Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt
Chapter 14 of 27
*PAGE 14*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
~Har lau dai kuna samun garaɓsar free page ne kafin a tsaya ƙoƙarta ka/ki turo kuɗin karantar littafin har ƙarshe~
_Turo katin mtn na É—ari uku kacal ta wannan number 09097853276 ,ko kuma ka/ki turo É—ari ukun ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki_
Cikin tsananin firgici da kad'uwa jiki na tsuma murya cike da taraddadi Ummi tace.
"Bayida rai ko Raihana? Raliya baya numfashi ko!? yamutu ko shikenan Saifuddeen shima yatafi yabarmu inna'lillahi wa'inna'ilaihirraji'un,!sai ta kuma fashe da kuku mai matukar ban tausayi.
jiki a mace tasulale kasa ta ta zauna kan kujerar dake gefen k'ofar cikin muryar kuka mai cike da taradaddadi takefad'in.
"Ya Allah karufamin asiri kakara rufamin, kad'aga kafad'ar wanna bawan naka, Saifuddeen idan katafi kabarmu yazamuyi da rayuwar mu ina rayuwa zatata kaimu Saifuddeen kadawo garemu."
sai ta kuma kalli yadda Raliya ta kife kai jikin k'ofar tana wani irin narkekken kuka,
cikin matsanancin tashin hankali Ummi tamike tsaye kamar anzabureta.
Da sauri su Raihana suka rungumeta suma suka fashe dakuka mai sanyin sauti nan gurin yakacame da koke-koke duk wanda yagansu saisun bashi tausayi.
Dr Adnan dake zaune acikin offece inshi kuwa shima sai sharar kwalla yake time to time sai kuma yamike da sauri jin hayaniya a waje, dasauri yafito.
kana Dr Arabi yamara masa baya,
ganinsu Ummi ne yasa Dr Adnan saurin saida hawayenshi, yanufi inda suke.
A hankali yasa hannu ya Yajanye su Raihana ajikin Ummi,
dasauri Ummi tariko hannunsa tare da zuba mishi ido murya a raunace tace.
Adnan Saifuddeen yarasuko!? dan Allah ka kaini naganshi."
wasu zafafan hawayene yaji nakokarin zubo masa dasauri yamaidasu dan gudun kada takuma shiga wani tashin halin,dukda shima hankalinsa amatukar tashe yake sai dai ya fahimci bata cikin haiyacinta matar da take tsananin jin kunyarshi ko sunanshi bata fiye kira iya gaisuwa ke hadasu sabida fulakun fulanin gaske tunda ya zama surkinta suke kunyar juna, amman gashi yau ciwon Saifuddeen yasa ta mance komai har tana rik'e hannunshi cikin sama musu k'arfin guiwa yace.
"Ummi ki kwantar da hankalin ki.
Saifuddeen yana raye, babu wani abunda yasame shi natashin hankali, illa d'an buguwa kadan kuma duk anyi settling d'in komai yanzu haka yasamu bacci.
Ummi addu'arki kadai Saifuddeen yake buk'ata, kidaina kukanna dan kinsan bazaiji dad'iba idan yatashi ya taddaki ahakan."
da sauri tasa tafin hannunta bisa fuskarta hawayenta tashiga sharewa cikin hanzari, dan tasan abinda yafada gaskiya ne.
Dan a duniya idan dakwai abinda Saifuddeen yafi tsana arayuwarsa, baiwuce ganin bacin ran mahaifiyarsa ba in yaga tana zubda hawaye hankalinshi tashi yake ya birkice mata, tuno hakan yasa ta tsagaita kukan,
dai-dai lokacin kuma
Dr Arabi ya k'araso inda suke nan suka hadu sukayita k'arfafa wa Ummi guiwa, harsaida sukaga tad'an sami nutsuwa kafin, suka juya suka nufi office d'in Dr Adnan kasan cewar shi babban doctor daya ke kula da masu irin matsalar da Saifuddeen yake ciko.
Shi kuwa Hayatuddeen gudu yake akan U.D. d'inshi tamkar zai bar garin batareda bata lokaciba ya'isa Medical Center,
dasauri yafaka mashin d'insa acikin harabar asibitin,
kana yanufi cikin asibitin inda Raliya ta kwatanta mishi.
