Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: NAKASA BA KASAWA BACE PART 1.txt
Chapter 7 of 27
*PAGE 7*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡ðŸÂ‡
_Pleees in kin san baki turo kuÉ—inki ba,kada ki wahal da kanki ki wahaÆ™ dani, ga nan hanyoyin da zakibi ki biya dan Allah masu cewa ina zan biya to gata inda zaku biya, katin mtn na 300 ta wannan number 0909783276 ko kuma ka/ki turo ta ac na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar kin biya ta wannan number 09097853276 to kina yin haka ko baki cemin komaiba zan saki a groups É—in da zanke post. Kada kuce zakuyi min transfer É—in katin etisalat bana so! In kuwa kikayi to yaseen sadaka kika bani, gareku masoyana mutanen Niger ga number da zakuyiwa mgna +22788137740 500CF zaku tura_
Zai sha tea. Da sauri Raliyya ta mik'e ta shiga kitchen tea d'in ta had'a mishi kana ta dawo ta bashi sanan ta zauna sukaci gaba da hirarsu suna kuma cin ferfesun,
shi kuwa gyara zama yayi ya d'an matsa ya basu daman su sake dan kamar sun matsu zaman taburmar ta d'an musu kad'an.
Bayan sun gama cine, Hayatuddeen ya mik'o musu buta da sabulu suka wonke hannayensu sannan suka sha ruwa,
daga nan suka mik'e zasu tafi, ganin haka yasa Ahmad da Saifuddeen mik'ewa suka rakasu k'ofar gida nanma suka d'an tab'a hira sannan kowa ya nufi hanyar gidansu.
Bayan sun shigo gida ne Saifuddeen ya shiga wonka kafin ya fito kuwa tuni Hayatuddeen da Raliya da Raihana sunyi bacci dan sun san anjima kad'an Ummi zata tashesu dan dama in an shiga goman k'arshe tafi tashinsu da wuri,
Ahmad kuwa da bai saba baccin dareba sai hira yake ta yiwa Ummi da Rahma.
Yana fitowa ya shige d'akinshi mai ya shafa tare da fesa turare sannan ya dawo inda suke nan suka d'an tab'a hira suna cikin hirar Saifuddeen yayiwa Rahma alumun ta kawo asusun shi gane abinda yake nufi yasa ta mik'e ta nufi d'akin Umminsu asusun duka biyu ta kwaso tana zuwa ta mik'a mishi sannan ta zauna,
k'aramin asusun ya b'alle sannan ya juye kud'ad'en a tsakiyarsu tare da musu alamun su tayashi had'a kan kud'in,
nan duk suka fara harhad'e kan kudad'en ganin Ahmad ya fisu had'a mai yawane yasa duk suka mik'a mishi na hannunsu,
amsa yayi ya had'a dana hannunshin kana ya fara irgasu,
shi kuwa Saifuddeen mik'awa Rahma babban asusun yayi tare da mata alamun ta medashi,
Ummi kuwa gyarawa Hayatuddeen konciyarshi takeyi.
Bayan ya gama irgasune ya d'ago kai ya kallesu ganin kowa harkar gabanshi keyi ya sashi yin gyaran murya wanda yasa suka d'an kalleshi,
cikin d'an bud'a kafad'u ya bugi cinyar Saifuddeen haka yasa ya zuba mishi ido shi kuwa Ahmad murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillahi Ummi munyi kud'ifa wlh dole a fara ce damu alhazai."
cikin dariya Rahma tace.
"Toh al'hazai nawane asusun naku?."
gyara zama yayi tare da cewa.
"Kud'infa da yawa har dubu hamsin da takwas ne da d'ari biyu ne."
cikin jin dad'i Ummi tace.
"Alhamdulillahi Allah ya musu Al'barka."
Amin Amin sukace baki d'aya,
shi kuwa Saifuddeen gyara zamanshi yayi kana yayiwa Ahmad alamun ya cire dubu takwas da d'ari biyun saman ya bawa Ummi su,
haka kuwa yayi dan yana gane maganar abokinshi kuma d'an uwanshi, cikin lumshe ido Ummi tace to ni me zanyi dasu?."
kanshi ya tonk'oshe hagu da damanshi sannan cikin mgnar kurame ya mata bayanin,
"Ta karb'esu in akwai wad'anda take son yiwa wani ihsani tayi amfani da kud'in."
gane abinda yake nufi yasa tayi murmushi tare da cewa.
"To Allah ya saka maka da mafi kyawun sakamako Allah ya bud'a muku k'ofofin samu,
wannan zan sayi kayan yara koda kala uku ne a bawa ungiyar marayu."
kai ya jinjina mata alamar hakan yayi,
sai ya kuma yiwa Ahmad alamun ya cire dubu goma ya ajiye mishi,
bayan ya cire goman ne sai ya amshi sauran 50k d'in sannan ya zare dubu biyar ya bawa Adda Rahma yace ta d'auki dubu biyu ta bawa Raihana da Raliya 1-1,500 godiya tayi mishi sosai kana yasa 45k d'in a aljihunshi tare da musu bayanin dasu zai musu kayan salla.
Daga nan sukaci gaba da hira har zuwa 12:15 Am na dare jin masallatai sun fara tahajjudi yasa basuyi batun wani bacciba kawai sukayi al'wala suka nufi masallacin fada dan ba'ayi a masallacin k'ofar gidansu.
