Complete Hausa Novels

Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Faɗime Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 5 of 17

*FAƊIME...💋🌸💕*
_(Dangin Jinnu)_

©By Nainarh KD & Zahrah Royal Star

*Dedicated to Salma Ahmad Isah (Candy)*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*A love & Laugh story that will capture your heart and soul.*

04

*FAD'IME POV*

"Inna Fatuh kiyi sauri ki ban kud'in nik'an mana, K'awaye na na jira a waje fa"

Fad'ime ta k'are maganar tana kallon k'ofar d'akin Inna Fatuh.

Da sauri Inna Fatuh ta fito tana k'irga kud'i, ta kalli Fad'ime dake dubanta ta ce.

"Y'ar albarka Fad'ime ta, dan Allah karki tsaya wasa da jan matune fad'a kinji, kar a kawo min k'ararki yau kinji, karki tsaya ko ina ki amso nik'an kawai ki dawo gida kinga yamma tayi"

Turo baki kawai Fad'ime tayi tasa hannunta ta amshi kud'in tayi waje da gudu.

Tana gaf ficewa daga zauran gidan kawai taji ta bangaje mutum, bata tsaya bada hakuri ba zata k'ara gaba, taji an jawota ta baya an d'auke ta da wani irin Mari tasssss.

"Kan uba"....

Fad'ime ta fad'a tana ware idonta akan Auta dake tsaye yana kallonta cike da jin haushinta sosai, duk da yasan tab'a Fad'ime a wajansa ba abu bane mai dad'i da zai biyo baya.

"Banza shashasha kawai mai kama da aljanun farko, komai mutum zaiyi bayayi irin na mutane, dubi ke dan Allah kamar wacce aka tonu daga kabari".

"Auta ni ka mara?".

"Na mare ki ko zaki rama ne?"

"Hmmm bazan rama ba amma ka guje abunda zai biyo ba, sanadin wannan marin da kayi min wallahi".

"Idan kin fasa yi min wani abu kin raina Allahn daya halacci ki kinji?, aikin banza kawai".

Ya k'are maganar yana k'arawa gaba ya shige cikin gidan.

"Uhmmm"

Kawai Fad'ime ke yi tana rik'e da kuncinta har yanzu, wani mugun haushin kanta ma take ji mi yasa ma bata d'aga hannu a nan take ta sauke masa marin ba, komai ta fanjama fanjam.

Juyawa tayi ta idasa ficewa daga gidan. Tana fita ta iske su Laure da Sa'ade na jiran fitowarta. K'awayenta ne tun sadda suka dawo gidan Gadonsu, a unguwar suke, tasu ta zo d'aya tsabar suma ba jin magana suke ba.

Tafiya suke buguzun-buguzun, basu aune ba suka ji wani Yaro dake d'an nesa dasu yana cewa.

"Wayyo Jama'a ga dangin Jinnu can ta biyo hanya dangin Aljanu kenan"

Ya idasa fad'ar haka yana nunama wasu Yara dake kusa dashi.

Wani mugun b'acin rai ne ya kama Fad'ime duk duniya idan akwai abunda ta tsana to ace mata dangin Jinnu.

Da gudunta ta k'arasa inda suke, kwai sai dai suka ga tsayuwarta a gabansu kamar wata walk'iya.
Zaro ido sukai a waje suna rarraba ido, wadda ya fad'i maganar ne yayi saurin juyawa zai baza da gudu, kamar walk'iya Fad'ime ta rik'o hannunsa tana kallonsa, jijjga jikinta take tana jefa masa wani mugun kallo.

Laure ce ta rik'e sauran yaran ita da Sa'ade suna cewa.

"Ubanwaye kuke kira da dangin Jinnu iyee?"

"Wallahi Allah bada ku muke ba"

Cewar wani daga cikinsu yana fad'ar maganar jikinsa na d'aukar rawa.

Wadda Fad'ime ta rik'e kuwa yana ji da rashin kunya bai san abunda zai biyo baya ba, yana ji da rashin kunyarsa, saboda wani abu bai tab'a had'asa da Fad'imen ba sai yau.
Ya ce "kaii Isah an fad'a d'in, ance K'anwar Jinnu, ai haka mukaji mutane na fad'a, muma kuma munje mun fad'a, laifi ne mukayi dan mun fad'i sunan da mutane ke fad'i akanki?".

