Baqin Ciki Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Baqin Ciki Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 5 of 9
BAKIN CIKI 2***9 Abba bai ga ta zama ba, 7:30
suka kama hanyar minna shida Alh. Adamu tare
da Umma, domin ita tana bukatar ganin likita.
Saboda ha ane aka tafi da Inna saude don ta
rinka taimaka mata. Basu iske abdulkareem a
gida ba, ya riga ya fita aiki. Hankalin Aunty Rabi
ya dugunxuma nan da nan ta dauki waya ta kita
wayar ofis dince, Yaya abdul yaji kamar zai
mutu, saboda tsabar bacin rai, amma ba yadda
zaiyi ya fito saboda tsarin aiki irin na banki.
Daga nana aunty amina ta kira, itama ta shaida
mata, kafin ayi haka labari ya gauraye ko'ina.
Asibiti suka fara aje Umma tare da inna saude.
Aunty Rabi itace jagora domin asibitin da banki
ke da reg da su ne. Daga can da Abba da alh.
Adamu suka dumfari gidan marafa. Da ganin su,
gaban Mami ya fadi, fara'ar karfin hali kawai
takeyi. Bayan su natsu a falo. Abba ya tambayi
marafa? Tace, ai kuwa yayi sammako ya tafi
Lafai, don shaidawa mutannan gida maganar
daurin auren, shi kuwa ango na san ya ma kai
zariya yanxun Insha Allahu. Kasan a can
yawancin abokansa suke saboda can yayi krt.
Ina fatan lfya? Ya sauke numfashi idanuwan sa
suka kara juyewa yace, babu lfya Hjya, Ki
Innalillahi Wa inna ilaihir raji'un! Alh. Adamu ya
gaya mata. Ya gayara xama, yace hajiya
wannnan al'amari babu dadin ji, a takaice dai
sakeena ta gudu tun jiya har yanxu ba mu san
inda take ba. Tsaye ta mike dafe da kirji, ta yi
me? Ta kame a hakan bata iya kara komai ba.
Abba yace, nayi iya yina Hajiya, amma mama ta
nuna min ta karfina, hanyar da zabarwa kanta ta
wuce da sani nan. Kuyi hkr hajiya, ni ban ma san
da kalmar da xan gaya maku ba. Ta koma a
hankali ta zauna cikin kasala tace, ai shikenan,
duk abinda Allah yayi daidai ne, mu mun hkr,
Allah ya musanya wa Al- ameen da mafi
alkhairi, sukayi ji. Shiru kafin Abba yace mu na
nan garin nasan har Alhji ya dawo. Itama hajiya
tana nan na kawo ta asibiti tun jiya ciwon ta ya
tashi abin sai yadda Allah yayi. Ta maida tagumi
tace, dole Umma tayi ciwo, ubangiji Allah ya
bata sauki ya kuma shirya mana zuri'a, suka
amsa amin. Suka mike sukayi mata sallama
suka tafi. Hawaye suka kubcewa mami, hannunta
a kunci tace, ta faru ta kare kowa sai ya hkr!
Tab, wannan yarinya ta daure min kai. Allah
kayiwa Al-ameen sakayya! Iya da ladi suka jiyo
hajiya na sambatu, suka fito suka taushi
xuciyarta, babu bata tym ta sa driver ya kaita
Lafai. Gado aka ba Umma, saboda yanayin jikin
nata, yana bukatar kulawar likita sosai domin
jininta ya hau, har ya haye yadda ko alama ba 'a
so. Anan su abba suka ci gaba da zama har
karfe 4. Yaya abdulkrm ya samu ya baro ofis.
Kai tsayr asibitin ya nufa a sukwane. Da ka dube
shi, kasan ransa a nbace yake, yana ganin
Umma kuma al'amarin ya kara gigita shi. Ya
dubi Abba ido jajur! Yace, yanxun wane mataki
aka dauka? Abba yace, ni na sallama mama,
tunda ta iya toazarta ni haka. Na kuma je gidan
su Al-ameen, matslar kawai ban same su bam
duk sun tafi raba goron gayyata, sai hajiya na
samu shaida mata. Alh. Adamu yace amma ni
ina ganin zai fi kyau abada cigiyar a gidajen
Radio da Tv. Abba ya amshe, da kudin wa?
Saceta akayi? Ba xan kara asara ba, yadda ta sa
kafa ta bar gidana, ta tozarta ni, ta wulaknata
ni, ta nuna min ban isa da ita ba. Wlh ni ma na
hkr da ita. Ba xan yi mata baki ba, dan ko bance
wani abu, tabbas ita da kanta ta kai kanta
mkrntar koyo hankali. Za ku ce na gaya maku.
Taje duniya cem ta ishi kowa riga da wando har
da mayafin yafawa. Ya abdulkrm ya numfasa,
yace ta yiwa knata, Allah ya shiryar da ita, yasa
ta gane, suka amsa da amin. Jimawa kadan ya
ba Aunty Rabi mukullin mota ta wuce dauko su
Ameera daga sch. Kai tsaye ta wuce da su gida.
Ta kama hidimar shirya abinci. Tana gamawa ta
kwashe gaba daya da yaran suka koma asibiti.
Ta iske kofar dkin da Umma take dankam! Da
Jam'a, ashe bayan tafiyarta kadan su ya Abdul
kadir da abdulrhmn suka iso. Can kuma sai ga
dady da mami. Al-ameen ne kadai bai dawo ba.
Duk tabisu ta gaida su. Dady kam yama rasa
yadda xai fassara al'amarin Allah ya sa bai riga
ya yayyada xancen ba ko 'ina, iyakar sa cikin
babban gidansu. Allah ya kawo Mami tayi masa
birki. Shi kansa yadda yakeji a tym din, idan
xa'a gwada jininsa dole ace ya hau, amma daya
iso ya dubi halin da iyayen Mama ke ciki sai
yaga ashe shi nafila ne, tashin hankali na inda
yake. Shi yasa ya nutsu sukayi magana ta
fahimta da abba...... Ya Dubi halin da Iyayen
Mama ke ciki sai ya ga ashe shi nafila ne, tashin
hankali na inda yake. Shi yasa ya nutsu sukayi
magana ta fahimta da Abba. Suka dauki komai
suka barwa Allah tare da rokon Abba daya
amince ya bawa mama wanda ta sake xaba.
Abba bai ce komai ba anan. Don baya jin zai iya
ba Danliti 'yarsa su hada zuri'a da mutuncin sa
da komai a gari. Yanxun tunaninsu dan gogan.
Yaya al'amarain zai kasance? Bayan abba ya
kauda masa duk wani shakku, ya bashi tabbacin
babu wani face shi, shi ya kara karfafa masa
gwiuwa har ya sami kafar tafiya gayyato abokan
taya shi murnar angwanci? Wannan amsa sai
wanda ya gani da idanuwansa. Gab! Da kiran
sallah magriba duk suka bar asibitin, aka bar
Inna saude ita kadai tare da Umman, wacce har
yanxun barci takeyi, domin allurar da akayi mata
mai karfi ce sosai, saboda ana son ta samu hutu
kwarai da gaske. Su dady na isa gida, kamar
tare suke da Al-ameen. Bai fhimci komai a
fuskokinsu ba, don basu yarda yaga sauyi ba ya
baje a kujera yace, wsh! Ai fah an fara kenanm
kinji yadda naga ji Mami? Ta danyi murmushi
tace, dan Iya kena, to abinda ya kamata ka
hanzarta yin wanke ne, don gab ake da kiran
magriba. Haka za'ayi Mami na, dadi ya aka baro
mutanan Lafai? Ina fatan zaka jaddada musu su
taso da wuri? Wannan ai dole ne, kama san
kawunka ba shi da wasa. Yana ta far'a gaskiyya
ne ni ma frnds dina ne ce masu kai tsaye su
wuce Fandagori, ai gidan Uban dawaki ba
boyayye bane, suna tambaya za'a nunna masu.
Dadi yace, kayi daidai, yanxun tashi ka shiga
wankan nnima shi xanyi aga wanda xai riga
fitowa cin abinci. Ya mike xumbur! Yana dariya
ni ne xan riga Dadi, to shikenan, mami ki na ji
ko? Idan kuma na riga shi bulala tara, tace ni
kuma xan cikashe dayar, su zama goma. Na
yada. Bai jira komai ba ya kwasa da gudu, ya
shige bangarensa. Mami ta bishi da kallo. Dadi
ya sa hannu ya cire mata tagumi yace, ke ma
tashi ki daina damuwa. Ta sauke numfashi,
amma ba tace komai ba, ta yunkura ya taimaka
mata ta tashi suka wuce. Kowa ya shige
dakinsa. Al- ameen ya fara fitowa falon, ya nufi
gefen tebur inda ya hangi ladi na jera abinci. Ya
isa wajen yana fadin, angaida Maman abinci.
Tayi dan murmushi. Tace ni ma na gaida dr.
Yace na kusa dina cin abincinki Ladi, ina ganin
daga yau nai masa bye bye. Tayi 'yar dariya, to
aci gaba ne dr. Amma ina ganin akwai gobe
kafin amaryar ta iso ko? Ya gyada kai, yana dan
murmushi, wa ya gaya miki xan dawo ni kadai?
Tana 'yar dariya ta amsa, au can xaka zauna?
Kafata, kafarta, zata sake magana, ya dakatar
da ita, shisshhh... Tayi tsit! Tana kallon sa yana
boyewa bayan kujeru. Dadi ya fito mami na biye
dashi, madalla, kinga bulala ta hau kan danki,
kira shi na tsatstsala masa. Tace, yanxunn nan
ma xaka ganshi a sukwane, kwai ganin sa sukayi
yana gyara xaman kujera xai xauna. Gaba daya
suka kwashe da dariya. Ladi na tasya su sannan
ta bar wajen. Dady yace, gaskiyya ba haka ake yi
ba, ai dai sai ya bari mu fito tare ko mami?
Dariyar Al-ameen ta karu, yayin da Mami ke
fadun, kaji wayau! Ta xuba wa kowa abinci yaci,
suka kashi suna ta biye masa, suna labarin biki.
Bukatarsu ya cika cikinsa, kuma ya ci sosai.
Bayan su kammala Dady ne ya fara barin tebur
din Al-ameen ya byi shi xasu yi wata magana,
nan da nan ya mike ya bi bayansa. Mami ta
kwala wa Ladi kira tace ta gyara kan tebur din,
ita ma kai tsaye ta wuce, ta iske su xaune bisa
kafet. Dayan gefen ta xauna, suka sanya shi
tsakiya. Dadi yayi gyarn murya yace, wasu 'yan
tamnbayoyi xan yi maka Al- ameen, ina fatan
xaka nutsu ka bani amsa shakikiya. Da farko dai
shin Al-ameen wa yake badawa, wa yake
hanawa? Yace, Allah. To idan ya baka, sannan
ya dawo ya karba, me yakamata kayi? Ya amsa,
nayi masa gdya, watakila ya musanya min da
alkhairi, ko Mami? Tace, Gaskiyya ne! Dadi
yace, Madalla, abinda nake ka sanya wa ranka
kenan. Idan har ka tabbata tsakanin ka da Allah
ka amsa min tambayoyi na. Ka kuma san imani
shine cikar dan musulmi, ko ba haka ba? A
salube yace, sosai dady. Yauwa, to kayi hkr
maganar da xan gaya maka. Nasan ka na son
sakeena, sannan kayi imani Allah ne ya hadu ku
ya sanya maka sonta, a da mu na ganin kamar
itama tana sonka, kamar yarda kake sonta.
Amma yanxun ta nuna yaudara ce kawai, saboda
haka ka hkr da ita. Kamar yadda kace Allah xai
musanya maka alkhairi. Ya dubi Mami, ya juya
ya dube shi, Dady ban fahimce ka ba, ai sakeena
na so na, xuga ce kawai kuma na tabbata da
xarar aka daura auranmu, ni masan yadda xan da
hankalinta gareni. Dady ya ka kada kai, maganar
ka dawo da hankalinta gareka duk ya kau. Al-
ameen sakeena ta gudu tun jiya babu wanda
yasan inda take saboda haka nake rokonka
arziki da ka kwantar da hankalinka, kayi imani
da furucin da kayi daxu, Allah ba xai bari kasha
wuya ba. Ya Dubi Mami fuska kunshe da tashin
hakali yace mami ban fahimci ta gudu ba? Me
dady yake nufi? Tace iyakar kiyayya sakeena ta
nuna maka, tunda ta xabi ta dauki akwatinta ta
bar gidan iyayen ta ada ace ta aure ka. Ta xabi
ta ci mutuncin mahaifanta akan auranka.
