke,
amman nace musu su dawo jibi suji yadda mukayi daku."
Sai ya kuma yi gyaran murya tare da cewa.
"Yauwa to sai batun filinku na nan bakin kasuwa,
wanda kace min filin Bello ne mahaifinsu Saifuddeen ka shaida min cewa baka da ko sulai d'aya a kud'in sayan filin,
to kuma kasan tun last year hukumar bankin nan na GT bank sukayi ta zirya kan suna son sayan filin dan suna son su bud'a cibiyar bankin nasu a nan dukku,
to rashin amincewarka yasa suka hak'ura duk da sunyi ta nacin filin,
a cewarsu wai rigima kuke musu,
to kaga bayan nan kuma A. A Rano ya buk'aci sayan filin dan bud'e gidan mai nanma kak'i bada fuska,
dole ya hak'ura yaje ya nema a mashigan hari."
sai ya kuma d'an tsagaita tare da kallon yadda suke zaune cikin kamala da cikar haiba,
kanshi ya juya ga wazirinshi da Garkuwanshi kana sai sauran tsirarun mutane,
cikin tattausan lafazi yaci gaba da cewa.
"To fili dai na yaran d'an uwanka ne kamar yadda kasha jaddada min na kuma fahimceka baka son shiga hakk'insu ne ko ince kana gudun kar ka zama sanadin rabuwansu da kadarar mahaifinsu,
to nima bana son takuraku ko in saku yin abunda bakuyi niyaba,
to amman ba yadda zamuyi domin wannan filin ya kasance fili mafi girma da daraja gashi a bakin hanya gashi a bakin kasuwa gashi babban filine to wannan dalili yasa idanun manyan masu hannu da shuni ke kan filin dan duk abinda akeso za'a iya yi a wurin,
hakan yasa tun makon daya gabata hukumar ACCESS BANK suketa yi mana zirya,
na gaya musu duk yadda akayi a baya to sai sukayi ta k'ara farashin yadda zasu sayeshi sama da yadda sauran suka sayeshi a baya, har ta kai da sun ninka kud'in,
to shiyasa nace bari dai in sanar muku in kun amince la basa in kuma kunk'i amincewa bani da abin cewa,
sai dai kuma dole ku dage kuyi koda shaguna ne a wurin domin kauda idanun mutane."
jin yayi shiru alamun ya dasa aya ne yasa Waziri cewa.
"Wannan gsky ne babu dole cikin cinikin, amman kuyi k'ok'arin gine wurin in har bazaku saidaba."
cikin kamala Bappa Ali yace.
"To ba matsala ai Alhamdulillahi tunda zuwa yanzu Saifudddeen ya girma ya kuma mallaki hankalin kanshi,
ya kuma ji komai dan haka zamuje gida zamu tattauna duk abinda ya dace,
kana in mun yanke hukunci zamu zo mu sanar muku,
amman yanzu sai munje mun sanar da mahaifiyashi da k'annenshi dama yayarshi."
gyaran murya Garkuwa yayi tare da cewa.
"To ba matsala muna jiranku sai munji shawarar da kuka tsaidan."
Shi kuwa Saifuddeen wani kekyawan murmushi yayi wanda ya k'ara baiyana asalin kyanshi kai ya jinjina musu alamun sai kun jimun.
To da haka dai sukayi sallama suka tafi gida.
Koda suka koma gida kai tsaye sashin Ummi suka nufa inda suka shige har cikin d'aki kana Saifuddeen ya kira Rahma,
nan Bappa Ali ya musu bayanin duk yadda sukayi da sarki,
to ita Ummi cewa tayi ba matsala a kamfanin Mtn d'in hayan filin ko ba komai ai zasu rink'a samu ribar filin,
shima Bappa Ali ya amince da hakan hakama Saifuddeen da Rahma, to duk dai sun amince bayan sun gama mgnar wannan filin sai kuma Bappa Ali ya kalli Ummi cikin mutuntaka da tausayinta a matsayinta na yar goggonshi kuma matar yayanshi murya a tausashe yace.
