Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt
Chapter 5 of 27
*PAGE 5*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
_Wannan shafi gaba É—ayanshi tukuicine da saudaukarwa ga Umar ibrahim Wambai, Allau rabbi ya baka lafiya!_
Free pageðŸ¤ÂðŸÂ»
A hankali ya koma ya zauna, rai a b'ace ya fara rubutu.
"Meyasa kuka karb'a ne? Bappa Ali wancan karonma da ya kawo saida nace muku kada ku amsa!
ai tunda muka rasa Ya Nuruddeen mgna ta k'are munce mun yafe mishi to me sa zayi ta d'awainiya damu, ko yana zaton abinda yake mana zaisa mu manta tabon daya zama sanadin samuwarshi a ah'linmu ne?."
Gyara zama bappa Ali yayi kana ya fuskanceshi cikin sanyi yace.
"Kana tuhumarshi kan shine ya kashe mana Seyo ne?."
da sauri ya girgiza kansa alamar a a.
Shiko Bappa Ali ido ya kuma zuba mishi tare da cewa.
"To haushinsa kakeji ne? Kodai baka yafe mishi bane? Ko baka yarda cewa k'addara bace da tsautsayine ya rufta mishi?."
cikin lumshe ido yake jujjuya kai,
sai kuma ya bud'e idanun nashi da tuni sunyi jazir dan tuno d'an uwanshi da k'unar da yakeji a ranshi.
murya a tausashe Bappa Ali yaci gaba da cemishi.
"Nima da Umminka k'in amsar kayan mukayi,
koda aka shigar da kayan su Mudassir nasa suka fara fitar da kayan,
ganin ana fidda kayanne ya sashi cewa aiyi mishi sallama dani,
niko sai blnace ya shigo daga ciki sabida lokacin akwai yara a wojen suna karatu."
shiru Bappa Alin yayi tare da sharte guntayen hawayenshi kana yaci gaba da cewa.
"Yana shigowa gaban Umminka dasu Rahma ya durk'usa duk da girmanshi da shekarunshi da arzik'inshi ga d'anshi Arabi wanda zai kai sa'an Seyoji yana ganin mahaifinshi ya rusuna a gabansu shima sai ya rusuna."
Cikin zubda hawaye Bappa Ali yaci gaba da cewa.
"Suna durk'usawa sai Alhaji Gid'ad'o yayi ta zubda hawaye cikin rawan murya ya kalli Umminku dasu Rahma hawaye na zuba yace.
"Kuyi hak'uri ku gafarceni, nasan duk abinda zan muku bazaku tab'a farin ciki dashiba,
nasan na cutar daku cuta mafi muni tunda na kashe muku Garkuwarku,
wlh bawai dan in biyaku bane ko wani abu yasa nazo na kawo muku yan wannan kayan ba a a,
sai dan nasan nine na kashe me ciyar daku kullum hankali na baya konciya in na tunaku saina rasa sukuni tunda na buge Nuruddeen dan Allah ku gafarceni ku dena k'in abinda nake kawo muku halal inkune tunda na kashe mai cidaku."
cikin rawar murya da zubda Hawaye Ummi tace.
"Ba kaine ka kasheshiba dan babu mai rayawa da kashewa sai Allah, nasan kwananshi ne ya k'are,
amman in mun amshi kayan Saifuddeen zaiyi fad'a ranshi zai b'aci shiyasa bazamu amsaba."
da sauri Arabi yace.
"Dan Allah Ummi ku amsa ku bawa Saifuddeen hak'uri hankalin Abbana a tashe yake tunda ya buge Nuruddeen please Ummi ku amshi abincin nan wlh in baku amsaba zaiga kamar baku yafe mishi bane."
rumtse ido Bappa Ali yayi kana yaci gaba da cewa.
"Jin haka yasa ni cewa ba komai mun yafe musu mun kuma gode Amman kada ya k'ara kawo mana wani abun.
haka yasa sukaji dad'i sukayi ta godiya suka tafi suna k'ara bamu hak'uri.
To kaji yadda akayi dan haka ba laifin kowa bane fashe ni Aliyu in kuma na maka laifi sai in kwashi kayan in meda musu."
da sauri ya jujjuya kai kana ya rubuta mishi.
"Kayi hak'uri bappa Ali, duk abinda kayi ya zauna."
to daga nan ya shaida mishi dama yau zai fasa asusunshi da niyar gobe in zai tafi yaje da kud'in ya sai musu kayan abinci mu samman cefenen ramadan da cin kud'i.
bayan ya karanta ne ya kalleshi cikin gwarin guiwa yace.
"Yanzu dai to kada ka fasa asusun ka bari sai azumi ya d'anyi nisa in yaso ka fasa kayi hidiman kayan sallah."
cikin gamsuwa ya jinjina kai tare da cewa.
"Ba matsala hakan zanyi."
daga nan suka d'an tattauna shirye-shiryen Ramadan,
nan Bappa Ali yake sanar mishi an gayyaceshi cewar zaiyi tafsir a masallacin Fada har zuwa saba'an watan ramadan d'in.
nan kuma yace Saifuddeen d'in zaike fassarawa kurame kuma da hannu tunda da dare zaike yin tafsir d'in zai fara k'arfe 8 a tashi 9 nan dai suka gama tsara komai yadda zai tafi.
Daga nan wurinshi kai tsaye woje ya fita wurin abokanshi Mudassir k'anin Ya Adnan sai Salisu da Saminu dan gidan sarkin Dukkun sai kuma Warisu,
duk su lafiyayyune sai dai sun matuk'ar iya body language sabida abokanshi ne tun na yarinta,
bakin titi sukaje suka zauna iska na kad'awa suna tsaka da hira Ahmad yazo d'an Goggo Dada cikin body language Saifuddeen yace mishi.
"Kai a daren nan ka ratse wannan dajin naku,
to ni dai bani raka."
sai ya kuma duggure kan Ahmad dake dariya tare da cewa.
"Yaseen sai kun rakani, yo kewarkuce ai ta sani zuwa,
tunda ka fara zuwa Gombe ka rage zuwa Shabewa Dada ma sai cekiyarka takeyi."
Sai ya kuma harari su Warisu da Saminu yace.
"Su dama wad'annan al'barkacinka suke zuwa,
shine wai Dada tace ai dama saida karenka kake ganin karen wani, ba gashi yanzu tunda ya Seyo ya rasu bata kuma ganin abokanshi ba."
sai kuma yayi dariya kana yaci gaba da cewa.
