Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt
Chapter 3 of 27
*PAGE 3*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
_Wannan page É—in nakune gaba É—ayanshi Æ´an Hukuncin Allah fans Especially Mom Asas, Zee Ya'u, Jannart Salis, ina muku fatan al'khairi._
~Gareku masu buƙatan biyan kuɗin littafin ,turo katin mtn na ɗari uku, ta wannan layin 09097853276 ko transfer ta nan 0005388578 jaiz bank Asha Aliyu Garkuwa~
Cikin tsananin razana da tsoro jiki na rawa mai jan motar ya fara kiciniyar taka birki.
Amman ina abin ya gagara, tuni birkinta ya kubce mishi, ido ya zaro da sauri lokacin da yaga motar tashi ta nufi kan Nuruddeen gadan-gadan
ji kakeyi k'uuuuuiyyyyhh.
motarnan ta bugu machine d'in Nuruddeeen bugu mai tsanani wanda yasa, Nuruddeen yayi tsalle yayi sama kana ya fad'o kan bump d'in tsakiyar titin,
"Innalillahi'wa'illaihi rajiun. Hasbunallahu wani'imal wakil."
Shine abinda tarin mutanen dake zageye da Nuruddeen suke fad'i,
yayinda wasu suka ma kasa mgna sai d'aura hannu sukayi a kai, kana wasu sai jujjuya kai sukeyi.
mai mota kuwa da ker ya samu ya fara sarrafa motar har ya samu ta tsaya,
yana fitowa da gudu ya nufi inda dandazon mutanen suke,
kutsawa yayi tayi tsakiyar mutanen har ya samu ya isa,
ido ya rumtse da k'arfi cikin tsananin fargaba ya sunkuyo kan Nuruddeen da yake konce lib bisa titi, ida nunshi a rufe kirib sai numfashin shi dake korar juna,
da sauri ya tallaboshi tare dagowa ya kalli mutanen cikin tashin hankali yace.
"Ku taimaka min mana in d'agashi in sashi a mota."
wani k'ak'k'arfan matashi ne,
yayi maza ya sunkuyo ya ciccibi Nuruddeen kana cikin, d'aga murya yace.
"Biyoni."
yana fad'in haka ya juya ya tsallaka titin zuwa d'aya hannun kana ya nufi cikin asibitin MUSABA dake fuskantar tashan Dukkun,
cikin rawan jiki mutumin ya mik'e kana yabi bayanshi.
suna shiga Reception suka nufa,
ganin sun shigo hajaram majaram yasa Nurse's yin kansu da tambayar meke faruwa,
cikin kad'uwa mutumin nan yace,
"Accident ne ku taimaka doctor ya dubashi."
juyawa sukayi suka kalli juna, kana d'aya daga cikinsu tace.
"Ko an gayawa doctor bazai dubashi ba sai an nemo police."
jin haka yasa mutumin nan juyawa da sauri ya fita,
gudu-gudu sauri-sauri ya tsallaka titin kana ya nufi wurin motar tashi, yana shiga ya nufi Gombe division yana zuwa ya musu bayanin abinda ke faruwa,
ba b'ata lokaci suka had'ashi da police d'aya, kana suka tafi tare,
suna zuwa Doctor in ya amsheshi bisa sa hannun hukuma kana fara bashi taimakon gaggawa, sannan daga bisani ya ce su tafi Medical Center.
Ba b'ata lokaci suka amshi shawararshi suka tafi can,
suna zuwa aka amsheshi.
shi kuwa police yasa d'aya police d'in yaje ya d'auki machine d'n nashi ya kaishi officensu.
kana sun samu wayarshi y'ar Nokia dake jikinshi tanan aka kira Bappa Ali aka sanar mishi meke faruwa.
Lokacin da aka gayawa Bappa Ali yana cikin garin kurugu da yake ranar larabace,
to yaje cin kasuwa,
ana gaya mishi bawan Allah ya bar duk abinda yakeyi ya nufi cikin Gombe kai tsaye Medical Center din ya nufa, inda yana zuwa fargabarshi ta k'aru domin tunda Nuruddeen ya fad'i bai sake bud'e idanunshi ba kuma uwa uba yana konce tamkar gawa komai sai an mishi ga roba a hanci da baki da k'asanshi wannan abu yayi matuk'ar firgitashi, duk da k'arfin zuciya irin na bappa Ali sai da yayi ta kuka,
mutumin daya bugi Nuruddeeen ma sai kukan yake sabida kukan da Bappa Ali keyi ya matuk'ar karya mishi zuciya sai hak'uri yake bashi da neman yafiyarsu.
Cikin raunin murya yake cewa.
"Ku gafar ceni tsautsayine, nayi iya k'ok'arina inga na tsare motata bataje ta bugeshi ba amman ina Allah ya k'addara faruwar hatsarin bani da tsumi ko wayo bare k'arfin hanawa."
sai ya kuma sharte hawayenshi kana yaci gaba da cewa.
"Tunda nake ban tab'a shiga cikin tashan Dukku ba, sai yau, ashe ashe ban saniba masifa ke kirana."
shi kuwa Bappa Ali ya gaza cewa komai domin da ganin mutumin ya girmeshi kuma bisa dukkan alamu mutum ne mai daraja da ka ganshi kasan mai kamalane,
shi kuwa mutum shirun Bappa Ali sai ya sa mishi rauni yana ganin shike nan ya cucesu,
yana bashi hak'uri yana tuno dalilin zuwanshi tashan,
dan matarshi da ta kasance yar Ngalda to kullum shi ke kaita to yau kuma har ya shirya zai kaita sai kuma motocin kayanshi suka iso, so shiyasa yace bari ya kaita tasha ta shiga motar kasuwa, to shinefa ya kaita kenan yana fitowa wannan hatsarin ya auku.
Bappa Ali kuwa ganin yanata bashi hak'uri ya sashi yin k'arfin halin cewa.
"Ba komai Allah ya bashi lfy, ai shi tsautsayi ba ta inda baya wakana."
sosai mutumin ya d'anji sanyi kana yace.
"Wacce uguwa kuke ne?."
cikin sanyi Bappa Ali yace.
"Har Dukku muke."
da sauri yace.
"Ina mamanshi?."
kai ya jinjina kana yace.
"Mamanshi da babanshi duk basu saniba, suna Dukku ni kuma dama ina Kurugu to da aka kirani sai na taho nand'in.