"To sai kuma batun filin su Saifuddeen d'in na bakin kasuwa ya kuka gani,
kun ga dai tsawon shekara ake bibiyar filin wanne hukuncin kuka yanke?."
shiru Ummi tayi ta nisa cikin nazari tana tuno mafarkin da tayi kwana biyu da suka gabata inda taga Abbansu Saifuddeen tamkar a zahiri yana ce mata.
"Kada ki hanashi saida filin, a saida ki kuma bawa Saifuddeen kud'in kada ki damu d'anki zai kula da komai."
to a ranar wuni tayi tana nazarin wanne filin ne zata bari su saida sai yau ta samu amsar dan haka cikin nitsuwa tace.
"Ni dai a karan kaina na amince a saida filin,
dan banga amfanin zaman nashiba tunda ba komai muka gina a wurinba."
sai ta kuma kalli Saifuddeen cikin kula da yanayinshi tace.
"Babana ko kana da kud'in da zaka gina mana shaguna ne a wurin?."
da sauri ya girgiza mata kai dan shi Allah-Allah yake su amince a saida filin,
murmushi tayi tare da cewa.
"To ya ka gani ka amince a saida ne?."
murmushi yayi tare da lumshe mata ido kana ya bud'esu a hankali sannan ya zaro woyarshi tare da rubuta mata.
"A tambayi Adda Rahma dasu Raihana in sun amince dai to ni na amince na kuma amincewa Hayatuddeen tunda shi har yanzu k'ara mine."
yana gamawa ya mik'awa Ummi bayan ta karanta ta mik'awa bappa Ali shima yana karan tawa ya mik'awa Rahma, koda ta karanta murmushi tayi tare da zubawa k'anin nata idanu cikin sanyin muryarta tace.
"Ni na amince Raihana da Raliyya kuwa amincewar Ummi itace tasu, tunda suma har yanzu yarane gwara Raihana za'ace ta kai matakin balaga."
murmushi yayi tare da mata alamun ta kira Raihana.
Koda ta kira wota da akayi mata bayani sai ida nunta suka cika da hawaye cikin rawan murya tace.
"Bappa Ali ka cewa Hamma Saifuddeen yayi duk abinda ya dace a kan duk abun da mahaifinmu ya bar mana ba sai an nemi shawararmu ba."
itama Rahma sai cewa tayi.
"Damu da kadararmu ai duk kaine Garkuwarmu."
to nanfa suka tsaida mgna akan za'a saida filin.
Cikin ikon Allah a kwana biyar aka gama duk mgnar filin da za'a kafa services d'in da kuma filin da za'a gine Access bank.
Jin kud'in hayan filin services d'inma ya matuk'ar bawa Ummi Mamaki inda sukace duk shekara zasu biya one million,
sannan filin bakin kasuwar kashi uku suka rabashi in duka ce kashi biyu zasu saida d'aya kuma zasu ajiye kasan cewar filin k'atone eka-eka ne bila adadin,
to bankin sun amince dan kashi biyun zai ishesu suyi gininsu mu samman in sunce bene zasuyi har filin zai zarta zatonsu, million biyu da dubu d'ari uku da hamsin aka karkare cinikin a cikin fadar masarautan dukku, ranar ma Saifuddeen bai je kasuwaba.
Sai washe gari tun da sanyin safiya suka tafi shida Salisunshi,
koda yaje sauri-sauri ya raba ledodinshi kana ya wuce shagon Alhaji Kabiru inda yayi kicibis dashi yana shirin fita zaije gidan Alhaji Sani,
koda Saifuddeen yace mishi zai sari magin ya samu kud'in da ake buk'ata sosai Alhaji Kabiru yayi mmki,
dan haka sai ya d'aukeshi suka tafi gidan Alhaji Sani,
shima kanshi Alhaji Sanin yayi mmki sai sukaji tsoron sharrin zamani dan haka sukace dole sai yazo da manyanshi an gaya musu ina ya samu kud'in,
bai damuba ya basu tabbacin zai kawo manyan nashi.
Koda suka dawo kasuwa ranan bai saida pure water ba, gidansu Ishaq ya wuce,
ya kuma yi sa'a ya sameshi a gida nan ya tad'a mishi komai nan take kuma Ishaqn ma ya bashi k'arfin guiwa ya k'ara da cewa.
