Complete Hausa Novels

Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 9 of 17

Ba tare da FAD'IME ta gama shanye raken da ga gabza ba ta ce.

“ke Laure banason gulma fa ki bar wani nuƙu-nuƙu ki fito ki sanar dani mene ne yake faruwa...”

“au da gasken baki sani ba ke nan to dai gobe aurenki da Ɗan Abba Mijin Zulay kacao-kacao gaba ɗaya ƙauye labari ya ɗauka a kan za'ayi miki Auren dole da Ɗan Abba Mijin Zulay kacao-kacao....”

“Kutm*r ub*a! kayyasan can...”

Zagin da FAD'IME ta mulmulo ya sa Sa'ade da ta katse ta tana bayanin ta yi tsitt tana zaro ido don kuwa a yadda FAD'IME ta yi wannan ashariya zata É—auka mutanen nata ne suka motso....

“wata FAD'IMEn kike magana a kai! Sa'ade kada ki ce mini ni FAD'IME kike nufi?”

FAD'IME ta yi maganar idanunta a wani wawware tana duban su Laure da Sa'ade gaba É—aya sai dai wannan karon ba a zafafe ta yi maganar ba, ba kuma cikin nutsuwa ba sannan ta yi maganar ne tana nuna kanta tare da sakin wani shu'umin murmushi.

Sai dai kafin ga ɗayansu ya kai ga bata amsa suka ga an yi sama da FAD'IME sannan a ka saketa ta faɗi ƙasa bata gama dawowa hayyacinta ba a ka shiga kifa mata wasu zafafan maruka hagu da dama sai lokacin suka lura da Zulay kacao-kacao da wasu ɗirka-ɗirkan maza biyu dake tare da ita kuma ɗaya daga cikinsu shi ne ya yi ma FAD'IME wannan aika-aika yayin da ɗayan shida da Zulay suke tsaye sai wani numfashin tafarfasan zuciya Zulay ke fitarwa ta riƙe ƙugu tana bin FAD'IME da kallon banza.
FAD'IME da mamaki da kuma ɓacin rai ke nuƙurƙususarta ta miƙe tsaye tana karkaɗe jikinta sannan ta dube mutumin ta ce.
“Waye kai ɗan uwa kuma waye ya saka ka yi gangancin ɓata lafiyar Dangin Jinnu to ina tabbatar maka da ka taɓo tsuliyar dodo domin ba zamu taɓa lamunta ba dole a yi maka hukunci daidai da abin da kayi.”
A tare Laure da Sa'ade suka kalli juna jin kalaman da ke fitowa daga bakin FAD'IME da ta juya musu baya tana fuskantar mutumin sai dai kafin É—ayarsu ta kai ga furta komai Zulay ta wani saki dariyar bosawa tana kallon FAD'IME É—aiÉ—ai ta ce.

“sannu Dangin Jinnu! Nace sannu Dangin Jinnu to ina tabbatar miki da ba Dangin Jinnu ba ko Dangin ifritu ce ke yau ban ga mai hana na lallasaki ba...”

Kalaman Zulay suka tsaya cak sakamakon juyowa da FAD'IME ta yi tana fuskantarta idanunta sun sauya kala daga na Brown kamar na mage zuwa baƙi mai ratsin ja.

Murmushi FAD'IME ta saki tana faɗin “mene ne na hanzari Aunty kacao-kacao ai sai ki bari nazo kanki ko”

Ta faɗa tana ƙari sawa wurin da Zulay take tsaye jikinta na rawa amma duk da hakan ta yi ƙarfin halin faɗin. “ai kuwa dole nayi hanzari tun da har kika shiga gonata a tunaninki zan bari inaji ina gani ne ki auremin miji hahaha ai bazan taɓa bari hakan ta faru ba shi ya sa ma na hayo waɗan nan ɗirka-ɗirkan mazan majiya ƙarfi su lallasa min ke ta yadda ba zaki ƙara moruwa ba har abada. John a fara aiki.”

Zulay ta ƙare maganar tana sakin dariyar mugunta tare da kallon Wanda ke kusa da ita, ta yi tana yi masa nuni da FAD'IME dake tsaye ta harɗe hannu ko'a jikinta da jin kalaman Zulay..