Yanzu in ba matsala in akwai masu kula dashi zan wuce Dukku inje in sanar musu."
cikin kad'uwa yace.
"To kai waye d'inshi ne?."
"Ni bappanshi ne k'anin mahaifinshi kuma mahaifin nashima baida lfy."
kai ya jinjina kana ya zaro kud'i a aljihunshi sannan ya mik'a mishi tare da cewa.
"Ba matsala zan kula da komai kayi maza kaje ka sanar musu."
k'in amsar kud'in yayi, shi kuwa mutumin ya sashi karb'a a dole.
Haka dai ya amshi kudin badon ya soba ya tafi,
shi kuwa mutumin shida kanshi ya zauna wurin kana ya bada duk abinda ya dace na jinyar Nuruddeen.
Shi kuwa bappa Ali daya koma Dukku jiki a mace yayiwa Ummi bayani sai dai ya boye mata hak'ik'anin halin da Seyojinta ke ciki, yace mata da sauk'i sosai baiji ciwoba an dai mishi allurar bacci ne dan ya huta.
To shiyasa hankalin ta bai tashi sosaiba,
Saifuddeen kuma tun lokacin da Yayan nashi ya tafi sai yaja hannun Hayatuddeen suka tafi gidan Goggo Dada, to shiyasa bappa Ali bai tarar dashi a gidaba,
kuma gidan Goggo Dada nada d'an nisa don ita a Shabewa take.
Abba kuwa baida lfy ba damar yaje,
haka yasa Bappa Ali ya juya shida Adnan babban abokin Nuruddeen d'in,
kana sai Rahma.
Koda sukaje gaba d'aya hankalinsu ya tashi ganin yadda Nuruddeen ke kwance tamkar gawa Rahma tayi ta kuka tamkar ranta zai fita,
Adnan yanata rarrashinta,
Bappa Ali kuwa mutumin ne keta rarrashinsa.
Ganin dare ya fara nisa yasa Bappa Ali cewa Rahma ta koma dan har takwas na dare yayi,
jin haka yasa mutumin nan k'iran d'anshi mai suna Arabi yazo.
Kana yace ya maidata Dukku da motar da yazo,
ba musu ya d'auki Rahma ya maidata Dukku,
yana ajeta ya juyo Gombe.
Ita kuwa Rahma jiki a mace ta shiga gida,
Ummi dasu Saifuddeen da Abba dasu Raihana suka tasats a gaba da tambayar ya jikin nashi.
sanin in ta gaya musu gskyar halin da yake ciki ba mmki jikin Abba ya tashi, Ummi ta k'ara shiga damuwa dan haka sai tai ta ce musu jikifa da sauk'i,
koda Ummi ta bata abinci sam ta kasa ci, sai hawaye da take zubdawa time to time, kana tana sa hannu tana goge hawayen dan kar Ummi ko Saifuddeen su gani dan sam ta lura hankalin su a tashe yake.
haka dai sukayi ta jimantawa juna kana sukayi shirin bacci da nufin gari na wayewa Ummi da Saifuddeen zasu shirya suje.
Rahma kuwa har ta konta Ummi ta kuma biyota d'akinsu tana k'ara tambayar yanayin jikin nashi nanma dai boye mata gskyar tayi.
a haka dai suka kwana da fargaba.
A can Gombe kuwa k'arfe d'aya dai-dai na dere Nuruddeen yace ga garinku,
Allah sarki rai bak'on duniya,
bayan likitan ya sanar musu ya cika,
Bappa Ali kam sai ya rasa inda zaisa ranshi kawai sai ya shiga d'akin da gawar yake yayi ta zagaya gadon yana wani irin azabebben kuka maicin zuciya da tada hankalin mai sauraro,
Adnan kuwa kanshi ya kife gefen kan Nuruddeen yana wani irin sassayan kuka mai zazzafan hawaye,
hakan mutumin nan tunda aka gaya musu ya zame a wurin ya zauna bisa kujera yana kuka mai ban tausayi yanayi yana tasbihi da hailala,
sabida hankalin shi yayi matuk'ar tashi tunda yasan shine sanadin mutuwarshi.
Bayan an d'auki gawar an kaita macuwari,
su kuwa duk su uku sai suka nufi masallacin dake cikin asibitin bayan sunyi al'walane suka fara nafifili da k'auna Qur'an tare da yimishi Addu'a.
Koda gari ya waye mutumin nan yayi duk kan abinda ya kamata kafin a basu gawan,
Aka yi mishi wonka aka shiryashi kamar yadda musuluncin ya tanadar mana,
bayan an gama kimtsashi ne, suka barshin nan cikin asibitin tare da Adnan kana shi kuma ya d'auki bappa Ali ya nufi gidanshi dake Fantami,
nan ya sanar musu abinda ke faruwa,
kana ya fara gaiyatar jana'izar,
bayan ya gama abinda ya sauwaqa sai kuma suka nufi Dukku.
Suna isa sukayi cikibus dasu Saifuddeen da Ummi da suke shirin tafiya yanzu.
ganin Bappa Ali da wani mutum a cikin zazzafar mota yasa zuciyar Ummi karaya,
sai tayi maza ta koma cikin gida,
yayinda Saifuddeen kuma ya zubawa Bappa Ali idanu tamkar zai mannasu a jikinshi duk sun kasa yin Magna tuni mak'ota sun taru a wurin anata tambayar jikin Nuruddeen,
amman ba mgna Bappa Ali sai jujjuya kai yakeyi yayinda mutumin nan kuwa yaketa zubda hawaye,
ganin haka duk aka gane cewa Nuruddeen baya raye.
Ita ku Ummi tana shiga cikin gida da sauri Rahma dasu Raihana sukace.
"Ummi meya faru." duk da taji abinda sukace amman ta kasa mgna sai nufar inda Abba ke zaune tayi yayinda shi kuwa yayi mutuwar zaune,
cikin rawar murya tace.
"Bappan Saifu ne ya dawo shida wani mutum."
wani irin zabura Abba yayi sai ya kuma koma ya zauna da sauri sabida azabar da yaji mak'ogoronnshi na mishi.