Wulakanci ya kai makura Al-ameen, ya kamata
ka nuna mana ka haihu dan halas, kace kai ma
ka hkr da sakeena. Ya xura mata ido, du sun
kadu, mami kina nufin an fasa daura auran
gobe? Tace abinda Abbanta yayi sammakon
xuwa shaida mana kenan, ia ske ba ku nan kun
riga kun tafi gayyata, ni na bi dadynka Lafai na
dakatar da shi. Kai ma ina so ka dauki waya ka
kira abokin ka dr. Lawal ka gaya masa an fasa,
don ya gaya wa saura kar su yi wahala. Ya kada
kai yace, baxan iya ba mami, na rantse da Allah
sakeena na so na, ina xata gudu taje? Ban yarda
ba mami sace min ita kayi, don a raba mu....
Rufe min baki! Mami ta daka masa tasawa mai
karfi, daga nan ta balle da masifa, kar ka yarda
Al-ameen, amma ina son ka sani, babu maganar
auranka gobe da sakeena! Idan kuma ka sake
tak a wurin nan sai na tsinka mata mari, don ka
gane ba wasa muke yi da kai ba! Yaya ana
rarrashinka ana numaka gaskiyyar magana ka
naso ka akrya ta mu? Sakeenar banxa sakeenan
wofi? Ita kadaice mace a duniya? In sake jin
xancen ta abakin ka sai na saba maka! Ku ma
ka sani, daga daren yau ka fara shiri gobe xuwa
jibi xaka koma sch! Kaji ko baka ji ni ba? Ya aje
kai kasa. Dadi yasa hannu ya dago fuskarsa.
Tuni hawaye suka wanke masa kunci, shi ya fara
fadin, me yasa zata gudu ta barni Dady? Ko
baxan hkr da ita ba, ai bai kamata ta gudu ba,
hatsari ne babba ga diya mace, wa ya san hannu
da take yanxun? Mami tayi caraf? Ta cafke, tana
hannun wanda take so. Dama ka daina bata
hawayenka a banxa. Sannan kama kunnunwanka
da kyau ka ji ni, tun daga ranar da ka daina jin
muryar sakeena awaya ta daina sonka, ta mance
da kai, ta share ka a rayuwarta. Saboda kin da
ta ke ma. Sakeena ta diro daga mota, da abin ya
zo da karar kwana da yanxun an kusa mata
sadakar arba'in. Sakeena tayi kwana da kwanaki
tana yajin cin abinci, tayi ta suma ana mata
karin ruwa a asibiti. Kai saboda kiyayyar ka,
gabada dabi'iun sakeena suka sauya, bata
gannin kowa da daraja, nballe ta saurari fada, da
iayeynta da 'yanuwanta ke mata ba dare ba rana.
A karshe sakeena ta aikata abinda yafi komi
muni akan diya mace. Duk saboda bata sonka,
ashe ya kamata ka hankalta kasan halin da kake
ciki, don kai ba yaro bane, kuma ba alfahari ba,
ilimi muhammadiya da boko sai dai a yiwa wani
gori ba dai kai ba Al-ameen, duk kuma wanda
yayi imani da kaddara, baya tabewa Al-ameen.
Ka maida al-amarin ka wajen Allah shi xai maka
magani. Ya dube su daidai tamkar karamin yaro,
murya na rawa yace, gaskiyya ne Mami, duk
abinda ki ka fadi na yarda, kuma na hkr da
sakeena, sai dai son ta ba xan iya cire shi cikin
raina ba, saboda ba ni na aje shi ba, kuyi hkr, ku
yafe ni, idan furuncin danayi ya muku xafi,
sannan ina rokon ku don Allah da son Manxonsa,
kar ku kullaci sakeena cikin xukatan ku akan
wannan maganar. Wlh har yanxu ina ji ajikna
sakeenna tawace. Dady ya rungumo kafadunsa
yace, shikenan,ya Isa, munji rokonka mun amsa.
Zamu cigaba da taya ka addu'. Yanxun abinda
nake sonka da shi shine, ka kira Dr. Lawal ka
gaya masa, don su sani. Sai dai in baka
lambobin ka kira shi dady, bakina ba xai iya
furta mummunan labarin nan ba. Ya mike ya jao
durowar dadi ya dauki biro da paper ya rubuta ya
bashi, ya mike xai fice, ya kusan kaiwa kofa
mamy ta kira shi, ya juyo tace kayi nafilfilu cikn
dare. Allah zai saurareka, ya nisa kafin yace
xanyi mami. Ya sa kai ya fice. Mami ta dubi
dady ta hadiye hawayenta, tace gobe in Allah ya
kaimu xan koma Lafai wajen baba liman in samo
masa ruwan addu'a ya sha ya sami sanyi cikin
ransa. Yace hakan ma yayi, Allah ya sa mu
dace. Tace amin. Ta jawo wa dady kan waya ya
nemi Dr. Lawal, ya sanar masa. Yace an fasa?
Subhanallahi? Wannan abu baiyi dadi ba. Don
girman Allah dady a samu a daidaita, wlh Al-
ameen yana son yarinyar nan ba kadan ba. Ya ce
ba sai ka rantse ba Lawal, ni kaina nasan hakan,
amma fadan da ya fi karfinka dole ka maida shi
wasa. Mu nan muna ta addu'a Allah ya zaba
mafi alkhairi. Ya numfasa, yace amin. Ina Dr.
Yake? Ai sai da ka neme shi xuwa gobe, yanxun
kam babu sukuni yana dakinsa. Yayi dan jim,
kafin yace Allah shi kyauta, amma ayi kokari
Dadi idan xai yuwu a sasanta. Ba komai mun
gode a gaida Iyali. Zasuji, ya aje wayar tare da
tsananin mamakin wannan abu? Me ya faru haka
da xafi? Haka ya kwana da tambayar kansa, don
babu alamar wata mishkila a tattare da soyayyar
abokinsa da sakeena, ko daya zo sanar da
xancen auran ma babu alamat akwai matsala
babba. Labarin barci dai babu shi a wajen Al-
ameen kuma xuciyarsa bata daina karyata masa
xancan ba. Ko alama ta ki amsar sakon, saboda
tsabar shakkun da yake ciki, wai sakeena taci
amanarsa? Har 8am yana kan sallaya, ba don
wai yana sallah ba, a'a kasala ce ta hana masa
tashi. Mami tayi sallama ta shigo da tiran kayan
karin safe. Ya xubo mata ido. Mami tayi sallama
ta shigo da tiran abinci, ya xubo mata ido, ta aje
a agbnsa, ta xauna gefe, sannan yace, ina kwana
mami? Lfya lau, ina fatan ba ka tsananta wa kan
tunani ba? Ya kada kai, ya xanyi mami? Kin san
ba yin kaina bane? Ta dafa shi a sanyaye, kllm
ina kara gaya maka Al-ameen, kai kadai ne
garemu, kuma ka zama tamkar dubu, ba gare mu
kadai ba, gabadaya al'umma za su so rayuwarka
ta daure cikin fciki da walwala, saboda
muhimmancinta, ina so ka san wani abu yau.
Wlh na yi maka rantsuwar da ba kaffara da
rayuwarka ta salwanta, gara ni in mutu, don
na..... Ya rufe bakinta, a hankali, idanuwansa
taf, da hawaye yace, kiyi shiru mamina! Da ni
dake zamu rayu da yardar Allah cikin farinciki da
kwanciyar hankali. Har ga Allah na hkra da
sakeena mami, kawai ciwon fitar son ta ke
azabtar da ni. Ka kwantar da hankalinki mamina,
a hankali zaki gan ni yadda kike so. Tayi dan
murmushi tace, Allah yayi ma albarka! Da sauri
ya kwanta a kafadarta yana fadin amin mamina.
Zauna da kyau na hada maka brkfst. Kaga masa
na sa iya ta shirya maka da sassafe, na san
kana so kuma kana kewarta, don ba'a samu a
Rasha. Ya bita da kallo dauke da tausayi. Yace
nagode mamina, amma tare xamu ci ko? Ta jawo
fileta tana fadi ah! Me zai hana? Bari ka gani. Ta
loda waina a plate tana xuba miya ya ware ido,
yace mami kin cika abincin nan! Ita ma ta ware
idon tace injiwa? Ni da kaine fa? Sa hannu ka
gani ko asa man shanu? Ya kada kai, a'a kinsa
banso kayan karni. Ka bar dadi yaro. Yayi 'yar
dariya yace Allah ko? Ta tura masa a baki tace,
haba ai ba sai na fadi ba. Dady yai sallama
dakin ya karaso da sauri yana cewa iye! Masa
kuke ci kuka nuna min 'yan ubanci? Gaskiya ba
ha akeyi ba, ai sai ku kira ni ko? Ya tambaya
yana kallon al-ameen cikin ido. Ya gayara masa
wwuri, yace laifin mami ne, xauna abinka
Dadyna. Ya xauna yasa hannu ciki, yace ai mami
akwai rowa, Allah dai ya tsaga da rabona. Suna
dariya ta bashi amsa, ka san kuwa da na kawai,
na aka yi ma. Kaji ko? Tafi son ka akaina. Yayi
wuf ya rike hannu da yake kokarin kai loma
yace, ba xaka ci ba sai ka fadi! Gaya min, mami
ta hau dariya shima ita yake yi. Dady na ga dai
da ta rikice kanka. Tace babu wani sai kai,
sannan aka sameni, ko ba haka bane mami?
Tace ni xaka tambaya? Dady ya karbe yanki
wainar daga hannunsa ya tura masa baki, yace
cinye dana, ka bani amsa daidai. Bai gama
cinyewa ba ya dauko cinyar kaza ya tura msa, ka
ra da wannan kayi brush! Duk suka sa dariya,
ganin al-ameen na neman kwarewa, kan kace
kwabo sun yaudari Al-ameen ya cinye wainar da
mami ta zo da ita, domin dai shi suka yi ta
turawa da wasa da dariya ya take cikinsa. Bayan
sun kare, mami ta dube shi tace yanxun ka tashi
ka shiga wanka ka kimtsa, muje asibiti ka gaida
Umma.... Umma? Me ya sameta? Tashin hankali
ya sa ta sami hawan jini tuntuni, maganar jiya
kuma ta kara birkita ta jininta yayi mugun hawa.
Tana nan asibitin sun bata gado. Jiyan abba ya
taho da ita. Ya marairaice yace, Umma na asibiti
tun jiya baku gaya min ba? Ban dadin hakan ba,
dady yace kayi hrk, ganin kai ma baka da sukuni
ya sa muka kyaleka, kaji da guda 1. Ya mike
yace ba sai nayi wanka ba, yanxun xan tafi, idan
na dawo nayi, bai saurara ba ya wuce ya jawo
dirowa ya dauko key ya fice. Mami ta biyo shi
tace Al-ameen, ya tsaya cak! yana dubanta, ta
matsi sosai ta dafa shi, ka tafi a hankali, idan
kaje kace ina gaishe ta, ni ma xan biyo in na
dawo daga Lafai, ya dan lumshi ido, ya bude
yace xan kula mami, amma me xaki je yi Lafai?
Tace uzurina xai kaini. Allah ya kiyaye hanya, ta
amsa amin. Ya daga kai dubi dady dake tsaye
yace, sai na dawo dady, to ina jin ma xan
sameka asibitin. Yace shikenan sai kazo. Ya juya
yayi waje, su iya na kokarin fitowa su gaisa.
Amma ina saurin da yakeyi, ya hana su su same
shi falon, tuni ya kai ma'ajiyar motocin, ya
murza ya bar gidan. Umma na xaune an jera
mata filo, ruwan lipton kawai ta iya kurba, ya
xuna cikinta. Likitan ne yace ta dan jingina
kadan ta huta. Duk 'ya'yan sun kewayeta, abba
na xaune gabanta bisa kujera. Gaba daya tausar
xuciyarta suke yi don ta fidda abin a aranta.