Wata muguwar shak'a da Fad'ime tayi masa, yasa shi fasa wata gigitacciyar k'ara, bai gama dawowa dai-dai ba, tasa d'ayan hannunta ta d'aukesa da wani gigitaccan mari. Wasu taurari ne yaron yaji sun gifta masa, kunnansa ne yaji yayi wani dummmmm, gaba d'aya jinsa ne ya d'auke kwata-kwata baya jin abunda ke wakana.

Fad'ime ta kallesa tana cewa.

"Daga yau idan kunga na taho ku tsaya dan Allah ku jani kunji, idan banci kutumar uban Yaro ba".

Duk abunda take fad'a fa kwata-kwata yaron nan baya ji, jinsa da gaske ya d'auke. Ai ko yana fahimtar haka ya saki wani mugun kuka mai k'ara yana fad'uwa k'asa yana birgima yana magana da k'arfi yana cewa.

"Wayyo Allah na shiga uku na, jama'a ta dod'e min kunne bana ji kwata-kwata, jama'a ku taimaka min na shiga uku".

Abunda yake fad'a kenan yana uban kuka.

Sauran yaran kuwa wani fitsari ne ya kwace masu, sakinsu su Laure sukai suna dariyar mugunta suka kalle suna cewa.

"Abunda yasa zamu barku kuma dan baku fad'i sunan nan bane, kuma zaku iya zuwa ku gaya ma iyayensa, sai a fara nemar masa magani, dan da alama ya kunnansa ya daina aiki".

Suna fad'ar haka Fad'ime tayi gaba suka take mata baya.

Sunzo wani wajan mai tsire kawai Fad'ime ta tsaya tana had'iyar miyau, matsawa tayi kusa sosai da mai tsiren tana cewa.

"D'an juma mai tsire a yanka min na d'ari uku"

Washe baki D'an juma mai tsire yayi yana kallon kyakykyawar fuskar Fad'ime yana lashe baki ya ce.

"Ahh masoyiya Fad'ime ke ce a tahe keda K'awayenki?".

Murtuke fuska Fad'ime tayi tana jin haushin D'an juma mai tsire, wai masoyayirshi, Ubangiji ya kiyaye mata ta so wannan bawan Allahn.
Wani tsaki taja tana k'ank'ance ido ta ce.

"Kaga D'an juma idan zaka bani tsire na d'ari ukun dana ce ka yanke min, ka bani kawai bana son yawan surutu kaji Malam, ko wace ma masoyayir tashi?".

Ta k'are maganar tana harararsa.

Washe baki ya sake yi, shi dai tunda za'a masa ciniki ai ta wuce, domin son kud'i ne da shi baya jin ko yana sonta zai iya bata tsiren nan a kyauta.

Sa'ade ta matso ta kalli Fad'ime a sadda D'an juma ya mik'o mata tsire yana cewa a bashi kud'insa. Hararsa tayi ta ce "kaga na cinye na tafi ban baka kud'inka ba?".

"Ahh to ai kin san bana da mutumci akan kud'i na"

Banza dashi tayi tana jin Sa'ade na cewa.

"Amma Fad'ime karki ci masa tsire kuma al'halin baki da ko sisi fa".

Wata harara itama Fad'ime ta maka mata, ba shiri Sa'ade ta tsuke bakinta tayi shuru.

Guda d'ai-d'aiya ta basu suka amsa suka cinye suna tand'e hannu.

Sai da ta gama ci sana ta kalli D'an juma ta fiddo kud'in nik'an da Inna Fatuh ta bata naira d'ari ce ta mik'a masa.

Amsa yayi tana washe baki, can ya murtuke fuska tamau ganin naira d'ari ce, kallon Fad'ime yake, bala'i cike da cikinsa.

"Kan uba Fad'ime kinga nawa kika bani kuwa?".

"Na sani mana"

"To miye kike nufi dani".

"Yo mifa nake nufi da kai, iya kud'in da nake da su kenan, kama gode Allah ka samu d'ari d'in".

"Ai ko yau akwai bura uba a garin nan, keeeee Fad'ime ni zaki ci ma tsire ki tsaya ido cikin ido ki ce bazaki biya ni sauran kud'i na ba?, to ai ko uwar data haife ce ta dawo duniya na rantse d........ Maganar ce ta katse jin an wasa masa k'asa har kan idonsa.

Murza idonsa yake a haukace, yana murja ido da kyar ya bud'e idon nasa muten sun zagaye shi.

Ihu ya saki ganin yadda tsirensa ya b'aci da uwar k'asa a cikinsa gaba d'ayansa ya lalace, babu wadda zai iya cinsa a haka.

Hango su Fad'ime yayi sun baza da gudu.

Wani ihu ya saki yana cewa.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.