A tsaye yataddasu Ummi ganinsu tsaye cirko-cirko yasa zuciyarshi bugawa da azaban k'anrfi ido ya tsura musu tare da sassarfa cikin kid'ima ya'isa inda suke,
jikinsa nab'ari ya kalli Umminsu cikin tsoro yace.
"Ummi ina Hamma Saifuddeen?."
kai ta sunkuyar cikin son samawa yaran nata nitsuwa tace.
"Ba matsala fa ka kontar da hankalin ka ya yana bacci ne."
sai ta kuma sa hannu ta share hawayenta kana ta nuna mishi inda su Dr Adnan sukayi tare da cewa.
"Kaje ka Adnan na son ganinka."
ba tare da yace komai ba yabi inda ta nuna mishi kasan cewar yasa ofishin Adnan d'in so kai tsaye ya shiga,
in da ya samu Dr Arabi yana nunawa dr Adnan wasu takardu da sukafi kama da hoton k'ashin bayan mutun da jijiyoyin.
Da sauri ya k'arisa gabansu jiki na rawa yasanya hannunsa acikin aljuhu yaciro kud'ad'en daya d'ebu,ya mik'awa Dr Adnan tare da cewa.
"Ya Adnan gashi dan Allah ayiwa Hamma Saifuddeen duk abinda yadace in bazasu isaba in k'aro wasu, mu dai lafiyarshi muke buk'ata in Allah yasa yanada sauran rayuwa."
cikin kulawa Dr Adnan yace. "Ay an mishi komai duk abinda yadace duk wani taimakon da ya kamata abashi anbashi yanzu dama numfashinsa mukeso ya dai-dai ta,
kuma Alhamdulillahi munsami nasarar ceto numfashinsa yanzu jira muke zuwa gobe muga abinda Allah zaiyi,"
Cikin sanyi Hayatudden yace.
"Ya Adnan ina tsoro, kar mu rasa Hamma Saifuddeen."
kafad'arshi Adnan ya d'an bubbuga kana yace.
"In sha Allah bazamu rasashi ba,
sannan kacewa Ummi kada a gayawa Rahma abinda ya faru a bari in na koma zan san yadda zanyi in gaya mata."
Shiru Hayatuddeen yayi fuskarsa d'auke=da matsanancin damuwa, saikuma yace.
"Ya Adnan yanzu zamu'iya ganin sa?".
girgiza kai Dr Adnan yayi,
tareda fadin.
"No yanzu yana buk'atar hutu so bazai yuwu kugansa yauba."
komawa dabaya Hayatudden yayi yajinginu da jikin garu
tareda dafe kansa da yayimasa nauyi, a hankali ya rumtse idonunsa yanajin zuciyarsa nayi masa kuna wasu zafafan hawaye na zubo mishi,
tausayin Hamman nasa dasu kansu yacike ilahirin zuciyarsa afili yafurta.
"Ya Allah kabashi lfy ka d'aga mana kafad'unshi ka rufa mana asiri."
Tare suka fito wurinsu Ummi bayan sun isane.
Dr Adnan yadubi agogon dake daure a hannunsa, kana yadubi Ummi cikin girmamawa yace.
Ummi kuje gida dan dare ya fara nisa yanzu inyaso saimu zauna da Hayatuddeen kafin zuwa goben muga abinda Allah zaiyi,
dasauri Ummi tace.
"A a sudai sutafi ni subarni anand'in nakwana."
Raihana ce tace.
"Ummi muma bazamu iya tafiya ba tareda munga farkawarsa ba."
kai ya jinjina dan yasan dama hakan bamai yuwuwa bane, dan yasan k'auna da shak'uwar da ke tsakanin ahalin,
dan haka saiya kyalesu yace su shiga office inshi, kana shi ya koma office d'in Dr Arabi.
ya rasa meyasa tun d'azu Rahma keta kiranshi gaba d'aya sai ya rasa me zaice mata lokacin daya amsa kiran nata dan a zatonshi ko taji abinda ya farune,
ita kuwa Rahma cikin sanyin jikin da takeji tunda yamma tace.
"Ya Adnan kana lafiya kuwa inata kiranka baka amsawa?."
numfashi ya d'an fidda kana yace lfya lau Rahma meya hanaki bacci har yanzu?."
gyara konciyarta tayi tare da cewa.