3:12 Am aka idar da tuhajjdin,
daga nan kowa ya nufi gidansu,
suna dawowa suka samu Rahma tana kitchen tana d'umama musu zabin, Ahmad ne ya nufi kitchen d'in tare da cewa.
"Adda Rahma nifa ferfesun nan ya ishen, me zaki dafa mana a sauk'ak'e?."
mik'a tayi tare da yin hamma kana tace.
"Dama nayi miya tun da dare dan nasan Ummi tafi son tuwo to nayi miyar bisasshiyar kub'ewa yanzu kuma na tuk'a tuwon semo."
"Yauwa to yafi kam."
cewan Ahmad yana juyawa yayi tsakar gidan inda ya samu Saifuddeen konce yayi pillow da cinyar Ummi,
suna zaune a nan dasu Raihana da Raliya har Rahma ta gama komai, kamar kullum Saifuddeen ne ya karb'i na gidan Babba Ali ya kai musu sannan ya dawo,
yau ya d'anci abinci sosai al'barkacin Ahmad,
bayan sun gama yin sahur d'insune ya mik'e sauri-sauri ya shiga wonka dan ganin an kusa kiran salla,
yana fitowa Ahmad ya shiga kafin ya fito tuni anyi assalatu,
yana fita ya kimtsa yasa wasu kayan Saifuddeen wanda shi kuma tuni ya kimtsa cikin k'ananun kaya wanda sukayi matuk'ar mishi kyau,
tare suka fita zuwa masallaci inda Hayatuddeen ke gabansu.
Suma su Ummi tuni sunyi haraman salla.
Ana idar da sallan Ahmad da sai hamma yakeyi ya yunk'ura zai tashi da sauri Saifuddeen ya kamo hannunshi tare da mishi alamun yayi azkar tukun,
tsaki ya d'an ja tare da cewa.
"Kai ni bacci nakeji."
bai kulashiba kuma bai sake mishi hannuba dole dai ya zauna sukayi azkar d'in a tare.
Suna shiga gida sauri-sauri Ahmad ya gaida Ummi sannan ya nufi d'akin Saifuddeen k'ure iskar fankar yayi sannan ya tura k'ofan d'akin kana ya hau bisa katifar yayi lub tuni bacci yayi awon gaba dashi.
Shi kuwa Saifuddeen bayan ya gaisa da Ummi da Rahma su Raliya suka gaidashi sannan ya tambayesu me sukeso ya saya musu kayan salla,
kab d'insu zabi suka bashi so da haka ya fita ya nufi k'ofar gida inda Salisu ke jiranshi,
yana zuwa suka gaisa kana ya hau yaja machine suka tafi.
Bakwai dai-dai suka isa, Saifuddeen na sauk'a Salisu yaja machine ya tafi,
shi kuma Saifuddeen kamar kullum cikin masallacin nan ya wuce dan baccin da yakeji yau yafi na kullum,
yana shiga ya koma gefe ya konta yana tasbihi a ranshi tuni bacci mai dad'i ya figeshi,
sai k'arfe tara da kwata ya tashi al'wala yayi sannan yayi walaha bayan ya idar ya fita ya tsallaka titi ya shiga cikin kasuwar da tuni ta cika tayi mak'il da bani adam.
Kai tsaye layin kantin kwari ya nufa inda nanne layin da dilansu yake,
yana zuwa ya samu ba kowa a gabanshi nan aka ware mishi aka bashi, daga nan ya cika k'aton kwalin nan ya azashi a kanshi ya fara bin layi-layi lungu da sak'o yana raba musu suna bashi kud'in na jiya.
Cikin awa hud'u ya gama, to yau sai bai nufi karb'o omonba sai ya wuce shagon Alhaji ishaq mai atampopi dasu laces materials shadda da dai sauransu.
Yana isa Alhaji ishaq d'in da kanshi ya tarbeshi fuska a d'an sake yace.
"A Balarabe yau babu omone?."
numfashi ya d'an fidda kana cikin yanayin zafin rana ya mishi nuni da kaya yakeso zai saya,
gane abinda yake nufi yasa Alhaji ishaq d'in nuna mishi ya tsallako ya shigo daga ciki dan ganin mata sun cika bakin shagon nashi mak'il ,
yana tsalla kowa ya shiga Ibrahim ya bashi hannu suka gaisa irin gaisuwar nan ta abokai,
cikin bada umarni Alhaji Ishaq d'in ya cewa.
"Yauwa Ibrahim kama fini gane mgnarshi maza kula da lamarinshi ka bashi duk abinda yake so a farashin sari."
cikin jin dad'i Ibrahim yace.
"Toh ba matsala."
sai ya kuma maida hankalin shi kan paper da Saifuddeen ya bashi inda ya rubuta mishi.
"Ina son atampa masu kyau da taushi guda biyu ka bani masu kyau na Ummi nane,
sai ka bani laces guda uku masu kyau Adda Rahma orange color takeso Raihana kuma lemon green da ratsin white take so,
Raliya kuwa red mai ratsin yellow color,
sai ka had'a musu da atampa d'ad'd'aya masu kyau fa."
cikin kula Ibrahim yace.
"Ba matsala."
sai ya kuma juyo ya fara zabo atampopi da laces masu kyau yan ma dai-dai tan kud'i,
duk wanda ya zaro in ka ganshi saikayi sha'awarshi.
nan ya gama zaro kusan laces kala goma atampa goma,
duk ya jibgesu gaban Saifuddeen,
nan shi kuma Saifuddeen ya fara zab'o wad'anda zai saya laces uku ya zaro sai atampopi biyar biyu na Ummi ne,
sosai ya zabo masu d'an karen kyau.
