Complete Hausa Novels

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt

Chapter 15 of 27

*PAGE 15*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

~Free page~

Suka gano matsalar shi, kana suka dugufa kanshi dan samo numfashin sa ya dai-dai ta, domin babu wani aiki da zasuyi mishi har sai ya dawo haiyacinshi.
Hakan yasa suka meda hankali ganin komai ya dai-dai ta, cikin ikon Allah a daren ranar ya farfad'o yana kuma cikin haiyacin sa, kasan cewar dare yayi nisa, yasa aka bar batun dubashi zuwa safiya.

Bappa Ali da Warisu da Mudassir kuwa tunda Hayatuddeen ya sanar musu gaba d'aya hankalin su ya tashi sai dai sun meda hankali wurin yi mishi addu'ar samun lfy a cikin ka'aba.

Ishaq kuwa, tunda aka shaida musu bazasu dubash yau ba sai gobei, sai ya kira babban yayanshi dake nan Abuja da iyalanshi ya shaida mishi, ba jimawa kuwa Ya Rabi'u yazo tare da direbanshi, domin dukkan sashin zuriya biyun sun san abotar Ishaq da Saifeddeen domin abotace tun na yarinta, hakan yasa har iyaye su suke mutunci da zumunci mai k'arfi.
Kasan cewar babban doctor uban gidane ga Dr Adnan hakan yasa tun kafin suzo an shirya komai, hatta da masu kula dashi, ya tanadar cikin ma aikatan nasu,
ya kuwa kontarwa Ummi hankali ta tare da bata k'arfin guiwa.
Haka yasa Ya Rabi'u ya tafi da su gidanshi, cikin sa'a ma kuwa asibitin ba tazara sosai da diganshi.

Ummi kuwa da Hayatuddeen dugufa sukayi da Addu'a jigon nasu.
Deren ranar sam basu rumtsaba, shima Ishaqa bayi bacciba.

A can gida Gombe kuwa, bayan su Raihana sun koma gida, kai tsaye falon Ummi suka wuce,
cikin sanyin jiki Raihana ta zauna bisa kujera,
idonta ta rumtse da k'arfi, a jere wasu zafafan hawaye suka zubo mata,
ita kuwa Raliya wayarta ta d'auka, ta fara 'yan dube-dube bayan yan wasu dak'ik'u ta kara wayar a kunne,
a hankali ta bud'e labbanta tare da cewa.
"Wa'alaikassalam, Abban Farida, yaushe zaka dawo?."
a can d'aya sashin Abban Farida yace.
"Lafiya dai ko?."
murya a sanyaya tace.
"Alhamdulillahi ala kulli halin."
jin haka yasan to tabbas akwai matsala sai dai iya sarrafa harshe na matar kwarai wacce tasan yadda zata isar da sak'o wa mijinta ba tare data firgitashi ba,
cikin dakiya yace.
"Meke faruwa?."
tallabe hab'arta tayi tare da cewa.
"Abban Farida ka dawo gobe, please inda hali in zaka samu jirgin yau dan Allah ka taho gida."
cikin kad'uwa yace.
"Raliya meke faruwa ki gaya min mana, zuciyata ta cika da zulumi."
"Hamma Saufudddeeen! Saifuddeeen!! Saifuddeen..!!!."
tai ta maimaita mishi murya na rawa.
mik'ewa yayi tsaye cikin fargaba yace.
"Innalillahi wa Inna'illaihi rajiun. Meya sameshi? ina Hayatuddeen? Ina Ummi?."
Cikin kuka tace.
"Suna Abuja an tafi dashi asibiti."
daga nan ta sanar dashi dukkan abinda yake faruwa,
ta k'ara da cewa.
"Ya Adnan ya turasu Abuja. Abban Farida ka dawo wlh Hamma Saifuddeen ko motsi baya yi sanda suka tafi dashi."
ta karishe maganar tana zubda hawaye.
Shi kuwa Abban Farida datse kiran yayi kana ya fara harhad'a yan abin buk'atunshi, kai tsaye Airport ya nufa cikin sa'a ya samu jirgin Abuja, dama shi bai niyar zuwa Gombe ba.