"Alhamdulillahi dama jibi Ya Rabi'u zai shigo Gombe kaga zai zauna maka matsayin lawyernka mai kare dukiyarka da kadarorinka sannan yasa hannu a lamarin dan gudun kada su cutar da kai ko su damfareka zan kuma sanarwa Babanmu ma dan ya kasance da saninshi."
ruggumeshi Saifuddeen yayi tare rubuta mishi sak'on
godiya.
daga nan ya koma kasuwa ya d'an zazzagaya da ruwan.
Shi kuwa Ishaq Saifuddeen yana tafiya ya sanarwa babansu tare da neman shawararshi ya amince ya kuma basu k'arfin guiwa sannan ya kira barrister Rabi'u ya sanarmishi komai yace ba matsala sai ya shigo Gomben.
Shi kuwa Saifuddeen koda ya koma gida,
cikin nitsuwa yayiwa bappa Ali bayanin komai.
Cikin nisan nazari da zurfin tunani Ummi da Bappa Ali da Rahma suke karanta duk bayanin da ya musu,
tun randa ya fara kai kaya shagon Alhaji Kabiru da yadda yake sonshi da yadda ya samu su Alhaji Sani suna tattauna batun tallan sirri da company maggi ta kawo musu,
da yadda yaje ya sameshi da mgnar da yadda ya gaya mishi batun yawan kud'in sarin da ake buk'ata, ya kara musu da cewa ya gayawa Ishaq shi kuma zai gayawa Babansu, da Babban yayansu Barrister Rabi'u dan yasa mishi hannu a cikin lamarin ya tsaya mishi a matsayin lawyer inshi.
Ya kuma sanar musu cewar suma su Alhaji Kaburu sunce sai sunga iyayenshi sunji inda ya samu kud'in kafin su amince da batunshi.
Gyara zama Bappa Ali yayi tare da fuskarshi kana cikin sauk'e numfashi yace.
"To inaga dai mu barshi ya gwada mu gani, domin bahaushe yace matsoraci bashi zama gwani ko shi wanene,
mu bada yak'ini a kanshi tunda munada makama kuma ba da ka za'ayi abinba kamar yadda abokinshi ishaq ya bada shawara hakan za'ayi,
dan su kansu sun tsorita da batun yadda yace yanada kud'in shiyasa sukace sai sunga iyayenshi kinga alamun gsky kenan domin da 'yan damfarane ce mishi zasuyi kada ya gayawa kowa har uwa da uba in yana dasu kada ya gaya musu,
in kin amince ni dai na amince na kuma gamsu da kasuwancin."
Ya k'arishe mgnar yana kallon Ummi da Rahma jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
"Ba matsala Allah ya bashi sa'a ya sanya al'khairi da al'barka a cikin lamarin ni na amince."
sosai Saifuddeen yaji dad'in amincewarsu domin suna bada dukkan yardansu a kanshi tamkar bashida nakasar komai,
shi kuwa Bappa Ali cikin nitsuwa yaci gaba da cewa.
"Zan je in samu Malam Ashiru abokin ya Bello, in mishi bayanin komai sannan muje gomben mu samu Babansu Ishaq da shi barrister Rabi'un sannan muje wurinsu Alhaji Kabirun sai mu tattauna duk abinda ya dace."
cikin nitsuwa Rahma tace.
"Hakan yayi Allah ya shige mana gaba."
Amin Amin sukace baki d'aya sannan suka tashi daga taron nasu.
Washe gari tun da asuba bayan an fito masallaci Bappa Ali yasa Salisu ya kaishi gidan Malam Ashiru bayan sun gaisa ya mishi bayanin abinda ke tafe dashi kan batun Saifuddeen,
sosai suka tattauna a kai nan suka tsaida cewar gobe zasuje su samu su Alhaji Kabirun.
Salisu na dawowa suka d'auki hanyar gombe suna isa Saifuddeen ya rarraba ledanshi kana yaje shagonsu Alhaji Kabiru ya shaida mishi cewa gobe iyayenshi zasu zo cikin mutuntaka alhaji Kabirun yace to sai sun zo d'in.