Sallamar al-ameen cikin dakin ita ta dauki
hankalin kowa, suka amsa kona masa duban
tausayi, ganin yadda ya xabge kamar mai ciwo,
wai don ma su mami na yin iya kokarinsa
akansa. Ya bisu daidai sukayi musabaha, sannan
ya tsugguna gaban Abba suka gaisa. Tuni
ganinsa ya sa hawayen Umma suka tsinke, yayi
shiru a tsugunne. Abba ya dafa shi, yace sai ka
dawo ka sami labari maras dadi? To ina so ka
kwantar da hankalinka kayi imani da kaddara, ka
sani yau da ace mama na da 'yar uwa xan baka
ita, don in nuna maka iya kaunar da muke maka.
Mama ta zabi ta wulakanta mu, shi yasa na ke
son kowa ya cireta a ransa, mu manta da ita mu
kyaleta duniya ta hora ta. Kayi hkr kaji? Ya goge
kwalla yace naji abba, kuma nagode akan iya
kokarin da kukayi min, amma abba ina rokon ka,
don girman Allah ku ya fe mata, sannan ku
sanya mata albarka, a auran da xatayi. Duk
sukayi shiru, kowa ya xuba masa ido. Tausayin
sa na ratsa su, umma ta goge kwalla. Tace
Mama ba abar tausayi bace Al- ameen, don haka
ka daina rokon ayi mata afuwa laifin data aikata.
Ya kata matsowa gaban gadon yace, ba haka
bane Umma, ki san sharrin shaidan, sannan
xuciya bata da kashi, ba 'a son ran mama zata
aikiata wannan abin ba, xuciya ce ta saka mata,
na tabbata duk ranar da ta nutsu tayi tunani
xata gane lallai bata kyauta ba. Don Allah Umma
ko ina nan ko ba nan, idan Mama ta dawo ku
amshe ta hannu 2, ku samata albarka. Insha
Allahu shaidanin daya rinjaye xuciyarta, xai
kyaleta, ta dawo diya ta gari kamar yadda take
da. Abba ya kara dafa shi, yace idonka ya riga
ya rufe a son mama, shi ya sa baka kallon
girman laifin da ta aikata. Ya juya ya dube shi,
ba haka bane Abba nasan ina son mama kuma
har na mutu ba xan daina son ta ba, amma ku
yafe mata, don rayuwar ta, tayi kyau nan gaba,
ba farin cikin mu bane ace mama ta lalace tabi
duniya, tunda gaba dayan mu nan, muna son ta.
Kun yafe mata ko Umma? Tace kayi hkr Al-
ameen ba xan iya cewa komai ba tukunna, ya
abdulqadeer yace, ko mu bamu goyi bayan su
Umma suyi afuwa gareta ba, har sai ta sauya
zabin da tayi da. Tunda tace ba kai ba, to ka
kawo wani dan mutunci tamkar kai, amma ba
Dan liti ba. Wanna itace shawarar da muka
yanke. Yana rufe baki dadi ya turo kofar ya
shigo tare da gaishe-gaishe. Ya dubi al-ameen
yace, dr na jiranka. Da mamai ya dube shi, dr.
Lawal? Yaushe ya zo? Bai dade ba, muna shirin
fitowa, sai gashi shine nace ya xauna xan biyo
na gaya maka. Ya mike yayi sallama da su ya
bar asibitin. Bai sami mami ba, don itama driver
ya wuce da ita lfya. Dr. Lawal na babban falon
gidansu, ladi sun adana shi da kayan kusa da
baka, amma da ka dube shu kasan baya cikin
sukuni. Yana shigowa ya mike da sauri ya tarbe
shi suka kama juna. Dr. Lafai! Yace banyi xanton
xaka xo ba. Dole na xo, wannnan mummanan
labari ya hanani barci jiya. Yayi dan yake, kai
dai bari, mu xauna aboki na. Suka zauna kujera
daya, dr lawal yace, me yayi zafi likita?
Idanuwansa suka kada yace, bansan me ke
faruwa ba dr sama da sati 4 ina can na daina jin
wayar sakeena, aka ce min bata da lfya ne,
dalilin da yasa na dawo kenan don hankalina
yaki kwanciya ita kawai nake son gani. Ina xuwa
na iske labari ya sha bambam, wai sakeena ta
sami wani ya hure mata kunne, har ta mance da
manyan alkawuran da ta daukat min. Kowa yayi
iya kokarinsa wajen nuna mata gaskiyya, amma
sam tace ba san wannan ba. Abban ta kuwa ya
sha alwashin ni da ta fara kawowa akayi mana
baiko, ya sani ba xai daura mata aure da kowa
ba, face ni don haka yace ba xan koma sai an
daura auran. So da kaunar da nakewa sakeena
yasa bana tunanin komai Illa xumudin a daura
mana auran, shi yasa koda naje jiya bana nuna
maka komai ba.a xato na bai kamata in tona
kwanne sirri na sakeena ba, do kar a zage ta
matsayin maci amana, ina ganin kamar idan
muka kebe matsayin miji da mata, xan iya
rinjayar ta. Son da take take min ya sake
dawowa xuciyarta. Ashe duk abin da nake zato
ya wuce nan dr.lawal kawai na dawo jiyan su
dady ke gaya min sakeena ta gudu cikin dare ba
a san inda take ba. Al-ameen ya jingina da
kujera ya runtse ido sai hawaye shar... Na
malala, hankalin dr. Lawal ya kara tashim ya
xura masa ido jim sannan ya sauke numfashi ya
dafa shi, yace, kana cikin tashin hankali aboki
na amma Allah yace duk inda tsanani yakem to
tabbas da akwai sauki. Pls ka zama jarumi a
cikin jarabawar nan, ka bari hkr ya xama
sanadin samun saukin tashin hankalin nan. Ya
bude ido taf da kwalla, yace inason sakeena Dr.
Kai kasan hakan, yace kwarai da na sani kuma
xato na itama tana tsananin sonka. Ya matso shi
sosai yace haka ne, wlh sakeena tana sona, to
me yasa ta kini tym 1? Yace mata kenan Dr.
Lafai. Balle sakeenna na da kyau da xata iya
wasa da hankalin kowane da namiji. Watakila
kuma wancan yafi ka duk abubuwan da take
bukta. Dan wani minister ne a abja? Yace ban
nemi sani ba, a yau ne nake jin sunansa bakin
yaanta wai shi Danliti, danliti? Daga jin sunan
kasan ba wani bane. Da sauri ya amsa ai kuwa
wani ne.... (Hahaha Allah sarki lazy Dr.) tunda
ya sace min sakeena. Ko da kuwa kwara masai
yake yi. Inda ace xan gan shi xan iya durkuwa
gwiuwa 2 in roke shi, ya bar min sakeena ta.
Wlh itace rayuwata dr. Ya kada kai yace, ka
daina fadar haka Dr. Lafao kar fa ka mance wani
hani ga Allah baiwa ne, xa iya kasancewa
sakeena kyan dan miciji gareta.... Ya dakatar da
shi ta hanyar daga masa hannu.... Yace gaya
min kowace kalma dr. Amma kar ka aibata min
sakeena, ba xan taba ganin farinka ba. Ya xura
masa ido, kunshe da mamaki, kafin yace, ba nufi
nake nan ba aboki na, ina so ka gane cewar
bakomai da kake bane yake kasancewa alkhairi a
gareka, shi ya sa kullum ake son bawa ya roki
alkhairi wajen Allah. Yace sakeen alkhairi ce
gareni, tuni mafarkai na suke nuna min hakan,
har xuwa yanxun kuma jiki na yana bani sakeena
tawa ce, mishkila aka samu wani wurin, bana so
musu da su Dady ne kawai, shi ya sa nake nuna
musu na hkr da ita. Yace to idan baka hkr ba,
yaya xakayi yi? Tunda batayi da kai? Babu
abinda
BAKIN CIKI 2***10 Amma nan da iya shkrun da
xanyia duniya ba xan daina son ta ba har na
koma Ubangiji. Ya xura masa ido, yace Al-
ameen kar ka manta akwai gagaruminn aiki
gabanka wanda kowa ya xura ido don ganin
rawar da xaka taka, kasancewar kai kadai ake
tunanin xaka iya taka ta kuma mutanenan arewa
suna jiran daya tamakar dubu ya dawo masu da
abin alafahrin a duniya baki daya. Ina ka sami
nutsiwa ka fuskanci abinda ke gabanka ka tare
da jadda imani a cikin ranka, lallai Allah xai iya
baka wata. Ina fatan xuwa na ba xai xama abnxa
ba ba, kuma addu'ar duk masoyanka a zariya ba
zata fadi kasa banxa ba. Kowa yace Allah ya
musanya maka da lakhairi, na tabbata Allah xai
duba ya kawo sauyi na fadi daidai? Ya numfasa
yace ka fadi daidai abokina na, na gode ma kowa
bisa addu'ar da suka yi min. Xan koma rasha da
yardar Allah cikin yardarsa xan dage na fidda
kowa kunya. Sai dai abinda nake so ka sani har
in mutu ina son sakeena. Yace tuni na sani,
sannan ina da ilimin xuciya daya gareka, duk
abinda Allah ya xuba cikin ta, babu me iya
dauke shi. Ya koma ya jingina da kujrea,
rungume da hannayensa, ya dan numfasa ya
kada kai, dr. Lawal ya bubbuga kafadarsa ya
sake fadin, ka manta kawai abokina, ya wuce,
ya bishi da kallo kawai baice komai ba su dade
tare. Dr. Lawal na kara kwantar masa da hanakili
tare da nuna masa mahimmancinsa ga al-
aumma. Bayan azahar suke asibiti ya gaida
Umma, daga can ya wuce zariya, shi kuwa Al-
ameen gida ya dawo, don shima ba ya son yana
ganin Umma kwance tausayinta yana kara karya
masa xuciya. Ya rinka jin kamar su abba ba xa
su yafe wa sakeena ba. Wannan shine babban
tashin hankalin sa. La'asar ta kawo jiki yana
xaune shi kadai bisa gadonsa, tym-tym ya kan
dauki hoton da ke bisa kirjinsa ya duba. Hotonsu
ne shi da mama wanda sukayi a dakin Mami,
xuwan ta farko gidan. Karo barkatai kenan daya
daga hoton ya xura masa ido tsawon lokaci,
sannan ya mike ya sake kife shi. Ya laluba
aljihunsa ya dauko xoben da Mama da dawo
masa dashi, ya xare na hannunsa ya hada su
waje daya, ya xura masa ido. Sannan ahankali
yake wasa da su, ya rike kowanne yana hada su
karo. Cikin idanuwansa yake ganin ita ke rike da
wanda ya bata, suke karawa juna. Wannan karon
da karfinsa ya kara mata, na hannunta ya karye
nan da nan ta shagwabe, gaskiya ba hake ake yi
ba! Ba haka ake ba Dr. Al- ameen! Al-ameen
tsananin kiran ya dawo da shi tunaninsa duniya.
A firgice ya dubi Mami dake gabansa xaune. Ba
xai iya cewa ga tym da ta shigo ba, don haka
yake mata kallon mamaki, haka itama ta xura
masa ido mai dauke da questions. Mami! Yaushe
kika dawo? Ta sauke numfashi ta kada kai,
kafin tace, tsoron na Allah tsorona kar ka xaunce
al-ameen ka dawo cikin hankalinka mana! Yai
sauri ya runtse ido yana fadin Hasbunnallu wa ni
Imal wakil, Allahuma ajirni fi musibati wa
akhlifini khairan minha. Ya bnude ido jajur ya
dubeta, kiyi hrk mami.... Takatshe shi ba xan
bari rayuwar ka ta salwanta ba Al-ameen sai
inda karfi na ya kare, Allah na gani yarinyar nan
ta xalunce ni. Kafin yace wani abu, ta mike da
sauri tai waje, ya bita yana kira, ba su hadu ba
sai a dakinta... Mami.... Ta daga masa hannu.