Kafin su isa abuja dare ya d'an fara nisa kuma yayi ta kiran number Hayatuddeen da Ummi duk basu d'agawa, haka yasa ya nemi masauk'i inda ya kwana da nufin da safe zai nemesu.

Dr Adnan kuwa, saida yaga tashin su Ummi sai da ya koma asibitin kafin ya koma gida.
Shiru parlour nasu ba kowa haka yasa ya zauna bisa 1 str zuciyarshi da jikinshi na cike da fargaba da tsoron halinda martashi Rahma zata shiga in taji abinda ya samu d'an uwanta,
ya rasa tudun dafawa, a fili yace.
"Ya ilahi ya mujubbat da'awati ko taya zan sanarwa Rahma."
sai kuma yayi sauri zaro woyarshi Ishaq ya kira,
bayan sun gaisa yace.
"Kun isa lfy,?."
"Lafiya lau Alhamdulillahi."
gyara zamanshi yayi tare da kallon k'ofar corridor d'in part d'in Raihana sannan yace.
"Kun samu Dr Aliyu ko?."
"Eh to gsky mun samu tarba daga wurin Doctors har uku to gsky ban sanan wanne ne Dr Aliyun ba a cikinsu."
cikin sanyi yace.
"Zakaga Dr Aliyu shima nakasasshene ai domin shima yanada matsalar spanal cord kuma shine big doctor a k'asarnan in dai a wannan fannin ne, uban gida nane kuma wa nane d'an kawuna."
cikin jin dad'i Ishaqa yace.
"Alhamdulillahi, hakan yayi kyau domin dama shi nakasa ai ba kasawa bace, kuma ya yi mana k'arin bayani kan mu kontar da hankalin mu, Alhamdulillahi kuwa tuni ya farfad'o kuma yana cikin haiyacin sa, so zuwa gobe da safe zasu fara bincikan adadin zurfin ciwon."
lumshe ido Dr Adnan yayi kana yace.
"To Allah ya kaimu, in sha Allah nima gobe zan taho please kuke kontarwa Ummi hankalinta."
"In sha Allah ba matsala." cewar Ishaq.
Kana daga nan sukayi sallama,
shi kuwa Dr Adnan Dr Aliyu ya kira bayan sun gaisa yake mishi godiya tare da tambayar ya mai jikin, so shima Adnan ya samu d'an nitsuwa duk da cewa Dr Aliyu ya tabbatar mishi cewa Saifuddeen ya samu nakasar lakkar bayanshi.
bayan sun gama woyar ne yana d'ago kanshi ya hangi Rahma tsaye bakin k'ofar kitchen ta kafeshi da ido gaba d'aya jikinta tsuma yakeyi tuni hawaye sun jik'a fuskarta,
mutuwar zaune yayi domin tabbas yasan taji duk wayar da yayi dasu, dan sam hankalinshi bai bashi ko tana kitchen ba.
Ita kuwa matsowa ta farayi a hankali take taku still jikinta na rawa,
gabanshi ta tsaya tare da tirtsetsen cikinta,
da sauri yasa hannu ya jawota jikinshi kan cinyarshi ya ajiyeta, suna fuskantar juna, murya na rawa tace.
"Me kuma zaka boye min Ya Adnan me zaka boye min? gaya min me zaka boye min. wani abune kuma ke tinkarar rayuwarmu? meya samu d'an uwana? ina yake, waye zai nak'asa Saifuddeen ne ko Hayatuddeen gaya min wani hali Ummi ke ciki?."
gaba d'aya ta birkice ta gigitashi da tambayoyinta yama rasa wanne d'aya zai amsa mata kuma tana k'ara tuno mishi fargabar da Ummi ke ciki.
Kawai sai ya had'eta da k'irjinshi ya ruggumeta da k'arfi kana ya fara magna cikin dakiya yace.
"Madadin kiyi mishi addu'a sai kiyi mishi kuka? kin san halin da yake shiga duk sanda yaga hawaye a kwaranya a idanunki, meyasa rauninki yake yawaita, da can baya da juri na sanki to meyasa bazaki ruggumi k'addaraba, ki godewa Allah a cikin dukkan lamarinki."
tunda yace mata kin san baya son kukanki ta gane Saifuddeen ne, to wani zafin ya wuce inda hawaye yake fargabarta da nitsuwarta duk sun had'u sun hargitse sun danne hawayenta,
sai tayi wani azabebben murmushi da yafi kuka zafi cikin sanyi tace.
"Alhamdulillahi ala kulli halin, ya Allah ka fini sanin waye Saifuddeen ya Allah ka fini sani adadin mutanen da ya zame musu uwa uba yaya k'ana, ya Allah ka fini sanin rauninshi dana mahaifiyarmu ya haiyyu ya k'aiyyum ya zirjalali wal ikram ya Allah ka bashi lfy ka d'aga kafad'un shi."
da sauri Dr Adnan yace. "Amin Amin, Ameeen ya rabbil izzati."
daga nan yayi ta bata baki da nuna mata ciwon baiyi tsanani ba.
Amman duk da haka daren wannan ranar itama sam bata rumtsaba.