Daga nan Saifuddeen ya wuce gidansu Ishaq yana shiga yayi kicibis dashi da a tsakar gidan,
a tare suka shiga parlour Babansu nan ya samu Ya Rabi'u ya iso, bayan sun gaisane suka tattauna lamarin nan ya sanar musu gobe ma su Bappa Ali zasu zo sundai ajiye zance sai goben.
Washe gari kuwa koda su Bappa Ali da Baba Ashiru suka taho da babban yayansu Samisu yariman Dukku kenan kai tsaye gidansu ishaq suka wuce.
sosai suka samu tarba ta mutuntaka,
suka gaggaisa sannan sukayiwa juna k'arin bayani,
daga bisani suka sa ishaq yayiwa Saifuddeen text cewa sun isofa a ina zasu had'u dasu Alhaji Kabirun.
Yana ganin text d'in ya wuce shagon Alhaji Kabiru d'in ya gaya mishi cewar sun isofa,
cikin kula ya mik'e tare da cewa.
"To muje can gidansu abokin naka sai muyi musu jagora zuwa can gidan Alhaji Sanin."
cikin jin dad'in haka Saifuddeen ya gyad'a mishi kai sannan ya juya yabi bayan Alhaji Kabirun,
motarshi suka shiga kai tsaye suka isa gidansu ishaq sosai Alhaji Kabiru yayi mamaki ganin manyan mutane dan barrister Rabi'u sanannene hakama mahaifinshi baraden Gombe, ga kuma Yariman dukku ga kuma Malam Ashiru da Bappa Ali wanda da ka gansu kaga kamala irin ta malaman addinin musulumci.
bayan sun gaggaisa ne kuma suka mimmk'e suka nufi gidan Alhaji Sani wanda tuni Alhaji Kabiru ya mishi bayanin zuwansu a waya.
G.R.A suka nufa inda nanne anguwar gidan Alhaji Sanin yake,
suna isa mai gadi ya bud'e musu gate ganin tsaleliyar motar ya Rabi'u a gaba wanda Saifuddeen da Ishaq ke ciki a baya Yariman Dukku kuma yana gaba kusa da Barrister Rabi'un,
sai kuma motar Alhaji Kabiru wacce Malam Ashiru da Babba Ali ke ciki Babansu Ishaq kuma na gaba kusa da Alhaji Kabirun,
suna shiga harabar gidan sukayi parking,
suna firfitowa wanni d'an matashi wanda zai kai sa'an su Hayatuddeen ya iso gabansu cikin nitsuwa ya gaidasu,
kana ya kalli Alhaji Kabiru tare da cewa.
"Abba ku shigo ciki inji Daddy na."
shafa kanshi yayi tare da cewa.
"To Sulaiman." sai ya kuma juyawa ya kalli su Babba Ali tare da cewa.
"Bisimillanku mu shiga ciki."
to sukace kana suka biyo bayan yaron da aka kira da Sulaiman ,wanda yake rik'e da hannun Alhaji Kabiru yana cewa.
"Abba ina Isma'il baka zo min da shiba."
dai-dai lokacin kuma suka shiga cikin tamfatsetsen parlour yayinda Alhaji Kabiru yayi sallama tare da cewa Sulaiman.
"Isma'il baya nan ai sun tafi Yola shida Maminshi."
sai kuma yayi murmushi ganin Alhaji Sani ya nufi gaban Babansu Ishaq cikin mamaki yace.
"A a yau inada manyan bak'i kenan kaida kanka Baraden Gombe ai da kayi aike ka kiranima zan amsa kiran."
Sai ya kuma kalli su Bappa Ali dake cikin shiga ta kamala cikin sakin fuska yace.
"Marhabikun ku iso ku iso."
cikin kamala suka zazzauna shi kuwa Alhaji Sani cewa Sulaiman yayi.