"Shine yanzu da zan fito nace to Dada bari inje in cekinta miki karnukan naki tunda kice saida karenka kake ganin karen wani."
dariya sukayi baki d'aya kana suka kai mushi bugu,
Mudassir ne yace.
"Hege Ahmad d'an iya juya mgna,
ai hausace haka ba wai tana nufin mune karnukanba."
shi kuwa Saifuddeen mik'a yayi tare da lumshe ido kana ya amshi wayar Saminu rubutu yayi kana ya bawa Warisu karantawa ya farayi da d'an sauti.
"Hege mai dogon k'afa yau zamuyi mgnaninka yaseen bazamu rakaka ba,
dan ni baccima nikeji."
suna jin haka duk sukayi dariya.
Nan dai suka zauna sukayi ta hira,
daga bisanu dole suka raka Ahmad har shabewa suna tafe suna hirarsu ta abokai tamkar ba dareba.
So koda suka dawo dare ya d'anyi nisa basu wani tsayawa ba kowa ya nufi gida.
Shiko Saifuddeen yana shiga gida ya samu Umminshi da Rahma suna hira inda Rahma take goge mishi kayanshi data wonke mishi
tsakiyarsu ya zauna ita Rahma tana k'asa ita ko Ummi tana kan kujera,
haka yasa ya zauna k'asa kusa da Rahma sannan ya jingina kanshi kan cinyar Ummi wanda take rik'e da k'afafun Hayatuddeen tana yanke mishi farce.
numfashi ya furzar kana ya d'ago ya kalli Umminshi dake shafa kanshi,
murmushi yayi kana ya lumshe ido tare da bud'esu ya zuba matasu alamun yana sauraronta
Cikin kula tace.
"Yau Alhaji Gid'ad'o yazo."
ga mmakinta sai taga ya gyad'a mata kai kuma fuskarshi ba fushi,
sai ta kuma sa yar yatsarta manuniya ta shafa gashin girarshi ta kontar dashi kana tace.
"Na k'i amsar kayan nida bappanku, to kuma sai yayi ta kuka yana bamu hak'uri dole bappanka yace mu amshi kayan."
murmushi yayi kana ya gyada mata kai sannan ya amshi rezar hannunta ya juya ya fuskanceta da kyau kana ya kamo hannunta ya fara yanke mata farcen hannunta,
saida ya yanke na yatsu biyu kana ya kalleta tare da dungule hannunshi ya mik'ar da babbar yatsarshi yayi alamun jinjina,
sannan ya jujjuya mata kai alamun karta damu ba matsala.
sai ya kalli Rahma ya lumshe ido ya d'aga hannu yasa bisa goshinta ya sharte mata zubafar data tsastsafo mata sabida zafin anyon.
Murmushi tayi tare da zare bakin igiyar daga jikin kuros d'in,
dan ta gama gugar nashi har ta goge uniforms d'insu Hayatuddeen da Faruq na boko da islamiya.
gyara zamanta tayi suna fuskantar juna,
a hankali ya bud'e bakinshi kana ya had'a lips enshi da alamu furta.
"Sannu Addana ngd."
lumshe ido tayi tare da cewa.
"Godiya kuma a kan me?."
zuba musu ido Ummi tayi tana jin so da k'aunar yaran nata da tausayinsu na ratsa mata zuciya musamman Saifuddeen,
hannu ta d'aura bisa kan Saifuddeen d'in, shafawa takeyi a hankali tare kallon yadda ya manna kanshi bisa cinyarta murya a tausashe tace.
"Babana kayi shiru kamar ranka baiso mu amshi kayan bako?."
jujjuya mata kai yayi kana suka juyo suka kalli Rahma data shafa k'afarshi tare da jan 'yan yatsunsi biyu kana tace.
"Kada ranka ya b'aci muma bisa dole muka amsa bawan Allah nan har durk'usa mana yayi yana kuka yana bamu hak'uri,
k'in amsar kayan zaisa yayi ta zaton ko bamu yafe mishi bane."
murmushi yayi tare da lumshe ido cikin kurma-kurma dayin body language ya had'a hannunshi duka biyu ya karkad'a kana ya shafa gemunshi tare da nuna musu kunnenshi alamun yace.
"Ba komifa na fahimta, ai Bappa Ali yamin bayani."
sai ya kuma kalli Ummi kana ya gyara zama sannan yayi mata bayanin canjin kasuwancin da zaiyi,
haka nan Ummi ta tsinci kanta cikin farin ciki dan wannanma wata alamace dake nuna Saifuddeen inta yana tare da mutanen kirki nagari kuma wannan ya nuna mata kasuwa tasan da Saif d'inta.
"Alhamdulillahi Babana Allah ya sanya al'khairi yasa ka fara harkar a sa'a rabbi yasa ka shiga da k'afar dama."
Amin Amin suka amsa shida Rahma,
kana ya mata bayanin fasa asusunshi nanma tace.
"Hakan yayi yadda bappankun yace haka zakayi,
ka bari tukun kaga yadda kasuwar ledan take."
kai ya gyad'a mata kana sukaci gaba da hirarsu har zuwa 11:36 pm sannan sukayi saida safe,
Rahma ta tafi d'akinsu ita dasu Raihana Ummi kuwa ita da Autanta da Faruq,
shiko Saifuddeen d'akinshi ya tafi,
koda yaje buta ya d'auka al'wala yayi sannan yazo yayi nafilfili daga bisani ya fara karatun Qur'an yayi kusan awa biyu sannan yayi addu'o'in da neman sa'a da nasara a kasuwancinsa ya rok'i Allah ya tsareshi da cin amana sannan daga bisani ya mik'e ya kashe wutan d'akin kana ya matso da fankanshi kusa da gadon tare da k'ara gudun fanka,
gefen katifar ya zauna tare da yin addu'o'in bacci qulhuwa 3 falaqi 3 nasi 3 sannan ayatul kursi'u 1 ya shafa sannan ya konta da hannun dama,
a hankali ya gyara konciyarshi tare da yin mik'a ido ya lumshe yana mai mamakin Al'amarin halittarshi a ranshi yake cewa.
"Anya kuwa ni lafiyeyye ne."
sai ya muka juya rigingine ya kuma yi mik'a still ba sauyi ajiyan zuciya yaja tare da barin abin a ranshi kana ya fara tasbihi dan ya samu bacci ya saceshi cikin k'ank'anin lokaci kuwa yayi bacci abunshi.
Washe gari kuwa kamar kullum da sassafe suka tafi gombe shida Salisu nan suka wuni kasuwancinsu,
bayan sallan isha suka koma Dukku.
washe gari wanda ana gobe za'a d'au Azumi sabida ana zaton ganin wata yau,
wanda ranar ne kuma Baba bello zai sallami kasuwa sai kuma bayan salla.