Raihana kuwa har dare Allah baisa ta tuno da Affan ba domin tunda suka dawo data haura sama d'akin Saifuddeen kuka tayi tayi,
sai bayan sallan isha da Amira 'yar Alhaji Kabiru ta dawo mata da shi itama haka ta kwana yiwa d'an uwanta addu'a.

A can Abuja kuwa, tunda asuba matar ya Rabi'u Aunty Mami ta tasa yar aikinta gaba suka shiga kitchen, dan Ishaq ya gaya mata da sanyin safiya zasu koma asibitin.
bayan ta gama komai ne ta d'auki na su Ishaq da yayanshi da Hayatudddeen ta kai musu bisa dinning table dake nan men parlour nasu,
inda tunda suka dawo masallaci suna nan zaune suna tattauna matsalar inda shi Hayatuddeen yake cewa shi yafi son a fita woje da Hamma Saifuddeen nashi yaci gaba da cewa.
"Ance Jermaine itace k'asar da tafi shahara da kwarewa ta fannin wannan ciwon, ni kam da zan samu mu fita dashi."
ya k'arishe mgnar yana mai kallon Ishaq da yanayin neman izini.
Cikin tausayawa Ya Rabi'u yace.
"Ba matsala ! Hayatuddeen in sha Allah tun da Dr Aliyu yasa hannu kan lamarin so ko can Jermaine aka kaishi iya abinda yace zasu ce, kana nasan zaiyi duk abinda ya dace in kuma yaga fitar da shid'in nema maslaha to tabbas, nasan zai bada dama a fitar dashi, kuma zai shige mana gaba yadda komai zaizo da sauk'i.
Yanzu ku matso muyi breakfast saimu hanzarta zuwa, tunda ya shaida mana kwana zai a asibitin kana da safe zai dubashi kafin ya tafi gida."
cikin lumshe ido irin na marasa gani Ishaq ya d'an shafa kan Hayatuddeen tare da cewa.
"Zo muje kaci abinci in sha Allah Saifuddeen zai samu lfy."
haka dai sukayi ta bawa juna k'arfin guiwa.

Ummi kuwa sam ta gaza samun sukuni, abinda ta sanine bazata iya cin abinciba, amman ganin yadda Mami ta matsa akan dole taci abinci yasa tace.
"Bani tea kawai in sha."
cikin jin dad'i Mami tace.
"Yauwa Ummi gwara kici wani abu kafin ku tafi domin, bamu san yaushe zaku dawoba, kuma shima zama da yunwa cutane."
amsar cup d'in tayi tare da cewa.
"Sannu Mami Allah ya saka."
Amin tace tare da mik'ewa ta fida dan ta bata wuri, tasan in tana nan ba sha zatayi zabida sabida poolaku irin na al'ummar Dukku.
ita kam Ummi ji take tea d'in tamkar da mad'aci aka tafashi ba sugar ba.
Haka dai ta d'an sha rabi nai, kana ta kimtsa ta fito dan Hayatuddeen ya kirata akan tazo su tafi, tare da Ya Rabi'u da Aunty Mamin suka tafi, ita Ummi da Aunty Mami suna motar ya Rabi'u shiko Hayatuddeen key d'in mota ya Rabi'u ya bashi kana suka taho shida Ishaq.