Dai-dai lokacin kuma Bappa Ali da mutumin nan suka shigo,
gefen Abba suka zauna kana Ummi kuwa ta matsa can gefe ta zauna bisa kujera yar tsuguno gaba d'aya jikinta tsuma yake zuciyarta na harbawa da sauri-sauri,
shi kuwa Abba ido ya zubawa mutumin da ya tasashi gaba yana kuka da shesshek'a a hankali,
cikin firgita da rauni murya can k'asa Abba ya kalli k'anin nashi da matarshi da yaranshi baki na rawa yace.
"Innalillahiwa Inna'ilaihi rajiun."
sai ya kuma rumtse idanunshi wasu zafafan hawaye ne suka kwaranyo mishi masu tsananin k'una murya can k'asa yace
"Mutuwa ta barni ta d'auke Seyo na ko?."
cikin zubda kolla bappa Ali ya gyada mishi kai,
ido ya rumtse kana yayi murmushi tare da cewa.
"Hmmm Seyo na ya tafi ya barni! nasan nima bazan kai bad'i iwar hakaba, zan bishi zanbi bayanshi, Aliyu na tausaya maka zan tafi in barka da nauyi,
Saifuddeen zai d'auki nauyin da shekarunsa basu kai ya d'aukaba."
kawai sai suka had'e kai suna kuka,
hakama su Raihana da Raliyya da Hayatuddeen Amman Ummi da Saifuddeen da Rahma sun gaza kuka domin ance wani zafin ya wuce inda hawaye yake.
Mutumminan kuwa shima kuka yakeyi cur-cur da hawayenshi yana basu hak'uri.
Ita kuwa Ummi wani abu mai tsananin k'arfin taji ya tsoki k'afon zuciyarta ya danne kukan da takeji tana son yi,
hakama Rahma sai d'anta Faruq daya tasa a gaba yana kuka ita kuwa sai dafe zaciyarta dake barazanar tarwatsewa tayi kana zuba musu idanu tamkar zautacciya.
Aunty Nina kuwa matar bappa Ali fargaba yasa cikin jikinta b'arewa.
Saifuddeen kuwa Allah ne kad'ai yasan abinda yakeji a ranshi, in ya kalli Ummi da Rahma ji yakeyi tamkar zai fad'i ya mutu dan tsananin zafin da k'una da zuciyarshi ke mishi.
shi ko Abba yunk'ura yayi a hankali ya tashi kana ya kalli k'aninshi yace.
"Ina gawar take?."
cikin tausayawa mutumin nan ya mishi bayani kana duk masu zuwa jana'iza a dauko motocin a tasha ya biya kudinsu,
nan aka dugguzuma aka nufi Gombe.
bayan sallan azahar aka sallaci gawar, sannan akaje aka binneshi,
motocin nan suka jidi mutanen Dukku suka meda su, kafin su dawo duk yan uwa da abokan arzik'i an hallara tuni Goggo Dada ma da tazo,
dama Ahmad da babanshi kam dasu akaje gombe.
Nan sukayi zaman makoki na kwana bakwai,
mutumin nan shima yayi zaman makoki a gidanshi na tsawon kwana uku,randa akayi sadakan bakwai yaje Dukku ya k'ara basu hak'uri,
nan sukace sun yafe, domin k'addarace ta rigayi fata sannan shi kuma yayi musu al'khairi sosai dan harda kayan abinci ya kawo musu
tuni kuma ya fara azumi settin d'in da zaiyi.
Rayuwa dai taci gaba da tafiya a haka.
Yau da dad'i gobe akasin haka.
Abu da dama ya faru cikin watanni ukun nan.
Bayan wata uku
Ranar wata asabar bayan sallan magrib,
duk suna tsakiyar gida, Ummi ta tasa Rahma dasu Raihana da Raliyya suna d'an hira,
Saifuddeen kuwa da Hayatuddeen suna gaban Abba.
mik'ewa Abba yayi kana ya kalli Ummi da yaranta da suke shawarar a saida kayan d'akin Rahma a kaishi asibiti ai mishi aikin mak'ok'on .
murmushi ya d'anyi kana ya d'auki butar dake gefenshi tare da nufar hanyar ban d'aki yana mai ce musu.
"Uhumm Rahma kenan, kada ku yarda ku saida wani abunku a kaina fa, domin wannan ciwon nawa tabbas wata rana shine ajalina."
d'an tsayawa yayi jin Rahma na cewa.
"Dan Allah Abba kayi hak'uri mu kaika asibiti, bazamu iya ganinka hakaba."
murmushi ya kumayi kana yace.
"Rahma iyayena mafa haka sukayi ta nema min mgni k'arshe har suka rasu ban samu lfy ba, hakama k'annena gaba d'aya Ali ya saida gonakinmu da filayanmu na gado,
a kan nema min mgni yanzu du-du du gonaki ukune suka rage sai wannan filin da ke can bayanmu wanda shi kuma dama nine na sayeshi da sunanku.
dan haka ku dena wahal da kanku ai sauk'in yazo."
yana fad'in haka ya juya ya nufi bayan gidan,
a dai-dai bakin k'ofar ya fad'i.
Wanda kafinma a d'agashi ya cika.
Wannan rana anga tashin hankalin wannan ahlin,
dole Abba kwanan keso yayi,
washe gari da hantsi akayi mishi sutura, wanda tuni k'ofar gidansu ta cika da al'ummar annabi.
Bayan an mishi sutura an kimtsashi kamar yadda musulunci ya koyar damu
anzo za'a d'auki makar ne za'a fiddashi.
da sauri Bappa Ali ya kalli Saifuddeen daya rik'e makarar yanayin wani irin kukan da yasa dukkan bani adam dake wurin zubda zazzafan hawaye,
tuni shima Bappa Ali sai ya zame kana ya ruggumi Saifuddeen da Hayatuddeen dake ruggume dashi, kuka sukeyi wanda duk kan mai imani zai tausaya musu.
shi kam Saifuddeen duniya ta mishi zafi ji yakeyi tamkar bai tab'a farin cikiba, fata yake inama shima mutuwar tazo ta d'aukeshi.
tausayin kanshi da mahaifiyarsu da k'anneshi da yayarshi yakeji tamkar zai d'auke numfashi sa.
Man Liman ne suka janye bappa Ali kana Baba Hamisu yasa hannu ya janye hannun Saufuddeen daga rik'on da yayiwa makarar.
Baba Ashiru kuwa da wani abokinshi wanda kuma malamin islamiyarsu Saifuddeen ne sune suka kamashi ganin yanayin da yake ciki,
cikin sanyi Baba Ashiru ya cewa Hayatudden.
