Baqin Ciki Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Baqin Ciki Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 1 of 9
HADA DOCUMNTS BY
ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA AND ENGLISH NOVELS
@ WASAPP 08066360176
BAKIN CIKI 1***1 Sarautar Uban dawaki babbar
sarauta ce a garin fandagori can cikin jihar naija.
Babban gari ne wanda al'ummar cikinsa suka
bunkasa wajen noma da kiwo. Gidan uban dwk
Alh Awaisu Malami katafaren gida ne cike da
zuri'a masu yawa na kannensa guda 2 kuma
shine babbansu kat! Sassan sa yafi na kowa
girma da tsari ginin zamani. Matarsa daya Haj
Halima da yaya maza uku a jere. Abdulkadeer,
Abdulkareem da Abdulrahman sai kandensu "ya
mace tilo a cikinsu Sakina, sunan mahaifiyar
uban dwk gareta shiyasa suke kiranta "Mama".
Santaleliyar yarinya wacce Allah yayiwa sura
tamkar ita tayi kanta kusan zuri'ar gidan haka
suke da kyau na fulani. Amma ita mama ta fita
daban wajen cikar sura daka gganta dole
gabanka ya fadi sbd tsabar kyau. Shiyasa tun
shekarunta basu kai ko'ina ba samari suka
yanyameta kowa na so, musamman cikin
gidansu watau yan'uwanta abin har yana so ya
zama rigima a tsakaninsu. Saida Uban dwk da
kansa ya tara su ya soke maganr soyayya da
Mama ya kuma kar wanda ya kara kiranta da
sunan tadi. Yayi haka ne don a sami masalaha
da zaman lfy. Allah kuwa ya taimaka kowa ya
gama bacin ransa ya hakura. Baya ga haka yana
ganin Sakeena bata kai shekarun da zata tsoma
kanta kogin soyayya ba alhali tana tsaka da
karatunta mafarin kenan da zata tafi babbar
sakandire yayi kokari ya samar mata makarantar
kwana ta yanmata dake bakori (FGGC Bakori)
Sannan hankalinsa ya kwanta amma wann
hukunci nasa yayiwa wasu daga cikin iyaye mata
ciwo har suna ganin sbd kyaun da Mama take
dashi ne yasa ake wulakanta yayansu suka rinka
ganin kamar suna sn su dauki dogon buri ne su
dora mata. Tabbas uban dwk nada buri akan
yarsa tilo mace saidai yasha bamban da irin
burin da matan gidan ke nufin ciki zukatansu
wanda bazai wuce ya aurar da ita ga hamshakin
me kudi ba ko basarake. Shi burinsa yarsa tayi
zurfin karatu kamar sauran yayyinta maza
wadanda a halin yanzu Abdulkadeer major nr na
soja, Abdulkareem accountant ne a CBN, sai
Abdulrahman dake NYSC a Jalingo. Ya kuwa
lashi takobin ko bashi da rai yan'uwanta su cika
masa wann buri nasa. Kwanci tashi Mama ta
shiga SS2 kuma yau sukayi hutun 2nd term tun
safe Uban dwk ya tura drivernsa ya daukota,
basu iso fandagori ba sai bayan la'sar kowa na
ta murna musamman yara da suka yanyameta
suka kwashe mata kaya zuwa sassansu. Ta shigo
da sallama Ummanta ta tarbeta ta rungumeta, ta
shiga sauran sassan ta gaishesu, Salisu da
Danlami kadai ta samu acikin samarin sassan.
Ta zauna suka taba yar hirar skul sannn ta tashi
koma sassansu tana shiga ummanta tace
Abbanki na nan ya dawo ta wuce da sauri ta
sameshi a falonsa, bakinta har kunne ta dan
rankwafa tace Allah ya taimaki mai martaba!
Fara'arsa ta karu: Allah yabar min Mamana na
shigo akace kin shiga sassa. Ta zube gabansa
tace eh naje gaishesu ne, ina yini Abba? Lfy lau
ya karatu? To mungode Allah, yace ina report
sheet a kawo na gani. Ta mike taje ta kwaso duk
takardun yayi ta dubawa yana fadin da kyau!