Ban son jin komai, ta mika masa wani ruwa da
ke hannunta tace shnaye shi ka bani kofi. Yace
na menen? Ban son tambaya ni na umarce ka
kashanye, ka bani kofin. Ya daga kofin da sunan
Allah, ya kafa aabki ya kwankwade. Ta karbi
kofin ta aje gefe. Ya sake tambaya mami ruwan
me nasha? Tace baba liman ya bani taimako na
kawo maka, anjima zaka sake sha, gobe ka kara
da safe da yamma. Jibi in Allah ya kaimu lfya
za ka koma sch, domin fitar da dadin ka yayi
bookin ya je maka, ina fatan kajini? Jikinsa yai
sanyi, ya kamo hannnayenta 2 ya ja suka xauna
bisa kujera yace Allah sarki mamina. Allah bar
min ke. Nagode da karfafa min gwiuwar da
kukeyi. Idanuwanta taf da hawaye tace,
hankalina bai taba tashi ba irin na yau. Ban taba
jin faduwar gaba ba irin ta yaukai da zobuna
kake hira kana dariya, Al- ameen ban same xai
faru ba nan gaba. Kafadunta 2 ya dafa yace sai
alkhairi mamina, kawai xancen xuci ne ya fito
fili mami... Tace daga haka sai tabin hakali al-
ameen , yayi dan murmushi yace Allah ba xai sa
ba mamina, ya san ni kadai ya baki, kuma shi
mai tsananin tausayi ne. Allah sa ruwan da kika
bani ba wanda xai cire min son sakeena bane. Ta
xura masa ido cikin xafi tace, shine Al-ameen
Insha Allahu sakeena ba xata zama ajalinka ba,
ya numfasa yana murmushi da bai kai ciki ba
mami kenan, wa ya gaya miki sakeena xata
kashe miki tilon danki? Kuma wa ya gaya miki
danki xai ji dadin rayuwa ba tare da soayyar
sakeena ciknin xuciyarsa ba? Duka 2 tafiya suke
kafada da kafada mami, Allah yayi hukuncinsa,
don haka ban ji Baba liman xai iya cirewa. Bayin
kaina bane, kiyi hkr mami. Tayi masa xuru duk
jikinta ya mutu a hankali ta ce ko bai fita ba
xaka ji sanyi cikin ranka. Tunaninn ka xai
daidaitu da aikin kwakwalwar ka ta yadda xaka
yi mu'amula kamar sauran mutane. Wannan
shine farinciknm. Yace, Allah ya taimake ku
akan burin ku. Nima ya taimakeni akan nawa.....
Tace xamu ci gaba dayi da fada idan har kana
gaya min irin wadannan kalaman. Ya kada kai ba
xa muyi ba mami. To ka daina. Ya lumshe ido,
ya bude yace na daina, Allah yayi maka albarka.
Ya dora kansa kafadarta ya amsa da amin. Ta
ciga da yi ma nasiha yana sauraronta sai dai can
kasar xuciyarsa cike yake da xulumi, Allah ya sa
ruwan da mami ta ba shi ya sha ba wanda xai sa
ya mance da sakeena bane. Da wannan xulumin
ya tafi yin sallah la'asar hankalinsa bai kwanta
ba, sai da ya tura yatsansa ya arce
makogwaronsa ya kirkiro wa kansa aman dole.
Bayan sallar magriba dady ya shigo ya tsare shi
yaci abinci. Sannan mami ta debo ruwan
addu'arta ta mika masa, ya shanye. Allah Allah
yake yi tashi ya koma dakinsa ya jawo aman,
amma kmar dady ya sano ya ki barinsa tashi.
Yayi ta jansa da hirarrakin duniya, wai don ya
rage tunanu. Kafin ya bar wajen ya kwashe awoyi
sama da 2 takaice ya ishe shi, don ya tabbata
ruwn nan ya gama bin jininsa. Wannan karon bai
nemi yin aman ba, gado ya fada ya fara tunanin
iska, har bacci ya samuyi, da alama an fara
samun nasara. Shi kansa yayi mamakin irin
barcin da yayi bugu da kari ya rage jin xugin
xuciyarsa ke y, hankali kwance suka yi karin
safe. Mami ta kara bulbuo ruwan addu'ar ta a
gora, ta mika masa. Ya kwankwada duk ba a son
ransa yake sha ba, a yau takardun komawarsa
Rasha xasu kammalu, haka dady ya gaya masa.
Saboda haka ya umarce shi daya kasance cikin
shiri koda yaushe xa'a iya basu tym din tashi.
Jikinsa babu kasala ya koma bangarensa ya jwo
jakar kayansa yayi ta lda kaya har da wadanda
ya dade bai anfani da su ba. Ya wuce dirowar
madubinsa ya jawo ya kashe takardun cikin kaf,
dinsu ya dauko xai xuba jaka, wata ambula ta
fado duk hotuna ciki suka watse bisa kafet
daidadi shigowar mami dakin. Ya aje takardun
gefen gadon yana amsa sallamarta, sannan ya
tsugunna ya kwashe hotunan, akasarinsa duk na
mama ne, sai kalilan wanda suke tare. Tayi tsye
tana kallon katuwar jakar da yake lodawa kaya,
ya akayi mami na? Tace kamar bada jakar nan
ka xo ba? Ya mike dauke da hotunan a hannunsa
yana amsawa, xan kara wasu kayan ne, shi yasa
na sauya jaka. Ya matsya xai cusa hotunan, tayi
wuf ta karbe ina xaka da dasu? Ai wadannan
hotunan wuta ya kamata ka cinna musu. Wuta
mami? Me ya san xan sa wa sakeena wuta?
Saboda nan gaba xata xama matar wani, ka ga
haramun ne gareka kallon hotonta. Ina fatan ka
gamsu? Yayi shiru na 'yan dakikai kafin ya
numfsa, ya dubeta idanuwan har sun kada, yace
kin fadi gaskiyya mami, amma baxan iya cinna
wa jikin sakeena wuta ba, sai dai ina rokonki
dan girman Allah ki adana min su har xuwa tym
din da xata halasta gareni. Tayi masa xuru tana
shakku cikin ranta, addu'ar Baba liman batayi
tasiri bane ko kuwa bata fara aiki bane tkunna?
Ta kada kai ta dubi hotunan ta sake dubansa,
amma shi ya riga ta magana. Mami pls ki ajeye
min su inda ba xa su salwanta ba. Ta sauke
numfashi, xan boye maka sun tunda kafi son
hakan, gwaggo ce ta xo tana daki na. Ya ware
ido sosai. Gwaggo? Da sasssafen nan? Dole tayo
sammako, hankalinta a tashe yake, ka fito tana
daki.Tayi waje da ambulan din a hannunta,
shima ya biyo bayanta. Tana xaune a shimfida
bisa kafet ya xube gabannta dauke da murmushi,
uwargida ran fida, kuma sai ki bugo min
sammako kamar ban aika da cefane ba? Duban
tausayi take masa, ta dafa kafadarsa tace dole
nai sammako, in xo in ga halin da kake ciki. Ina
fatan xaka sanya dangana cikin ranka. Ka mance
da yarinyar nan, domin dai.... Ya katse ta, ya
kamata mu gaisa gwaggo kinxo lfya? Ya tsufa?
Tace tsufa na nan kuma lfya lau na xo. Amma
me yasa ka katse min magana? Babu komai gani
nayi bamu ko gaisa ba, alhalin ya dace na fara
gaisheki. Haka ne to ina fatan duk shawarwarin
da kowa ke ba, kana ji ka kuma dauka? Ka
manta sakeena... Da sauri ya katse gwaggo tuni
na hkr da ita, hasalima yau ko geb xan koma
sch. Ban xan dalilin katseni ba Al- ameen akwai
abinda baka so na fadi. Mami ta amshe, sosai
kuwa kina so ya mance da sakeena,
kunnunwansa ba sa son ji, shi yasa yake
katseki. Tace oho, to wahalar banxa kakeyi,
domin dai labari ya tabbata tare da shashashan
saurayinta suka tafi, kaga kuwa sai abinda Allah
yayi. Gara ka kama kanka ka san inda ke maka
ciwo. 'yan mata dai ga su nan birjik duk wacce
kace kule xata ce cas. Rayuwa kawai sakeena ta
xaba, don na tabbata yaron nan baxai aureta ba,
nawa ya lalata, ya watsar tana gani kuma ta
bishi, inm banda ita ma, rayuwarka ta sha
banban da wacce sakeena ta dauka, kaga kuwa
tafiyarka ba xata xama daidai da tata ba. Ka
fahimce ni? Wasu kwalla masu xafi suka sauka
bisa kuncinsa, hakan ya jawo mamaki ga
gwaggo da Mami suka xuba masa ido baki sake.
Xugum sukayi, daga bisani mami ta numfasa
tace ikon Allah! Gwaggo ta xare tagumi tace,
akwai sauran aiki, kuma ina mai tabbatar maka
, bata tym dinka kakeyi. Ya jawo hankaci ya
share fuska, yace, ko kadan gwaggo, labarin ki
tsananin tausayin sakeena ya cusa min, sakeena
ba haka take ba, nayi rayuwa da ita sosai na
fahimci halayenta, xan iya cewa nafi kowa
saninta, na fahimci halinta. ,Zan iya cewa nafi
kowa sanin ta hakika ya zalunce ta tunda ya
sauyamata rayuwa ya bata tarbiyarta ya gurbata
mu'amalarta da iyayenta da yan uwanta ya datse
tasananin soyayyar dake tsakaninmu ka ALLAH
bazai kyale shi ba ta ko wace hanya ya bi yayi
nasa a kanta sai ya ga sakayya,"ya mike da
sauri zai bar dakin gwaggo ta kwala masa kira
ya tsaya bakin kofa yana goge kwalla tace dawo
ka zauna ai ban gama magana da kai ba yana
daga tsaye gaskiya gwaggo kunnuwa na ba za Su
iya sauraron irin wadannan labarurrukan akan
sakeena ba,tausayin ta bazai barni sukuni ba
gara a bar ni cikin bakin duhu ina laluben inda
ALLAH zai sake hada fuskokin mu har ta zama
mata a gare ni," jikin gwaggo yayi mugun sanyi
tace dawo zauna nan ya dawo ya zauna gefenta
ya hade kai da guiwa ta dafa kansa tace idan
nayi kuskure kayi min afuwa amma ba laifi na
bane ka sani ko wace uwa tana kishin danta
kuma abinda ya faru da kai dole mai kaunarka
yayi bakin ciki balle mu da muka fi kowa kusa
da kai, na san kana son sakeena sai dai ba na
son idon ka ya rufe ka kasa ganin aika aikar da
ta aikata a garemu, ya cire kai ya dube ta ni
kuwa hakan na fi so gwaggo domin na yi imanin
ba yin kanta bane sace min ita akayi hure mata
kunne akayi da kalmomin shaidan addu'a zatayi
maganin abin, da zaki taimake ni da ita ma zan
fi farin ciki akan wadannan labaran da ki ke son
bani," gwaggo " mami ta karbe za a yi maka in
dai addu'a ce ka samu tashi kaje kaci gaba da
shirinka bai tofa komai ba ya yunkura ya bar
dakin,kamar daman can ya kosa ya
barshi,"gwaggo ta dubi mami hankali tashe tace
bai kamata ku kyale yaron nan ya koma haka
kawai ba tare da wani taimako ba tace tun jiya
na je lafai na samo masa wajan baba liman wai
nan yama sha ruwan addu'ar ke nan tafdijan ki
na kallo fa ko laifinta baya son a fadi wannan so
yayi yawa gara ma da auran bai yuwu ba da
muna kallo zai zama mijin ta ce,abin haushi
nama na jan kare, mami tace me ki ka gani
gwaggo?ALLAH dai ya zaba alkairi abin cewa ke
nan anan gwaggo ta wuni, Shi kuwa Alameen a
dakinsa ya wuni don baya son ana daga masa
hankali da labaran sakkena kazantar da baka
gani ba tsafta ce,kai a yadda yake jin mama
cikin ransa koda ya ga kazantar da idanuwansa
zuciyarsa ba za ta amince masa ba bai fito ba
sai da gwaggo zata koma suka yi sallama daga
nan dakin iya ya shige ya kudundune kamar
maraya sama da awa guda tana tausar zuciyar
sa da kalamai masu dadi,ya kuwa ji dadin cikin
ransa saboda kalaman iya sunfi rinjaye ga. Bashi
tabbacin idan sakeena matarsa ce duk rintsi duk
wuya sai ya aure ta karfe shidda dai dai dady ya
dawo masa da takardun tafiyarsa sun kammalu
kuma gobe da yardar ALLAH sha biyu ranan zasu
tashi don haka yana gama cin abincin dare mami
ta ba shi ruwan addu'a ya kwankwada kai tsaye
asibiti ya wuce don yin sallama dasu abba,kowa
yayi masa nasiha kuma sun jaddada masa ya
maida hankalinsa akan anibda ya kaishi kar ya
tsaya bata lokacinsa. Akan tunanin iska wanda
ba zai fisheshi ba,sai dai abin yana basu
mamaki yadda lafuzzan alameen ke nuni da
tsantsan son mama a zuciyarsa. Wanda ko alama
na bayyana har yanzu bai yarda sakeena. Taci
amanarsa ba, akwai mishkila wani wuri shiyasa
yake ta rokansu dasu taya shi addu'a ALLAH
yasa wata rana sakeena ra zama mata a gare
shi,gaba daya ya kwabe masu guiwa har suka yi
masa alkawarin yin yafiya a gareta idan har ta
dawo ta nemi gafara,kowa ya dubi alameen sai
ya ji tarin kwalla cikin iadanuwansa lokacin da
yake barin asibitin yana gugar fuska shi kansa
yaya soja a yau zuciyarsa ta karaya,tausayi ya
kwarara cikin jikinsa ya nemi haddasa masa
abin mamaki domin kwalla ya ji tam da
idanuwansa suna zubowa da saurinsa ya bar
wajan bai gama ganin wucewar alameen ba
AKIN CIKI 2*** 11 Karfe 8am suka dauki hanyar
abj tare da mami. Hankalinsu bai gama tashi ba,
sai da tym ya cika aka kira passengers. Al-
ameen ya rungume su, idanuwan sa cike da
hawaye, bakinsa na son yin magana amma kasa,
haka su ma Allah ya doro masu nauyin baki,
kallon juna sukeyi. Da sauri ya juya ya wuce,
yana goge fuska da hankici. Shi yasa suke tafe
cikin mota kowa shiru. Mami dauke da
taguminta. Tunaninta yay rayuwar dan nata xata
kasance a kasar da babu wanda ya damu da
wani balle ya sami wata kulawa ta musamman.
