Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 6 of 17
"Na rantse da tsarkin mulkin Allah yau sai na ci kutumar uban wancan yarinyar Mai kama da aljanu, wallahi Mutane sunyi gaskiya da ake ce mata dangin Jinnu, ai wallahi yau ko za'ayi yak'in duniya na biyu sai an biyani duka kud'in tsire na na rantse kuwa".
Hakuri mutane suka rink'a basa amma ina sai tsine ma su Fad'ime yake daga ita har K'awayen nata, yana Allah wallahi sai an biyasa kud'in tsirensa ko za'ayi mi.
______________
Dai-dai sun iso wajan amsar nik'a, suka ja birki suna sauk'e lumfarfashi.
Dariya kawai Fad'ime keyi su Laure na tayata.
"Kee amma Fad'ime kin shammace sa fa, kawai sai dai yaji saukar k'asa akan kayan sana'arsa".
Cewar Laure tana rik'e cikinta domin ji take ya d'aure sosai, saboda gudun da suka sha da kuma uwar dariyar da suke.
Sauk'e lumfashi Kad'an Fad'ime tayi tana yin gaba taje inda ake saka layi domin amsar nik'a, ita bata sa layi ba ta shige gaba kawai.
Tana cema su Laure.
"Ai kad'an ma ya gani ya ci gaba da tab'a min iyaye sai na yi sanadiyar rugujewar sana'ar tasa walla...
Maganar Fad'ime ce ta mak'ale jin yadda aka wani bangajeta ta fita daga gaban data shiga.
Wata yarinya ce mai jiki sosai k'ibarta har tayi yawa tana kallon Fad'ime data ture tana cewa.
"Keee baki ga layi ake sawa bane?, sai ke isassa kin wani zo kin shige gaba, dama na dad'e ina jin rashin kunyarki to yau da alama zan sauk'e miki ita ne".
Tashi tsaye Fad'ime tayi tana kakkab'e jikinta saboda har sai da ta fad'i lokacin data bangajeta, domin ba k'arama bace wacce ta ture tan, bata jin wannan ko d'an bigeka tayi ba zakai taga-taga zaka zube k'asa ba, yo wannan abu kamar buhu.
Duk irin girman yarinyar hakan bai sa Fad'ime jin wani abu ba, bare azo ga tsoro.
Rik'e k'ugu tayi tana matsowa sosai inda take ido cikin ido ta kalleta ta ce
"Ni kika bangaje?".
"An bangaje ki d'in, ko akwai abunda zaki yi ne?".
Ta fad'a a tsawace tana sake matsowa sosai kusa da Fad'ime kamar zata had'iyeta da ranta.
D'an shafa kanta Fad'ime tayi tana kallon su Laure kyafta masu ido tayi, ai ko suna ganin haka suka shige wajan nik'an da gudu suka warto nik'an dake ajiye, an nik'a shi, suka fito da gudu sukai gaba, mai nik'a na faman kiransu su bashi kud'i, amma Ina sunyi gaba. Fad'ime kuma ganin hankalin mutane ya koma wajan su Laure har wacce ta tureta ma tana binsu da kallo. Batai aune ba kawai taji anyi sama da ita an fyad'a da k'asa ji kake timmmmmmmmm.
Yadda kasan an kada gini.
Kamin ta gama dawowa dai-dai taga Fad'ime ta haye ruwan cikinta ta kama fuskarta sai yakushi take tana kai mata naushi a ciki, sai k'ok'arin k'are kanta take amma ina, taji uwar bari sai kuka take tana kiran azo a ceceta zata kasheta.
Duk irin taruwar da jama'a sukai wajan suna k'ok'arin b'anb'are Fad'ime a jikin yarinyar nan amma Ina abun ya gagara. Shi kansa Mai Nik'an dole tasa ya fito daga Shagon nik'an aka taru dashi ana sun kwace Fad'ime daga jikin baiwar Allahn.
Da kyar da sub'in goshi aka samu Fad'ime ta saki Y'ar mutane, tana uban nishi, tana tashi kuma bata tsaya ba ta k'ara gaba da uban gudu kamar wata zakanya.
Tashi tayi da kyar yarinyar tayi tana kuka. Wata ce ta rik'eta tana cewa.
"Binta mi yasa kika ja Fad'ime, wadda kowa yasan Fad'ime duk garin nan shaid'aniya ce, duk bala'inka waccar yarinyar ta fika".
Kuka Binta ta k'are fashewa dashi tana cewa.