Bayan ta kammala ya dubeta kinyi kokari sosai
Mamana na baya miki amma har yanzu kina da
yar matsala a biology sai kin kara bada himma
kinsan dalili? Ta kada kai yace kara matsowa
kiji ta matso kusa dashi sosai kafin yace: buri na
ki zama likita Mamana, sbd a rayuwa ta ina
sha'awar in ga ya mace likita, abin yana burgeni
kwarai, shiyasa tun ranar da Allah ya bani ke
nake ta addu'ar Allah ya raya minke in samu in
cika burina, ko kuwa ke bakya sha'awa? Tace
sosai ma nakeson zama likita Abbana. Kuma
I.S.A zan kara himma don ganin na gama da
biology. Ya dafa kanta cike da farin ciki yace
yauwa Mamana, Allah yai miki albarka tace
ameen Abbana. Daga nan suka ci gaba da hirarsu
saida akayi sallama dashi ya tashi ya shiga
babban zaure inda Majalisarsa ke taruwa.
Mamana ta koma gurin Ummanta a kicin suna
aikin abinci tana bata labarin abnd Abbanta
yace, Umma tace yallabai kenan Allah dai ya
cika masa wann buri nasa tace I.S.A Umma
saina zama likita. Tace Allah ya yarda wai waya
gane min Mama da farafen kayan nan? Mama
tana dariya tace na dan ratayo wann abun da
suke sawa a kunne ina takawa ana ga Dr
Sakeena nan zuwa. Suka fashe da dariya.
Washegari misalin 10:am Mama ta fesa ado da
koriyar atamfa sannn ta dora after dress ta yafa
mayafinta ta sami Umma a daki, sai ina? Zani
gaida Inna saude ne. A'a kice dai zaki gun
Baraka. Tayi dan murmushi Umma ai duk dayane
Idan na gaida Inna ta sai muyi hira da Baraka
kawata... Uhummmn... To kodai lauya zaki zama
a fasa likitan nan? Tayi dariya wai kinaso ki
hada ni da Abba kenan.. Lallai kam to kice ina
gaida Sauden idan ta gama dinkunan ta baki
kizo min dasu, shikenan amma ina fata akwai
nawa aciki. Umma tace babu naki aciki duk
nawa ne, Mama ta dan kirne fuska kai umma ai
kuwa zan zabi daya aciki, tace duk zannuwa ne
ciki da alakum rigunan kuma masu hannu ne,
zan canja style ni inaso a haka, to ban yarda ba
ki anso min kayana kawai idan ta gama. Ta
jinjina kai shikenan umma nina tafi, adawo lfy
karki dade... Ta saba jakarta tana fadin to
Umma.. Salis ne zaune a kofar gida tana fitowa
ya kare mata kallo sama da kasa kafin yace sai
ina kuma? "Gidan Inna Saude zanje" 'Okay na
kuwa ga Baraka jiya itama ta dawo". Ya mike
muje in rakaki ko bakiso? "Muje mana ta wuce
ya biyota suka jera. Wai Mama meyasa Abba
yake takuraki dayawa? "Kamar yaya?" Baya son
kina kula samari kin kuwa san har yanzu yaya
Ali yana sonki? Ta dube shi farin sani kuwa
tunda yana gaya min a sace amma fitinar duk
waya fara daukota? Yace a'a ba don muna uwa
daya uba daya dashi ba, abnd yaya Sa'ed yayi
bai kyauta ba, tunda yasan shi yana sonki
menene na shi na shigo nemanki? Ya fa san
halin Yaya Ali ba hakuri ne dashi ba yanzun nan
sai ya nuna maka hauka. Ta dan tabe baki tace
hmmmnn... Kai nifa karatu ma zanyi dama sun
sa ransu a inuwa, babu wanda zan aura acikinsu
koda Abba bai dakatar dasu ba.. Ya zura mata
ido kina wulakanci Mama kice dama kema ba
sonsu kike ba? Baka gane ba.. Me kikeso ki
fada? Karatu zai hanaki aure ne? Ta kada kai
nutsuwa nafi bukata sbd karatuna mai son
nutsuwa ne.. Me zaki karanta? "Akikin likita" ya
ware ido Uhmmnn.. Dokta Sakeena kenan! Tayi
murmushi har kasa naji gingiringin! Yayi dariya
daidai lokacin da suke tsayawa gefen babban
titi.. To Dr Sakeena ni anan zan juya.. "Ngd ai
kaga har nayi sauri da yake ana hira" yace dadin
abokin rayuwa kenan, don ma ba Ya Ali bane
tayi dan tsaki get lost donAllah ka rabani da
wann zancen, yana dariya ta tsallaka titi ta
barshi hanya shi kuma ya juya ya koma gida.