Wata mata dake cikin taron matan da suka cika bakin shagon ne ta zuba sshi ido tace.
"Kai wannan kekyawan yaro ya iya zab'an abu mai kyau gsky nima to shi zan bawa zab'i."
murmushi mutanen wurin sukayi dan gsky ta fad'i.
shi kuwa Ibrahim kud'insu ya rurrubuta mishi,
bayan ya amshi takardar ya karanta rubutun Ibrahim sai ya rubuta mishi amsa da cewa.
"Nima in nazo nan ba a farashin sari nake baku ledodina ba so nima kada kuce bazakuci riba a kainaba ai ita kasuwa ba k'arya bace kuma dan riba akeyinta sai ni kuma ba sarin zanyiba so naji duk yadda kuka saidawa saura laces in nan nima haka zan biya,
dan haka samin su a leda."
dole a dai yadda suke saidawa kowa a haka ya biyasu.
Daga nan sai ya nufi shagon Alhaji Yawale nan ya sayi wasu datsastsun yaduka masu hegen kyau yad'i ashirin ya saya dan sun bashi tabbacin yadi uku zai isha kamanshi d'inkawa dan haka ya sai yadi ashirin, yayi lissafi yadi tara shida Salisu da Ahmad yadi tara kuma Warisu da Mudassir da Saminu yadi biyun sama kuma Hayatuddeen.
sai ya kuma sayan wani yad'i mai kyau yadi shida uku nashi uku kuma Faruq da Adam,
bayan ya gama biyan kud'in sai ya kuma fito ya nufi shagon su Jabeer nan ya sayawa su Rahma gyale daddaya wanda zai shiga da kayansun duka bibbiyun,
kana yaje shagon masu d'inka hijabai ya d'inkawa Umminshi hijabai guda biyu,
sannan daga nan ya fito da ribanshi na yau ya sayawa Faruq da Adam kayan kanti kala daddaya.
Bayan ya gama had'a kayayyakin da ya sayan sai ya samu kowa ya samu kala bibbiyu sai Hayatuddeen ne ya samu kala d'aya,
so shiyasa ya ciro sauran kud'in nashi ya saya mishi wani yad'i kalanshi mai kyau,
daga nan ya had'a kayanshi kab wuri d'aya cikin irin k'attin ledodin nan,
sannan yaje ya ajiyeshi a shagonsu Hisham daga nan yaje ya d'auko omonshi yayi ta zaga yawa,
Alhamdulillahi yau garin akwai lumshi alamun hadarin forkon damuna sai manyan gajumare masu yiwa sararin samaniya rumfa.
Ya saida omon sosai inda ya samu riban 2,700.
Ganin yamma tayi sai ya saya musu fruits na 700 d'in.
ganin biyar tayi sai ya fito inda Salisu zai sameshi ba tare da ya d'auki kayan daya saya ba,
ya barsu a shagonsu Hisham sabida yana son sai gobe in yazo ya sayawa Goggo Dada da Aunty Nina da Bappa Ali kafin ya meda kayan,
sabida yanaga in ya medasu yau tamkar ya waresu ne.
Koda ya koma yayiwa Ummi bayani,
Ahmad kuma yau bai zoba a zatonshi Saifuddeen zaizo ne.
Washe gari kuwa kamar yadda yayi niya haka yayi,
daya gama hada ribarsa na jiya sai ya sayawa Goggo Dada turmin zani hakama Aunty Nina sannan ya sayawa Bappa Ali shadda mai kyau.
daga nan ya hada kayan sannan ya tafi tallan omonshi.
Biyar dai-dai suka nufi dukku suna isa Dukku,
kamar kullum bayan sun gama komai ne sunje tabsir sun dawo ne ya fito da kayan yayi musu bayani sannan ya bawa Ahmad kayan tare da cewa yau Salisu ne zai maidashi da mashin,
Saminu kuwa nan yake ce musu.
"Yauwa ni nama manta ban gaya muku ba na saya mana takalma da huluna, wanda zamuyi fitan idi dashi dama d'inkin naso in yi mana to sai naga takalma da hulunan zaifi armashi."
sosai suka cika da farin ciki nan Salisu kuma yace.
"To ni kuma zan saya mana agogo masu kyau."
Ahmad ne ya kalli Saifuddeen da yake mishi bayanin wannan 10k d'innan ya sayi kayan d'inki dasu.
harara ya mishi tare da zaro kud'in dan dama ya taho dasu dan ya zargi hakan bashi kud'in yayi tare da cewa.
"Ingo amshesu inada kayan d'inki kai dai ba ka saya ba ka kuma bani to ba ruwanka da batun d'inki in naga dama in d'inka na iyayenane da abokaina da k'annena da yarana in naga dama ink'i dinka naka in d'inka na kowa.
Ga dai kud'inka nadai ci naman dubu d'aya a cikin kud'in jiya."
murmushi yayi tare da amsar kud'in ya sasu a aljihu.
daga nan Salisu yaje ya fidda machine inshi yazo ya maida Ahmad can Shabewa.
Tun daga ranan Ahmad ya fara d'inka nasu na maza.
Shi kuwa Saifuddeen washe gari da yaje kasuwa takalma ya sayawa su Rahma da Ummi dasu Hayatuddeen duk da saida yayi ciko da ribar omonshi na yau d'in.