"Sulaiman maza je ka kawo musu abin sha."
da sauri yaron ya juya ya fita ba jimawa ya dawo da wani babban tire cike da ababen sha mai sanyi,
sai ya kuma juya da sauri ya fita,
yayinda tuni su kuma suna gaggaisawa,
cikin nitsuwa Sulaiman ya kuma shigowa tare da tire cike da fruits ya ajiye bisa stol dake tsakiyansu,
sannan ya fara ajiye musu gorunan ruwan dana juice sai cup d'ad'd'aya a gabansu.
yayinda tuni su kuma suna tattauna abinda ya kawosu,
sosai Alhaji Sani ya d'auki abin da mahimmanci dan ganin manyan mutane suna cikin lamarin,
nan take yayi musu k'arin bayamin sannan suka bashi kud'in da dama sun taho dasu nan shaidu suka sa hannu,
Barrister Rabi'u da Barrister Salman yayan Saminu kenan Yariman dukku suka rattaba hannu ga manyan shaidu.
A nan take kuma sukayi mgnar hayan shagon da in kayan sun iso zai ajiyeshi.
ba tare da b'ata lokaci ba Alhaji Kabiru ya shaida musu akwai wani shago can k'arshan layinsu amman a luggune,
murmushi Babba Ali yayi tare da cemishi.
"Ba matsala nawane kud'in hayan."
Alhaji Sani ne ya d'an gyara zama tare da cewa.
"Shagunanshi ne ai, in kunaso ku biya kud'in wata shida in kuma kunga ba matsala ku biya kud'in shekara d'aya yadda dai kasuwa ta kama."
Barrister Rabi'u ne ya kalli Bappa da Saifuddeen tare da cewa.
"In dai da hali ku biya kud'in shekara d'aya."
da wannan shawarar bappa Ali ya biya kud'in shekara d'aya,
sannan Saifuddeen yasa hannu a cikin dukkan takardun da ya kamata na company maggi daga nan suka gama komai sannan suka sallami juna a mutunce suka tafi.
Koda suka koma gida kuma Bappa Ali ya fito da sauran kud'insu na hayan filinsu da za'a kafa services ya nunawa Ummi dasu Saifuddeen dan cikinsune ya biya hayan shago,
nan kuma suka tsaida shawarar bappa Alin ya sari kayan abinci tunda dama sana'arsa ce aune-aune.
nan bappa Ali ya fara sari a duk kasuwannin da yake zuwa kamarsu.
Ngalda, bajoga, Nafad'a, Hashidu, dogon ruwa, kiri, Malam Sidi, Kurugu, kumo, Dad'in kowa D'ukul togo. Da dai sauransu.
kasan cewar lokacin Kaka'ace amfanin gona ya nuna so kayan abinci yana araha inda tuni masu kud'i keta sara suna boyewa da nufin sai yayi tsada su fitar to wannan dalilin yasa Bappa Ali fara sara da kekyawar niya dan taimakawa masu k'aramin k'arfi yayi aniyar zai canza salon wannan kasuwancin da ya sara ya ajiye in yayi tsada shi kuma ya fitar ya fara saidawa a farashi mai sauk'i.
to nanfa ya k'ara k'aimin bin kasuwannin k'auyuka yana sarar buhuhhunan su.
Masara, Dawa, Gero, Maiwa, Shinkafa, Rid'i, kalwa, Wake, Gyad'a, da dai sauran kayayyakin abinci,
cikin wata biyu duk ya gama sarin inda ya cika tsoffin d'akunan iyayensu duka biyu da buhunan kayan abincinshi.
Tuni Magginsu Saifuddeen kuma ya isa har an shirgesu a babban shagon da Saifuddeen d'in ya kama haya inda aka cikashi mak'il da katon d'in MAGGI mak'il kana aka ja shagon aka rufe, yayinnda shima burinshi irin na Bappanshi ne.
Ya kuma ci gaba da sana'o'insa da ya saba, yana kula da ahlinshi da ahlin Baba Bello,
yana kuma zura ribar shi a wani sabon asusunshi d'aya saya dan wancan asusun tuni ya cika a cewarsa sai ya cika asusu uku kafin ya bud'esu duka.
Bayan wata bakwai da saran Maggin kenan
Rayuwa taci gaba da gudana yau dad'i gobe akasin haka abu da dama ya faru.