Mota yake kakkabewa ya cire shimfidar foot mat
lokacin da Mama tazo wucewa, yayi tsaye yana
kallon wata surar da bai taba gamo da irin ta
ba.. Kai ya kasa daurewa saida yayi mata
sallama.. Ta dago ido ta dube shi tare da
amsawa, sautin muryarta ya kara rikita shi ya
bita da sauri donAllah ko zaki 5mins kadai in
tambayeki? Ta tsaya caka tana dubansa, dogo ne
sosai "Allah yasa na sani" yace donAllah anan
garin kike? Tambayar tasata a mamaki tace eh
mana, amma ban taba ganinki ba sai yau. Tace
kasan daurowa take , gsky ne, ah suna nan Al-
Ameen ina minna amma nan gidan kaka ta ne,
na kawo Mamana ne ma yanzu sau dayawa ina
zuwa nan shiyasa kikaji na tambayeki. Haka ne
yau ne Allah ya nufa zamu hadu. Ya sauke
numfashi gsky ne, allah ya hadamu kuma take
nan kin kwanta min a rai ko zan san sunanki? Ta
dan kauda kai yanayin mata saida gabansa ya
fadi tsoro ya kamashi kada ya sha kayi. Ya
marairaice dan daure ki gaya min ba don hali na
ba, hali? Nasan halinka ne? Yace na mita da
bakin naci! Tayi dan murmushi Sunana Sakeena'
kai! Sunan nan ya dace da kykkyawar fuskar
nan! Anan unguwar kike? Ta dan kada kai can
gidan zani wajen kanwar Ummana, ok to gidanku
fa? Ta yatsuna fuska alamun ta kosa ta wuce,
harta fara takawa ya biyota na dameki ko? Yi
hakuri so ne ya kamani ki taimake ni, ta tsaya
ta dube shi da idanuwanta farare kal dasu tace
kasan Uban dawaki? Can tsallaken titi kenan? Ni
yarsa ce idan kasan gidan, nan ne gidan mu
saidai akwai matsala. Ya hadiye murmushin sa
Matsala? Na shiga uku a ina matsalar take?
Tace Abbana baya bari azo zance wajena yace
sai na gama karatu hasali ma bording skul
nakeyi daga hutu sai hutu ake ganina, ya danyi
shiru jim kafin yace to ya za'ayi yanzu Sakeena?
Gsky ba da wasa nakeyi ba ya kike ganin za'ayi?
Tace ban sani ba amma ina ganin hakuri zai fi
kyau, mu saurari lokacin kammala karatun, ba
kai kadai bane akwai wasu wadanda suka rigaka
magana kuma sun hakura. Yace su zasu iya ne
nikam bazan iya ba Sakeena! Ina sonki sosai
babu abnd nake rayawa a cikin rain aface na
aureki. Ta dan kara dubansa sai taji ya fara
zama cikin ranta. Matsalar kawai batasan yanda
zatayi dashi ba har tace yaje gidansu. Don haka
tace kayi hakuri Al-Ameen.. Ta wuce da sauri ta
barshi yana kira Sakeena! DonAllah tsaya mana
kiji.. Gidaje biyu ta wuce na ukun shien nasu
Inna Saude. Ta sa kai ciki tare da sallama
baraka dake tsaye tsakar gida tana gyara zaman
mayafinta ta juya da sauri baki sake suka
rungume juna.. Gidanku zan tafi yanzu a haba?