Washe gari kuma da ya kuma zuwa yan kunne da sarka ya sassaya musu.
A takaice dai saida yayi kwana biyar baya ajiye ribarshi,
a cikin haka kuma ya kuma ya kuma sayan wani kayan yad'i shida ya bada d'inki cikin kasuwar kayan shida abokinshi Is'haqnshi.
tun randa akayi azumi ishirin da biyar ya gama hidiman dinkin salla da komai,
Daga nan kuma yaci gaba da zura kud'i a asusunshi.
Yau saba'an wota ishirin da bakwai kenan,
kuma yau yayi cinikin omo sosai,
k'arfe hud'u dai-dai ya shiga gidansu Is'haq,
Imran na ganinshi yayi sauri ya isa gareshi cikin murna yace.
"Hamma Saifuddeen gobe Ya Is'haq zai dawo yace min shi dai bazaiyi salla a Abuja ba."
kamo hannun Imran yayi wanda bazai wuce sa'an Hayatuddeen ba murmushi yayi tare da shafa kanshi sannan suka shiga parlour Baban Is'haq.
cikin fara'a yace.
"D'an halak kak'i ambato ko yanzu nake jajenka ka kwana biyu baka lek'oba ashe kana tafe."
kanshi ya d'an shafa tare da yin murmushi kana ya rusuna gaban Baba cikin body language suka gaisa har yake shaida mishi gobe Is'haq zai dawo,
sun jima suna hira daga bisani ya mik'e tare da cewa.
"Bari yaje yayi wonka."
daga nan ya fito parlour Mommy ya nufa step mom d'in Is'haq kenan bayan sun gaisa ne ta bashi key d'in d'akin Is'haq da woyarta dan tasan zasu gaisa da abokinshi.
Yana shiga d'akin Is'haq wonka ya farayi sannan ya fito ya canza kayan inda tuni ya wonke wanda ya cire ya shanya.
gefen gadon Ishaq d'in ya zauna tare da fara rubuta mishi sak'o kamar haka.
"Assalamu alaikum, ya gida da Ramadan, Baba ya cemin gobe zaka dawo ko?."
jim kad'an sai ga amsa.
"Wa alaikissalam, nayi fushi da kai yau kwana nawa baka zo gidaba kullum sai na tambayi imran."
bai ida gama karanta amsarba wani sak'on ya kuma shigowa.
"Eh gobe zan dawo ya Rabi'u yayi mana d'inki komai iri d'aya yace wai ai mu tagwaye ne.
A gombe zamuyi salla ai ko?."
murmushi yayi tare da rubuta mishi.
"Allah ya dawo daku lfy ka cewa Ya Rabi'u ngd matuk'a Allah bar zumunci da k'auna, ina Ammi na nayi missing nata tare zaku dawo ai ko.
Hahhm Imran k'arya yakeyi ko last week nazo ai yanzuma hidimar kasuwane ke hanani zuwa yanzuma sauri nake zan tafi."
daga nan kuma ya mik'e ya fita,
har ya mik'a Mommy woyar sai kuma ta mik'o mishi tare da cewa mishi gafa wani sak'on yana amsa yaga abinda ke rubuce.
"Dole fa a gombe zaka zo muyi salla, naga kak'i ka bani amsar inda zakayi salla,
to kuma nasha gaya maka inaso mu kasance cikin ungiyar.
Joint national association of persons with disabilities,
(Jonapwd) gombe state chapter.
All the best!. domin k'ungiyace mai daraja da mahimmanci kungiyace mai zaburar da nakassasu domin su dogara da kansu ta hanyar yin rayuwa kamar ko wanne mai lafiya suna jan hankalin da nusar da nakassasu cewa itafa Nakasa ba kasawa bace, kuma babu nakasasshe sai rago,
suna gina zuk'atan duk nakasashen dake k'ark'ashinsu da nunin nakasar zuciya fa itace sahihiyar nakasa ba irin tamuba ta jiki,
so a sallan ya kamata muje garesu domin had'a hannu dasu."
da sauri ya rubuta mishi amsa da cewa.
"To ba matsala Allah ya kaimu na amince."
yana tura mishi amsar ya sallamesu ya tafi kuma har cikin ransa ya gamsu da shiga cikin sahun members d'in k'ungiyar dan yaga sunada kekyawar niya.
Koda ya koma kasuwa bai wani sake d'aukan Omo ba shagonsu Jabeer yaje suka d'an zauna suna hira dan mutane sun d'an tsagaita shigowa shine ya bawa yaran shagon damar d'an hutawa.
Ganin hud'u da rabi ta godata ne ya sashi mik'ewa tare da bawa Jabeer hannu,
musabaha sukayi sannan sukayi sallama.
Daga nan shagonsu Hisham yaje inda ya samu suma ba mutane da yawa ko dan yanzu kasuwarsu ta d'anyi k'asa sai 'yan tsirarun da suke zuwa sayan kulolin abincin salla.
kusan tare suka fito da Hisham inda yake tambayanshi.
"Gobema zaka zoko?."
kai ya gyad'a mishi alamun eh sannan ya nuna mishi yatsunshi biyu tare da mannasu a goshi alamun rannan salla ma zaizo amman ba kasuwa zai shigoba zaizo wurin best friend nashi."
cikin happy Hisham yace.
"To in kazo zaka isa gidanmu ko?."
ido ya d'an jujjuya kana ya mishi alamun.