Shi kuwa Ahmad Abban Farida kenan,
yana gama kimtsawa ya kira Hayatuddeen cikin sa'a ya d'aga bayan sun gaisa ne yake cewa.
"Hayatuddeen wanne asibiti kuke ne?."
cikin sanyi yace.
"Ya Ahmad kazo ne?."
da sauri yace.
"Eh nazo kuma ban san inda kukeba."
meda hankalinshi yayi bisa tuk'in da yake kana yace.
"Kana ina yanzu inzo in d'aukeka?."

masauk'in da yake ya gaya mishi hakan yasa ya juya akalar motarshi ya nufi Royal Hotel,
a harabar hotel d'in suka sameshi,
ba tare da b'ata lokaci ba ya shiga kana suka juya suka tafi.

Su Ummi kuwa suna isaya Ya Rabi'u ya nemi ganin Dr Aliyu nurses en suka ce mishi ya d'an jira nanda 20 minutes.
dan yanzu yana woyane,
haka yasa suka zauna a yar farfajiyar gaban office enshi,
bayan kamar 15 minutes su Hayatuddeen ma suka iso tare da Ahmad nan aka gaggaisa, kana suka zauna zaman jiran lokacin.

Shi kuwa Dr Aliyu da Dr Adnan yake waya inda suka tattauna matsakar.

Bayan ya gamane ya kira nurses guda biyu.
bayan sun shigone ya d'an kallesu tare da kallon ta gefen damanshi yace.
"Amina kin shirya mana komai ko?."
cikin girmamawa da nitsuwa wacce a k'ira da Amina tace.
"Yes sir an gama komai ku ake jira."
sai ya kuma juya ya kalli ta gefen hagunshi tare da cewa.
"Rebeka jeki kira min doctor Ayman."
"OK sir." tace tare da juyawa, wani office nan kusa da nashi ta nufa bayan an bata damar shiga, ta tsaya gaban Dr Ayman tare da cewa.
"Good morning sir."
ba tare daya kalleta ba yace.
"Morning."
gyara nitsuwarta tayi tare da cewa.
"Sir, Dr Aliyu na kiranka ."
kanshi ya d'an d'ago tare da kallonta kana yace.
"OK ."
tana jin haka ta juya ta tafi, shi kuwa Dr Ayman ya fara tattara takardun gabanshi kana ya mik'e yabi bayanta.

Yana shiga ya samu Dr Aliyu tare da Dr Batul, sai nurse guda biyun,
bayan sun d'an tattauna ne,
suka fito cikin shirinsu na aiki.
Cikin mamaki Hayatuddeen ya zubawa Dr Aliyu ido wanda yake cikin welchair bisa dukkam alamu bashi iya mik'ewa cikin sauri yace.
"Ya Ishaq shima wannan gurgun likitane?."
A hankali Ya Rabi'u yace.
"Babba ma kuwa."
ganin sun isone yasa suka d'an matsosu kana suka gaisa ,
cikin kula Dr Aliyu ya kalli Ummi dake rik'e da carbi cikin fullanci yace.
"Ummi kiyi mana addu'ar samun nasara yanzu zamu shiga aiki."
ajiyan zuciya tayi tare da cewa.
"Allah ya baku sa'an aiki yasa ku fara lfy ku gama lfy, Allah ya bashi lfy dama dukkan Al'ummar annabi."
Amin Amin suka amsa baki d'aya,
yayinda Dr Ayman ya kalli Amina tare da cewa.
"Jeki shirya shi kafin mu shigo."
da sauri tace to kana ta nufi room d'in da aka kontar da Saifuddeen.