"Deen je ka kawo min ruwa.
cikin kuka ya mik'e kana ya kawo ruwan amsa yayi kana ya kalli Saifuddeen da idanunshi sukayi jazir tamkar zasuyi aman wuta, ganin bazai k'arb'a bane yasa Malaminshi amsar ruwan ya kai mishi har baki,
kana cikin sanyin murya yace.
"Saifuddeen kasha ruwa zakaji sanyi a ranka."
a hankali ya fara shan ruwan domin jin zuciyarshi yake tamkar ana soya mishi ita,
ajiyan zuciya ya rink'a sauk'ewa akai akai kana hawayenshi suka tsagaita,
Ya Nuruddeen d'inshi ne ya fad'o mishi a rai, tabbas da yana raye da bazai bari kukansu ya tsanantaba,
wani numfashi yaja kana ya kalli Malamin nashi da yake ce mishi.
"Tashi muje woje Saifuddeen muje ka tsaya a sallaci gawan mahaifinka,
kayi mishi addu'a a madadin kukannan da kake mishi, ka sani dukkan tsanani yana tare da sauk'i in sha Allah muna zatawa d'an uwanka da mahaifinka rahama, kada kayi musu kuka domin su mutanene na gari musu imani da tawakkali basu da abakan musu bare na fada ko gaba,
ka sani babu maraya sai rago, kuma nakasa ba kasawa bace.
Kada kayi ta kuka domin kukanka shi zaisa yan uwanka kuka, kuma kukanku shi zaisa mahaifiyarku kuka har ta kai ga ta kamu da wata cutar ka daure ka jumre ka zama Garkuwarsu."
Cikin tsanani rauni ya mik'e tare da yi mishi alama da yaji zai bari,
daga nan sukaje suka sallaci gawar kana aka kaita makwancinta.
Nan aka zauna zaman makoki.
Yau akayi sadakan Uku, duk da haka Bappa Ali dasu Malam Ashiru da Baba Hamisu dasu Saifuddeen d'in suna zama dan akwai masu zuwa gaisuwa.
Bayan sallan azahar ne duk suna zaune a gindin bishiyar limis dake harabar massalacin k'ofar gidan nasu,
wasu maza su uku sukazo wanda kusan abokan Abban ne bayan sun gaisa ne d'aya daga cikinsu ya zurawa Saifuddeen idanu yana kallonshi ido cikin ido,
shi kuwa Saifuddeen bai kauda idanshi bane dan ganin mutumin yana jujjuya kai alamun zaiyi mgn to sanin in ba kallon bakinshi yakeyi ba bazai gane abinda yake fad'anba shiyasa ya tsurawa mutumin ido,
shi kuwa mutumin cikin jujjuya kai yace.
"Allah sarki duniya mutuwa bata zabi,
Allah bai barin wani dan wani yaji dad'i."
sai ya kuma kalli su Bappa da Malam Ashiru da suke jinjina kai sannan ya meda hankalin shi ga Saifuddeen tare da cewa.
"Da ana bawa mutuwa zab'i ai da an bata zab'i ta d'auke wannan nakasasshen ta bar Nuruddeen da shike kula da rayuwar k'annenshi."
da sauri su Bappa Ali suka zaro ido tare da cewa.
"Subahanallahi Mala Bala wannan wanne irin mugun furuci ne?."
kai jinjina musu tare da jaddada musu cikin rashin iya mgna yace.
"A ai gsky ne Malam Ashiru shi wannan dame zai amfani kanshi ma bare ya amfami wasu,
yaron dashi da dutse bashi da banbanci ai su Rahma sun tagaira da mutuwa ta d'auke Nuruddeen ya bar musu mara amfani,
ko su da kansu ai zasuce da mutuwar ta had'a uban nasu dashi wannan kurman ta yashe su ta bar musu Nuruddeen."
cikin tsananin b'acin rai Malam Ashiru yace.
"Kai tafi daga nan gaisuwa kazo ko cin zarafi?."
Bappa Ali kuwa ya gaza cewa komai sai idanu ya zubawa Saifuddeen wanda ya rumtse idanunshi da tsananin k'arfi dan azabar b'acin ran kalaman da Mala Bala ya mishi gashi abokin mahaifinshi ne ba daman ya mishi wani abun.
Sauran abokansu biyun da suka zo tare da Mala balanne suka mik'e cikin jin haushin kalamanshi suka sallami su bappa Ali tare da basu hak'uri sannan suka tafi.
A daran wannan ranar Saifuddeen yayi kukanda bai tab'a yiba,
inda yake ganin inama shi mutuwar ta d'auke ta bar Ya Nuruddeen d'inshi a ranar mutuwar ta dawo mishi sabuwa a ranshi,
tausayinsu Rahma da Ummi ya hanashi sukuni ya zaiyi ya kula da rayuwarsu? haka dai kwanaki sukayi ta tafiya
Randa akayi sadakan bakyai duk yan uwa suka watse gida ya rage su kadai.
Hakan yasa suka zauna sukayi ta kuka.
Washe gari da safe duk suna tsakiyar gidan time to time in Ummi ta kallesu sai tayi ta zubda hawaye.
ganin haka duk sai jikinsu yayi sanyi,
Rahma kam tuni kuka takeyi dan ita kam rayuwa ta mata zafi ba miji ba uba ba yayansu jigonsu, wanda suke ganin zai zama gatan nasu kuma gashi kurmane.
jin kukan Rahma yasa Ummi tsananta kukanta,
shi kuwa Saifuddeen idanu ya rumtse sabida ba abinda yafi tsana a duniya kamar yaga hawayen Umminshi,
Raihana kuwa ruggume Hayatuddeen tayi tana kuka Raliyya kuwa su Faruq ta ruggume.
Suna cikin haka sukaji sallama,
cikin sauri Ummi ta d'ago kanta jin muryar Bappanta k'anin babanta da Goggonta, sai matar Bappan nata iya bukku muguwar mace, shiyasa Ummi take rayuwa tamkar bata da dangin Uba.
da sauri ta taso ta nufi Goggonta,
kan taburma suka zube nan raunin Ummi ya tashi ganin danginta kife kanta tayi kan cinyar Goggo Rabinta d'in ta saki wani marayan kuka.
itama Goggo Rabi kukan takeyi dan tausayawa d'iyar yayanta.
hakama Bappa idintan shima kukan yakeyi dan tausayawa rayuwar Ummi da yaranta,
ita kuwa Iya Bukku sai wani mugun kallo na rashin imani take bin su Rahma dashi.