"To ai ban san gidanku ba."
gane abinda ya ke nufine yasa Hisham cewa.
"Mu dai-dai ta lokacin da zaka zo sai inzo in sameka a bakin shagonmu sai mu tafi tare muje ka gaida Mom ena."
paper da biro ya zaro kana yace mishi.
"Jabeer ma yace dolefa wai sai naje gidansu wai Umminshi na son ganina so shi rubuta min address insu yayi, kaga kaima gwara kawai ka rubuta min address naku in sha Allah, in Allah ya nufa fa sai kaga nazo."
cikin gamsuwa Hisham ya rubuta mishi tare da cewa.
"In sha Allah, zama kazo."
dai-dai lokacin kuma suka isa bakin San HUSSAIN MALL inda nan Salisu zaizo d'aukan shi,
daga nan sukayi sallama da Hisham, shi kuwa Saifuddeen ya isa gefen masu fruits ya sassayi abinda ya sauk'ak'a, yana gamawa Salisu na zuwa daga nan suka tafi *Dukku d'iyam sad'i na kosam,* garin da ruwa yafi nono tsada, amman fa banda gidansu Saifuddeen dan su har rijiyoyi biyu ne a gidansu d'aya ruwan dad'i d'aya na zartsi, shiyasa duk 'yankin unguwarsu a gidansu ake zuwa d'iban ruwa, rijar dad'in ruwanshi sanyin ko yaushe ruwanshi k'alau ,na zartsin kuwa ko lokacin hutunrune in ka jawo ruwan sai ka sameshi da d'umi dai-dai yin wonka.
Suna isa.
Kai tsaye ya kusa kai cikin gida,
a tsakar gida ya samu Ummi rik'e da botiki,
bisa dukkan alamu ta gama tuyan masa da k'osan dan duk ta sasu cikin manyan kulolin da cikin kayan Rahma suka fito dasu,
ga kuma tukunyar dama kunu yana bisa murhu amman ba ruwa a ciki,
daga can gefe kuma Raihana ce konce lib da alamun bata da lfy,
sai Rahma dake kitchen tana aikin girki,
Hayatuddeen ne da Faruq suka rugo a guje suka nufi inda yake tare da yi mishi oyoyo,
d'aga Faruq yayi sama cak ya ruggumeshi kana yasa hannunshi na dama yana shafa tsakiyar kan Hayatuddeen wanda tuni ya amshi ledan hannunshi,
Ummi kuwa ido ta zuba mishi sosai ya rame alamun rashin hutu k'arara a jikinshi.
gabanta ya iso tare da dire Faruq cikin fidda numfashi ya kalli botikin hannunta kana ya kalli tukunyar dake bisa murhu,
cikin body language yace mata.
"Baki sa ruwa ba."
kai ta jujjuya tare da lumshe ido sannan tace.
"Yanzu zan jawo ruwanma."
juyawa ya d'anyi gefen dama inda randunansu ke jere taku kad'an yayi ya isa inda randunan ke jere bubbud'esu yayi duk babu ruwa a ciki sai kad'an-kad'an ,
gaban Ummin ya dawo tare da mata alamun,
"Ya akayi ba ruwa a randunan me Raihana keyi da bazata ja ruwan ba tunda Raliyya bata nan Hayatuddeen kuma bazai iya dan rijiyoyin suna da d'an karen zurfi,
Rahma kuma na fama da aiki."
juyawa tayi a hankali ta nufi can gefen wata k'atuwar bishiyar maggoro da rijiyoyin ke k'asanta duk suna cikin inuwan bishiyar da sauri yabi bayanta,
suna isa ya zura gugar a cikin rijiyar dad'in, ita kuwa Ummi da sauri ta rik'e tare da cewa.
"Je ka huta zan ja ruwan ita Raihana yau tun da safe cikinta ke ciwo,
Rahma kuma jiya ta yanke a 'yar yatsarta garin yankan lemu."
da sauri ya jujjuya mata kai kana yaci gaba da zura gugan alamun shi zai ja ruwan.
Ita kuwa Ummi tausayinshi ne ya rufe mata zuciya da jiki tasan muddin in dai yana nan tofa baya tab'a yarda taja ruwa, to shi kuma in dai yaja ruwa sai hannunshi suyi jazir musamman yatsunshi da sai sunyi alamun d'ura ruwa, Ummi tafi kowa sani jikin Saifuddeen baya juran wahala yana tsoron wuya so amman sai yake b'oye musu hakan da jarumtar zuciyarshi da take tirsasa gangan jikinshi jajircewa koda ko zai wahala.
ido kawai ta zuba mishi ganin yadda yake jan ruwan da karsashi tamkar baya jin wahalan,
yana cika botikin yaje ya juye mata rabin a tukunyar rabin kuma ya juye a rand'a kana ya yafito Hayatuddeen tare da nuna mishi d'an k'aramin botiki alamun ya d'auko yazo suna kai ruwan rand'a,
da sauri Hayatuddeen ya mik'e tare da suran botikin.
daga nan sukaci gaba da d'iban ruwan in ya cika botikin shi sai ya cikawa Hayatuddeen sannan su d'auka a tare suje su juye a rand'a.
Ita kuwa Ummi tuni ta koma gindin murhunsu na wojen tanata hidiman dama kunun Rahma kuma na kitchen tana k'arisa aiyukanta.