Suma har sun juya zasu bi bayanta Ummi ta d'anyi gyaran murya sabida muryarta data disashe sabida yawan kuka a hankali tace.
"Doctor Saifuddeen Nakasasshene, baya ji baya mgna, bazai iya ce muku ga abinda ke damunshi sabida shi kurmane."
sai kuma tayi shiru hawaye na zubomata,
Ishaq kuwa cikin karsashi ya amshi mgnar da cewa,
"Ummi kin mance nakasarshi ba kasawa bace,
Allah da yayishi a nakasashe ya kuma bashi basira da hikimar da mai ido baida shi."
sai ya kuma juyawa ya kalli Doctors d'in da suka zuba mishi ido, especially Dr Aliyu da dama burinshi kenan kada nakasa ta zama kasawa ga masu ita.
Shi kuwa Ishaq gyara tsayuwarshi yayi tare da yin taku biyu zuwa uku tamkar ba makaho ba domin babu sanda a hannunshi bare d'an jagora, yana tafiya kamar ko wanne mai ji da gani cikin kula yace.
"Kuna ji ko Doctor's Saifuddeen kurmane, amman yanada hikimar da yake gane duk abinda mutane ke cewa matuk'ar yana ganin yadda bakin mutun ke motsawa, kana shi mai tarin ilimine fasihine ta yadda zakayi mgna dashi kamar kowa sai dai shi a rubuce zai baka amsar da duk kake buk'ata a gareshi yakan iya rubutama a phone ko laptop ko a fefa."
cikin Jin dadi Dr Aliyu yace.
"Masha Allah. Alhamdulillahi komai yayi tsanani iya tare da sauk'i,
yanzu bari muje muyi abinda ya dace."
fatan nasara sukayi musu kana, suka koma suka zauna a kujerun dake jere can gefe,
sannan su kuma suka shige cikin d'akin.