Wllh yanzun nan kewa Inna sallama har ta bani
dinkunan Umma tace dama nima ta aikoni
akansu, ina Innar? Tana ciki suka shige tare Inna
tace au Mama ce? Har kin rigata kenan tana
dariya ta zauna sannu Inna ina kwana? Ta amsa
lfy lau an dawo lfy? Tace wllh lfy lau inna, kinga
dinkinta dama za'aje kai mata Mama ta fiddo su
a leda ta daddaga kai amma atamfofin masu
kyau. Suka dan taba hira suka wuce dakin
Baraka kowacce ta cire after dress. Mama ta
fada katifa tace tun dazu ya kamata in shigo
gidan nan bakon unguwarku ya tare ni. Bako? A
ina?tace oho! Wai nan gidan Alh lado suke cewa
ko? Eh nan ne gidan kakarsa Al- Ameen yace
min sunansa, bakinta har kunne ta jawo
hannunta suka tafa ban mu kashe yar'uwa bakar
fata kice kinyi gamao da katar. Likita bokan
turai yau shiya kawo Maman tasa kenan. Ta ware
ido kina nufin Dr ne? Kwarai kuwa ko bai
kammala ba kiris ya rage, don tuntuni naji ana
fadin sabis yake, ta kama baki har kin kara min
son shi ina ma ace wann abu ya tabbata kusa
bikin likitoci, au kema likitance? Tace zauna nan
in gaya miki jiy-jiya Abba ya gaya mina bnd zan
karanta kenan, kuma gsky Al- ameen yayi min
matsalar kawai Abba. A'a ina cewa ya soke
maganar su Ya Ali? Eh mana to ai baki sani ba
soke maganar ita ta janyo min tsiyar. Kina zaton
su kawu baza suji haushi ba? Ance karatu zanyi
kuma wani yazo an bashi? Ai sai Umma tayi
bakin jini acikin gidan. Bansan yanda zanyi ba
shi kanshi yaban tausayi tahowata kawai nayi na
barshi kinsanni da karfin hali Baraka ta bata rai
kai yakamata a nemi mafita Al-Ameen yayi
kawata zan soki dashi don na hango kun dace
kwarai. Ta sata ta zabga tagumi ta zuba mata
ido, ina tsoron Abba Baraka bazan iya
dumfararsa da wann maganr ba bayan jiyan nan
yaja min kunne ya gaya min burinsa akaina ina
zansa raina nima inason Al-Ameen! Ta dafe
goshi ga koshi ga kwanan yunwa, Baraka tayi iya
tunaninta ta rasa mafita, sbd tsoron hanyar da
za'abi a dumfari Uban dwk don haka ta numfasa
tace to ai shikenan sai ku dauki hakuri idan
kuma yana iya dakatawa ya jiraki ko kuwa? Tace
kyaleni haushi ya isheni dauko wani topic din
kona manta da wann. Tayi yar dariya to ya skul?
Mu koma wancan fannin dame-dame suka faru?
Ta gyara zama suka tsinke da hirar makaranta
daga abinci sai sallah har zuwa bayan la'asar
lokacin da Mama ke niyyar tafiya da zarar ta
idar da sallah.Tana sallamewa yaro ya shigo wai
ana kiran Mama ta leko tace jeka kace ta tafi
Inna ta leko tace uwaki baki zuwa ko wanene?
Kai kace gata nan zuwa. Yaro ya fice inna taci
gaba da fada ba kyau wulakanci ko baki son sa
ki saurare shi ki bashi hakuri a zauan lfy, ta
shige daki Inna kenan bazaki gane ba. Ta maida
after dress dinta tasa mayafi tace Baraka zoki
rakani, donAllah ki tafi ke kadai kinsan sirrin da
zakuyi? Ta ja tsaki ta fito yana tsaye a kofar
gidan haba gimbiya, kuma saiki tafi kibarni da
tension? Ina kikeso nasa raina yau wllh ko abinci
na kasa ci sbd tunanin matsalar da kika ambato.
Tayi masa zuru tausayinsa ne zalla ke bin jinin
jinkinta tace kasan Allah nima tunani na ya kara
na rasa me zancewa Abba ganin yan'uwana ma
na jini ya dakatar dasu balle wani kuma
watakila kana bukatar auren ne da wuri kaga
Abba bazai amince ba. Ya goge zufar goshinsa
da hankici, don dai in jure ki karee sakandire zan
iya jira mana. Idan ma kinaso cigaba ne bayan
munyi aure ni zan dauki nauyin ki karanta duk
fannin da kikeso donAllah ki taimakeni kiyiwa
Abba wann bayanin. Ta dafe goshi! Wane zan
masa ya gane? Ya fada a ransa yace na dameki
ko? Yes nima nasan na fiye naci ga duk abnd
nake so. Yace mata tunda baki da abinyi ni ina
dashi abnd nake bukata daga gareki kawai ki
tabbatar min tsakaninki da Allah har cikin mind
dinki kina sona? Ki fada kanki tsaya kawai!