Yayinda shi kuwa Saifuddeen ita ya zubawa idanu ganin mugun kallom data juyo tana yiwa Ummimshi.
cikin tausayawa Goggo Rabi ta d'ago Ummi cikin sanyin murya tace.
"Kiyi hak'uri Bisije dukkan tsanani yana tare da sauk'i, ki dena musu kuka Allah yana sane dake da marayunki."
murya a disashe Ummi tace.
"Goggo Rabi ya zanyi ina zan shiga a duniyar nan inji dad'i wa zai rik'e min yarayuna wazai tallafawa maraicina dana yarana da marayun jikokina?".
sai ta kuma juyowa ta kalli Bappa idin nata cikin rawan murya tace.
"Bappa ya zanyi wa zai zama gatanmu wa zai zama garkuwarmu, tunda shima bappan su Rahma ba wadata yakeda shiba, sana'ar me zanyi in rik'e yarana?."
kafin Bappa idin yayi mgna tuni iya bukku ta cab'e mgnar da cewa.
"Wannan kurman d'an naki mai kama da dutse shi baida amfanin komai ne?."
sai ta kuma tsuke fuska dan bata son bappa idi yace zai d'aukesu su koma garinsu dasu,
da sauri ta kauda kanta lokacin da ta kalli Saifuddeen sabida wani irin mugun kallo daya watsa mata.
sai kuma ta tsuke fuska kana taci gaba da cewa.
"In dai bazai amfanekiba ai sai ku jefar dashi ku huta da ciyar da mai zubin mutanen b'oye yaro tun yana k'arami ni tsoro yake bani dan wannan kyawun nashi ya zarta na mutanen mu.
in kuma bazaki iyaba, tunda ke jakar 'ya'yace akan yaranki zaki mutu,
to sai ki shiga cikin gari kije gidajen masu kud'i kina musu share-share da wanke-wanke da girki, suna baki dubu 6 a wata kullum kuma kina kwatsawa zugan yaran naki tuwo, nasan harda k'anzo zasuke baki."
wani irin mugun kallo da tsana Saifuddeen yake cilla mata,
domin tunda yake a duniya bai tab'a jin mgnar da tai mishi zafi kamar wannarba, kana bai taba jin mutun mai munanan kalamaiba kamar iya Bukku ba.
Goggo Rabi kuwa kai ta rink'a jujjuyawa alamar batajin dad'in kalaman da matar yayan nata takewa d'iyar yayanta marigayi.
Bappa idi kuwa sunkuyar da kanshi yayi dan yasan motsi kad'an zaiyi iya Bukku zata solleshi.
Raihana ce ta share hawayenta tare da murgud'a mata baki kana tace.
"Allah ya kiyaye Umminmu tayi ai katau a gidajen wasu,
kuma Hamma Saifunmu ba k'aton banza bane kurwarshi kur sai dai kici kanki wlh yafi k'arfinki,
har zakice mishi baida amfani to in sha Allah aniyarki kanki zata kom...!"
da sauri tayi shiru dan bugun da taji Ummi ta kaimata a baki tare da cewa.
"Raihana ki kiyayeni fa, banfa miki irin wannan tarbiyarba maza tashi ki bar nan."
cikin sanyi ta mik'e tare watsawa iya Bukku harara kana tace.
"Kiyi hak'uri Umminmu bazan k'araba."
Goggo Rabi kuwa ji tayi kamar ta goya Raihana dan dad'in ta sulle iya Bukku.
shima bappa idin dad'i yaji.
shi kuwa Saifuddeen, Ummi ya zubawa ido yana karanto bac'in ranta,
sai ya kuma juyawa ya kalli Rahma da ta sunkuyar da kanta hawaye na zubo mata.
itako Iya Bukku cikin masifa da rashin mutunci tace.
"Kaji hegiyar yarinya mai kama da aljan kujiye min fitsarerriyar yariya da uwarta bata haifeta da bisimillaba,
ke har kin kai ki zageni?
to na fad'a bashi da amfani, ai da yana da amfanin da ya tsare muku maraicinku,
ya zauna kamar dutse ya wani zuba min shegun idanunshi ya had'e wannan fuska tashi mai kama data al'jamu."
sai ta kuma ja tsaki kana ta mik'e tsaye tare da juyowa ta kalli Saifuddeen da zuciyarshi ke tafarfasa da sauri ta kauda idonta daga kanshi sabidah arararda yake watsa.
cikin k'arfin hali tace.
"Wannan da gani rabi mutum ne rabi aljan, mutun da aljan.
Dan duk zuriyar kakanunku babu kekyawa kamanshi wannan kyau bana Allah da annabi bane, hege mai jajen kunnuwa da labban baki."
sai ta kuma juyo ta fuskancesu baki d'aya kana tace.
"Bisije in kin yarda da shawarata wlh ki kaishi bakin kogi dan da gani wannan d'an ruwane,
in kuma kingi to ki bashi k'ok'on bara yaje yayi ta bara a cikin Gombe nasan wasu ko dan kyanshi zasu bashi sadaka, tunda nakasasshene bararce kawai aikinshi ai."
cikin zafin rai Rahma ta mik'e tare da tsuke fuska kana tace.
"Bamu jikiba! aniyar kura tabi daji!
k'anina ba nakassashe bane, domin nakasar zuciya itace sahihiyar nakasa ba nakasar gangan jikiba.
In sha Allah har abadan Saifuddeen bazaiyi bara ba, in Allah ya yarda hannunshi bazasu tab'a rik'e k'ok'on baraba.
Kuma acan zuriyarku ne ba kyawawa mu ki kallemu gaba d'ayanmu ba mummuna ki kuma bincika zuriyarmu kab kyawawane waya ce miki Baddukke yana muni bare bak'i,
to mu mune dukku jinin Dukku bamu da mutuwar zuciya,
bare muyi maula,
ki kama bakinki sai randa muka nemi al'farma a wurinki kafin ki gaya mana ba sugari,
in kyawun Saifuddeen ke baki tsoro to sai dai ki makance. Ke! da kin san k'uruciyar Abbanmu sanda yanada lfy da suma zakiyi in kin ganshi, dan haka mu kyau gadanshi mukayi ki dena cewa k'anina d'an ruwa eh!."
shiru Ummi tayi dan tasan Rahma nada hak'uri k'ureta akayi,
Raliyya kuwa sai harara taketa dokawa iya Bukku,
Goggo Rabi kuwa murmushin jin dad'i take.