Ana cikin haka rana tsaka Maggin da aka sani a hud'u goma sai gashi yayi gauron zabbi ya koma biyar ashirin kusan ninkin ba ninkin kenan,
yayinda yan kasuwa masu harkan magging da sun samu sun sara suketa farin ciki anata hidimar kasuwa anata hidima.
kusan tsawon mako uku kenan da farashin maggin yayi sama,
wanda yayi dai-dai da cikin tsakiyar damuna ne sama ruwa k'asa ruwa, kayan abinci yayi tsada,
tuni talaka ya fara shiga hau'ula'in rayuwa,
bappa Ali da Saifuddeen kuwa tuni sun fara shirye-shiryen bud'a kasuwancin nasu Yau jumma, kuma tun bayan sallan la'asar aketa zuga ruwa kamar da bakin gwarya,
dole cikin ruwan Salisu da Saifuddeen suka kamo hanyar dukku,
daga gombe har cikin Dukku ruwane yake dukansu tamkar zai jasu ya tafi dasu,
k'arfe shida dai-dai suka isa cikin dukkun sauri-sauri gudu-gudu Saifuddeen ya shiga cikin gida lokacin da Salisu ya sauk'eshi dan har lokacin ana d'an yayyafi irin na alamun ruwan ya d'auke sai yaf-yaf ruwan keyi.
Yana shiga kai tsaye d'akin Umminshi ya nufa dan wannan al'adarshi ce muddin ya dawo ko ruwa ko iska ko dare ko rana sai ya fara shiga inda take ya ganta ta ganshi kafin ya wuce d'akinshi,
yayinda ita kuwa Ummi duk nisan dare bata tab'a iya yin bacci har sai taga dawowanshi, duk ruwa kuma bata rumtsawa sai taga ya dawo.
Yana isa bakin k'ofarta yasa hannu ya bud'e labule,
murmushi yayi ganinta zaune ta zubawa k'ofar idanu yayinda Hayatuddeen ke konce yayi pillow da cinyarta Rahma kuwa na gefenta tana gugan kayan data wonke,
Raihana kuwa nayiwa Ummi kitso,
ajiyan zuciya Ummi tayi tare yin murmushi ganin gudan jininta,
cikin tausayawa Raihana tace.
"Sannu da hanya Hamma Saifuddeen."
kai ya jinjina mata alamun yauwa.
Rahma kuwa ajiye anyone d'in tayi tare da cewa.
"Saifuddeen jeka canza kaya kalli yadda ka jik'e jilik sanyi zai kamaka illah fa."
cikin body language yace da ita.
"To."
sai ya kuma yi musu alamun ina Raliya dasu Faruq."
gane abinda yake nufine yasa Ummi ce mishi.
"Suna wurin Aunty Nina."
kai ya jinjina dan yasan dama su Faruq suna son zuwa wurin Aunty Ninan wacce tuni ta haifi d'anta wanda akayiwa Abba mai suna shiyasa su Rahma ke kiranshi da Abban tuni yaron ya girma har yana rarrafe.
Juyawa yayi ya nufi d'akinshi daga bakin k'ofa ya mik'a hannunshi ya jawo towel inshi dake shanye a kan k'ofanshi, botiki ya d'auka ya cikashi da ruwa kana ya d'auki kondon soson wonkenshi,
ban d'akinshi ya juya ya nufa dan jin ruwan ya d'auke kit.
Wonka yayi fes sannan ya d'aura towel d'in ya fito,
buta ya d'auka yayi al'wala sannan ya shiga d'akinshi mai ya dauka kana ya zauna bakin katifarshi murze jikinshi yayi ciki da woje sannan ya mik'e tsaye ya zaro tattausan boxer inshi fari k'al ya fesheshi da turare sannan ya saka,
yana gama gyara zaman boxer d'in a k'ugunshi ya konce towel d'in ya d'anyi taku biyu zuwa uku sannan ya isa bakin k'ofar wore towel d'in yayi ya shanshi kan k'ofar,
sannan ya juya ya isa bakin 'yar durowar tashi ya zaro farin vest fara kal ya fesa mata turare yasa sannan ya kuma zaro bak'ar jallabiya ya zurata a jikinshi,
sai ya kuma feffesa turaren,
sannan ya matso gaban madubin shin hannu yasa ya gyara suman kanshi da yake konce lib sai shek'i yakeyi wayarshi ya zura a al'jihu sannan yasa takalmanshi dake bakin k'ofa ya fita.