Ranar sammako sukayi sosai shida Salisunshi k'arfe bakwai dai-dai na safe suka isa birnin bubayero,
bayan Salisu ya sauk'eshi sai ya tsallaka bakin tashar gombe line,
ya fara d'aukan irin masu kai aike tasha da sanyin safiyan nan.
Shi kuwa Saifuddeen yazo dai-dai mashigar kenan yaga Jabeer ma,
da sauri Jabeer ya iso gabanshi tare da bashi hannu cikin fara'a yace.
"Tab Lallai wannan balaraben dukkun da himma kake wato in junin wani sammako kai a tafe ka kwanako?."
hannu yasa ya d'an bugi k'eyar Jabeer irin ya cika surutu nan.
shi kuwa Jabeer kama hannunshi yayi suka nufi cikin kasuwar da yanzu ake shirin bud'eta sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da d'aga mishi gira kana yace.
"Ko dai kudin aure kake nema ne wannan iya sammako haka har ka rigamu mu yan cikin gari,
nima dana fito yanzu yaseen Ya Adamu ne ya matsa wai inzo in kimtsa shagon yau zuwa jibi kayanmu zasu iso zamu fara baza hajar cinikin salla ne."
murmushi ya d'anyi kana ya jinjina mishi hannu alamun mgninka ai.
suna isa shagon Jabeer ya bud'e sannan ya fara kikimtsa wurin,
yayinda Saifuddeen ke taiyashi,
tuni suka kimtsa shagon suka gyara komai yayi ras,
kafin su gama tuni kasuwa ta fara cika duk masu shaguna sun firfito da kayayya kinsu
cikin yin mik'a alamun gajiya.
Jabeer ya kalleshi tare da cewa.
"Yauwa Balarabe jirani bari inzo."
kai ya gyad'a mishi kana ya konta bisa tattausan sallayan daya shimfid'a cikin shagon ga iskan fanka na kad'ashi ido ya lumshe tare da gyara kinciyarshi.
Shi kuwa Jabeer yana fita bakin tashar ya nufa inda wasu masu saida abinci suke,
soyayyan dankali da kwai,
sai gasashiyar kaza ya sai musu kana ya shiga shagon gefen wurin ya saya musu Faro k'ananun roba guda biyu, sai molt,
kana ya juya rik'e da ledojin ya nufi cikin kasuwar.
Bayan ya isa ya tsallaka wani dandamali da akayi wanda yake shamaki tsakanin masu shago da masu sayan kaya,
kusa da Saifuddeen d'in ya zauna bubbud'e musu takardun abincin yayi kana ya kalli Saifuddeen dake konce yanata tab'e baki cikin tsuke fuska yace.
"Ka tashi muyi breakfast."
fuskar ya kuma ya mutsawa tare da jujjuya mishi alamun bazai ciba ya koshi,
ido Jabeer ya tsura mishi domin tabbas yasan wannan d'abi'ace ta fulani yin fulaku wa kowama.
shi kuma Saifuddeen tashi zaune yayi ganin kamar ran Jabeer ya sosu sai ya d'auki ruwa kana ya b'alle marfin sannan ya d'an sha ruwan har kusan rabin robar,
a hankali yayi gyatsa kana ya ajiye goran ruwan sannan ya d'auki na molt,
ya fara k'ok'arin mik'ewa da sauri Jabeer ya rik'o hannunshi kana yace.
"Meyasa ne kake min haka shin baka d'aukeni aboki bako bare in kai matsayin amini."
kai ya jujjuya mishi kana ya zaro bironshi tare da ballan takarda ya rubuta mishi.
"Am so sorry my friend, wlh a k'oshe nake Ummi ta cika min ciki da d'umame yau da kanta taimin dan Adda Rahma taje gidan Goggo Dada can ta kwana,
kana ni bana cin kaza,
shiyasa,
sannan dankalin kuma ba irin suyan da nake so bane akayi shiyasa bazanci ba,
ai dani da kai yanzu mun zarta abokai mun zamma aminai,
ka fahimceni."
yana karantawa yace.
"To gaya min me Kakeso in sayo maka?."
amsar takardar ya kumayi ya juya bayanta kana ya rubuta mishi.
"Am sorry Jabeer ba wai nak'i ci bane haka nan badan wani abu ba because inada wani banzai kyakk'yani wanda ni kaina yana damuna ba ko ina nake iya cin abinciba.
Kaga zansha molt baka tab'a lura daniba haka nake wuni bani cin komai wani lokacin sai dai in had'a molt da pic milk sai insha."
tabbas Jabeer yasan hakane so duk da haka baiji dad'in rashin cin nashiba,
amman dole ya hak'ura dan Saifuddeen da wuya yaci, shi kuwa Saifuddeen tsallaka madandalin yayi kana ya nufi shagonsu Hisham wanda yau cikansa ya zarta na kullum,
bayan sun gaisane yaje ya amshi botikinshi sabida lokacin wasu nata karya kumallonsu so zasu buk'aci ruwa da kayan zak'i.
cikin sa'a kuwa a safiyar yayi ciniki kusan na 3,500
sha d'aya dai-dai ya kuma komawa da nufin k'aro ruwan sai ya samu Baba Bello ya iso yazo wurin yana nemanshi,
haka yasa ya ajiye botikinshi anan shagon su Kabir kana suka juya suka nufi dilan ledodin.
Bayan an gama warewa Baba Bello adadin da yake amsa kullum,
sai aka rubuta sunan Saifuddeen dasa hannun shi dana baba Bello kana akasa kud'in kayan da akabashi ganin yawan kayanne da yawan kud'in yasa Saifuddeen yiwa Dottijon alamun.
"Kayan basuyi yawaba kuwa?."
Murmushi Baba Bello yayi kana ya fara loda ledodin a k'aton kwalin dake bayan kekenshi,
saida ya loda kusan rabin ledodin kana ya hau kekenshi sannan ya kalli Saifuddeen cikin yin kasa da murya yace.
"Kada Ka damu ai zan had'aka da customers d'ina duka,
kaga duka-duka kayan dubu hamsin nake amsa dama,
nakan sa na ishirin da biyar,
in fita inje in rarraba in ya k'are inzo in kuma kwasar rabin.
Yanzu muje duk zamu rabashi sai mu dawo mu debi sauran."
cikin gamsuwa ya gyad'a kai kana yabi bayanshi.
tafiya kad'an suka isa shagon wani mai saida takalma bayan sun gaisa Dottijon nan ya d'ebo banduran leda takwai,
ya bawa Saifuddeen kana ya juyo ya kalli mai shagon tare da cewa.