Mamana tana gab da fitowa zamu tafi.Tace Al-
Ameen na amince kar kaji wani shakku a ranka
amma...... Ya dan daga mata hannu don't sai it
pls! Kin faranta min rai Sakeena na tabbata zan
samu inci abinci ya wuce min. Sauran magana ki
kyale min, nace yanzu me zaki bani na rike na
alkawari? Al-Ameen fa na bata mmk na yadda
gaba daya ya sallama kansa gareta ko shiyasa
itama ya mamaye mata ko ina? Tayi dan
murmushi me zan baka kuwa? Ya nuna yatsanta
wann ring din yayi min kyau shi zaki bani, ai
bazai yi maka ba, inji wa? Miko shinan ki gani.
Ba musu ta zaro ta mika masa ya turawa
karamin yatsarsa zobe yayi zamansa daram
kamar daman can na sane.
BAKIN CIKI 1***2 Ya dubeta yana murmushi U
see? Mu biyu akayiwa zoben nan kika kama ke
kadai kika rike, tayi yar dariya "haka naji" "nima
kuwa hakan naji" amma matsalar ni bani da jar
azurfa dana baki wann kuma saidai kiyi warwaro
dashi ba dai zobe ba. Ta zubawa zoben ido yana
ta daukar ido ko in baki zoben haka? "Kawo" ai
yayi miki yawa gimbiya ayi min hakuri a biyoni
bashi in Shaa Allahu zan biya. To Allah ya baka
iko, ya kara zubo mata ido yace to ameen
gimbiyata. Ya cigaba da kallonta sannan ya
sauke numfashi wai yanzu zamu tafi gashi ban
gaji da ganinki ba. Yadda kikasan in saki a
aljihu in tafi dake. Tace ka saceni kenan? Yayi
yar dariya me karawa fuskarsa kyau da kwarjini
kamar yanda kika sace ni ba. Ji sukayi ana
tambaya ina Al-Ameen din ya nufa ne? Yace
gani Mama anan. Ta fada zaure da saurinta ta
fara dariya zoki ganta Mama donAlla! Ta kama
baki Oh ni Hafsatu Goggo fito kiga ikon Allah!
Itama yar tsohuwa ta fito ina kishiyar tawa duk
ta susuta min miji! Mama ta manne da bango ta
rufe fuska ruf da mayafi. Ta sulale kasa tun
kafin su karaso, Goggo zoki sha kallon yar bebi
ba irinki ba bude fuskar su ganki. Maman da
kanta ta bude fuskar yayin da take gaishesu. Ta
amsa cike da fara'a ah! Mashaa Allahu Al-
Ameen ka iya zabe, Allah yasa albarka Goggo
tace ameen dai. Ai ka kwantar da hankalinka nan
gida ne babu abnd zai gagara In Shaa Allahu!
Yace Allah yasa Goggo suka baro zauren Hajiar
na fadin kai fa nake jira karka shanya ni.. Gani
nan Mama, Mama tace Allah ya kiyaye ta amsa
da ameen. Ya gyara tsayuwa yace kingani? Bani
kadai nake sonki ba Sakeena sbd haka ki saurare
ni, tace ina nan ina sararonka Allah ya tabbatar
mana da alahiri, ameen gimbiyata to bari mu
lallaba tace Allah ya tsare amma zaka yi min
alkawari? Me zai hana? Fade shi indai ba zakice
in daina zuwa gunki bane , tayi yar dariya bashi
bane kayi min alkawarin zaka ci abinci idan son
samu nema mama ta dan jiraka kaci ko yaya ne,
kai Dr ne kasan matsalar rashin cin abinci ya
ware sosai yace waya gaya miki ni Dr ne? Tayi
nuni cikin gida yar'uwata dake nan gidan. Yayi
jim! Murmushi kawai yake fiddawa kafin yace its
true 4mnths back aka damka min letter of
appointment a ABUTH Zaria hope kinason Dr? ta
dube shi da gefen ido sai ya tsira mata ido
domin kallon yayi masa sosai ko shi kadai ya isa
amsar tambayarsa, in ba don son jin baki ba
bata ga ma dalilin wann tambayar ba don haka
ta juya zata shiga gida. Sakeena! Ya kirata a
sanyaye ta juyo dauke da murmushi tace a sauka
lfy Allah ya tsare ta karasa cikin gida don ta
lura idan ba hakan tayi ba bazai tafi ba kuma
ana jirransa. Gaba daya kasala ta sauko masa
ya sauke numfashi ya jima tsaye bakin zauren
sannan ya fito wajen mota inda Mamansa ke
jiransa. A hakikanin gaskiya Al-ameen ya kamu
da wata sabuwar cuta wacce shi kansa a
matsaynsa na likita bai taba cin karo da
maganinta ba. Duk iya karatnsa da yayi kuwa.