Dadi yayi tana share hawaye ya dan dube ta,
kada kai. Amma bai iya cewa komai ba don ya
san mami tana mukatar zubda hawaye ko ta ji
dadi cikin ranta, amma da ya ga abin yaki
karewa, dole ya tanka, ina ganin bai dace ki ci
gaba da bata ranki ba, wanda kika yi ai ya isa,
ko sai ya jefa ki wani hali ni in rasa da wanda
xanji? Ta goge kwalla, tace Alh. Ba haka bane
ganin Al-ameen na da abin fadi, amma yakasa
ya wuce da damuwar cikin ransa? Wa zai gaya
mawa a can? Kai tsaye ya bata amsa, Allah zai
gaya mawa, kin kuwa san ya fini, ya fiki, yafi
duk wanda kike tunani zai ba Al-ameen wanni
taimako, saboda haka ki bar shi da buwayin
sarki, shine xai masa dukkan gudunmawa. Ta
zare tagumi ta numfasa, haka ne, Allah ya
taimake shi, to amin kuma na tabbatar zai
taimakeni shin, tunda kika furta, addu'ar uwar
yankan wuka ne, don haka ki kwantar da
hankalinki. Ina fatan kin ji ni. Tace, naji alh.
Allah ya shige mana gaba, yace amin. Daga nan
Mami ta saki jikinta suka ci gaba da hira. Suna
shigowa gari, asibiti suka wuce gano jikin
Umma. Alhmdlh, Umma na samun sauki,
watakila ma xuwa gobe a sallameta. Ba su iske
yaya abdulkadeer da Abdul- rahman ba, duk sun
koma a wannan yammacin. Sun dan jima
asibitin, sannan suka dawo gida. Mami ta dukufa
rokon Allah cikin sallolinta, Allah ya sanyaya wa
Al-ameen xuciyarsa, ya cire masa wannan
makahon so sa ya ke wa Mama. Haka ta kwana
tunaninsa har barci tayi mafarkinsa xaune yana
wasa da xobunan guda 2. Shiyasa da ta fara tayi
ta da na sanin da ta raba shi da zobunan kafin
ya tafi. Suna karin safe karfe 8:30, waya ta
dauki kuka, mami ta baro tebur ta zo duka tayi
sallama. Muryar dan lelenta taji ya amsa. Farin
ciki ya lallube ta tace, Allah sarki Dr. An sauka
lfya? Yace lfya lau Mami, ina dadina? Ga shi
nan, ya taso ya ji kaini, ina fatan ba matsala?
Babu mami, na ma iske time table din jarabawar
mu ya fito, karatu kawai xa mu fuskanta, ni da
abokan karatuna. Dadi ya tsaya wajen tana
fadin, kai naji dadi sosai, to Allah ya baku sa'a
baki daya. Ga dadinka. Ya ce, to nagode Mami.
Dadi ya amsa suka gaisa. Dady time table ya
fito a taya mu addu'a. Yace kullum a cikinta
muke, amma xa mu kara kaimi. Ubangiji Allah
ya taimako. Yace amin. To xan wuce cikin sch,
sai kun sake jina. Yace, yayi kyau, all d bst!
Cike da fara'a ya amsa. Nagode Dadina. Ya aje
waya ya dubi mami yace hankalinki ya kwanta?
Bakinta har kunne ta amsa. Kai bari Allah ya
kara masa hkr. Yace amin, muje muci abinci ko?
Suka koma tebur. Mami tace abinci hankalinta
kwance. Ba Haka al'amarin yake wajensu Umma
ba, domin yau sun koma Fandagori sun iske da
kuara da suka bari baya. Hankulansu su kara
tashi yadda xance ke ta yamadidi a agari. Zagi
iri-iri babi irn wanda ba'ayi ba wasu suna ba
iyayen Mama laifi, amma da dama sunfi zargin
mama akan rashin hankali da ta aikata. Wani
abinda yafi daga wa Ubandawaki hankali shine,
wai gaba daya gundarin labarin daga bakin 'yan
uwansa da matayensu ya fara fitowa. Bayan
gaskiyya ga tarin karya da karairayin da suka
yiwa labarin kawanya, don haka ya tara su falon
sa bayan sallar isha'i. Wannan shine karo na 2
da na tara ku akan wasu maganganu na batanci
da suke fitowa daga gareku. A zatona ku masu
rufa min asiri ne ko bayan raina a matsayin ku
na 'yan uwana da muka fito ciki daya. Amma
bansan abinda nayi muku ba kuke min bita da
kulli, ko kuma ince kuke farinciki don wannan
abin ya sameni. To abinda nake so ku gane
shine, da frko dai bamu mukayi kanmu ba. Allah
ne yayi mu, mu kuma shi ya rubuta duk abinda
zai faru da mu. Babu wanda yasan kaddarar
mu2m bnalle ya share masa mummuna kafin
tazo. Da anayi da na gogewa Mama, don na duk
fadin duniyar babu wanda zai kaini BAKIN CIKI,
sai kuwa mahaifyar ta. Idan kuwa hakane, bai
kamata ace ku da matayenku, ku dauki wannan
al'amarin ya zamar maku abin hira a gari ba.
Kaddara na kowa, idan baku duba kusancin mu
ba, ya kamata ku duba wannan. Allah yai sani
ban zalunci kowa ba cikin ku ba, haka ban
xalunci mama ba, kamar yadda kuke yadawa
cewar mu ne muka dage sai mai kudi xata aura,
alhalin kun san komai a game da alkawarin
auran ta da Al-ameen. Kun fi kowa sanin
gaskiyya, amma kuka boye ta, saboda son rai to
na bar kowa da Allah, yayi min sakayya, Da
yardar Allah BAKIN CIKIN Mama bazai kashe mu
ba, haka zalika ina mata fatana shiriyar koda
yaushe. Mai surutu da dariya kuma Allah ya
bashi sa'ar yi. Amma kar ya mance kaddara bata
fatan shiryar kowa! Yana sa aya, ya mike ya bar
falon ba tare da wani yayi magana ba, ita ma
umma tashi tayi ta bi bayansa, yayi sauran ke
mazuran rashin gaskiya. Haj. Gaje ta buga tsaki,
ta bar falon. Daga bisani Haj. Hajjo ta lallaba ta
sulale, Alh. Basiru ya dubi Alh. Adamu. Yace
mutane munafukai ne, wai daga dawowarsa, an
sami wani kusugurmin ya feshe shi, don neman
fada. Alh. Adam yace, wai me akace? Au ya faru
ba za'a maida yadda akayi ba? Me za'a baoye
bayan ta gudun kowa kuma ya sani tare da
shegen yaron nan suka tafi! Ai ko ba 'a fada ba,
amsar a bayyane take. Tace, bata so, ba sai a
kyale ta ba, ta auri dan iskan da ake ganin ba
shi da asali ba, ba ita zata zauna da shi ba?
Wahalar tace tunda tasan halinsa. Tace sai shi.
Wai kuma mu ake ganin laifin mu, don fin karfi!
Mts.... Ya ja tsaki yayi waje abin sa. Alh. Basiru
ya mike yana kada kai, shi ma ya fice. Zaman
doya da maja yaci gaba da yaduwa cikin gidan,
duk da ba gaba daya sukeyi ba, amma babu wata
kyakkaywar fahimta atsakninsu. Shi uban dawaki
yana ganin ya kamata su ba shi hkr a
matsayinsa na babban su, sannan yana gani sun
yi masa laifi, don sun bada labarin yadda akayi
mama ta gudu, tunda ba su suka xuga ta ba,
komai ya kwana gidan sauki saboda haka basu
ga dalilin da xai sa Uban dawaki Ya dauki dalan
laifi ya dora masu ba har ya rinka jiran kalaman
tubansu. Su ma fah yanxun ba yara bane, girman
'ya'yan su ya kai, ya gane shekarun su sun cika
daidai matsayin masu 'yanci. Zuwan Ali da Ya
saed don duba jikin Umma da kuma jin labarin
Mama ko ta bayyana, Al-amarin bai yi musu
dadi ba, ganin Yadda iyayen su suka ware
ubandawaki suna masa yankar baya. Musamman
Ya ali, hankalinsa yayi mummunan tashi, babu
bata tym ya gurfana gaban abba yana bashi hkr.
Daga bisani Ya saeed ya shigo falon. Ya ali Yayi
rantsuwa da ace mama zata dawo ta amince da
auransa, maimakon Danliti, a shirye yake a
daura masu aure. Ko a gaban iyayen sa haka ya
maida zancansa. Haj. Hajjo ta rufe shi da bala'i
Allah wadarn wannan so kuwa, tunda yake hana
ka kishin kanka. To idan ma mafarki kake yi, ka
wanke idon ka, ka saurareni, idan har ni na
haifeka, ba xaka auri ragowar Danliti ba. Wannan
kalma tayi masa ciwo, bai san tym daya tasshi
ya tabbatar wa su Haj. Hajo cewa kashe miciji
sukeyi basa sare kansa. Domin ko banza sun
kwana da mamakin Ya ali da yayi tafiyarsa,
daga magana, shima ya gudun kenan? Ko mene
nufinsa? Muna iya cewa matsalarsu ce, ko dama
abba ya fadi kaddara na kan kowa....... Inna
saude ke xaune gefen gadon tana mata fifita.
Kallo daya zakayi mata, ka gane cewa ta jima
tana fama da ciwon tsananin damuwa, domin dai
ta fyade ta fita kamanninta. Amma hakan bai
hana ragargazar shagalin bikin da akeyi cikin
gidan ba. Nasan xakuyi mamaki, idan na gaya
musu cewar bikin yaya Ali da Ya Sa'ed akeyi.