Cikin k'ank'anin lokaci suka cika randa biyu sun fara sawa ana ukun ne Rahma ta fito daga cikin kitchen d'in tana ganin Saifuddeen ne ke jan ruwan tayi maza ta isa gindin rijiyar cikin sauri tasa hannu ta kamo igiyar gugan tare da cewa.
"Ka bari haka ya isa, Ummi ya za'ayi ki barshi yaja ruwa kinsan yanzu hannunshi zai d'uri ruwa."
cikin kula Ummi tace.
"Yak'i ya barni inja kin san ba yarda zaiba, kuma bazai bari mu zauna ba ruwa ba."
fuska ta kwabe ganin ya amshi gugar yaci gaba da jan ruwan,
cikin sanyi tace.
"To ka rink'a ja nida Hayatuddeen zamu rink'a jida,
ni da ka bari ma dan na aika Mudassir yazo kuma nasan in yazo in na sashi ba k'i zaiyiba."
cikin k'arfin hali ya nuna mata alamun karta damu,
daga nan sukaci gaba da jan ruwan.
Suna gamawa ya cika botikin ya shiga wonka,
tuni Ummi kuma ta gama dama kunun,
inda Raihana da cikinta ya d'an lafa ta tashi zaune ta jingina da bishiyar dimurin dake tsakiyar gidan nasu kusan nanne wurin zamansu,
Rahma kuma duk ta had'a komai na bud'a baki har miyar asuba tayi musu tunda Raihana maiyin bata da lfy,
Hayatuddeen kuwa tuni Ummi ta d'ora mishi kulan masa ya kai ya dawo kana ta d'ora mishi na k'osan tare da bashi robar dake cike da dabino a hannu bayan ya dawone ta kuma aza mishi kulan kunun tare da cewa.
"Zaka iya ko autana?."
cikin dakiya da jarumtar da yake koya a wurin Hamma Safuddeen d'inshi yace.
"Eh Ummi zan iya."
kai ta gyad'a sannan tace.
"To in kaje kace a sauk'eka kada kace zaka sauk'e da kanka dan bazaka iyaba."
juyawa yayi yana fita tare da cewa.
"To, duk da yaso yayi irin na Hamma shi duk abinda ake tunanin bazai iyaba sai ya yin, to amman ina ai shi Autan Ummi akwai ragwanci over.
Shi kuwa Saifuddeen bayan yayi wonka yana fitowa ana kiran salla.
Ummi da kanta yau ta zuba mishi madara da sugar bisa kankanan ta kuma wonke mishi dabinon,
yana isa inda suke ya zauna gefe bisa wani dutse wanda nan suke zama suyi al'wala, Faruq ne ya mik'a mishi buta yayinda Ummi kuma ta mik'o mishi dabinon,
Ummi da Rahma da Raihana duk tafin hannunshi suka zubawa ido ganin sunyi jazir tamkar ka tab'a jini ya tsallo,
kan yatsunshi kuma sunfi ko ina yin ja,
cikin muryar ciwo Raihana tace.
"Dan Allah Hamma kada ka sake jan ruwa kalli yadda tafin hannunka sukayi fa."
yi yayi kamar bai gane me take cewaba.
Ummi kuwa kamar tasa kuka takeji dan tausayinshi,
Rahma kuwa hannunta tasa ta shafi tafin hannun nashi ganin duk inda ta shafa sai jinin wurin ya gudu wurin yayi fari sai kuma a take wurin yayi ja kamar da,
sai kuma duk suka juyo kan Raihana dan ganin ta kamo hannun Umminta ta rik'e gam alamun,
ciwon cikin nata ya murd'a,
gaba d'aya jikinta rawa yakeyi dan azaba,
kusan a tare suke ce mata sannu,
shi kuwa Saifuddeen nuni yayiwa Ummi da ta,
had'awa Raihana zuma da ruwan zafi ta bata tasha."
cikin gane abinda yake nufi tace.
"Na bata ta sha tunda da yamma nace tasha amman tak'i wai ita sai ta kai azuminta, to sai yanzu da auta ya kai dabino masallaci yace ansha ruwa to shine ta amshi ruwan zafin da zuman tasha yanzu kuma inaga cikin ya kuma murd'awane."
sai kuma suka bita da idanu ganin ta mik'e da sauri ta zari butan dake gaban Saifuddeen d'in ta nufi band'akinsu,
tuni kuma Al'adar tata ta iso har ya d'an b'ata mata zani,
ai da sauri Saifuddeen ya rumtse idanunshi dan yanada tsananin k'yank'yani yanzu haka bazai sake cin abin hannun Raihana ba har sai yaga ta samu tsarki tana salla,
Rahma kuwa dariya tayi tare da cewa.
"Hmmmm Deeen kenan tunda kai na mijine ai da sauk'i,
sai dai kuma tunda zakayi aure ba mmki wata ran kayiwa matarka wonki."
kame jikinshi yayi alamun tsikar jikinshi ya tashi da batun wai shi dai yayiwa matarshi wonkin wannan k'azantar,
Ummi kam tuni ta bar wurin shi kuwa yawu ya tofar kana ya d'auki pillet d'in kankana ya mik'e tare da yiwa Adda Rahman tashi alamun Allah ya kiyasheshi da sharrin bakinta, dariya tayi tare da bin bayanshi da ido,
tabbas tasan su duka zuriyarsu kyawawane amman babu wanda ya kai Saifuddeen ita kanta wani lokaci ganinshi take tamkar balarabe ko ba indiye,
gashi komai nashi da nitsuwa da tausayawa,
gashin k'eyanshi ta zubawa idanu har saida ya b'acewa ganinta.