Sosai yake ji a ckn ransa idan bai auri mama ba
babu makawa zai fusknci matsala. Shi yasa
tunda ya damki hnya baya iya magana da kowa
illa addu'ar Allah yasa sakeena matarsa ce!
Hakazalika al'amarn yake wajn mama, tas!
Al'ameen ke neman rusa shirinta na son zurfn
karatu, kamar ynda tayi wa Abbanta alkawari. A
halin ynzu kam shirun da tayi bisa shimfida tun
shigowarta gidan, tunanin auren al'ameen take
yi, kuma da son samu ne kar aja lokaci mai
tsawo. Anya abbanta zai yarda kuwa? Baraka ma
taso ta kauda mata wannan tunanin, amma ta
kasa. Ta yunkura ta tashi zaune tace, "bari in
wuce baraka". Kallnta kawai take yi, ta mika
hannu ta jawo jakarta ta rataya, tayi waje.
Yaynda baraka ta dauko mayafi ta biyo ta. A
dakin inna ta sameta suna sallama, hannunta
daya rike da ledar kayan dinkin umman ta, "ki
gaida min ita da kyau, sai na zo" tace, "to zata
ji insha Allahu". Ta juya suka fito tare da baraka.
Sawun tayoyn motarsa ta tsaya tana kallo tsawn
lokaci, kafn ta dubi baraka, "al'ameen ya wuce,
ban jin zan sake ganinsa......." "wannan mugun
zato ne, me yasa kike wa kanki mugun fata?" ta
kada kai, "ba mugun fata bane, sauya ra'ayin
abba shine fargaba na, tabbas babu abnda zai
hana shi dakatar da al'ameen, tunda ya iya
dakatar da 'ya'yan 'yan uwansa na jini daya".
Tace, "ni kuwa a tawa wautar gani nake
al'ameen zai iya jiranki, tnda yana sonki". "lallai
kam wauta, baki ganin al'ameen ya girma sosai,
na tabbata a halin yanzu iyaynsa basu da wani
buri da ya wuce su ga yayi aure. Yaushe zasu
lamunci jirana shekaru barkatai masu zuwa?
Banzan tunani kike yi baraka, kawai ki yarda zan
iya rasa al'amee".! Ta fizgo hannunta suka wuce
tana fadin, "ni banji a jikina ba, kuma ai Allah
na nan, ba sai mu kai kukanmu gunsa ba" "haka
ne, dole in gayawa Allah, don gaskiya ban taba
jin wani sauyi a zuciyata ba, sai a kansa. Zaki
tayani kawata?" tayi dan murmushi tare da kamo
habar ta, "mama kenan, sai ma kin tambaya?
Matsalarki ai tawa ce. Ki sha kuruminki, insha
Allahu by nxt year zamu sha bikin likitoci, ranar
duk wani mai ciwo a fandagori zai warke" Ta
fara dariya, "au dariya na baki ko? Kinag dai
PANADOL shine tekaway dinmu, ANTI BIOTIC
kuwa su kowa zai sha a wajen dinner, to ina cuta
zata zauna?" Ta buge kafadarta tana kara
darawa, "surutunki yayi yawa baraka, ubangiji ya
cika mana burnmu" ta amsa da amin. A bakin
titi suka yi sallama akan zata ji duk yadda
al'amarin ya kaya nan gaba. Ta tsallako hanya
tana tafe zuciyarta kunshe da sake-sake kala-
kala. Wani lokacin ta kanji kamar kwalla zasu
zubo mata sbd tsabar damuwa. Ta shigo gida
yaran gidan sunyi nisa da karatun allo, kamar
kullum. Malamin su ke zuwa ya basu darasi.
Taja birki ta gaishe shi, ta wuce da sauri ta
shige gida, ta mika wa ummanta dinkunan ta.
Bata tsaya bata lokaci ba ta sungumo Kur'aninta
da sauran littattafai ta koma wajen malam ta
kwashi karatu. Sai da ta tabbatar karatun ya
kama bakinta, sannan ta koma dakinta ta ci
gaba da nazari. Hakan ya dan kauda mata
damuwar da ta tsinci kanta ciki yau. Shi yas ma
taki sassauta wa karatun, don bata son ummanta
ta fahmci wani sauyi a game da ita. Sun Sallaci
Isha'I sun ci abinci tana like gefen Abbanta
Umma ke fadin wann karon kuma ina zaki hutu?