Iyayeyn sun hur masu wuta, tun tym din da suka
lura da take taken shi Ya alin, sam hankalinsa
ba shi akan abinda zai fishshe shi. Shi yasa
suka matsa kwarai da gaske akn ya fiddo matar
aure ko su su fidda masa, ya kuwa tabbatar da
mahaifiya sa xata ita. Gudun kar ta manna masa
alakakai ya sa ya fito da yarinyar da ta dade
tana sonsa a birnin gwari. Amina sunanta, kuma
makwabtansa ne a gidan daya ke xaune. Sa'ed
tuni yake tare da Hassana a kd. A yau ne maza
suka daura auran 11am. Daga can suka wuce kd,
inda xa'a daura na sa'ed bayan azahar. 8pm
wannan rana motocin amare ke shigowa layin
gidan angwayensu, haka daidai wannan tym
motar Danliti parkn a kofar shagon sa dauke da
tasa amaryar. Cike da mamki ayuba ya taso, ya
bude kofar yana fadin, wa nake gani kamar
amafarki? Wai dama kuna tunanin gida? Dan liti
ya fito yayi doguwar miki, yana dariya, yace ah
gamu kuma mun dawo, ya juya cikin mota ya
cigaba da fadin, ya Gimbiya anan zaki sauko ko
na karasa dae gida? Ta kada kai, tace, naji tsoro
ya kamani Danliti, bansan yadda xanyi ba? Yayi
'yar dariya. Yace tsoro kuma? To me xa suyi
miki? Ta kada kai bari dai na sauka nan, canm
ajima na karasa gidan. Ya kace da dariya. Amma
ke shirmen ki yayi yawa, to fito ki shiga ciki. Ta
ballo murfin ta fito, kai! Anya kuwa Mama ce?
Tayi wata shegiyar kiba ta kara ja, ina ganin shi
yasa Ayuba ya xura mata ido, tym din da take
mika masa gaisuwa. Danliti ya bude but suka
ciro manyan jakunkuna guda 2 da kit, sai manya
ledoji guda 3. Ayuba ya taimaka suke shige da
su cikin shago. Kai tsaye dakinta shige ta xube a
katifa. Duk suka biyo bayanta. Danliti ya xauna
kusa da ita. Yace kin gaji ko? Tace kai dai bari,
kamar in kwanta inyi ta barci wlh. To ki kwanta
mana, ai ba kya jin yunwa ko kinaji? Ta kada
kai, banji, to ki kwnta ki huta ne, xuwa karfe
goma sai in tashe ki, ki koma gida. Haka za'ayi,
ta jawo filo ta yada kai, suna kallon juna suna
musayar murmushi. Ya lukuce mata hanci, yace
baby na kenan. Ta juya gefe tana 'ya dariya. Ya
mike ya dubi ayuba yace, to muje dogari. Ya
juya yana murmushi, ina tsarabata? Yace yauwa
ka tuna min, ya suri jakar leda suka fice da ita.
Ya xauna bisa kujera ayuba na kan tabarma, ya
zazzzage kayan kedar a gabansa. Gaba daya
kayan sawa ne. Na gayu ya siyo masa, ya dube
shi suka hada ido, yace ga tsarabar legos nan.
Baki sake yace babu wai, har ma ga tsaraba nan
duka naka ne. Ya washe baki m amma na gode,
watau shi ya sana kunyi jajur abinku, ashe kuna
bakin teku. Yace, hutu ba karya bane ayuba, ga
kuma lafiyayyar bebi na, nake gaya ma. Yayi
shiru yana kallon sa, fuskarsa gaba daya
tabayyana babu abinda bai faru ba. Ya numfas
duk jikinsa ya mutu yace, bakaji Danliti. Me nayi
ma tukunna? Ko kaji surutu ne a gari? Ya gyara
zama yace ba'a tonawa Danliti, abinda nake son
ka da shi, ku sasanta ka aureta kawai, ka ba
masu surutu kunya, donn sunce ba auranta
zakayi ba, tayi saki reshe ne, ta kama ganye, ya
shafa habarasa yace, ko? To ai ba suyi karya ba,
shagali kuma basu ga komai ba daga nan ma
illa masha Allah ba za mu daina ba. Ya kada kai
yace, meye nawa a ciki? Idan ka huta ko xuwa
gobe mayi lissafi. Yace ina fatan akwai kudi
sosai, don wanda na tafi da su naci uabansu, ya
amsa ciniki na na ba laifi, sati biyu ma da suka
wuce na je kno na karo kaya da cinikin yafi
haka. Da kyau mutumina, shi yasa nke sonka
wlh. Yayi 'yar dariya yana daga kayan da aka
kawo masa, ni kuma ina sonka da nutsuwa ba
amma kakiji. Ya mike ya nufi daki yana cewa,
kai ka fiye surutu, bari in baka wuri. Ya shige
dakin ya bar ayuba da kallonsa. Ya kada kai
yace aransa, Allah ka shiryemu. Shi kuwa Danliti
komawa yayi ya hana mama barcin. Karfe 10 ta
dan gota, dan liti ya umarci Mama da ta koma
gidan iyayenta, su san ta dawo, dan su san
matakin karshe da zau dauka. Watakila hakan su
ta cimma ruwa. Watau su amince da auransu
cewarsa madugu uban tafiyar. Ya hado mata
kayanta taf! Da katuwar jaka, tana xaune tana
kallonsa, kafin tace gaskiyya ba xan dauki jakar
nan ba, guda uku kawai dauka cikin kit, in tafi
dasu. Ido waje ya tambaya, sabda me? Ka sani
ko su koroni? Ka bari tukunna mu gani, idan
suka kyale ni, sai in dawo in kwashe sauran.
Idan basu kyaleki ba fah? Sai na dawo nan ka
yanke hukunci duk da zaka yanke. Ya xura mata
do, ai iyayenki na san ba su ki karbarki ba,
hasalima ai laifin su ne, na tabbata yanxun sun
gane kuskurensu, dole su lallabaki. Ta doke
kafadarsa tana dariya, har ma kasan dole su
lallabani? Kai dai ka yi fatan su amince da
auranmu. Yace shikenan, yanxun ki dauki abinda
xaki dauka na rakaki, dare nakara yi. Ta bude kit
ta xuba kaya kala 3, yasa hannu ya dauko wata
'yar karamar doguwar riga yace..... Yace ba xaki
dauki wannan rigar ba? Tace wannan shegiyar
rigar? Shegiya? Lallai ba ki san yadda take mi ki
kyau bane, a'a ka dai barta anan, sanin kanka
ne, su Abba bna za su barni na sanya taba cikin
gidansu. An wuce wurin, ki barta kyasa a gidana.
Ta yada kai kan kafadarsa tace ashe ka gane. Ya
tsikare ta, ta mike xumbur! Ban fa so Danliti
banso! Ta figi kit dinta, tayi waje baki a ture. Ya
kwaso mata gyale da takalmi ya biyota yana
fadin sorry 'yar bebi na! Taja ta tsya tana
haraarsa, ya yafa mata gyalen, ya aje takalmin
gabanta ya jawo kafufuwanta, sa abinki mu tafi.
Ta xura kafar tace wa Ayuba, sai da safe. Yake
yayi ya amsa, Allah ya kaimu. Suka fice, Danliti
na cewa, har kin tabbatar da xamanki a gidan ne
kike ce masa sai da safe? Tace gane min hanya
wai, makaho ya so gulma. Ya ci gaba da dariya,
suna tafe suna hira. Gab da gidan, ya tsaya
sukayi sallama, idan kuma ya gan ta ta dawo
shikenan. Y koma ita kuma taci gaba da tafiya
hankalinta kwance yake, don bata saka komai
illa in su koroto, ta koma inda ta fito. Daga
bisani ma wata dabara ta fado mata. Tana
dosowa kofar gidan, ta hangi kamar ana hada
hadar jama'a, duk da dare ya fara yi, kana iya
gane wa ana sha'ani a gidan. Bata yi wa kowa
magana ba,a haka suma babu wanda ya
shaidata. Sai da ta shige xauran karshe ta aje kit
dinta, ta xauna akai ta hade kai da guiwa ta
kirkiro kukan dole ta shiga yinsa har da
shesheka, sannan hankulan masu wucewa ya
fara xuwa gunta kuma, Ya ali shine mutum na
farko daya fara dosar ta da tambaya, wai wacece
xaune? Gida kike son komawa? A zata son cikin
'yan kawo amare ne, yayi dan murmushi, don ta
bashi dariya. Da girmanki da komai kike
kauyanci? Dan Allah tashi ki koma cikin gida
tun kafain yara su fara miki dariya. Ko an yi miki
wani abu ne? Daga ji ta gane mai magana, shi
yasa ta dago sosai ta dube shi, kawai batare da
tayi magana ba. Gabansa ya tsinke ya fadi
xuciyarsa ke ambato sunan, mama? Sannan ya
tsugunna gabanta ya furta a hankali, mama!
Hawayenta suka kara tsunkewa, ta sadda kai,
tana gogewa da bayan hannu. Innalillahi wa Inna
illaihir raju'un! Ya waiwaiga babu mai kallonsa
yayi sauri ya ja mayafinta ya rufe fuskarta, yace,
taso muje, kar ki bari kowa ya ganki. Ya ja
hannunta suka sulale dakinsy Danlami. Babu
kowa cikinsa, duk suna can wajen fatin da
sukeyi da abokansa. Ya xaunar da ita gefen gado
ya tsugguna. Yace, yaushe kika dawo mama?
Baki na rawa ta amsa, yanxun, idanuwansa suka
kawo kwalla a raunane. Yace abinda kikayi kin
kyauta kenan mama? Da mtuncin ki da komai?
Iyayen mu masu girma da daraja a gurin jama'a,
kika tozarta su? Haba mama, kamar baki sami
tarbiya ba? Ta goge kwalla. Tace, ba haka bane,
Ya ali me yasa zaku rinka ganin laifi na ni
kadai? Nace ga wanda nake so, ba sai a ba ni
shi ba. Ina ruwan kowa da rashin asalinsa? Ai
dai ba daga sama ya fado ba, da uwarsa da
ubansa. Yace, Maganar banza ce wannan mama,
don na tabbata Daliti bai fi miki iyayenki ba. Kin
kuwa san halin da umma ke ciki tun ranar da
kika sa kafa kika bar gidan nan? Kin daure min
kai, ban taba xataon zaki aikata irin wanan
mummuna aiki ba. Tace hakan kadai xai memin
mafita kuma akan bakana na dawo ko Danliti, ko
su rasa ni baki daya. Ya xura mata ido, yana
kada kai. Afuwa ya kamata ki nema ku sulhunta
da iyayenki, su sa miki albarka, ko kin ga
rayuwa mai kyau da anfani nan gaba. Saboda
haka ki xauna anan ki jirani, xan shiga wajensu
in kwantar musu da hankali tukina, gaskiyya
bana so ayi miki taratsi cikin jama'a, kuma
gidan cike yake da baki. Baki? Me akeyi a
gidan? Ya amsa, biki na akeyi dana seed. Kana
nufin kunyi aure? To Ya xanyi, tunda kinki ni
Mama? Akan dole na yi auaran nan, su Baba sun
matsa min. Ina muku murna, nima Allah yasa ni
a danshinku. Ya xura mata ido gwanin tausayi.
Yace, nasan ba xaki ji komai a ranki ba, tunda
ba so na kike ba, amma ni har kwanan gobe ina
sonki, shi ya sa abinda ke faruwa da ke ya xame
min ciwon cikin raina, ki yiwa girman Allah
mama ki sanya tunanin ki dawo sak! Yadda
kowa ya sanki. Karka damu dani Ya Ali, ko da
yaushe ina gaya ma kai dan uwana ne, kauanar
mu ta jini ce mai asali. Kwanciyar hnakalina
kuwa Danliti ya zama mijina. Ina fatan iyayen
Al-ameen sunyi xuciya su fasa? Ko baka ji
komai akai ba? Ya xuba mata ido yana
mamakinta, ya jima bai amsa ba, kafin yace, Al-
ameen ya koma Rasha da ciwon xuciya Mama.....