"Alhaji bala ga Jikana ya fara kawo muku daga yau,
insha Allah kullum zaike kawo muku kamar yadda nakeyi daku sai in Allah ya kaimu bayan salla."
wanda aka kira da alhaji bala kuwa cikin kula ya irgo dubu 4 ya bawa Dottijon kana yace.
"To baba Bello Allah ya kaimu bayan sallan, Allah ya sadamu da al'khairi."
Amin Amin, yace kana suka shige shago na gaba nanma ya basu kaya suka bashi kud'i.
haka dai sukayi tayi har suka gama wanda suka kwason kana suka koma suka kwaso sauran kashi d'ayan.
Kai tsaye shagonsu Jabeer sukaje inda sukace a basu na dubu 5, nanfa Saifuddeen ya basu suka bashi kudin na jiya ya bawa baba bello,
Jabeer nata musu tsiya wai.
"Tab ku dai kam kun more dan ko bamu sayarba ku dai kun sayar."
dariya sukayi kana sukaci gaba dan inda sabo sun saba da shek'iyancin Jabeer.
daga nan suka zagaya har layin masu kayan kitchen nanma shagonsu Hisham suka saya,
sai kuma suka mik'e babban layi har kan shagunan ba miskila,
cikin sa'a suka sameshi shida kanshi bayan baba bello ya mishi bayanin Saifuddeen ya gamsu kana yace.
"To Baba Bello Allah ya taimaka mana,
yanzu ni daga gobe ya rink'a kawo min na 15k dan shaguna na babbar kasuwama za'a rink'a kai musu da na kasuwar mata da shagunan cikin unguwanni dan naku ledodinku suna da kyau, muna jin dad'insu."
shiko Saifuddeen murmushi yakeyi yana ganin darajar mutumin sabida duk inda yaranshi sukayi awu sai ya amshi kwanon awun ya kamfata ya zuba a ledan wanda aka gamawa awun,
yara sai godiya sukeyi.
daga nan suka ci gaba da rabawa har layin masu kayan kolliya.
Wasu na 5k wasu 4k wasu 3k wasuma na 1k wasu ma na 500 yayinda wasu 6k ko 7k kowa dai dai-dai cinikaiyarshi yake karb'a
Koda suka gama sai suka tafi can dilan nasu,
a hankali baba Bello yaja hannunshi suka d'an koma gefe,
kana ya fito da kudin da suka tattaro ya had'a kansu,
sannan ya irga inda ya samu kud'in dubu hamsin da shida ne da d'ari uku.
Gyara zama yayi kana ya ware dubu hamtsin sannan ya kira d'aya daga cikin yaran shagon ya bashi kudin ya irga,
sannan ya d'auko wani babban littafi yaja gud a kan sunan baba bellon tare da rubuta bama binshi ko asi,
sai bayan salla in ya dawo.
Sai kuma yasa sunan Saifuddeen k'asan na Baba bello tare da rubuta .
"Munada kayan dubu hamsin a wurinshi."
sai ya kuma basu littafin sukasa hannu shima yasa hannu daga nan ya koma bakin aikinshi.
Su kuwa su Saifuddeen cikin nitsuwa Baba bello ya kalleshi tare da bashi 2k sannan yace.
"Kaga wannan ribanane na jiya,
ladan yawon da nasha yi cikin rana,
kuma kaima zaka iya samun haka a kullum koma fiye da hakan cikin duk kayan dubu goma ina samun ribar dubu d'aya da dari biyu,
wani lokacin in naga kasuwa bata gudu duk bandir din dubu goma sai inbi dubu d'aya rak kaga kenan duk fakitin dubu d'aya ina bin nera d'ari d'aya kacal ne,
kuma Alhamdulillahi a cinikin da nikeyi dubu hamsin kullum ina samun dubu shida ko biyar in na rage farashi na,
ta iya yiwuwa kai ka samu fiye da haka tunda kai yanzu ana hidiman cinikaiyan salla,
dole masu shaguna suna k'ara sayan leda,
kaga misali yanzu ba mishkila daga sayan na dubu 5 yanzu yace gobe na dubu 15 zaka kai mishi,
kaga Alhamdulillahi kasuwa ta fara a sa'a, dan haka kai gobe kayan dubu 60 zaka amsa,
yanzu zan gayawa shi Alhajin in dai ka buk'aci k'ari to ayi maka."
cikin jin dad'i da tsananin mamaki Saifuddeen yake kallonshi domin jin k'udurar ubangiji.
Mutun nawa ke raina kasuwar leda rashin sanin al'barkan dake cikinta ne yasa haka da yawa raina riba ke wahal da matasanmu da ganin sunfi k'arfin sana'a kaza sai kaza ko a a su sunyi karatu sunfii k'arfin talla a kasuwa sai zaman office.
cikin kurmanci yayiwa baba bello godiya tare fatan al'khairi.
Shi kuwa Baba bello 2k d'in ya kuma bashi tare da cewa.
"Amshi wannan ka sayawa Mamanka sugar ka kai mata taci al'barkacin sana'ata."
Da sauri ya girgiza kanshi alamun a a bazai amsaba ai ya gama mishi komai ma daya bashi aron sana'arshi ba tare daya mishi hasadan abinda zai samuba.
Shiko Dottijon cikin girma da isa yace.
"Bana son musu a tsakaninmu da mahaifinka ne ya baka zaka k'i amsane?
niko da ace Allah yasa inada d'a da na bashi ai bazaik'i amsaba sai daima yace in k'ara mishi dan haka maza karb'i kud'innan."
cikin tsananin ganin darajar Dottijon yasa hannu ya amshi 2k d'in kana ya mishi godiya.
Shi kuwa Baba bello,
ubangidan nasu yayiwa bayanin kan ba mmki Saifuddeen ya nemi k'arin leda.
cikin mutuntaka ogan nasu yace.
"Ba matsala aimu haka mukeso."
daga nan ya sallamesu, kana ya yafito Saifuddeen sannan ya hau kekenshi,
yana janta a hankali kana Saifuddeen na binshi a baya har sukaje bakin titi,
cikin kula ya bawa Saifuddeen hannu da sauri Saifuddeen ya bashi nashi hannun sai kuma ya zuba mishi ido jin ya rik'e mishi hannun cikin bada shawara yace.
"Ita sana'a bata yiwa mutun yawa,
kaga shi leda cikin awa uku duk zaka gama kaiwa kostomominka ka kuma tattara kud'i har ka biya kana ka zare ribarka.