Shiko yana fitowa woje yayi gefen su Warisu nan suka shanye kankanan a tare amman time to time yakan rumtse ido in ya tuno jinin da ya gani sai ya kuma tofar da minyau.
Ana idar da salla suka shiga gida inda suka samu,
yau kuma awaran couscous Adda Rahma tayi musu sai masan da ta d'iba musu cikin na masallaci sannan tayi musu miyan alaiyahu da tontok'oshi wanda da miyar zasuci masan,
sai kuma tea da ta kawo musu amman ba madara, dan azumi yazo k'arshe mafi yawanci cefenensu yayi k'asa
sai kuma kunun gyad'a,
nan sukaci sukasha kamar kullum,
sannan suka tafi jin tabsir wanda yau zasu rufe 27 ga watan Ramadan d'in kenan.
Suna dawowa ta kawo musu tuk'ek'k'en tuwon shinkafa da miyar ganye wanda miyar asubane to da yake miyar da d'an yawa shiyasa ta tuk'a musu tuwo,
a zatonta bazasu wani ciba amman kuma sai gashi sun cinye tas yau harda Saifuddeen da yake abinda yake sone Warisu ne ya d'anci kad'an.
Bayan sun gama cine Ahmad ya firfito musu da d'inku nansu baki d'aya,
sosai sukayi mmkin yadda ya gama d'inkunan cikin k'ank'anin lokaci kuma d'inkunan sunyi kyau sosai da salon tsarin d'inkunan wannan shekarun.
Nan Saifuddeen ya bawa kowa nashi,
duk sukayi godiya dama tuni Saminu ya kawo musu takalmansu da huluna Salisu kuma ya kawo musu ogogunansu.
Daga nan duk sukayi sallama suka tafi sai Ahmad da yace yau nan zai kwana,
to bayan su Mudassir sun tafine Bappa Ali da Aunty Nina ma sukazo yiwa Saifuddeen godiya nan sukaci gaba da hira,
a nanne Saifuddeen yace dasu,
Hayatuddeen zai rink'a zuwa wurin Ahmad ya rink'a koya mishi d'inki,
to kuma duk sunyi na'am da hakan daga nan suka d'an tab'a hira sannan duk sukayi saida safe suka watse.
Washe gari kamar kullum suna isa ya d'an shiga massalaci yayi baccin awa d'aya da rabi yana tashi yayi al'wala yayi walahanshi,
yana fitowa kai tsaye layin da zai sadashi da kantin kori ya shiga,
yana isa d'ab da kantin korin ya tsaya a bakin shagon Malam Habu mai saida mayukan shafa da turatuka powder da dai sauran kayan kolliya na mata,
Sadiq na ganinshi cikin fara'a yace.
"Barka da isowa Balarabe."
murmushi yayi tare da mishi alamun bafulatani dai daga nan suka d'an gaggaisa da mutanen layin sannan ya isa dilansu na ledan yana zuwa aka bashi kamar kullum sannan ya fara zazzagayawa ya rabawa kowa.
Koda ya gama sai ya d'auko omonshi nan yayi ta zagayawa sosai kuwa yau ya sayar koda ya gaji ya koma shagon Malam Habu ya zauna yana d'an hutawa dan yana son yaje gidansu Ishaq to ya kuma yanaga kada yaje ya samu basu isoba da wannan tunanin ya bari sai gobe yaje,
cikin body language ya tambayi Malam Habu ko yasa inda gidan Baba Bella yake?."
kai ya jujjuya alamun gsky bai saniba to amman sai ya bashi shawaran yaje ya tambayi Alhaji Aliyu dilansu na ledodin kenan dan yana kyautata zaton shi zai san unguwar da Dottijon yake,
nan yake cewa Malam Habu ya mantane Alhaji Aliyu baya k'asar ya tafi umrah,
to nan yace ya tambayi yan shagonshi wata k'il zasu sani,
toh fa abu kamar da wasa ya tambayi duk mutanen da yake zaton zasu san gidan Dottijon nan baba Bello amman duk sai kowa yace ko unguwar da yakema basu saniba yayinda wasuma sai suke mmki da ce mishi ba yace kai jikanshi bane to ya za'ayi kai jikanshi baka san gidanshi ba sai mu.
Shi kuwa Saifuddeen ribarshi na yau na omo dana leda harda riban omon jiya ya had'an kud'in 10k da nufin zai yiwa Baba bello ihsanin yayi hidiman salla,
to kuma gashi ya rasa wanda yasan gidan,
dole haka ya hak'ura sannan ya bawa malam Habu ajiyan wannan 10k d'in dan ya rigada yayi niyar wannan kud'in Dottijon zai bamawa.
K'arfe biyar nayi Salisu yazo suka tafi Dukku.
Washe gari kuwa ta kama ranar ne ishirin da tara ga watan Ramadan wonda ana zaton ganin watan salla yau ko gobe dan haka da zai fita tafiya gombe sai ya harhad'a duk sauran kud'ad'en da yake adanawa ya sasu a aljihu ya tafi dasu.
To koda ya gama rarraba ledodinshi kamar kullun ya saro omonshi yayi ta yawatawa har aka k'arfe uku saura kwata bayan ya had'a ribarshi ya wuce ya maida omonshi daya rage,
daga nan ya wuce shagon Alhaji Kabiru wanda ake saida duk wani kayan d'and'anon miya kama daga Magi, raico, onga gishiri kafi Mai, Manja, fulawa, madara, sugar, sufageti, macaroni, indomi. da dai sauransu suna bada sari suna saida kad'an-kad'an kuma suma shine ke saida musu ledodin da suke zubawa kostomominsu kaya in sunyi sayayya.