Kanta tasye ta bata amsa wajen Ya abdulkareem
zani. Baki sake take kallonta wai! Wai! Yau
kuma aljanun can suka buga? Tayi yar dariya
umma kenan ai dama ba wai bana son zuwa
minna bane kawai Anti rabi ce matsalata kayita
aiki kamar boyinta. Ta dan harareta uhumn ke
kuma malalaciya uwar son jiki ba a haka ake
koyo ba? Ta kada kai a'a wllh naje hutu kuma
inyi ta aiki ina amfanin hutun ko Abba? Yace
kyalle Umman nan kema kike zuwa gunsu kiyi
zamanki wajen Abbanki inga me samin ke aiki.
Umma tace oho! Shi zaki goya miki baya? Ta ai
gidan wani zata aiki kam dole tayi shi ko anan
dinma. Yace ok hakane? Kinga kiyi tafiyarki Abj
wajen soja. Ta kada kai bari dai in tafi minnar
Abba, kasan shima yaya yana ta korafi wai ban
zuwa gun sa. Yace amma nasha mamaki.....
Name Abba? Son zuwa minar nan koda yake duk
yarinta ce take saki zuwa hutun nan da zarar kin
fara jami'a ajewa zakiyi, Umma tace likita ba!
Dokta Sakeena! Ta langwabe jikin Abbanta tana
dariyar dole amma cikin ranta tausayawa junan
su takeyi musamman Al-Ameen da kansa yake
rawa yana ganin matsalar me sauki ce abin ya
kara kashe mata jiki data dubi Abbanta taga
yadda muraran fuskarsa ta nuna alfahari da
kalaman Umma. Kwance bisa gadonta amma
barci yaki yuwuwa dabarar ta taje hutu minna ko
Allah yasa su kara ganawa da Al-Ameen koda
Uban Dwk ya soke bukatarsa. Shin yaya zatayi
ne? Mafita kam babu sai abnd Allah yayi. Ta
kuwa kwana gayawa Allah don ya zaba mata
abnd yafi alhairi. Ko karatu ko auren Al-Ameen
wanda zamu iya kiransa mai sa'a gwarzon da
yayi nasarar ciwo zuciyar Mama da yaki har take
tunanin dama ace burin Abban ta aure ne bason
zama likita ba. Shawara ta zauna kan jibi da
yardar Allah zata wuce minna. Sha biyun rana
daidai tana shimfide bisa gadonta tare da
muguwar kasala, shigowar Uban Dwk gida
dawowarsa kenan daga kewayen gonakinsa. Ya
daga labulen dakinta tare da fadin yaya dai yar
gidan Abba? Ta tashi zaune tana murmushi,
babu komai Abbana har ka dawo? Yace na dawo
Mamana lfy dai? Naga kamar jikinki a mace
yake. Ta amsa Allah ya taimaki mai martaba lfy
kalau Mamanka take bacci ne bai isheni ba. Ya
karasa shigowa dakin ya tsaya akanta yace ni
kuwa banason ki saba da yawan bacci Mamana
kin fa san karatun da zakiyi mai wahala ne
bayason lalaci ko kin manta ne? Ta dan rausaya
kai tana murmushi ban manta ba Abba ko
yanzun ma rashin abin yine yasa. Rashin abin
yi? To taso muje in dai abin yine ni zan baki shi
yanzun nan. Ta fara dariya meye shi Abbana?
Yace ki zagaye tsakar gidan nan sau 12, ta kame
baki wuuu! Abbba a tsakar ranar nan? Ai sai in
zube sumammiya, duk suka dauki dariya yayin
da wani matashin yaro yayi sallama sassan yace
ana sallama da Alhaji. Umma dake waje ta
karaso da sakon. Shi mutum ne me girmama
bakinsa don haka bai bata lokaci ba ya fice don
ansa sallama, wata zungureriyar marsandi ya
fara cin karo da ita a kofar gidan sannan
idanuwansa suka kai ga bakinsa maza su 2 a
tsaye wanda kallo daya zakai musu ka tabbatar
manyan mutane ne. Kai! Guda a cikinsu ma Uban
Dwk ya sanshi farin sani kuwa domin fitaccen
mutum ne a gwamnatin data shude ambassador
ne 10yrs back, watau Alh Saifullahi Sodangi
Lafai kuma marafan lafai. Take nan mamaki ya
saukarwa Uban Dwk ganin cewa babu abnd ya
taba hadasu na mu'amala. Cike da mamaki ya
bisu da sallama cikn fara'a suka yi musabaha,
sannan ya kira yaronsa Kalla yace maza ya bude
masa falon baki. Can suka rankaya da bakin
nasa, ya nuna masu kujeru yana fadin "bismilla!