Tuni kafinma su shiga sun samu Nurse d'innan Amina ta gama kimtsa komai ta matso da dukkan abin buk'atarsu na yin aikin.
Yayinda shi kuwa Saifuddeen yake konce rigingine yayi lib bisa gadon ida nunshi na lumshe dan sam baya jin dukkan motsin da takeyi kana zuciyarshi da ranshi na gaya mishi wani yanayi da yakeji a jikinshi, domin yafi sau biyar yana yunk'urin zai tashi zaune amman sai yaji jikinshi na b'ari kana sai yaji bayanshi tamkar ba nashi ba, yana jin jijiyoyinshi a sake, haka yasa ya koma yayi lub yana nazari nan take yake tuno abinda ya faru dashi kana ya gane ya samu wata matsalar.
Ita kuwa Amina,
gaban gadon ta matso dan kimtsashi,
yayinda dai-dai lokacin su Dr Ayman Dr batulu da Dr Aliyu suka shigo,
gab da gadon Dr Ayman ya turo welchair d'in dr Aliyu, kana ya d'an sunkuyo ya danna wasu abu guda biyu sai ga keken ya d'an baje kana ya mik'e yayi sama yadda har ya d'an d'ara gadon da Saifuddeen yake konce a kai,
ta yadda tsowonshi ya kamo nasu Dr Ayman hakan yayi dai-dai yadda zai iya yin aikin tamkar ko wanne mai lfy.
sai kuma Dr Batula data kasance abokiyar aikinsu kuma babbar macece dan zata haifi Amina da Rabeka Kana zata girmi Dr Ayman sosai shiko Dr Aliyu su iya zama sa'anni,
ba mgna a tsakanin su sai nuniya kowa na shirya kanshi, ita Dr Batula taku tayi zuwa k'arshen gadon inda nan kan Saifuddeen yake, kana shi kuwa Dr Ayman yana gefen hagu yayinda Amina ke kusa dashi, shi kuwa Dr Aliyu yana gefen daman shi yayinda Rabeka ke gefenshi da wasu tarkace irin nasu na doctors bisa wani d'an abu mai kama da tire bayan ta ajiye kusa da gadon sannan ta juya ta fita ta bar d'akin.
cikin nutsuwa Dr Aliyu yayiwa Amina nuni data d'an janye mayafin dake jikin Saifuddeen,
kai ta d'an juya ta d'an zuba mishi idanu tana kallon kyau da cikar haibar da ubangiji yayiwa wanan bawa nashi, haka nan taji tausayin shi na ratsata domin tasan matsalar da ya samu a wannan yar jinyar,
shi kuwa Saifuddeen cikin fidda numfashi ya bud'e ida nunshi dan jikinshi ya bashi ana kallonshi, a hankali ya bud'e idanunshi, kan fuskarta ya sauk'e idanunshi,
da sauri tayi k'asa da kanta dan wani irin mashahurin kyau da korjini da ya mata fararen idanunshi da suka d'anyi lulu-lulu alamun sun dad'e a rufe suka k'ara k'awata kyawunshi.
A hankali ta kuma d'ago kanta ta d'an kalleshi cikin sanyin murya tace.
"Sannu ya jiki?."
sabida ita bata san kurma bane don kafin a gayawa su Dr Aliyu shi kurmane ta shigo ciki ta barsu a wojen.
Shi kuwa Saifuddeen idanunshi ya d'an jujjuya kana ya lumshe tare da gyad'a kanshi alamar yauwa,
sosai hakan da yayi ya gamsar da ita a fahimtarta amsa ya bata da body language wanda normal ne sometimes akan samu mutane da wannan d'abi'ar.
shi kuwa sai ya kuma bud'e idanunshi tare da kallon Dr Aliyu wanda yaketa mishi murmushi mai cike da tausayawa.
Dr Batulu ce ta d'an kalli Amina tare da cewa.
"Gyarashi lokaci na tafiya."
kai Amina ta gyad'a tare dasa hannunta a hankali ta janye mayafin, ya rage doguwar rigar da anka zura mishi,
wacce takeda mab'allan
daga samanta har zuwa k'asanta,
cikin sabo da k'warewa da sanin makaman aikinta ta fara b'alle boturan daga wuyanshi har zuwa k'irjinshi,
tanayi tana bud'a rigar yayinda tuni Dr Batulu ta fara nata aikin na duba raunu kan dake kan yalwataccen k'irjinshi,
wanda yake faffad'a fari k'al sai tattausan suma bak'i mai sulbi da Shek'i dake konce lib-lib,
batabi ta kan sumarba kasancewar raunu kan a gefe da gefe suke,
Dr Aliyu kuwa hang gulp yake sawa,
dan fara nashi aikin,
yayinda tuni shi kuwa Dr Ayman yake had'a wata na'ura mai k'ok'olwa.