"Ji nake zuciyata nata tsinkewa gabana nata fad'uwa shine nace bari in kiraka inji lfyarka."
cikin son sama mata nitsuwa yace.
"Kiyi baccinki ni lafiyata lau, in kuma wani abu kikeso ki gaya min gsky Baby in dawo in miki kona 30 minutes ne in dawo bakin aikina."
cikin jin kunya tace.
"A a ni bance wlh."
da sauri yace.
"Kin ce mana tunda du du du fa bayan sallan isha na baro gida kuma wuni mukayi tare amman yanzu har kwadayinki ya tashi ko?."
da sauri tace.
"A a wlh to kayi zamanka, kaga saida safe."
kafinma yayi mgna ta katse kiran.
Ance bacci b'arawo ne mesace idon kowa,
to yaudai baisami damar sace idanun wanna ahalin ba.
Acan d'aya sashin kuwa cikin New G. R. A.
Hargida police d'in da aka had'ashi da Zaliha yakaita, abakin makeken gate d'in gidansu tatsaya,
kana yafita amotar tayimasa godiya yatari abin hawa yatafi,
dasauri tafita takoma gefen driver tunkan takarasa zama tadanna horn dan har'alokacin amatukar tsorace take,
da gudu maigadi yataho dan jin yadda aketa danna hon ba sassauci da sauri ya wangale mata get d'in,
da sauri ta kutsa hancin motarta cikin farfajiyar gidan nasu da gudu,
asakar farfajiyar gidan tayi parking tafito,
maigadi nakokarin rufe get
wata lafiyayyiyar mota mai azabar kyau da tsananin shek'i ta danno hancinta cikin gidan,
Zaliha kuwa har tajuya zata shige cikin gidan,
ganin shigowar motar yasata tsayuwa, yayinda gaba d'aya zuciyarta da tunaninta ke can wurin kelyawan mutumin daya taimaketan
har aka faka motar tana nazari asannu akabude marfin motar yazuro kafafunsa yafito,da murmushin sa yanufi inda Zaliha take,
itako kwabe fuska tayi tareda langwab'ar dakai gefe,
yakaraso inda take waro idanu yayi ganin galashin motarta afashe cikin mamaki
yace.
"Hatsari ki kayine Zaliha?." cikin muryar shagwaba ta tura baki tare da yarfa hannu tace.
Ya Ahmed ba y'an kalare bane na taddasu a hanyata ta dawowa sunata fad'a shine suka fasamin gilashin mota, badon a mota nikeba nima da sun fasa min kai."
takarasa maganar kamar zatayi kuka dan tausayin Saifuddeen da ta baro suna shirin kashewa,
dasauri Ya Ahmed d'in nata yace.
"Ina dai ke basu ji miki rauniba ko?."
kai tagyad'a masa tare da cewa.
"Amman dai ai sunyiwa motata illa ai."
cikin kula da shak'uwa yace. "To Alhamdulillahi da Allah yasa akan motace ba kan 'yar kekyawar k'anwata aka fasaba,
gobe ida Allah yakaimu zamuji kizabi motar da kikeso.
Amman fa mai sauk'in kud'i Hajia na sanki baki san zafin neman kud'iba sai son ayi ta kashesu ba sassauci."
bayanshi tabi tare da cewa.
"To Ya Ahmed duk yadda kace hakan za'ayi."
shi kuwa Ahmed motar tata ya d'an kalla tare da cewa.
"Wannan d'in za'a gyara sai a saida ta in cikata miki ki samu sabuwa koda wacce bata kai wannanba,
ki samu ta zuwa aiki."
tsalle tarikayi tareda rike hannunsa,
tana fad'in.
"Na gode Ya Ahmed Allah ya k'ara bud'i rabbi ya k'arawa Baba Malam daraja da lafiya da tsawon rai."
murmushi yayi cikin tsananin jin dad'in addu'arta ga mahaifin nasu ya rik'o hannunta suka shige cikin gida.