To in dai ka gama da wuri to zakafa iya saida ruwanka d'in in kaga alamun zai saidu,
in kuma Kaga bazai saiduba tofa kada ka zauna banza ka samu sana'ar da zaka had'a dana ledan kafin bayan sallan ka komawa ruwan."
Cikin gamsuwa ya jinjina kai alamun in sha Allah hakan zaiyi.
shi kuwa Dottijon ya jima yana mishi nasiha da rik'o da amana da tattali,
sannan daga bisani sukayi sallama shi dottijon ya kama hanyar gidanshi kana shi kuma Saifuddeen ya koma cikin kasuwa ya d'auki bitikinshi ya kuma saran ruwa.
Koda Jabeer ya ganshi yai ta mishi tsiya wai shine sana'a goma mgnin baccin safe.
Haka dai ranarma ya wuni saida kayan sanyinshi,
saida akayi sallan isha suka kama hanyar dukku wanda tuni anga wotan Ramadan,
gaba d'aya al'ummar annabi gobe za'a tashi da azumi.
Kamar yadda ko wanne gida ke shirin d'aukan azumi hakama gidansu Saifuddeen domin.
bayan yayi wonkane yaje ya samu Umminshi da Adda Rahma da Raihana,
nan ya gayawa Umminshi lamarin kasuwar sai dai bai gaya mata ribar da Dottijon nan ya gwada mishiba don baison ya fad'ad'a burinshi kan ribar gudun kada ya shigar da son zuciya.
Rahma ya kalla wacce ta kawo mishi abinci cikin sanyi tace.
"Yauwa Saifuddeen wannan k'awar Raliyya Salma sun zo d'azu tace wai in gaisheka in ka dawo."
ta k'arishe mgnar tana murmushi da son ganin fuskarshi dan tasan sam Saifuddeen baya shiri da Salma
Shi kuwa yi yayi kamar bai gantaba bare ya gane me take fad'i dama in baya son mgna da mutun haka yakeyi.
Ummi kuwa ido ta zuba musu tana murmushi,
abincin ya d'an tsakura kasancewar shi baida yawan cin abinci.
saida ya d'an gyara zamanshi kana ya kalli Hayatuddeen dake gefenshi tare da mishi tambayar azumi nawa zaiyi?."
cikin d'oki yace.
"30 zanyi ko d'aya bazan shaba."
dariya Ummi tayi jin Raliyya na cewa.
"Ko kuma ko d'aya bazakayi ba ko?."
cikin dariya Rahma tace.
"Ai kam saidai hakan."
shi kuwa Saifuddeen hannun Faruq yaja tare da cemishi shi kuwa nawa zaiyi.
yatsunshi uku na tsakiya ya d'aga alamun zaiyi uku da yake duk sun iya kurmanci.
Raihana kuma tana tsakiyar gida tanata kiciniyar tafasa tea da yin miyar asuba,
miyar dege-dege take musu dan Ummi dubu d'aya ta bada Hayatuddeen ya sayo musu hanta da jan nama,
tofa shine aka gyarashi tayi miyar ganyen albasa da yaji kayan miya dana d'an-d'an dan aji dad'in yin sahur.
koda ta gama tafasa tea d'in da tasa citta da kanumfari,
sai ta d'ura a filas kana miyar kuma ta barshi a tukunyar sai ta dorashi saman kanta sannan taja kitchen d'in ta rufe sai da asuban Rahma zata k'arisa aikin.
tana rufe kitchen d'in taje sukaci gaba da hira,
nan Saifuddeen ya bawa Ummi shawarar a hana Aunty Nina girki dan tana laulayin wani cikin,
to shiyasa yake son a hanata girki su had'a tukunyar,
sosai Ummi taji dad'in haka dan itama taso hakan sabida tasan Bappa Ali mutum ne mai kawaici tana sane cutar mijintane ya medasu basu da wasu yawan kadarori.
koda Saifuddeen ya tashi daga nan k'ofan Bappa Alin ya nufa inda ya samu Aunty Nina tana kiciniyar hura wuta a murhun gawayi yayinda shi kuma bappa Ali,
yake ruggume da Qur'an alamun zai fita masallaci.
nan ya gaya mishi shawarar da suka yanke shida Umminshi.
bawan Allah Bappa Ali sai yake jin kunyar wai shi ya kamata yaci dasu ya gaza sai kuma shima su ciyar dashi,
da fari kamar bazai yardaba to dole dai ya yarda dan Saifuddeen ya kafa ya tsare haka ya hak'uri,
sannan suka kama zance tafsir d'in da zasu fara gobe ya jaddawa Saifuddeen ya shirya dashi za'ake zuwa bayan sun gama mgnane ya fita wurin abokanshi.
Salisu ya samu da Mudasir sai Warisu ganin Saminu baya nanne yasa suka raja'a gidan sarki gidansu Saminun kenan,
a d'akin saminu suka yada zongo sunata hira,
har dai dare ya fara nisa kafin suka fito,
Warisu ya shiga gidansu shima Mudassir yayi hanyar gidansu.
Saifuddeen kuma da Salisu tare suke tafiya dan kusan katangar gidansu d'aya ne.
suna isa bakin masallaci Saifuddeen ya zaro biro kana yayi rubutu a jikin takardar daya b'alla.
"Yauwa Salisu dama inaso in gaya maka an rage balance enka ka rink'a bada dubu biyu duk sati,
sai mu rink'a tasowa biyar dai-dai na yamma kafin a kira magrib kuma mun iso dukku kaga zamuyi bud'a baki a gida kuma zamu dena tafiyan dare,
in kuma gari ya waye in yaso ana fitowa masallaci mu tafi tunda ba batun jiran karyawa."
cikin tsananin jin dad'i Salisu ya ruggumeshi tare da cewa.
"Kai Alhamdulillahi wlh ka kawo shawara mai kyau, amman dubu biyu yayi kad'an gsky zan dai bada 4k tunda du-du du dai awa d'aya da rabine aka rage.
Ngd matuk'a Allah bar zumunci da k'auna my friend."
cikin sanin mutuncin juna ya kuma ce mishi.
"No kai dai kabar 2k d'in ai kaima kanada buk'atun kanka dana iyayenmu."
cikin sanin ya kamata Salisu yace.
"To naji na kuma gode, amman gsky 3k zanke badawa kada ka cemin komai."
jin haka yasa Saifuddeen rubuta.
"To Allah ya musu al'barka."
da haka sukayi sallama,
Koda ya shiga gida tuni su Ummi sunyi bacci acewarsu kada suyi dogon hira su zo su makara.