Bappa idi kuwa tsorone ya rufeshi yasan in sun koma zaisha rashin mutunci dan sunfi kwana biyar da jin mutuwar tace bazasu zoba da yake can garin Hashidu suke.
shi yayi ta lallabata kan dole su zo, to yasan kanshi zata huce cewa zatayi da gayya yasata suka zo dan jikokinshi suci mata zarafi,
shiyasa duk sai ya tsure da yake dama mijin tacene.
Ita kuwa iya Bukku mari ta yarfawa Rahma,
wanda yasa suka mik'e gaba d'ayansu kana cikin masifa tace.
"To me amfanin kyan naku? Uban naku da yayi kyau d'in ina da aljani ya rayu a jikinsa ya zama mahaukaci tuburan.
To wane rana kyan naku ya muku,
tunda gaki ke bazawara baki auruba ga kuma kitika-kitikan yan mata har biyu suma basu auruba,
wata k'il basu da ko mashunshini,
gaya min me amfanin kyan naku, uwar rashin kunya?."
gaba d'aya jikin Saifuddeeem b'ari yakeyi sabida zafin zuciya irin na kurame,
ita kuwa Rahma rik'e hab'arta tayi tana kuka hakama Ummi.
Itako iya Bukku cikin iya bak'ar mgna taci gaba da cewa.
"To tunda baki san amfanin da kyan naku zai mukuba, ni bari in gaya miki,
kuje ku fara *KARUWANCI* nasan tabbas zakuyi kasuwa, kuyi karuwanci ku tara kudi dan nasan shima wannan Saifuddeen aljanin uban naku kanshi zasu dawo dan haka kuje kuyi karuwanc...?"
bata kai ga k'arishe mgnarba ta kurma wani irin razanenne ihu da ya cika unguwar baki d'aya.
bata ida dawowa haiyacintaba ta kuma kurma wani azabebben ihu,
sabida wasu zafafan maruka da Saifuddeen ya yarfa mata,
wanda a take sai ga hagwaranta a biyu a k'asa.
Ihu ta kumayi jin yasa k'afarshi ya tad'eta ta zube kasa rakacab ji kake d'im kamar an tila kayan wonki,
cikin rufewar ido da fita haiyaci Saifuddeen ya zaro ball inshi ya tsula mata d'aya zai kuma na biyu ne Ummi ta rik'o hannunshi tana kuka tana cewa.
"Saifuddeen ka rufa mana asiri muji da maraicinmu,
gaishemu fa sukazo yi."
Raliyya kuwa da Raihana sai murmushin jin dad'i suke yayinda Hayatuddeen yake tsalle yana cewa.
"Allah shi k'ara Ummi barshi ya dakata hegiya mai k'aton d'uwawu."
iya Bukku kuwa ai tana samun Ummi ta rike mata Saifuddeen cikin tsananin gigita da tsoro,
ta mike ta wawuri takalmanta a hannu gabas ta nufa a gigice sai ta kumayi kona tayi yamma kana ta juyo arewa, ganin har yanzu dai bata gane hanyar fitarba sai ta kuma yi kudu cikin tsananin gudu ta fita tare da cewa.
"Rabi, malam ku fito mugudu, aljanin sun motsa dama ba nace muku ruwa biyu bane shi ku fito mu gudu karya kashemu."
ita kam Goggo rabi niyarta zata tsaya, to ganin yayanta yabi matar tashi a guje shiyasa itama tabi bayansu a saba'in suka bar garim Dukku akan baburdin Bappa idin.
A cikin gidan kuwa Raihana da Raliyya da Hayatuddeen sai su kalli juna kana suyi yar dariya.
Cikin fad'a Ummi ta watsa musu harara, kana ta fuskancesu da kyau dan duk sun tsaya sunyi cirko-cirko sun tasa a gaba cikin nuna b'acin ranta tace.
"Dariyar me kukayi? dan baku da wayo baku san halin da muke cikiba, wani farin cike muke dashi da har zai saku dariya?
kema Rahma da nake miki kallon mai hak'uri ashe ba haka bane."
sai ta kuma nuna Raihana tare da cewa.
"Duk kece kika jawo abinnan da baki tanka mataba da tayi ta bari,
amman sai kika tsafe ido zaki zageta bayan kunsan ba hak'urine da itaba."
sai ta kuma juyawa ta kalli Saifuddeen nan take sai zuciyarta ta raunata cikin zubda hawaye da rawan murya tace.
"Babana meyasa kayi haka? ka mance yanzu bamu da kowa a duniya dole muna buk'atar taimakonsu."
cikin tsananin kunar zuciya ya tsuguna k'asa ya fara rubutu da sauri yayinda hannunshi har rawa yakeyi dan bac'in rai.
"Dan Allah Ummi karki sake cewa bamu da kowa,
kin mance munada Allahn daya haliccemu shine mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa shine wanda ya mana gida biyu duniya da lahira,
shine mai azirta bayinshi a duk sanda yaso shine yake ciyar da dukkan abin halitta, kuma muma shine zai cidamu,
shine gatan kowa kuma muma zai zama gatanmu baifa mance da muba.
Ummi koke da kike yarsu dame suka amfaneki a rayuwarki? bare mu jikokin d'an uwansu da ya rasu shekaru da dama.
Ummi ki kalleni nayi al'k'awari in sha Allah zan nema da k'arfina da lfyta zan kula daku iya iyawata, karki sake kaiwa kowa kukanki ki kaiwa Allah shi zai biya miki buk'atunki ba gajiyawa bare gori.
Ummi kiyi min addu'a ki sanya min al'barla in sha Allah ni d'innan zan cidaku in kuaa shayardaku in jinyaceku in suturtaku."
ita kam Ummi ta kasa cewa komai sai ido ta zuba mishi domin yana tsugune sai rubutu yakeyi in inda yake ya cika kana sai yaja baya yanayi jikinshi na rawa cikin zubda hawaye taci gaba da bin rubutun da yakeyi tana karantawa.