Wani babban parlour suka shiga wanda yake wadace da tsananin tsabta, wasu manyan kujerune na alfarma ke zagaye da fad'in parlour kana sai wani tattausan carpet mai tsananin taushi sai can gefen dama wasu manyan kanta guda biyu da suke cike da tarin Qura'anai da sauran littafai kama daga na addini dana boko harda su baibul wanda.
sai wani babban tv dake manne da jikin ginin, kana gefen hagu kuma dinning area wanda yasha gyara,
sai kuwa wata kujera dake tsakiyar parlour wacce tafi kama data sarakuna sai wani stoll na glass dake gaban kujerar.
wani dottijone mai tsananin kyau fari k'al k'al dashi yake zaune bisa kujerar nan ta tsakiyar parlour, bisa dukkan alamu alwala yayi yanzu, duk da anyi sallan isha koda yake hakan baya rasa nasaba da kasan cewarshi baya zama ba tare da alwala ba.
zaune yake kana ya mik'e k'afafunshi bisa stoll d'in hannun shi had'e wuri d'aya yana murzasu kana yana d'an karkad'a k'afafun nashi,
a hankali yake motsa labbanshi bisa dukkan alamu tasbihi yakeyi kasan cewa d'abi'arsa ce duk abinda yake bashi hanashi ambaton Allah.
can gefenshi kuwa wata kekyawar matace mai d'an ma dai-dai cin tsawo da jiki, bona ce ta jona jikin soket d'in wuta kana tasa wani turaren wuta mai dad'in k'amshi,
labulayen parlour ta sassake sabida yanayin hazo,
kana ta rage gudun fankan, sannan ta kashe A, C gaba d'aya.
cikin nitsuwa dottijon ya juyo ya kalli k'ofar parlour inda yaji muryar yaran nashi,
amsa musu sallamarsu yayi tare da basu izinin shiga.
a tare suka shigo gabanshi suka zauna cikin cikar tarbiya sukace.
"Barka da dare Baba malam."
cikin son yaran nashi yace.
"Allah ya muku Al'barka."
cikin tsananin jin dad'i Ahmed yace.
"Amin Amin Baba malam mun gode."
murmushi yayi dan yasan yadda Ahmed ke tsananin jin dad'i in ya mishi addu'a,
ita kuwa Zaliha cikin nitsuwa sanin a gaban Baba malam suke ta kalli Hajia Aisha mahaifiyar Ahmed kenan wacce suke kiranta da Mamy, cikin logob'ar da kai tace.
"Mamy yunwa nakeji."
cikin nitsuwarta ta matso inda suke kana tace.
"Ke kinada tsiya ne komai aka dafa kice bai mikiba, sai kije kitchen ki dafawa kanki dan ni dai tuwo nayi."
a hankali ta mik'a tare da cewa.
"Baba malam saida safe."
ido ya d'an juyo ya kalleta kana yace.
"Allah ya bamu Al'khairi kada ki konta bakiyi al'wala da adduba kada kiyita jin kid'e-kid'enan da kike sawa a gidan radionku."
cikin sanyi tace.
"Toh". kana ta juya ta fita.
Ahmed kuwa murmushi yayi sanin an d'aureta tunda an hanata shan kid'a,
nan sukayi ta hira da mahaifinshi da mahaifiyarshi,
ita kuwa Zaliha kai tsaye parlour Mamanta ta nufa,
gefen wata mata mai d'an k'iba da alamun rashin fara'a a fuskarta gefenta ta zauna da gani matar k'abilace ba hausa fulani bace sam bata da fara'a
cikin sauk'e numfashi tace.
"Mama barka da dare."
murya can k'asa a dak'ile tace.
"Sai yanzu kika dawo ko can d'akin uwar taki kika je."
konciyarta ta gyara bisa 2 str kana tace.
"Nida ya Ahmed ne kuma wurin Baba malam muke."
kai ta gyad'a kana tace.
"To tashi kije kici abinci Zulaihat ta muku awaran kuskus."
jin haka ta mik'e da sauri ta nufi dinning table, gefen washing hand baby ta nufa hannunta ta wonke sannan tazo ta zauna tanaci suna d'an hira da Mamansun.
Kad'an ta ci ta mik'e jiki a mace ta nufi d'akinta
tazo gab da bakin k'ofarsu Zaheera taji Zulaihat nata hayaniya alamun tana tarfawa Zaheera rashin kunya,
kai ta kauda ta wuce d'akinta dan bata cikin yanayin jin dad'i bare konciyar hankali.