Shima hakance a wurinshi shiyasa yanayin wonka yayi al'wala yazo yayi konciyarshi.
2:00 Am Ummi ta farka kamar yadda Ummi takeyi ko wanne lokaci in dai cikin Ramadan ne,
kana ta bud'e k'ofa ta fito tsakar gida yayinda iska mai sanyi ke kad'awa, babbar taburma ta shimfid'a kana ta fito da wani d'an madaidaicin cainis carpet amman irin na da fa,
ta shimfid'a bisa taburmar kana ta ajiye hijabinta da carbinta da Qur'an sai lantanta mai wadaceccen haske.
al'wala tayi kana kana taje baki k'ofar d'akinsu Rahma kira d'aya ana biyu Rahma ta amsa.
Itako Ummi tana jin Rahma ta amsa ta koma bisa taburmar ta fara nafila,
Rahma kuwa tana tashi ta tada Raihana Raliyya.
sun jima kafin suka tashi,
suna fitowa duk sukayi al'wala kamar yadda aka sabar musu tun basu kai hakaba,
kana sukazo ko wacce tayi iya nafilar da zata iya daga bisani suka fara karatun Qur'an.
Yayinda tuni Saifuddeen ma ya tashi yazo ya tashi Hayatuddeen sun je bakin k'ofar d'akinshi bisa k'aramar taburma ya shimfid'a musu sallaya,
suka fara nafila bayan sun zauna sun fara tilawa ne ba jimawa Hayatuddeen ya fara gyangyad'i yana rab'awa jikin Hamma Saifuddeen d'in nashi tuni bacci ya sureshi shiko Saifuddeen gyara mishi jinginar yayi kana yaci gaba da tilawarshi.
3:20 Am Rahma tayi addu'a tare da shafawa kana ta mik'e ta cire hijabinta ta ninke ta ajiye gefe sannan ta shiga kitchen ruwan zafi ta d'ora bayan ya tafasa ne ta d'an zuba man gyad'a cikinshi kana ta d'ebo couscous dai-dai misali tazo ta zuba kana ta meda marfin ta rufe,
sanan ta harhad'a kofuna tare da pilet da cokula,
ta fitar taje ta jera bisa babbar taburmar,
kana ta dawo ta d'auki filas d'in duka biyu babban da k'aramin,
sannan ta koma kitchen d'in,
bud'e tukunyar tayi tare da duba couscous d'in yayi lugub yadda akeso kuma yayi wasar-wasar bai kwab'e ba amfanin zuba man gyad'an kenan,
sauk'e tukunyar tayi ta ajeshi gefe sannan ta mik'e ta sauk'o dana miyar ta d'orashi kan rushin.
sai ta kuma sauk'o da kuloli guda biyu d'an madaidaci shi ta fara zubawa saida ta cikashi yadda zai iya isar mutun ukuma,
kana ta kwashe sauran duka a babbar kulan,
sannan ta kwashi kulolin ta kaisu bisa taburmar,
tana dawowa ta bud'e tukunyar miyar da sai bol-bol yakeyi sai mai da tsokokin da suka yiwa miyar k'awanya,
tukunyar ta d'auka baki d'aya kana ta d'auki d'an k'aramin kulan miyar,
tana fitowa ta zauna gefen taburmar kana ta kalli Raihana tare da cewa.
"Na mance ban d'auko biredin nan ba,
tashi ki kawoshi yana d'akin Ummi."
to tace tare da mik'ewa ta nufi d'akin.
Ita kuwa Rahma miyar ta saka a k'aramar kulan tare da tsokoki kusan shida kana tasa k'ashi biyu,
sannan ta d'auki k'aramin filas d'in nan ta had'a da kulolin kana ta amshi biredi d'aya a hannun Raihana da ta iso da su a hannunta,
cikin nitsuwarta tace.
"Yauwa Raihana bari in kaiwa su Bappa Ali nasu ke kuma ki sa mana ki sawa d'an uwana." da yake haka take kiran Saifuddeen wasu lokutan
ba musu Raihana ta tsuguna tare da fara zuba musu,
shi kuwa Saifuddeen da sauri ya mik'e yaje ya amshi abincinsu bappa Alin kana yayi mata nunin da ta koma taci abinci bari shi ya kai musu.
To tace mishi kana ta bashi kulolin,
sannan ita kuma ta koma ta zauna kofi ta d'auka tea ta had'a mishi mai kauri ta san ba wani abinci mai yawa zai iya ciba,
bayan ta had'a mishi ne sai ta kuma d'iba mishi couscous d'in tare da sa mushi miyar hantar a d'an k'aramin side soup tuni Raihana kuma ta gama had'a musu nasu a tire,
ta ajewa kowa kofin tea a gabanshi.
bisimillah sukayi tare da addu'a sannan suka fara sahur d'in.
Shi kuwa Saifuddeen koda ya dawo tuni k'arfe hud'u ta kusa gefen Umminshi ya zauna tare da d'aukan kofin tea d'in da Rahma ta had'a mishi ya fara sha,
ido ya lumshe jin k'amshin citta da kananfari da masoro da ganyen na'a-na'a, yana sha yana lumshe ido ko dan dama shi yana son tea yana nan kamar buzu,
ita kuwa Ummi cikin kula tace.
"Babana kaci abincin mana kanata shan ruwan zafi."
ido ya zuba musu yadda suka had'u su duka sunaci a kwano d'aya sai ya tuna mishi da baya, wanda baushe ke cewa kowa ya tuna bara baiji dad'in banaba,
idon ya kuma bud'ewa yana mai tunanin dah
ita Ummi taci da yaranta mata shida Nuruddeen kuma tare sukeci da Abbansu da bappa Ali koda last year haka sukeyi,
sai gashi bana kuna ba Abba ba Nuruddeen bappa Alinma da yake raye baizoba sabida rashin d'an uwanshi,
oh mutuwa wato dama haka abin yake ta rabaka da macecce ta rabaka da rayeyye,
gashi Hayatuddeen yanata baccinsa.
itako Ummi kamar ta gane me yake tunawa sai ta d'an gyara zama sannan ta zare cokalin cikin abincinshi ta saka cikin tiren da sukeci tace.
"To muci tare, kada kayi zurfin nazari gamu Allah ya barmaka mu gashi nanda bad'i kuma zakuyi taci da autana."
ganin ta tsareshi da ido ne kuma in baiciba bazata ji dad'iba yasa ya d'anci kad'an kana ya kuma amsar kofin tea d'in da Rahma take rik'e dashi tana sha kurb'a biyu yayi kana mik'a mata sannan ya mik'e da sauri.
ruwan wonka ya d'iba sannan ya shiga d'akinshi ruwan randar sanyinshi ya d'ansha kana ya d'auko soson shi da makilin da burosh.
a nitse yayi wonkanshi yana fitowa ana kiran assalatu.