Sun saba sosai da Alhaji Kabiru dan shima yanada d'anshi kurma shiyasa yake tsananin son Saifuddeen,
yana isa bak'in k'aton shagon nasu ya zaro pepar da biro ya rubuta musu duk abinda yakeso,
nan Alhaji Kabiru ya amsa da kanshi ya ware mishi duk abinda ya lissafa bayan ya gama sasu a leda cikin nitsuwarshi yace.
"Masha Allah Saifuddeen Allah yasa Isma'il d'ina ya zama mai nagarta kamarka, kalli yanzu wasu manyan magidan tama basuyi azamar cefenen sallaba amman gashi kai tuni ka gama komai abinka."
kai ya d'an sunkuyar tare da gyara hannun riganshi sannan ya d'ago kanshi tare da yin murmushi cikin girmamawa ya amshi ledan da yake mik'o mishi sannan ya bashi kud'inshi tare da mishi godiya da sallama sannan ya juya ya tafi.
Layin masu yankan kaji yaje nanma ya sashi zabbinshi guda biyar ya bada kudi kana yace musu in sun gyarasu su sa mishi su cikin firij sai k'arfe shida da rabi zaizo ya amsa,
dagana kuma ya sayi jan nama na dubu 3 sannan ya wuce layin masu tattasai, inda yaje ya sayi,
Tattasan, attaruhu, tumatur, al'basa, kabeji, karas, green beans. Da dai sauransu,
sai ya kuma sayi dankalin turawa kond'o d'aya,
daga nan ya wuce shagon da yake saran pure water inda ya samu Rabi'u nan ya sayi katon d'in fanta da Coca-Cola sai rabin ledan molt sannan ya had'a duk su tattasai ya kai aka marked'a mishi sannan ya ware wasu tattasan da taruhu da al'basan kuma wanda ba'a marked'aba ko za'a buk'acesu hakan.
Kana ya harhad'a duk abinda ya sayan a shagonsu Rabi'un dan yasan shi da masu nama suna kai har dare kuma dama ya gayawa Salisu yau sai anyi sallan isha zasu kama hanyar tafiya dukku,
k'arfe uku da rabi dai-dai ya gama duk sayyarshi sannan ya nufi masallaci ganin anata haraman sallan la'asar, baya an idar da sallan ne ya kama hanyan gidansu Ishaq wanda shi kuma tun jiya yake zuba idon ganinshi.
K'arfe hud'u saura mai machine ya sauk'eshi k'ofar gidansu Ishaq dake cikin tudun wadan nan layin fad'a,
yana sauk'a ya nufi cikin gidan,
tare da sallama a ranshi ya shiga.
Mommy ya samu a tsakar gida mai aikinsu tana mata kitso,
tana ganinshi ta fad'ad'a murmushinta tare da bud'a baki cikin d'aga sauti tace.
"Wa alaikassalam lale marhabin da Saifudddeen Ishaq ina kake ga amininka ya iso."
shi kuwa gefenta ya rusuna tare da gaita,
shi kuwa Ishaq da Imaran da Mamansu kusan a tare suka fito,
yana ganin ishaq ya mik'e ya nufi inda yake yayinda shi kuma ishaq k'amshi turaren Saifuddeen d'inne ke masa jagora,
ruggume juna sukayi lokacin da suka had'u sai kuma ishaq ya sakeshi sannan ya ware hannunshi ya manna bisa fuskan Saifuddeen cikin raha yace .
"Iye iyeh my friend watoma kai azumin nan k'ara maka kyau yayi ka ganka kuwa yadda kayi kyau."
dariya sukayi baki d'aya dan ganin yadda Ishaq yakeyin abu kamar mai gani,
shiko Saifuddeen wayar ishaq ya karb'a tare da rubuta mishi.
"To kanari sarkin zance da wanne idon kaga kyan nawa?."
da sauri ya kauce ganin Ishaq d'in zai kai mishi bugu shi kuwa Ishaq cikin fara'arshi yace.
"To kai da wanne kunnen kaji abinda nace?."
murmushi yayi tare da kuma rubuta mishi amsa a wayarshi da duk abinda aka rubuta sai ta fad'i amman shi kad'ai yake gane irin yadda sautin mgnar ke fita dan ko kanaji bazaka ganeba,
"Ni da idanuna na gane abinda kake cewa."
murmushi yayi tare da kamo hannun aminin nashi yace.
To ni kuma da idon zuciyata da tafin hannuna na gane kyawunka."
daga nan kuma sai suka nufi gaban Mama da taketa binsu da ido tana murmushi cikin fara'a tace.
"Yoh ai ba damuwa Saifuddeen ta amininka kake ni kam ko ka kulani."
kanshi ya shafa tare girgiza mata kai kana ya tonk'oshe kai alamun afwan Mama,
daga nan suka gaisa sannan suka shiga parlour Mama nan sukaci gaba da hira suna cikin hira Mama ta fito daga bedroom,
wani d'an k'aramin kwali mai kyau ta mik'owa Saifuddeen, wanda ya zubawa kwalin idanu cike da mmki ya kalli Mama da take ce mishi.
"G...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8
*NAKASA BA KASAWA BACE*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.