A tsakar gida ya samu su Ummi dasu Raihana da Hayatuddeen suna al'wala,
kitchen ya lek'a ganin Rahma na kwasar abinci,
ganinshi a bakin k'ofa yasa tayi murmushi tare da cewa.
"Yauwa je kayi salla ana idarwa ka dawo yau miyarka nayi tunda naga hadari nasan zaka dawo da yunwa."
murmushi yayi tare da mata alamun tayi sauri ta gama lokacin salla yayi,
sai ya kuma kalli fuskarta ganin alamun saida tayi al'wala kafin tazo ta fara kwasan tuwon shiyasa ya juya ,
ya kamo hannun Hayatuddeen da Faruq da yanzu ya shigo suka nufi masallaci.
Koda aka idar da salla, basu dawo gidaba nan ya zauna da Hayayuddeen da Faruq saida akayi sallan isha sannan suka fito.
a bakin masallacin Saifuddeen ya kamo hannun Warisu sai ya kuma yafito Salisu tare da musu alamun su zo suci abinci,
kasan cewar yanzu su ukune rak suka rage a dukkun dan Ahmad, Samuni, Mudassir, duk suna cikin gombe,
Cikin yamutsa fuska Warisu yace.
"Tab aini bani cin abinci da dare dan wlh kun sani bani son k'iba,
gwara kai Saifuddeen jikinka ba irin nau bane."
Salisu ne ya d'an harareshi tare da cewa.
"Kuma in sha Allah wata rana sai kayi k'iba."
sai ya kuma juyo ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Ni kam a koshe nake muna dawowa na samu iya shatu tana kwasar tuwo tayi wannan hegiyar koriyar miyar nan tata kad'a kwarya yunwace ta sani cinta dole."
dariyar mugunta Warisu ya mishi tare da cewa.
"Hege ka dai biyewa wannan tsohuwar yaseen sai ta toshe maka kwanyarka da koriyar miyar nan ka zama huhulahu."
yana fad'in haka ya juya da sassarfa ya gudu ganin Salisu zai kai mishi duka,
shi kuwa Salisu hamma yayi tare da cewa.
"Kaga mai jajayen kunnuwa ni zanje inyi bacci saida safe."
daga nan sukayi saida safe, shi kuwa yasa Hayatuddeen da Faruq a gaba suka shiga cikin gida yayinda Bappa Ali ke binsu a baya.
Suna shiga tsakiyar gidan ana dawo da wutar nepa,
kai tsaye d'akin Ummi suka shiga suna shiga ya mik'awa Raihana woyarshi tare da mata alamun taje ta sa mishi caji a d'akinshi,
da sauri ta karb'i wayar kana taje ta jona wayar sannan ta dawo.
tana shiga kuma Rahma ta kalleta tare da cewa.
"Je kitchen ki kawo musu abincinsu."
to tace tare da juyawa ta nufi kitchen d'in,
Ummi kuwa gyara zamanta tayi tare gyara sallayan da take zaune a kai sannan tayiwa Saifuddeen d'in alamun yazo ya zauna,
kai ya gyad'a mata kana yaje ya zauna a gefen damanta Hayatuddeen kuma ya zauna gefen hagunta yayinda Faruq ya zauna gabanta,
Adda Rahma kuma kan gadon ta hau ta kwanta tare yin mik'a sannan ta bugi k'afad'an Raliya da tuni ta fara bacci yayinda Adam ke bisa ruwan cikinta,
a hankali ta bud'e ido,
sai ta kuma yunk'ura ta zauna jin Rahma na cemata.
"Ke tashi kije ki shiga kada kiyi bacci anan ki d'auki Adam ku tafi tare."
Kai ta gyad'a kana ta mik'e ruggume da Adam ta fita ta nufi d'akinsu, tana fita Raihana na shigo musu da abincin.
By
*NAKASA BA KASAWA BACE*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.