*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_

©By Zahrah Royal Star & Nainarh KD

06

Aikuwa mutumin da Zulay ta kira da John gadan-gadan ya nufi FAD'IME yana sakin dariyar ƙeta cike da annashuwa na ganin banza ta faɗi Yarinya kyakkyawa haka a ɓagas.

Sai dai me? Taku ɗaya biyu ya yi a na ukun ƙafarsa ta maƙale ya kasa gaba bare baya duk kuwa da yadda yaso sai dai duk da hakan bai haƙura ba ganin wanda suke tare shi ma ya nufa Faɗimen gadan-gadan yana suɗe baki ya sa ya kai hannu zai fizgota ai kuwa saukar hannunsa saman kafaɗar Faɗime ya yi daidai da wani irin azababen duka da a kai masa a gadon baya Yayin da hannun nasa yaji shi tamkar ya sauka a kan wuta saboda wani raɗaɗin azaba da ya ziyarce shi ai kuwa ba shiri ya durƙushe a wurin tare da fasa ihu jin an ci gaba da zuba masa duka a gadon baya.

Cike da takaici ɗayan yaja wata doguwar tsuka yana kallonsa ya ce. “amma fa gaskiya John ban taɓa sanin haka kake ba ai ka bada maza Bara kaga yadda cikakken Namiji yake ji da Mace irin wannan kucakar ƴar ƙauyen domin ba Dangin Jinnu ba ko ƴar sarkin Jinnun ce da kanta tun da har an biyani ban ga abin da zai sa na kyaleta ba.”

Ya ƙare maganar tare da ƙari sawa wurin Faɗime har da gudunsa yana wani ihu tamkar ɗan kwallon da ya sama nasara.

Baya Faɗime ta yi daidai ya miƙo hannunsa da niyyar fizgota ta yi saurin sa hannunta ta riƙe hannun nasa da kyau tare da murɗewa ji kake Hannun ya bada ƙara alamar an karya shi ai kuwa sai ya zube shima a ƙasa yana zambaɗa ihu tare da magiyar ta saki Hannun.

Sakin hannun nasa FaÉ—ime ta yi tare da nufar Zulay da ta fara ja da baya cike da tsoro baki na rawa ta ce.

“ku...kuyi haƙuri na tuba Wallahi nabi Allah na kuma biku haƙiƙa na yarda Faɗime Dangin ku ne kuma ba wanda ya isa yaja da ita ya zauna lafiya...”

Zulay ta kai maganar wani fitsarin tsoro yana ƙoƙarin kwace ma ta hawaye da macijina sun gama wanke baƙar fuskarta.

Dariya Faɗime take tana dunƙule hannu ta ce. “me ma kika ce yau zaki saka a mayar dani ta yadda ba zan ƙara moruwa ba ko? To kafin ki mayar dani haka ni bara na fara canza miki halitta tukunna.”

Faɗime ta kai maganar tare da saka yatsunta mai cike da ƙumba ta karce gefe da gefe na fuskar Zulay ai kuwa take wurin ya fara fidda jini kaɗan kaɗan Zulay kuwa ta saki ihun azaba tana riƙe fuskarta tare da birgima a wurin faɗi take.

“jama'a ku kawo ɗauki Faɗime ta kasheni zane ta yi min a fuska da zaƙwa-zaƙwan ƙunbarta”

“mun shiga uku Faɗime ki kyalesu haka kizo mu gudu tun kafin kiyi kisan kai.”

Cewar Laure cikin tashin hankali tana janyo FaÉ—ime ai kuwa da gudun bala'i suka bar wurin gudu suke basu dakata ba sai da suka shiga kwanar da zai sadasu da anguwansu Laure sannan ne suka tsaya kowaccensu tana faman sakin numfarfashi na gudun da suka sha.

Laure ta ce.

“faɗime kin faɗar min da gaba wallahi nayi zaton da gaske ba ke ba ce.”

Ita kuwa Sa'ade cewa ta yi.

“wai Allah su Zulay kacao-kacao kuma shikenan an yi ma ta zanen barebari.”

Gaba É—aya suka kwashe da dariya.

Sa'ade ta ƙara da faɗin. “wai amma Faɗime ba zakiyi wani abu ba haka kina ji kina gani zaki bari gobe a ɗaura miki Aure da wancan Ɗan Abban bayan kin fi kowa sanin halinsa na neman Mata?”

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.