"Ummi rabuwarmu dasu shiyafi al'khairi domin muddin tana zuwa tana fad'i mana mugayen kalamai wata rana zan karya mata wuya,
Ummi na karkiji tsoro in sha Allah k'annena bazasuyi karuwanciba ni kuma bazanyi baraba bare maula, kema bazakiyi aikatauba, ki kalleni ki gaya min dukkan matsalarki kiyi shawara dani ko k'annena kada ki gayawa kowa matsalarki ki sirranta matsalarki damu yaranki.
Insha Allah zan fara neman sana'ar yi dan rik'eku ke dai ki samin al'barka."
Rahma kam sai hawayenta take shartewa,
su Raihana kuwa sai binshi suke suna karanta abinda yake rubutawan.
Ita kuwa Ummi da sauri ta isa inda yake hannunta tasa tsakiyar kanshi cikin k'arfin hali tace.
"Ya Allah kayiwa wannan bawa naka Saifuddeen al'barka ya Allah ka yalwata mishi samunshi hagu da dama rabbi ka al'barkaci duk abinda ya tab'a ya wahidun k'ahhar ka bud'a mishi k'ofofin samu gabas da yamma kudu da arewa.
Ya Allah ka kauda asara da gafala da tab'ewa daga gareshi dashi dama dukkan yan uwa musulmai, ya rabbil izzati ka al'barkaci rayuwar Saifuddeen ka raya minshi ka shirya minshi ka bashi arzik'i mai al'barka wanda musulmai da musulunci zasu al'fahari dashi ya ka bud'a mishi k'ofofin samu ka yalwata arzik'inshi."
kasan cewar tunda ta dafa kanshi ya d'ago kai ya kalleta shiyasa yake gane abinda take cewa,
yana kallonta still yatsarshi na k'asa yana.
Rubuta "Amin Amin Ameeen ya rabbil izzati".
daga nan suka zauna tayi ta musu nasiha mai ratsa jiki.
Bappa Ali kuwa da matarshi suna side d'insu sam basu san meya faruba.
A daren ranar Saifuddeen yaje ya samu Bappa Ali da fefanshi da biro,
nan yake neman izinin bappan nashi da kuma shawarshi cewa.
A d'auki machine d'in Nuruddeen a bawa wani d'an mak'ocinsu Salisu wanda shima d'an acaba ne to dama na haya yake karba, to kuma an karb'e machine d'in wai mai ita zai saidata ya cikata ya sai sabuwa,
ba musu bappa Ali ya yarda dan yasan ko ba komai balance d'in zai taimakesu,
shi kuwa Saifudden gyara zamanshi yayi kana ya rubutawa bappan nashi cewa.
Kullum da safe in Salisu zai tafi zai bishi su tafi tare,
in yaje zai shiga cikin kasuwan Gombe zai nemi sa'ar da zaiyi."
da fari Bappa Ali yak'i kasan cewar yanaga Saifuddeen d'in kurma ne,
to amman da suka dunguzuma sukaje wurin Ummi sai ta kauda kai yadda Saifuddeen d'in bazai ga bakintaba tace.
"Ba matsala Ali barshi yaje, in mun hanashi zaiga ko dan yanada nakasane, mukuma bamu son hakan to amman ai kasuwa saida jari,
amman tunda yace a barshi yaje,to mu barshin in yaje yaga ba abinda zai ai zai bar zuwa, mu kuma bishi da addu'a Allah ya taimaka mishi."
cikin sanyi bappa Ali yace.
"To shake nan ba matsala Allah ya bashi sa'a."
"Amin Amin." sukace baki d'aya.
Daga part d'in Ummi woje suka fita,
sukako yi sa'an samun Salisu a harabar matsallacin k'ofar gidan nasu.
Nan bappa Ali ya mishi bayanin yadda sukayi, aiko dad'i kamar ya kashe Salisu,
ya kuma yarda da shared'in zaike zuwa da Saifuddeen su kuma dawo tare.
A take bappa Ali ya bashi Key d'in machine d'in.
sannan ya wuce cikin sangayarsu ya fara ratsa tsakiyar d'aliban nasu.
shi kuwa Saifuddeen gida ya koma ya sanarwa Ummi yadda sukayi, ita ko Ummi sai addu'a da samishi al'barka takeyi.
A daren ranar Ummi da Rahma da Raihana da Bappa Ali kusan kwana sukayi sunayi mishi addu'ar samun madafa da sa'a.
Shi kam Saifuddeen baiyi bacci a ranar bare ya rumtsa,
Kwana yayi yana neman yardar Allah da sanya al'barkanshi ya bashi sa'a a cikin k'udurin da yayi.
Washe gari da sanyin safiya Saifuddeen ya shirya bayan ya karya Salisu ya shigo yace su tafi.
gaban Ummi ya tsuguna kanshi ta dafa tare da sa mishi al'barka.
sannan su Rahma suka mishi addu'a baki d'ayansu kana suka fita suka tafi.
Suna shiga Gombe Salisu ya wuce dashi k'aramar kasuwa,
gab da San Hussen mall ya ajiyeshi,
kamar yadda sukayi tun jiya da dare,
bayan ya sauk'ane Salisu ya kalleshi tare da cewa.
"Ana yin sallan magrib kazo ka tsaya a nan, dan zanzo in d'aukeka mu tafi in munyi sa'a bayan isha mun isa Dukku."
cikin nuna alamar ya gane ya gyad'a mishi kai alamar toh.
Salisu na ganin haka yaja machine inshi gaban wata yar budurwa data tsaidashi,
lokaci d'aya suka shirya kud'in da zata bashi kana ta hau yaja ya tafi.
Shi kuwa Saifuddeen juyowa yayi ya zubawa makeken wurin San Hussain d'in idanu a lokacin tun forkon-forkon bud'eshi kana wurin ba'a wani gyarashi sosaiba kamar yanzu ba,
ajiyan zuciya yayi lokacin daya karanta sunan wurin,
sai kuma ya k'auda kai kana yayi tafiya kad'an yazo dai-dai mashigar kasuwan,
inda zai bulla ta babban layin na k'aramar kasuwan.
ida nunshi ya lumshe kana ya bud'esu a hankali hannunshi ya had'e wuri d'aya kana ya fara karanto addu'o'i yayi kusan 16 minutes yana addu'o'in kana ya shafa a fuskarshi kasan cewar da d'an sanyin safiya ne wurin bai cika jama sosaiba kuma kowa sauri yake ya wuce ya isa wurin sana'arshi ya bud'e.
bayan ya shafa addu'ar ne yayi bisimillah tare da d'ago k'afarshi ta dama ya shiga cikin kasuwan.