Tana shiga ta cilla woyoyinta bisa gadonta kana ta zame ta durkusa a k'asa tare da kife k'irjinta bisa gadon pillow ta jawo tare da d'aurashin kanta a hankali ta rumtse idanunta sai kuma tayi saurin bud'esu da sauri sabida ganin tamkar yanzu ake sokawa Saifuddeen wuk'a a bayanshi kife kanta tayi cikin pillow ta saki wani irin zazzafan kuka mai sanyin sauti, ta jima tana kukan a hakan tayi baccin da baifi 45 minutes ba ta fara mafarki tana jujjuya kai da karfi ta saki ihu tare da cewa.
"Mu gudu kada su kasheka kazo mu gudu wayyo ya Ahmed sun kashe minshi."
sai ta kuma mik'e da sauri sabida farkawan da tayi,
kai ta kife bisa gadon tana wani irin kuka mai cike da tausayi da rauni,
sai ta kuma mik'ewa da sauri kai tsaye bathroom ta nufa al, wala tayi kana ta fito nafilfili tayi tayi wanda duk cikin sujjadanta shi take yiwa addu'a ranar da a haka ta kwana batayi bacciba wonkan da yake al'adar rayuwarta ma kafin tayi bacci amman yau bata Toshiba.
Washegari damisalin karfe 6:00 Am, Dr Adnan yafito daga room d'inda Saifuddeen yake,dukda sanyin asuba irinta hunturu dakuma sanyin AC dake zagaye awurin saida Dr Adnan yahad'a zufa sharkaf sabida tashin hankali da fargabar dake tare dashi,
kallo d'aya zaka yimasa kagane tsantsar tashin hankalin da ke shinfide akan fuskarsa cikin mutuwan jiki yayi isa office d'inshi,
Cikin hanzari Ummi dake zaune akan sallaya tana jan jarbi,
tamik'e tsaye tana mai zuba mishi ido tare da fad'in.
"Baban Adnan yafarka kuwa?."
saurin sai-sai ta nutsuwarsa yayi dan son boye tashin hankalin da yake ciki kana yace.
"Ehm Uhmm ba..ba..bakomai fa Ummi in sha Allah zai farka in Allah ya yarda ba wata matsala."
ita kam Ummi cikin rashin gamsuwa da maganarsa tafara magana cikin zubda kwalla tanafadin,
"Ka fad'amin halin da yake ciki in yamutune ma kada ka boye min dole inyi imani da k'addarata."
da sauri su Raliya dasuke zaune agefe suma bayan sun idar da sallah suka taso.
Hayatuddeen dayanzu dawowarsa daga masallacin dake cikin asibitin,shima ya'iso da sauri,
ganin haka yasa Dr Adnan cewa.
"Ummi baifa mutuba zo kuganshi ma."
kana ya juya yayi cikin room d'in dasauri suka rufamasa baya,can suka hangosa kwance ga na'urori sakale ajikinsa
da sauri suka nufi jikin gadon,idanunsa arufe ruf bayako motsi, abinda zainuna maka cewa yanada rai shine numfashin shi da yake ja tacikin na'uwar jan numfashi.
cikin rauni da fargaba jiki na rawa Ummi tariko hannunsa yayinda hawaye ke kwaranya a idanunta murya na rawa
tace.
"Saifuddeen wanene yayimaka wanna illa haka? waya zalincemu zalumci mafi muni arayuwar mu? memuka tare masa?."
a tare tajero tanbayar tareda kife kanta ajikin gadon ta saki sassanyan kuka.
Hayatuddeen,da shima kukan yake ganin dan'uwansa acikin mawuyacin hali,
Raliya Raihana duk kuku suke,
Dr Adnan ma shima kukan yake babu mai rarrashin wani a cikin su zuwa can Dr Adnan yashare hawayen sa cikin hanzari yamaso kusa da Ummi muryarsa narawa ya kwakulo murmushi dole yace.
"Ummi bawata masalafa ku kwantar da hankalin ku in sha Allahu zamuyi duk abinda yadace."
cikin muryar kuka Ummi tace.