Ta katse shi ido rufe ta dafe kirji. Tace, nagode
Allah! Har naji sanyi cikin raina. Ya kada kai
yana kallonta. Yace, baki masa adalci ba, baki
tsoron amanarsa ta ciki? Akan me? Bafa dole
bane na aure shi, ina son kowa ya gane wannan,
kawai kaje ka gaya masu na dawo din, kaji me
xasu ce? Yace ni ne nayi niyyar yin hakan, ba
sai kin bani umarni ba. Yi hkr Yaya, bai tanka
ba, ya tashi ya five, ta bi bayansa da kallo tana
fadin cikin ranta, je ka dawo, duk na kosa in san
babin da nake. Cikin dakin yayi sallama, abba
ya amsa masa yana kokarin hadawa Umma shayi
ta samu ta dan sha, ya akayi Ali? Ya xauna gefe
kusa da shi, yace babu komai abba, wata
alfarma naxo nema wajenku. Hankalin abba ya
dawo gare shi, yace ina jinka. Allah ya sa batafi
karfi na ba. Ya kada kai ya amsa, bata fi ba
Abba, duk mai laifi idan ya nemi afuwa, me
yakamata ayi masa? Ya dube shi da kyau da
mamaki yace, ayi masa afuwar, domin Allah
yana son masu yafiya ga bayinsa. Su kuma masu
laifin su yi alakwarin ba xasu sake komawa ga
wancanm laifin ba. Laifin me kayi? Ya amsa,
laifin mai girma ne Abba, a misali Mama ta
dawo ta nemi gafara, abba xa ka karbi tubanta?
Ba abba kadai ba harda Umma dake kwance ta
xubo masa ido, abba ya jima kafin ya numfasa.
Yace Bansan dalilin da yasa ka min tambayar
nan ba, amma ina so ka sani, mama ta aikata
laifi mafi muni a shafin tarihin gidan nan, da mu
karbeta da kar mu karbeta, bakin fentin da ta
shafa mana yana nan baxai goge ba, ina so ka
sani Ali, xaiyi wuya a fadin gari na Mama ta
sami wani mijin, face katon daya dauke ta ya
boye wani wuri tsowon watanni 3. Abu na karshe
da nake so ka snai, shine bai kai kadai ka rokeni
ba. Al-ameen ma ya rokar mata gafara kuma
nayi masa tare da alakwarin ba xanki karbarta
ba. Saboda haka ka kwantar da hankalinka,
muddin Mamma ta dawo gidan nan, ba xan ce ta
koma ba, haka xalika idan bata sauya ra'ayinta
ba, ba xan ce mata a'a ba, Allah na kallo, nayi
kokarin na, don nuna mata hanyar kwarai da
samun abokin zama na kirki mai kyan asali. Ko
duniya ta zageni, alhakin Na suka duka kuma
zamuyi shari'a da su gobe kiyama. Kawai ji yayi
kwallah na xubo masa, saboda tausayin Abba,
yasa hannu ya goge, abba ya riga shi sake
magana, ka daina kuka Ali, kaddara ce, tashin
hankalina daya, mahaifiyarta da ta kasa samun
nutsuwa. Ina jin tsoron kar ciwon xuciya ya
kamata kamar yadda likitocin da ke duba ta
suke gargadin ta kullum. Dalilin da yasa kenan
nake fatan Allah ya sa mama ta dawo, watakila
ya zama waraka ga mahaifiyarta. Na tabbata
hankalinta xaifi kwanciya idan tana ganin ta
koda a dakin auran Danliti ne. Ya Ali ya gyara
xama yace, gaskiyya ne abba, kuma naji dadin
bayanan ka. Saboda haka ina mai farin cikin
shaida maku cewar mama na nan ta dawo. Abba
ya xura masa ido. Umma kuwa ciccibawa tayi ta
tashi xaune. Ba fahimce ka ba Ali? Inji Abba,
yace Mama na nan a cikin gidan nan, idan kun
ban izini, zan shigo da ita ta roki gafararku.
Suka dubi juna shi da Umma baki sake, tuni
hawaye suka tsinke mata, tana kada kai tare da
salatin Manzo. Abba ya dube shi yace, je ka
ashigo da ita Ali. Har ya mike ya sake komawa
ya xauana, yace Abba ina fatan ba xaku daga
mata murya ba, kasan gidan na cike yake da
baki. Yace Insha Allahu, ba xan daga mata ba.
Yace nagde abba. Ya mike ya wuce, abba ya
bishi da kallon, sannan ya dubi Umma, ashe
haka Ali ke da hankali? Nayi kuskuran hana
masa auran Mama tunda farko. Umma ta goge
hwaye tace, hakika mama tayi asara masoya 2.
Haka Allah ya so, ba mu da abinyi, dai yi masa
godiya, abba ya sauke numfashi, sukayi xugum
suna sauraron ta yadda mama xata bayyana
garesu. Jimawa kadan suka tsinkayi muryar Ya
Ali yana fadin ki shigo mana! Na gaya miki
komai ya wuce, ki shigo kawai. Make-maken
munafurci takeyi ba wai ainihin tsoron bane cikin
ranta, da su abba xa suyi kuskuran cewa ta juya,
fes! Zata juya babu waiwaye sukayi sallama
dakin. Ya ali na dauke da kit dinta. Ta toge
bakin kofa, yasa hannun ya janyo ta har
gabansu abba dake sake da baki suna kallon
abin al-ajabi. Gata abba, umma ga Mama, ku
mance da abinda ya faru, ku amince da xabanta,
ku sa musu albarka, sai kuka ga Allah ya basu
zuri'a abin alfahari. Mama ki durkusa ki roke su
gafara. Ko dama a durkushen take kuma tuni
hawayen suka tsunke mata, murya na rawa,
tace..
BAKIN CIKI 2***12 Abba kuyi hrk, Umma ki yafe
min. Abba ya numfasa yana kada kai. Ya ce a
rayuwata gaba daya Mama ba tba xataon xaki
min irin wannan mugun butulcin ba. Na dauke ki
'yar da na dauki burin duniya na dora a kanki.
Kece kika bambamta da kowa cikin xuciyata,
kuma na nuna miki dukkan gata amma dare
daya, kika numa mana akwai wanda ya fi mu
muhimmaci a rayuwarki. Tabbas na yarda da
hakan, don a tunani na xan ga kin dawo kin
bushe a lalace saboda tunanin kin barmu cin
BAKIN CIKI sai gaki Fes! Kinyi kiba. Ban miki
baki ba, ba kuma xan miki ba, amma ina mai
tabbatar miki in rasa masoyi, kin rasa mai
tsanin kaunar ki tsakani da Allah, kuma a yau na
kara nadamar hana Ali auaranki tun farko.
Maganata karshe itace, tunda kin nace sai
Danliti to ki gaya masa ya turo magabatansa,
muyi magana, sannan kiyi wa Yayanki Ali
godiya, domin yayi miki dukkan taimako.
Zaciyarta fara sol! Jin Abba ya ambato Danliti ya
turo. Ta kara dukawa tana goge kwalla. Tace,
ngde abba, kuma ina kara baku hkr, don Allah
ku yafe min. Ta rarrafa gun Umma ta cusa kanta
jikinta, umma kiyi hkr! Ta share hwaye tace ai ya
wuce Mama, kinci albarkacin al-ameen da ali.
Amma gyara kayanka, ai baya zama sauke mu
raba ba. Ki bi duniya a sannu, domin ita duniya
budurwa ce mai kyale-kyale da yawa, da zarar ka
biye mata, to ka bace ka kuma shiga uku ka
lalace. Ban da abin kari a gareki, don nasiha
anyi miki, amma kin rushe saboda batan basira.
Allah ya ganar da ke, ya sa ki a hanya
madaidaiciya. Ya ali ya amsa da amin, yayin da
mama ke ci gaba da gugar hawaye. Alin ne ya
cigaba da cewa, don Allah abba karku nuna
kowa ta dawo har tym din bakin nan xasu koma.
Ko su Baba a kyale su tukuna. Ke mama ina son
ki cigaba da xama cikin dakinku dan Allah, na
san xuwa gobe da yamma kowa xai watse, sai a
kam magana ta gaba, kinji? Ta amsa da kai,
Abba yace shikenan Ali, kana son ka rufawa 'yar
uwarka asiri, asirin kuwa da ya riga ya tonu.
Yace kayi hkr dai abba, yace babu komai, ta
tashi ta koma dakinta, idan tana jin yunwa,
akwai abinci, yace xaki ci abinci ne? Ta kada
kai, to taso na raka ki dakinki. Umma mun gode,
tace Allah yayi albarka, ya amsa da amin. Tare
suka mike suka bar dakin. Umma ta tafa hannu
tana salati, sannan ta buga tagumi. Yanxun alh.
Danliti xata aura? Yace, t ya xamuyi, wa kike
ganin xai fito neman auranta, bayan ya san
wannan kwamacala? Haka nan xamu hkr da
abinda Allah ya kaddaro, yanxun dai bana ce ya
turo ba? Sai mu sa ido mu ga wadanda xai turo
din. Ta numfasa, tace Allah shi kyauta yace
amin. Ke dai ki kwantar da hankalinki, ki daina
xa damuwa a ranki don Allah. Tace naji alh. Ya
ciga ba hada mata shayin suna tattaunawa.
Kamar yadda ake tattaunaea da mama da Ya Ali.
Shawarwari kawai yake bata, tana sauraronsa
kamar gaske. Har kusan sha daya da rabi suna
tare. Dagab bisani yayi mata sallama ya barya
cike da farin ciki da baya misaltuwa. Nan da nan
ta fada bayi tayi wanka, ta kintsa jikinta ta
kwanta. Kewar Danliti ta lullube ta, fadi take
cikin ranta, ba dan dare yayi ba da naje yiwa
sweety Na albishir. Da kyar barci ya sace ta
saboda murna. Washe gari hidima taci gaba,
mama na cikin dakin na kulle babu wanda ya
san ta dawo, daga Ya Ali sai su Umma. Kuma
anyi sa'a taji maganar Ya Ali batayi marmarin
fitowa ba, sai shi ne ma ya kan saci jiki ya
shiga wajenta, ya ganta yaji dan ji sanyi aransa.
Allah sarki! Garin dadi na newa, iska na ta
wahalar da mai kayan kara, bayan sallahr la'asar
baki suka koma muhallin su aka bar amare da
angwayensu. Shi kuwa Ubandawaki 'yan uwansa
ya tara falon baki yace, naki ku ne a matsayin
ku na kannena na in shaida muku cewar Mama
ta dawo daren jiya, kuma har na yanke hukuncin
ta gayawa Danlitin ya turo magabatansa, muyi
maganar aure. Ban san yadda zaku karbi abin
ba, ko da mahimmanci ko ya zama abin dariya a
gareku, duk daya ne, ni dai na fita hakkinku.
Suka dubi juna cikin sigar tsarguwa, sannan
Alh.basir yace, ai shikenan yaya, amma banji
dadin yadda kayi mana fassara ba, ya kamata
kayi mana uxuri tunda mun ce maganar nan
bada wata manufa muka fadeta ba. Amma ace
mama ta dawo tun jiya, sai yanxun mukeji? Ba
komai. Alh. Adam ya cage, tabbas naga Danliti a
shagonsa, sai dain banyi tunani tare suka dawo
ba, tunda banji labarin ba a cikin gida. Sai dai
Yaya a gaskiyya muna so mu ganar da kai cewa
ba farinciki mukeyi da abinda ya sami mama ba,
mutuncin gidan nan, ai duk namune, me zai sa
muyi murna da rugujewarsa? Abba yace duk naji,
magana ta gaskiyya, Allah kadai yasanta, don
shine masanin sirrin xukata. Abinda ya sa bau
san Mama ta dawo ba, sai yanxun. Ali ne ya fara
ganinta kuma ya xo ya sameni guiwa 2 ya roke
ni da kyale mama kar in daga murya, saboda
baki fa ke cikin gidan nan. Idan sun tafi ayi su
wacce xa ayi. To maga ma ta kare, nacewa
Danliti ya fito a daura musu auran, su karata.
Allah dai ya gani ba da son raina bane. Fuska Ya
mutse Alh. Basir ke cewa, Dan liti xata aura?