Dama tuni su Ummi sun gama sahur d'insu har Raliyya ta tattare wurin.
D'akinshi ya shiga kasan cewar yau jumma'a ace kuma azumine,
shiyasa ya zaro wani tattausan yadi mai sauk'in kud'i fari k'al rigar anyi mata d'inkin zamani anyi d'an aiki da yellow zare, bayan ya gama sa kayan sunyi d'as a jikinshi sai yasa hular zannabukar mai d'an surkin yellown zare sai takalma suma farare masu d'an ratsin yellow.
Sosai yayi wani irin baiyanennen kyau,
wanda gani d'aya zakayi mishi kasan Allah ya masa cikar halitta da haiba, gaba d'aya alamun zarra da tsurar cikekken d'a namiji sunata baiyana a jikinshi tuni muryarshi tayi kauri alamun cikar balaga da d'an dad'ewa,
gwarabanshi suna ta hab'aka yayinda duk wani sashi na jin d'an adam dake iya fidda gashi,
nashi sunata yabanya,
hatta gefen kunnenshi yana ta nuna alamun tsirowar saje,
hakan sharabanshi da singalalin hannunshi da k'irjinshi,
tuni gashin girarshi ta zama d'aya daga cikin abinda ke Jan hankalin mutane ih zuwa ga kallonshi dan gashin girarshi har had'ewa suka bisa karan hancinsa,
hakama gashin idanunshi zar-zar dasu lips enshi kuwa jazir dasu ko yaushe kamar an shafa musu man baki zakaga suna shek'i sirarane sai dai sunada d'an fad'i da taushi dan ko d'an dannesu yayi da harshenshi sai kaga wani wurin ya lotso ya kuma yi fari,
yana kuma janye harshenshi zakaga ya koma janshi,
yatsun hannunshi da sawunshi kuwa suma kansu abin ganine.
Tsayuwa yayi gaban wannan dogon madubin hannunshi rik'e da turare,
feffesawa yayi a jikinshi yadda bazaiji gafinshi a mak'oshinsa ba.
carbi ya d'auka kana ya fita nan ya samu Raihana ta tada Hayatuddeen da Faruq sunyi al'wala,
shiyasa ya tasasu a gaba suka nufi masallacin k'ofar gidan nasu.
Bayan an idar da salla su Hayatuddeen suka tafi gida shi kuma sai ya d'an zauna yayi azkar saida ya gama sannan ya mik'e ya fita a harabar tsank'ayarsu ya samu Salisu na jiranshi.
Dan haka sai yayi sauri-sauri ya shiga gida a tsakar gida ya samesu duk suna ninnike hijaban da sukayi salla dasu,
Ummi kuwa har yanzu carbine a hannunta gefenta ya d'an rusuna kana ya motsa lips enshi a hankali alamun. "Ina kwana?."
"lfy lau Babana har zuku tafi ko?."
tace dashi cikin kula kai ya gyad'a mata alamun eh,
sai ya kuma gaida Adda Rahma kana su Raihana suka gaidashi,
Raliyya kuwa tuni ta har-had'a kwanun wonke-wonke tana wonkewa.
da sauri Ummi tace.
"To Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lfy ya dawo daku lfy." sabida jin Salisu nata danna mishi hon
Amin Amin suka amsa baki d'aya kana ya mik'e ya fita.
Suna isa gombe kamar kullum Salisu ya ajiyeshi kana yaja ya tafi ya fara aikinshi.
Shi kuma cikin masallaci ya shiga,
baccin da baibane ya dan fara fizgarshi haka yasa ya konta,
cikin k'ank'anin lokaci yayi bacci.
8:00 Am ya farka da sauri ya mik'e,
ya fita harabar wurin ruwa ya saya yayi al'wala sannan yazo yayi walaha,
daga nan ya nufi cikin kasuwa.
Yana shiga kai tsaye dilansu ya wuce yana zuwa ko yayi sa'a ba layi sosai tofa nan take aka bashi na 60k ganin bashi da wurin zubasu ne sai yace musu bari yazo,
shagonsu Hisham yaje yace musu kwali yakeso nan take suka bashi yankekken kwalin Gas
yana amsa yaje ya cika kwalin da lododin.
Da shagon ba mishkila ya fara dan yafi kusa dashi kuma yasan me yawa zasu karb'a zasu rage mishi nauyi,
yana zuwa kuma ya samu shagon a cike mak'il da masu sayan abubuwa irin su Gero, kunu gyad'a kunun wake k'osai, waken awara.
Rid'i, sugar, madara, acca, al,kama, masara, maiwa, shinkafa, dawa, fulawa, da dai sauransu a k'alla yaran shagon sun kai goma amman still ga layin masu awu,
d'aya daga cikin yaran shagon ne ya yafitoshi tare mik'o mishi 5k d'in jiyan kana yace.
"Alhaji yace yau na 15k zaka bamu ko?."
kai ya gyad'a mishi kana ya sunkuyo ya rink'a mik'o mushi faket-faket na ledodin hawa-hawa kamar dai yadda yaga Baba Bello ya basu jiya.
Yana basu ya rubuta kana ya bawa yaron shima yasa hannu,
daga nan ya fara bin duk shagunan da Dottijon ya nuna mishi,
inda yasamu wasu basu firfitoba,
sai ya wuce gaba, wasu a dawowa sai ya samu suna bud'e shagun nasu sai ya basu,
yana basu suna bashi kud'in na jiya,
haka dai tuni kafin k'arfe sha d'aya ya gama rabawa,.
Cikin nitsuwa ya koma rumfar dilan nasu inda ya had'a lissafin kud'in ya samu dubu hamsin da shida ne ga 2k d'in da Baba Bella ya bashi jiya nan ya had'asu wuri d'aya 8k kenan.
wato fad'in farin cikin da Saifuddeen yayi a wannan lokacin bazai yuwuba.
Kawai sai yayi sujjada ya godewa Allah gashi yau da ribarshi kusan 8k.
ai cikin aminci da farin ciki ya basu kud'insu 50k dai-dai kana aka d'auko littafi akayi alamar ya biya na jiya sai kuma na gobe 60k cikin tsananin farin ciki yasa kud'inshi a al'jihu kana ya bar shagon da zummar sai gobe.
Tuni kasuwa ta cika tayi tambul sabida yawanci akanzo da sanyin safiya koda maraice sabida yanayin azumi ba'a zuwa da tsakiyar rana.