"Na rantse da Allah bazan yarda ba, idan na yarda Allah ya tsine min, wallahi saina gaya ma Innata, wallahi yau sai an d'akko masu Y'an Sadda ko waye ya tsaya mata a garin nan wallahi".
Buguzun-buguzun ta wuce gidansu tana k'ara b'are baki.
__________________
Dandazon jama'a ne a k'ofar gidan su Fad'ime sun taro kowa na tofa albarkacin bakinsa, hayaniya ta kaure sosai a k'ofar gidan mutane na cewa.
"Ai wallahi a fiddo mana ita nan muci uwar shegiya tunda ta addabi kowa a cikin gari".
Inna Fatuh dake tafe har sauran kad'an ta kife a k'asa, ta fito k'ofar gidan tare da su Inna Lami da Malam dake biye dasu, da duk mutanan gidan.
"Wai miye ne da naji anata kiran sunan Jikata ne?"
D'an juma mai tsire ne yayi saurin cewa.
"Ai na rantse da Allah yau sai an biyani kud'in tsire na, Jikarki Fad'ime taje ita da K'awayenta suka watsa min k'asa a cikin tsire na, dan haka tsire na, na kusan dubu talatin ne, kuma wallahi ko za'a sake yak'in duniya na biyu sai an biya ni kud'i na, ko mu had'u a Ofishin Y'an Sadda".
"Ai ba kai kad'an bama Malama D'an juma, ni Yaro na ta kama ta kantsama ma Mari har jinsa ya d'auke, dan haka wallahi ko za'ayi mi yau sai tazo ta maido masa da jinsa yadda yake wallahi, ina nan ina jiran Jikar taki".
Cewar wata mata dake rik'e da Yaron har yanzu baya jin abunda ake cewa sai kuka yake.
Inna Fatuh ta wani k'ank'ance ido tana kallonsu d'aya bayan d'aya ta ce.
"da'aAllah Malamai ku tsaya min na ce, nasan dai Jikata bata jan fad'a sai an tab'a ta, su yaran naku baku tabbaye su miye sukai mata bane?, Kai kuma D'an juma akwai abunda kayi mata kaima wallahi. Kuma bamai tab'a min Jika wallahi ehee".
Inna Fatuh ta k'are maganar tana turo kallabi gaban goshinta, dan ko hijab bata sa ba, wani gyale na yafo saman kafad'arta.
Zasu sake magana wata mata ta shayo kwana ita da d'iyarta rik'e a hannunta had'e da Y'an Sadda guda biyu biye da ita fuska murtuke.
"Mun shiga uku, ku kuma fa, daga Ina?".
Cewar Inna Lami tana rik'e k'ugunta.
"Zuwa mukai a kama Fad'ime ta kama Y'ata Binta ta haye ruwan cikinta ta kama bugunta kamar ta sami Jaka, yo ko ni dana haifeta ban tab'a mata irin wannan uban dukan ba, dan haka banga ubanda ya isa ya bigeta haka na kyale shi ba wallahi".
"Wayyo Allah na shige su ni Inna Fatuh, ace duk garin nan duk an tsani Jikata, kamar ita ce kad'ai yarinya a cikin garin nan. Shine ke baiwar Allah harda zuwa ki kwasu Y'an Sadda domin kawai su kama Jikata?, ai ko wallahi banga wadda ya isa ya kama Jikata ba ehee kiji da kyau".
"Haba haba haba Inna Fatuh, Fisbilillahi sai tare ma Fad'ime fad'a kike al'halin kinsan ita ce wacce keda laifi. Ki bari kawai ma ta dawo daga yawon ta zubar d'inta su kamata su wuce da ita can Ofishin Y'an Saddan, su lallasa mana ita ma ko ta d'anyi halkali ma"
Cewar Auta yana duban Inna Fatuh.
Wata dak'uwa Inna Fatuh ta makama Auta tana cewa.
"Ungo nan Auta, kaci gidanku na ce kaji, idan kaga an tafi da Fad'ime to sai dai a had'a da ni da Ubanka duka a tafi damu wallahi".
"A'afa wannan d'aya, sai dai keda Fad'imen za'a tafi da ku amma dai banda Malam wallahi"
Malam ne ya kalli Auta ya ce .
"Karka sake magana a nan wajan, wuce ka shige gida na ce".
Malam ya fad'a yana nuna Auta dake kallon Inna Fatuh fuska ba Rahma.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.