Ita kuwa Amina a hankali take balla boturan har ta iso d'ai-dai kan mararahi,
ba tare da damuwa ba ta b'alla botur d'in,
ido ta rumtse da k'arfi kana sabida ganin joystick inshi konce samar maranshi kasan cewar yayi rigingine ne shi yasa ta koma saman maranshi,
wucewa tayi botur na gaba domin b'allesu gaba d'aya,
wanda tuni jikinta karkarwa yakeyi domin bata tab'a ganin sururar namiji ziraran miraran hakaba gashi kuwa tayi katari da ingarman na miji,
bayan ta gama bud'a rigar ne, Dr Batulu ta kalleta tare da cewa.
"Amina duba d'an buguwan dake kan mararshi nan ya yanayinshi."
kai ta gyada tare da dawo da hankalin ta kan mararshi,
ido ta kuma rumtsewa jin zuciyarta na neman faso k'irjinta ta fito woje.
jin muryar Dr Ayman na ce mata.
"Duba mana in da matsala a a dubashi tun wuri."
kai ta rusunar kana ta dawo da idonta kan joystick nashi dake konce kan wurin buguwar da yake jazir alum fatar wurin ya kurje har ya mele.
cikin tsuma tasa hannunta ta kamo joystick d'in nashi dan gyara zamanta don ta samu damar duba ciwon.
shi kuwa Saifuddeen idanunshi ya rumtse da tsananin k'arfi dan wata iriyar zabura da harbawa da yaji gabanshi yayi a take mood nashi ya canza a fili yake ganin hoton fuskar Zaleeha, a take yaji tsikar jikinshi na tashi tuno, lokacin data koma bayanshi ta ruggumeshi tana kwakumeshi tare da lek'o fuskarshi tana ce mishi.
"Kazo mu gudu, karsu ji maka ciwo, please kazo mu gudu zasu cutar da kai please mu gudu karsu kasheka dan Allah mugudu karsu cutar mana da kai."
yam ya kumajin tsikar jikinshi ya mik'e,
numfashi ya shak'a dan tuno wani irin assanyan k'amshi da jikinta yake,
taushin tafin hannunta ya tuno lokacin data rik'e damtsenshi,
a take lafiyarshi ta harba joystick inshi ta mik'e ta tsaya k'am tamkar zataci babu, bugu da k'ari ga fitsarin daya cika mishi mara,
shiyasa taketa harbawa tana k'ara mik'ewa da cika.
Amina kuwa wata iriyar razana da tsoro da fargaba da kunya mai tarin tsananine ya farufeta.
Cikin azabar tsoro ta janye hannunta jiki na tsuma tamkar mazari murya a hargize tace.
"Innalillahi wa Inna'ilaihi rajiun,
wayyo Allah na Wayyo Mommy."
ta k'arishe mgnar tana komawa bayan Dr Batulu,
ihun da tayi da janye hannunta yasa Dr Aliyu da Dr Ayman suka juyo gareta ganin meya razanata,
gaba d'aya jikinta tsuma da karkarwa yakeyi dan abun kamar a mafarki take ganinshi.
Shi kuwa Saifuddeen janye hannunta da tayi daga jikinshi ne ya sashi bud'e idanun,
sai ya kuma yi sauri yasa hannunshi na hagu ya janyo mayafin ya rufe sirrin jikinshi sabida yadda yaga joystick nashi a tsaye gam, kana sai harbawa takeyi uwa uba yadda Dr Aliyu da Dr Ayman suka wani murmushin da yafi kama da na tsantsar farin ciki.
Dr Batulu kuwa gaba d'aya yanayin Amina ya bata tsoro dan a fili ake gane firgitan da tayi, shiyasa ita bata ga sirrin jikin Saifuddeen ba dan hankalin na kan Amina dake bayanta,
janye kanta tayi daga rik'on da Amina tai mata,
hakan yasa ita kuwa Amina ta k'ara buya a bayanta,
sabi still har yanzu ana iya ganin yadda lafiyarshi ke harbawa a ta cikin mayafin.
ganin fa da gske a firgice take yasa Dr Aliyu ce.
"Amina fita."
kamar ace da ita ga qofar tsira a guje ta fice daga d'akin.
shi kuwa Saifuddeen gaba d'aya kunya ta mishi suture ji yake tamkar ya nitse cikin k'asa domin shi mutun ne mai tsananin Al'kunya dakawaici,
jin an kama hannunshi yasa shi bud'e ido,
idon ya zubawa bakin Dr Aliyu da ke cewa.
"Saifuddeen ka godewa Allah domin wannan alamace data nuna mana nakasarka bata shafi mazakuntanka ba, wannan mu a wurinmu wani sauk'i ne da alamun nasara da roggomi a cikin nakasarka, wannan alamace dake nuni da cewa har yanzu kana nan a cikekken na miji mai lfy wanda zai iya aure kana kuma zai iya haihuwa in Allah nufa."
sai ya kuma meda dubanshi ga Dr Ayman daya janye mayafin tare da cewa.
"Wannan yuna mana nakasarka ba mai zurfi bace, because zaka iya zama kana zaka iya tashi daga konce ka zauna da kanka ba tare da wani ya tallafa maka ba sannan zaka iya rayuwa ba tare da an sa maka ledar fitsari ba, hakan ya nuna mafitsararka lfya lau take haka kuma joystick naka ras yake zaka iya aure ka kuma sadu da mace ka kuma yi mata ciki matuk'ar tana da lfy, to amman fa sai in har ita matar ce zat.....!

*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.