Bayan ya gama rabawanne
sai ya kuma d'auko botikin pure water inshi ya saro leda d'aya,
dan bin shawaran baba bello amman ina a gari na gombe garin musulmai zakayi yawa har ka gaji cikin kasuwar gombe da wuya kaga arne ba irin kasuwar Yolanmu ba,
ita kasuwar gombe du musulmaine sai yerobawa da terawa kuma duk masallatane bana ce ba kirsoticiba amman gsky basu da yawa.
ganin wahalar banza zaisha sai ya rabawa Al'majirai ruwan.
Shagonsu Jabeer yaje wai ko su d'an tab'a hira amman ina sai ya samu shagon mak'il da mata ba ko hanyar wucewa,
dole ya wuce shagonsu Hisham still nanma shagon cike yake da mata,
gun bayarben nan mai robobi yaje canma kazalika,
koda ya koma shagonsu Kabir mai ruwa kuma sai ya sumu sun rufe wai saida yamma zasu dawo su bud'e.
gefen shagon nasu ya zauna ya lumshe ido yana nazarin to sana'ar me zaiyi,
ya dad'e yana tunani a ranshi yake cewa.
"Alhamdulillahi Allah ban raina sana'ar daka baniba,
Allah kaine mai badawa ka kuma k'arawa mutun ya rabbil izzati ka nunamin wata sana'ar da zanyi mana kar in wuni zaman kare a karofi."
yana gama fad'in haka a ranshi sai ya bud'e idanunshi yana bud'esu ko sai kan wani mai saida omo irinsu Good mama kilin Zep viva sabulun kamaru da dai sauransu.
da sauri ya mik'e yaje ga saurayin mai amalanken kana ya yagi takarda ya rubuta mishi cewa,
shima yana son saida su omon ya nuna mishi inda zai sara,
cikin gatsali da zoleya saurayin yace.
"Hahaha kanada amalanken ne, ko akai zaka d'ora kana da kud'in jarin ne?."
rubuta mishi amsa yayi cewa a kwali zasu bashi zai d'aura a kai.
cikin zolaya ya nuna mishi shagon da suke sari,
aiko yana zuwa sai yaga suma shagon ya kawo musu leda koda ya rubuta wa mai shagon dalilinshi ba b'ata lokaci ya bashi su Omo kan ya saida ya d'auki ribarshi ya kawo mishi uwar kud'i.
Kamar wasa ya aza kwalin su omo yana yawo koro-koro sak'o da luggu,
amman ina ko asi bai saidaba.
har azahar har yayi niyar in yayi salla zai maida musu sai ya kuma fasa,
koda akayi salla sai yaci gaba da zagaye har ya shiga layin yan badaru,
nan aka fara kiranshi ana saya kad'an-kad'an sai gashi kafin la'asar ya saida stab yana had'a kudin yaga dubu hud'u ne kuma kayan 3,500 aka bashi kenan yaci ribar d'ari biyar a ciki dan harda irin manyan nan na 500.
koda ya kai kud'in sai ya kuma amsar wani cikin ikon Allah shima ya saida.
aifa ranar da Jabeer ya ganshi dasu Omo da sabulu ya mishi tsiya wai ko dai aure yake bid'ane.
K'arfe biyar saura ya maida kwalin oman da sauran nan ya samu ribar 200 lissafin ribarshi yau dubu takwas kenan,
hamdala yayi kana ya duba agogon hannunshi ganin biyar saura kwata,
sai ya nufi gaban wani mai dabino,
mudu d'aya ya saya, kana ya fito bakin kasuwar inda yaga mai kankana dasu lemu da ayaba kankana ya saya babba da k'ari kana ya sayi lemun d'ari uku,
duk dai dubu d'aya ya kashe tsakanin dabino da lemu da ayaba,
ganin saura 7 minutes buyer ta cika sai ya gangara gefen masu nama/naman 1k ya saya,
sannan ya sayi su tattasai, albasa, attaruhu, karas, kabeji. da dai sauransu a ta k'aice dai 3k ya kashe kana sannan ya adana 5kbda zummar in ya koma zaiyi musu asusunsu da ban ribar omo d'ari takwai d'innan kuma ya barsu a aljihu ko ya rink'a jin kud'i a jikinshi. biyar dai-da Salisu yazo suka tafi.
Alhamdulillahi sun isa Dukku rana tanayin mudun kuyangi alamun ta kusa fad'uwa.
inda ya samu tuni Rahma sarkin aiki ita da Raihana sun gama komai,
inda sukayi kunun gyad'a mai kyau, da tea daya sha kayan k'amshi sai soyayyan doya daya sha kwai dasu albasa da citta kanumfari onga,
sai kuma tea wanda akayi dan Saifuddeen da Bappa Ali,
kana sai jolof d'in taliya da yasha kifi,
sannan sai biredi da aka soya da kwai sai kuma su dabinon da kankana da ayaba da lemun daya kawosu yanzu.
da sauri Raihana ta amshi ledodin kana ta mik'awa Adda Rahma ledan naman dasu tattasan,
ita kuma ta d'ebo ruwa a roba tare da d'an tarfa gijishi kana tazo wonkesu ayaban da kankanan da lemun kafin ta yankasu kana dabinonma ta wonke,
shi kuwa tuni ya shiga wonka yana fitowa yasa Hayatuddeen yaje ya kira mishi Salisu,
kafin ya shafa mai ya fito har sun taho tare,
kana su Ummi sun gama shirya komai Raliyya ta kaiwa Aunty Nina nata sannan na bappa Ali da ban,
tuni ita kuma Rahma ta had'awa Saifuddeen nashi da abokinshi,
su kuwa duk sunyi al'wala kowa na zaune rik'e da carbi,
yayinda Raliyya ke rik'e da dabino a hannu alamun kiran salla kawai take jira Raihana kuma ruwa tafi bege,
ana kiran salla duk sukayi addu'a kana aka fara bud'a baki,
da sauri Ummi ta rik'e hannun Raihana kana tace.
"Ki fara da dabino kafin kisha ruwa."
da sauri ta amshi dabinon.
Su kuwa Saifuddeen da Salisu dabinon sukaci bayan sunyi addu'a sannan suka sha kankanar da Adda Rahma tayi mata mayafi da garin madara,
saida sukayi gyatsa kana suka mik'e jin ana shirin tada ik'ama a massalacin nasu yasa suka kuskure baki kana suka tafi dan dama duk sunyi al'wala suna fita harbar matsallacin ana...!
By
*GARKUWAR FULANI*
*NAKASA BA KASAWA BACE*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.