Yace bamu da abinyi, haka Allah ya so, sai dai
muyi mata fatan alkhairi. Saboda haka bana son
abin yayi tsawo, yana turo sai aure. Ya turowa
za'a sa rana kuma ba zata wuce sati 3-4 ba duk
abinda Allah ya hore min shi xa'a kai mata. Ita
kenan maganara, kowa na iya tafiya harkokinsa,
mu saurari xuwan magabatan nasa shikenan,
Allah ya nuna mana. Haka suka fadi baki
dayansu. Abba ya amsa da amin, suka bar falon
ba yabo ba fallasa, cikin xukatansu, ma'ana
intayi ruwa rijiya in ba tai ba masai. Suna shuga
sasan su, suka bajewa iyalensu babu bata tym
suka fara xuba sharhi. Haj. Gake kuwa har da
guda. Daga bisani suka baxama sassan Uban
dawaki, don gain Mama tare da yiwa Umma
murna dawowar Mama fida, amma a zahiri a
cikin xukantasu yanayin Maman suke son gani.
Suka kwarara sallama, umma ta amsa, sai
mukaji daddadan labari! Ina maman? Inji Haj.
Hajjo, tana dakinta, gaba daya sukace Allah shi
kyauta na gaba. Yanxun da Danliti xa'ayi auran?
Tace, nufi ne Allah, duk abinda ya rubuta bamu
isa mu goge Ba. Haj. Hajjo tace gaskiyya ba
haka muka so ba. Sai dai hkr kwai. Haj. Gaje ta
tabe baki tace, ya xama dole, amma a hakikanin
gaskiyya mama ta bamu kunya. Ajin ai ba daya
bane in banda batan basira. Koda yake ance so
mako ne. Allah ya sanya alkhairi. Sukayi dan
shiru, kafin suka nufi dakin Mama, ina kike?
Kina jin mu amma ba xaki fito ki gaishemu ba?
Tana xaune gefen gado, ta fesa ado kyanta ya
kara bayanna, banda haka da ibar da ta kara
suka kalli juna sabe da haba, kafin Haj. Gaje ta
soma xuba, lallai Mama, watau hankalinki a
kwnace kika je, ki ka dawo! Wannan kiba haka?
To Allah yasa ki sami irin wannan a gidansa.
Haj. Hajjo ta amshe amin dai, kin dai riga
kinsan halinsa, komai yayi miki sai ki hadiyewa
cikinki, kar ki doshi kowa, tunda kin nace shi
kike so! Ko kuwa gaje? Tace haka yake yaya, ai
kowa ya sayi rariya yasan zata xubda ruwa.
Mayafinta dake bisa filo ta figo ta mike tsaye ta
xura takalmanta tayo waje tana yafa gyelenta, ta
barsu anan sake da baki, suna kallon juna. Ko
kinga dibar albarka? Inji Haj. Hajjo, Haj. Gaje
tace, mamaki kikeyi Yaya? Karfa ki manta
watanni 3 ta shafe a bariki, an kuwa ce xama da
madaukin kanwa, shike kawo farin kai. Mu meye
namu? Ta malam ai bata wuce amin. Can suka
sameta dakin Umma tana neman izinin zuwa
wajen Danliti, don ta shaida masa sakon abba,
suna isowa, umm ana fadin bance kije ki xauna
ba, mutunciki shine ya biyo ki nan kofar
gidanku. Saboda haka daga yau kar na sake jin
kin koma shagonsa. Tace, to Umma, insha Allah
yanxun xan dawo. Ta sa kai ta fice, ba tare da
Umma ta kara wani abu ba. Nan su Haj. Hajjo
suka xauna suka cigaba da kwasar tsegumi, ita
kuwa tana fitowa xauran farko, angwaye ta ci
karo dasu, saeed Ya maka mata harara, ya wuce
abinsa cikin gida. Ta dubi ya Ali, tace me nayi
masa? Yace kin fi kowa sani. Taja dogon tsaki,
aikin banxa, to shinme me? Don ya ki min
magana? Yace, kin baci da Rashin K mama, me
yasa? Da ba haka kike ba. Ta dan tabne baki
tace, ni ina da wurin xauwa, ba na fito magana
da Ya Saeed bane. Yace amma ba kije kinga
amare ba. Xanje ai, so nake in sauke wannan
nauyin ko ni,a na kama dahir. Yayi dan
murmushi yana kllonta, mama kenan, to a dawo
lfya, nasan sakon bai wuce na Danliti ba. Tayi
'yar dariya. Shi ysa nake sonka Yayana, bari dai
in dawo amaryarka ka xan fara xuwa na in gani.
Ta wuce tana cigaba da dariya, ganin yadda yayi
tsaye duk jikinsa ya mutu. Ya bita da kallo,
sannan ya kada kai, yace, ni ma ina mutuwar
sonki Mama. Ina ma ace hankalinki xai dawo
gareni? Ya sauke numfashi ya shige wajen
amaryarsa. Bakinta har kunne take sallama kofar
shagon, ayuba ta gani xaune ckin shagon ya
amsa mata cike da fara'a amaryarmu kenan, ya
gajiyar tfya? Tace tabi lfya, ina mutumin? Ya
amsa yana ciki tun azahar yake barci saboda
ragwanci. Ta fara dariya, lallai kuwa ragwanci,
barin inshiga dole ya tashi ya bani goron
albshiri. Ta wuce ciki, ayuba na fadin, ya dai
kamata ya tashi ko salla ya samuyi. Kan tsaye
bisa katifar ta fada, ta dada masa duka cinya,
don Allah tashi rago! Ka wani baje kana gugar
barci, ni ina can ina tunaninka. Ya bude ido
firgigi yana kallon ta jim, sannan yayi dan
gajeran tsaki. Yace kash! Wlh ba don ke bace,
marin Mutum zanyi. Kin ji dadin barcin kuwa?
Tayi far da ido, tace ko? To ka tashi, na tabbata
dadin barcin bai kai albishir din baki na ba. Ya
xuba mata ido yace fadi ina jinki. Idan kuma bai
fi ba, kinsan Allah sai na sanya ki kuka, ai kin
san gamuwar mu babu tausayi. Tayi 'yar dariya,
tace, haba duk wannan kukan wasa nakeyi,
kama daina hura hanci. Yayi murmushi, haka
kikace? To shiknen, fadi ina jinki. Ta gyara xama
albishirnka? Yamasa goro. Xaka bani Ah! Me xai
hana? Ke dai gaya min inji. Abba yace in fada
maka ka turo, ranar auren mu za a sanya. Ya
xuba mata ido, ya kasa ko motsi, kayi shiru? Ya
sa hannu 2 ya mutsutsuke idanuwansa yace, dan
Allah karki xalayeni! Ta ware ido, kana nufin
baka yarda ba? Gaskiyya ban yarda ba, yaushe
Abba xai yarda ya bani ke, bayan ya san bani da
kowa a garin nan? Sannan suna min kallon dan...
Tayi wuf ta rufe bakinsa, sau nawa xan gaya
maka ka daina dorawa kanka maraici? Ina sonka
Danliti..... su abba kuma sun amince ka turo asa
mana rana da gaske na ke gaya maka maganar
nan ba wasa ba da sauri ya figo ta jikinsa yayi
wani irin ihu wai shi murna ayuba ya kwaso a
guje ya fado dakin ya same si kankame da juna
dan haka. Bai tsaya tambayar komai ba ya juya
ya fita yana kada kai cikin ransa yana fadin
"Danliti akwai dan iska"ya jima bai kyale mama
taci gaba dayi masa bayani ba yanzu yaushe.
Zaka turo? Ya yunkura ya tashi zaune yace
bashine matsalar ba wadanda zan turar sune
matsalar ta dan bata fuska tace ai ba za ka
rasaba "Danliti ko yan dattijan daku ke gaisawa
sun isa su wakilce ka ko kuwa? Ya zura mata
ido duk sun juye, yace haka ne sai ki baru in gan
su mudaidaita tukunna sannan in gaya miki
ranar daza su zo ko" tace shi ke nan bari in
kwashe sauran kayana in koma gida ya kara
matsarta haba tun yanzu ?" Umma ta ce kar na
dade kuma tunda sun amince da kai ai zaka
rinka zuwa ne kan ka tsaye,"ya kankameta ya na
fadin haka ne amma ban so ki tafi yanzu sonki
kawai ke azabtar da ni ina kewarki da yawa jiya
da kyar nayi barci kinji yadda ki ke tashin
kamshi?gaya min dame dame ki ka shafa in karo
miki irinsu?"Bata iya bashi amsa ba don tun
tafiyar su yake koya mata irin wannan renon ya
gama da rayuwar ta gaba daya kai ALLAH ka
raba mu da sharrin masu sharri,magariba ta
wuce wadan da sukaje masallaci ma sun koma
gida yayin da mama ta fito daga shagon Danliti
jaye da katuwar jakar kayanta. -yar tafiya kadan
ya taka mata ya dawo abinsa bata sami dan
dakon da zai daukar mata kayanba ba don haka
da kanta tayi ta ja har gida abba da umma na
zaune a falo dauke da bakin ciki maras
misaltuwa mama ta turo kofa ta shigo sa
sallamar ta dauke da uwar jakar kaya babu
wanda ya amsa mata ta wuce ta gabansu ta
tsugunna tace sannu abba, wani irin kallo yayi
mata mai isar da sakon haushi da takaici kafin
yace daa ina kike?ta dan sunkuyar da kai tace
naje gaya wa Danliti sakon ka ne ai na gayawa
umma kafin na fita ko um..."Ya daka mata tsawa
rufe min baki don ALLaH shine zakije ki zauna
har bayan magariba kiji tsoran ALLAH mama ki
sani cewar mutuncinki ki ke zubarwa wannan
uwar jakar da kika shigo da ita tawace tukuna?
idanuwanta suka kawo kwalla ta fara rawar
murya na...nawa ne.. Kayan da...Danliti ya siya
min ne yace to ba a gidan nan ba idan yazo ki
maida masa kayansa ya baki can gidan sa,ai
kinji ni ko,?ta amsa da kai umma ta cire tagumi
ta kare mata kallo sannan tace Alhaji ya kamata
a tuhumi yarinyar nan idan idan tabada kanta
gareshi kasan istibira'i ya kamata, kafin a daura
auransu domin ni banyarda da mama ba a yadda
suke tare da yaron nan,ya numfasa ciki da bacin
rai yace ki na da gaskiya don ni ma wallhy ina
wasi wasi cikin raina ke mama ki gaya min
tsakaninki da ALLAH ki fi jin tsoran sa akan
komai na duniya ki gaya min gasjiyar abinda ke
tsakanin ki da Daliti kar kisa muyi kuskure da
gangan idan kin san da wani abu to ki gaya
mana mubi tsarin da ALLAH ya shimfida. -sosai
ta goce da kuka murya na rawa tace ALLAH abba
babu abinda ya shiga tsakanina da shi duk
sukayi shiru suna dubanta kamar sun gaskanta
ta kamar basu yarda ba amma dolensu yarda
tunda basu da wata hujjar kama ta don haka
abba ya daka mata tsawa ya isa don ALLAH tana
wani bare baki kamar mummuna tashi kiba mu
wuri kuma na gaya miki yana zuwa ki maida
masa jakar kayansa,ta goge hawaye ta dan
sunkuyar da kai tace yace ya gode insha ALLAH
zai turo din suka yi banza da ita shiyasa da dago
ido ta dube su uwar hararar da ta yi arba da ita
tilas tasa tayi saurin maida kanta kasa jim sun
kikara cewa komai yasa ta mike simi simi ta
janye jakar ta, ta wuce daki bakin nan tamkar na
agwagwa kai tsaye bayi tashige tayi wanka ta
dauro alwala ta fito ana ta kiran issha'i,don
haka tana yin magariba ta dora issha'i bayan ta
kammala ta fito neman abinci nan falo sukayi
kicibis da yaya ali wai me ki ke nufi baza kizo
kiga amarya ba?ta kama kugu hannu biyu tace
wannan amarya an damu nazo na ganta hala
tafini kyau ne ya kama dariya kafin yace soosai
kuwa tafi ki kyau muje ki ganta tace haka yake
amma duk kyanta dai ni aka fara so kifin ita
saboda haka a daga min kafa inci abinci
tukuna"kalamanta sun ruruta wutar zuciyarsa ba
kadan ba koda ganin yadda jikinsa ya saki
kasan ya fada wani yanayi ya zura mata ido
hannayensa rungume a kirjinsa murya sanyaye
ace zancan ki dutse yar uwata,.