"Adnan duba kaga halinda Saifuddeen yake cikifa sannan kace wai babu wata damuwa,
ka duba ka gani nice yau a gaban Saifuddeen amma yagaza d'aga ido yadubeni bare harya shiga farin ciki kamar kullum saboda ganina akusa dashi,
lallai Saifuddeen d'ina yana cikin mawuyacin hali."
sai ta kuma rik'e hannunsa tamatse acikin nata tanamai cigaba da kukan,
da sauri Dr Arabi yaturo k'ofar da sauri dan duk abinda suke yanajinsu daga cikin offece insa,ya'isa ciki tareda d'aura wata na'urar dake rike a hannunsa asaman kirjin Saifuddeen dan da alamun bugun zuciyarshi ta tsananta da sauri
yace.
"Ummi ku d'an je waje zamuyi aiki yanzu."
dakyar Ummi tasaki hannun Saifuddeen ta fita tana cigaba da sharar kwalla,
su Raliya ne sukabi bayanta.
Hayatuddeen ko wayar Saifuddeed ya d'auka wanda yagani agefensa sanna yafita, sunafita Dr Arabi yahad'a na'urar daya d'aura kan kirjin Saifuddeen,
kana ya juyo yana fuskantar Dr Adnan tare da cewa.
"Haba Dr Adnan a matsayin ka na Dr bai kamata karika kashewa majin yatanka guiwaba,
kamata yayi karika karfafa musu goiwa surika sawa aransu majinyacinsu zaisami lfy,
amma kaima kazauna agabansu kana zubda hawaye ai sai ka saka musu kokwanto azukatansu,
tabbas nasan shakuwar dake tsakanin ka da Saifuddeen,
so hakuri zakayi kabasu kwarin goiwa akan samun saukinsa sai kaga komai yatafi dai-dai."
a hankali Dr Adnan yashare hawaye kana yace.
"Hakane amman kaima kasan dai akwai babbar masala,
bazan tab'a iya mik'ewa ya tsaya da kansa ba,bazai iya morar kansa ba,
saboda illar da suka yimasa agadon bayansa zuwa kugunsa,bansan tayanda zansanarwa Ummi wanna mummunar labarin ba"
a hankali Dr Arabi yace. "Nasani,to amma ya zamuyi da ikon Allah, shi ya halicci Saifuddeen kuma ya fimu sonshi kuma insha Allah shi zai zama gatanshi,
yanzu dai ya kamata musan menene mafita."
shiru Dr Adnan yayi saboda tunanin hanyar data fi dacewa don dole a wuce da Saifuddeen Abuja.
Koda Hayatudden yafita Gefe yakoma yazaro wayarsa a'al'juhu dan tun jiya yake akashe yakunna sanna yasaka wayar Saifuddeen acikin aljuhun,
bayan yakunna wayarsa saiya lalub'o number Ishaq wato babban abokin Saifuddeen,
yana d'agawa yace.
"Hello Hatuddeen yau kuma gaisuwar sassafene za'ayiwa Hamma Ishaq."
cikin raunin murya yace.
"Ina kwana Hamma Ishaq."
da sauri yace.
"Lafiya lau, Hayatuddeen."
bayan sungaisanne Hayatuddeen yake ce masa. "Hamma ishaq muna asibiti Hamma Saifuddeen bashida lfy."
ba k'aramin tashin hankali Is'haq yashiga ba dajin cewa abokin sa na'asibiti wanda jiya da yamma suka rabu lafiya-lafiya sannan kuma yanada tabbacin cewa bakaramin ciwo bane zaisa Saifuddeen yakwanta a asibiti.
shiko Hayatuddeen katse wayar yayi yakoma inda su Ummi suke,
jugum-jugum sukayi kowa da abinda yake sakawa azuciyarsa.
sunan zaune har gari yayi haske.