Sannan ya mik'e gabanshi samb'et, yana tafiya a hankali.
har yazo dai-dai wani babban shagon seye da sayarwa inda mata keta shiga da fita irin masu zuwar sassafen nan shagon kuma cike yake mak'il da atampopi, shadda, laces, material, voyels, su wagbari, gyalulluka. da dai sauransu,
ido ya zubawa yaran shagon kowa na hidiman gabanshi.
a hankali ya kalli saman shagon inda yaga an rubuta.
Alhj Ishaq,
murmushi yayi dan sunan mai shagon ya tuno mishi sunan abokinshi wanda kusan sau biyu kenan yana zuwa Dukku bayan Abba ya rasu.
juyawa yayi d'aya sashin inda yaga wani k'aton shagon mai cike da gyalulluka da dogayen riguna,
kana ya kalli d'aya sashin inda yaga k'aton shagon saida takalma,
sai kuma kusa da inda yake shagon masu saida yadin hijabai ne da masu d'in kasu.
shiru yayi sai ya kuma ci gaba da tafiya ganin ya b'ata kusan 30 minutes a wurin.
A hankali yake taku har ya isa konan shagunan alhaji Yawale,
shiga yayi nanma ya dad'e a tsaye sai kuma yayi baya ganin kusan irin kayayyakin wancan shagon ne daya wuce,
kan babban layin ya dawo kana yaci gaba da tafiya,
Dai-dai shagunan ba mishkila ya tsaya yana kallon yadda mutane ke cike a wurin mazansu da matansu yara da k'anana,
ido ya d'an zubawa yaran shagon ganin kowa da abinda yake aunarwa kuma awu mai kyau irin awunda musulunci ya yarda dashi,
sunan shagon ya kalla sai kuma yayi murmushi ganin sunan shagunan ba mishkila a ranshi yace.
"Eh tabbas kam ba mishkila."
A takaice dai a wanan ranar kam kusan aikin daya wuni yi kenan ya zaga wannan layin ya zaga wancam layin, kana yana bin bakin shaguna yana kallon abubuwan dake ciki da yadda suke mu'amala da costumers insu, yana jin yunwa na k'ak'ularshi amman bai kulaba in lokacin salla yayi ya sayi pure water yayi al'wala yabi jam'in inda duk yaga ana haramar salla.
Kafin magrib ya gaji lik'is.
koda magrib ta kawo kai sai yaga anata rurrufe shaguna hakan yasa ya fita,
bakin inda Salisu ya ajiyeshi,
yana tsaye a wurin ya hango tsallaken titin anata Al'wala haka yasa shima yayi Al'wala kana ya tsallaka yaje akayi sallah dashi.
yana dawowa Salisu na isawa,
babu b'ata lokaci ya hau suka fara tafiya,
sunzo dai-dai wani wurin masu tuwo-tuwo Salisu ya tsaya kana yacewa Saifuddeen.
"Zo muje muci abinci kafin mu tafi naga alamun kamar ba abinda kaci."
juyawa yayi kalli wurin da Salisu ya nuna mishi,
baki ya tab'e kana ya girgiza mishi kai tare da nuna alamar kamar yana kekyamin abincin wurin.
murmushi Salisu yayi dan tabbas yasan Saifuddeen mutunne mai tsananin tsabta da gayu kuma yanada kyakyani,
dan yasan iya tsawon yarintansu bai tab'a ganin ya sayi koda ko kosai ko wani abuba cikin abubuwan da ake kawowa a yar majalisar k'ofar gidansu ba.
So dan haka sai ya hau machine d'in yaja tafiya kad'an suka isa wurin mai shayi, kana yace.
"To mu shiga nan kasha koda shayine."
Still tab'e baki yayi tare da juya kai,
alamun bazai shaba.
ganin haka Sakisu ya kuma jan machine d'in, kai tsaye hanyar tashan Dukku ya nufa dashi,
suna zuwa dai-dai bakin gate d'in Abba bakery yayi parking kana ya sauk'a sannan,
yacewa Saifuddeen.
"Zo muje nan ko zaka iya cin gashin wannan."
a tare suka shiga inda daga mashigar wurin mai naman yake,
ganin wurin fes komai a killacene yasa,
Saifuddeen yarda ya zauna a wurin,
naman d'ari biyar Salisu ya saya musu, kana ya shiga cikin asalin Abba bekery ya sayo musu yogurt k'ananun robabin guda biyu.
nan sukaci duk da Saifuddeen bai wani ci mai yawaba yanka hud'u yaci bai kuma k'arawaba sai yogurt yasha.
Tuni kafin lokacin an kira isha'i haka yasa sukayi sallan
kafin suka nufi hanyar Dukku.
Suna isa gida Ummi tai ta murna ganin ya dawo lfy kuma gashi babu alamun wahala,
shi kuwa Saifuddeen yaki yace mata komai sabida gudun kada ta hanashi zuwa gobe.
Washe garima kamar jiya suka shirya suka tafi bayan Umminshi tayi ta mishi addu'ar samun nasara.
A inda Salisu ya ajiyeshi jiya yauma nan ya ajeshi,
bayan yaja ya tafine shi kuma ya nufi bakin mashigar kasuwar,
yauma kamar jiya saida yayi addu'a kafin ya shiga da k'afan dama.
Kai tsaye layin masu kayan yara ya shiga a hankali yake bin shagunan daki-daki yana kallon yadda suke gudanar da kasuwancin su, mata masu ciki nata shege da fice, a hankali yake taku cikin nitsuwa.
duk wanda ya ganshi sai ya k'ara juyawa ya kalleshi sabida bak'ak'en kayan da ya saka ba k'aramin haskashi sukayiba farinshi ya k'ara fitowa hancin nan har baki, uwa uba sumar kanshi tafi sawa ana kallonshi sabida duk wanda yaga sumar zai tunanin balarabe ne,
fatar k'afafunshi da tafin hannunshi kuwa sunyi jazir, in ya taka k'afar tamkar jini zai tsillo.
Dai dai bakin wani k'aton shago ya tsaya,
yana tsayuwa kenan yaji an.....!
By
*NAKASA BA KASAWA BACE*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.