Karan ababen hawane yacika cikin harabar asibitin motoci da mashunan guragu irin masu tsada da kyau wanda zasu iya kaiwa 23 kana sai wasu motoci kusan guda 6 wanda sukeda tambarin (Jonapwd) Gombe state chapter all the best! bi ma'ana tambarin k'ungiyar nakassasu ta jihar wato Joint national association of persons with disabilities.
kuma kowani mashin guda mutane biyu ne ke kansa,haka sukarika faka mashin d'in suna sauka akansa,abin mamaki mutanen duk nakasassune,
sai dai bazaka tab'a banbance makafin cikiba domin babu sanduna a hanunsu bare yan jagora kana suna cikin tsabtacecciyar shiga ta alfarma mafi akasarinsu sunfi kama da ma'aikata, kuramen ciki kuwa bazama ka tab'a zaton sunada wata nakasa a jikinsu ba, guragu kuwa sai dai ka gane da sawun wasunsu da suke a shanye wasu kuma da sanduna suke dan tokarawa gaba d'aya sun cika harabar asibitin kuma ba hayaniya bare sowa suna komansu cikin tsari da wayewa fiyema da masu ji da gani yayinda wasu ke ambaton.
"Ya Allah! kabaiwa d'an uwanmu Garkuwarmu lfy,
idan kacire manashi a cikinmu bamu san ya zamu k'are da rayuwaba dan munsan cewa zamu tagayyara mudawo abin kyama abin gudu acikin al'umma sunai mana kallon wasu hallitu na daban." makafin cikinsu nata fad'in. "ku kaimu inda yake?."
Mutane sukarika fitowa daga cikin asibitin, wad'anda suke gefe da asibitin wato mazauna gefen asibitin suma suka shisshigo,danganin taron mutanen dasuka shigo cikin asibitin.
Dan ganin abinda kefaruwa,jama'ar dasuka fito dan kallon mutanen sunsha mamakin jin kallama da ya kefita abakin wadanna nakasassun,sai ambaton Saifuddeen suke,
jama'a duk suka cika da alhinin jin sunan wanna bawan Allahn dasuke ammaba,to waye shi dahar wadanna mutanen zasu nuna damuwarsu da tashin hankalinsu akansa,lallai wanna mutumin komai akayi adaline,sosai a garesu domin wasuma sunyi zaton ko zanga-zangar lumana nakasassun keyi,
gurin ya kacame da hayaniyar mutane dake tambayar meke faruwa.
Hayatuddeen ne yamik'e tsaye da sauri yace.
"Ummi mutanen Hamma Saifuddeen ne sukazo dan naji sunata kiran sunansa bari naje wurinsu."
kai kawai Ummi ta'iya gyad'a masa alamar toh.
Hayatuddeen yafito farbajiyar asubitin suna ganinsa suka nufi inda yake suka zagayeshi,suna fadin.
"Ina Saifuddeenin d'inmu yake kanunama inda yake."
hannu sa yad'aga sama yana juyashi, tare da yin sauri ya isa gaban Ishaq cikin girmamawa yace.
"Ya ishaq barka da zuwa."
da sauri ishaq ya mik'o hannu ganin haka shima Hayatuddeen ya mik'o mishi hannu tare da cewa.
"Gani nan Ya ishaq."
da sauri ishaq yace.
"Yauwa Hayatuddeen ta ina Saifuddeen yake muje mu ganshi."
cikin d'an murmushi Hayatuddeen yace.
"Hmmm kai ishaq kullum lamarinka akwai k'arfin hali da iya ruggumar k'addara wai muje mu ganshi sai kace kana gani."
shima Ishaq murmushi k'arfin hali yayi tare da cewa.
"ai ba idone gani ba, ku masu idone kuke d'auka da ido kawai ake gani, mu kunnuwanmu ma tamkar idone kana da zuciyarmu da k'ok'wolwarmu, yayinda kuramenmu kuma idanunsu ne kunnuwansu, ba gashi yanzu koda bana ganinka nasan kana zubda hawaye daga sautin muryarka."
cikin sanyi Hayatuddeen yace.
"Ku kwantar hankalinku,
ku dakata dan Allah kuyi hakuri yanzu bazaku sami ganin saba dan yasamu yin bacci saidai zuwa anjima."
cikin gamsuwa sukace.
"To yajikin nasa?."
saida ya maida hawayensa dake kukarin zubo masa dagudun kada hankulansu yatashi,danyasan cewa basu kadai ahalinsa kebukatar Hamma Saifuddeen ba, hardasu wadanna nakasassun,dama wasunsu baki d'aya,.
"Da sauki". yace dasu atakaice,
dakyar shugabannin nasu suka samu suka lallab'asu sukatafi,sanna shikuma Hayatuddeen yayiwa su ishaq d'in iso zuwa ciki inda su Ummi suke.
Suna shiga Dr Adnan nafitowa,
kana Dr Arabi nabiye dashi su Ummi naganinsu sukamike tsaye suka k'araso inda suke,Ummi kallonsu take fuska kunshe da tanbayoyi
Dr Arabi yakalli Dr Adnan wanda keta noke-noke yayi masa alama da ido,
jiki asanyaye Dr Adnan ya mik'awa Ummi wata doguwa takarda fara yace.
"Ummi wanna takardar ta transfer ce zuwa Abuja,
naturaku asibitin kimiya dake birnin tarayya Abuja National hospital Abuja
,idan kun isa saikiba su wanna takardar
da sauri Ummi tace.
"Abuja! Kuma?."
kai ya gyad'a mata alamar eh,
a hankali tace.
"Lallai ciwon Saifuddeen babbane tunda har katuramu Abuja."
Kai Adnan ya girgiza dasauri,dan bazai iya fad'a mata akwai masala ba, yafiso sai sunje can d'in asanar musu.
tana karbar takardar yayi saurin juyawa dasauri dan gudun kada Ummi takuma jefo masa wat tanbayar,
yanafita yayi duk wani cuku-cukun dayadace natafiyarsu ba tareda bata lokaciba yakammala komai bank'arensu.
Ishaq kuwa takardar ya amsa kana suka juya tare da Raihana, kai tsaye Federal low cos suka nufa,
E passport d'in Ummi da Saifuddeen dana Hayatuddden yasa Raihana ta kawo mishi,
daga nan direban k'ungiyar tasu yaja suka wuce Airport, nan ya gama musu dukkan shirin tafiya hardashi d'in suka kuma yi sa'a akwai jirgin da zai tashi zuwa Abuja k'arfe biyun rana zai tashi.
1:53 pm duk sun gama shirin komai,
takofar baya Dr Adnan yashiga yaturo gadon yafita takofar bayan,
Dr Arabi natsaye ajikin motar da zai kaisu airport da taimakon sa suka tura gadon cikin motar suka dai-dai zaman gadon sosai acikin motar,
Kana Dr Adnan yakoma indasu Ummi suke yace.
"To Ummi an gama shirya komai shirya komai ku akejira yanzu,
sanna kuma tafiyar zai kasance dole damutun biyune sanna kuma... da sauri Raihana tace.
"Ummi ku kutafi keda Hayatuddeen, mu zamu koma gida nida Raliya fatanmu samun saukin Hamma Saifuddeen zan kira Abban Farida yayi k'ok'arin dawowa,."
cikin gamsuwa Ummi tace. "to".
"kuyi maza kutafi nima zuwa gobe da yamma zan shigo Abujan."
Dr Adnan ya fad'i tare da juyawa yayi gaba,
da sauri suka bishi abaya.
koda suka'isa jikin motar, Ummi da Hayatuddeen suka shiga,driver yatada motar Raliya da Raihana nad'aga musu hannu dayimusu fatan samun nasara,yiyinda dukansu suke ta sharar kwalla,driver yaja sukabar harabar asibitin,
"Sukadau hanyar Airport, in da tuni ishaq na can su kawai yake jira.
suna isa bada jimawa ba jirginsu ya tashi.
3:00pm yamusu a cikin birnin taraiya Abuja direct National hospital suka nufa.
Kasancewar duk abinda yadace Dr Adnan yarigada ya'aiwatar dashi ta online , so ansan da zuwansu,basusha wani wahalaba,suna isa nurses suka taho jikin motar data d'aukosu daga airport nan suka fito dashi.
Kana Ummi
tamikawa d'aya dagacin nurse d'in takardar da Dr Adnan yabata,sanna suka turoshi sukashiga cikin asibitin, direct Emergence room aka shige dashi.
Nan Doctors suka dukufa akanshi basu yi wata-wata ba suka fara bincike akan laluransa kamar yanda yazo musu arubuce,
cikin k'ank'anin lokaci S.....!
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: [3/30, 10:50 AM]
ðŸ“ÂðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
*NAKASA BA KASAWA BACE*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.