Kai sannunku da zuwa!" Sun fara gaisawa kenan
kalla yayi sallama ya shigo da gorunan ruwan
(Swan) bisa tire da kofuna, ya aje gabansu. Ya
sake dibar gaisuwa ya fice ya bar falon. Uban
dawaki ya shayar da bakinsa suwan sanyi. Bayan
sun natsa Ambasada ya soma da cewa,
"watakila ka shaida ni, watakila kuma baka taba
sanina ba". Uban dawaki ya cafe, "farin sani
kuwa, mai girma marafan lafai". Suka yi 'yar
dariya, "babu shakka, to wannan kuma kanina
ne uwa daya uba daya, alh. Nuhu lafai". Uban
dawaki ya jinjina kai, "tabbas kuwa, ga kama
nan, sannunku da zuwa" Suka kara amsawa,
sannan alh. Nuhu ya zarce da bayani, "Allah mai
yadda yaso, kuma shi yake shirya al'amuransa
yadda yaga dama. Watau jiya yaron wajenmu
yazo garin nan, domin mahaifiyarsa, ya kuma ga
'yar wajenka wacce ta tabbatar masa cewa ita
'yarka ce. A hakikanin gaskiya dai yaro ya gani
yana kuma so da aure, shi yasa yana zuwa ya
sanar mana, mu kuma muka ce ai babu bata
lokaci dole mu kawo gaisuwa, tare da neman
izini. Domin a haln ynzu bamu da wani buri da
ya wuce Allah ya nuna mana aurensa, tnda ya
kammala karatu har aiki ya samu. Don a gaskiya
mun yaba da bayanin da yayi mana, yarinyar ta
fito daga babban gida. Ina fatan za'a karbi
kokon barar mu?
Go to Home
BAKIN CIKI 1***3 Uban dawaki yayi jim, shiru
yana tunanin me zaice da manyan bakinsa da
suka wanko kafa takanas takano suka zo da
babban alkhairi gidansa? Girma da kwarjinin
Marafa sun cika masu ido, har ya rika ji ckn
zuciyarsa bazai iya kabar da kokon bararsu ba.
Amma abin tambayar shine, ina burinsa na
tuntuni da ya kwallafa akan mama? Tun tana ckn
zanin goynta? Muryar ambasada yaji yana fadin,
"nasa daliln shirunka alh., Al'ameen yayi min
bayanin komai game da burinka na sakeena tayi
zurfin karatu. Wannan kuduri ne mai kyau, kuma
ni kaina ina sha'awar hakan. To amma ina son in
tunasar da kai cewar aure baya hana ilimi. Ina
roknka da ka tausayawa halin da al'ameen ya
shiga na fadawa tarkon son sakeena. Shi kadai
gareni alh, kuma daidai gwargwado soyayyar da
na nuna masa bata gurbata tarbiyyarsa ba. Yaro
ne mai ladabi da biyayya ga kowa, tare da
tsananin bin dukkan abnda muka umarce shi.
Dalilin da yasa kenan nima nake tsananin son
abnda yake so. Bana sanya wajen taimaka masa
da addu'a, a duk lokacn da ya tsinci kansa cikn
wata matsala kamar ynda na lura ya shiga wani
hali daga jiya zuwa yau da muka baro shi. Babu
sukuni a zuciyarsa, alh. Ka taimaka ka amince
wa al'ameen auren sakeena da zarar ta kammala
sakandare, karatu kuwa ko wane iri ne, ko a ina
ne sakeena zata yi shi da yardar Allah" Wannan
dogon bayani na marafa ya kwabe wa uban
dawaki guiwa, zcyrsa tayi rauni, ba zai iya ja da
nufin Allah ba. Ya gyara zama sosai yace, "ba
shakka naji duk abnda kuka fadi, kuma nayi
farin ciki kwarai da gaske, sbd haka na amsa
kiranku, duk da cewar ya kamata in shawarci
sauran 'yan uwana, amma babu komai zan yi
musu bayana idan muka zauna. Al'ameen ya ci
gaba da neman sakeena, Allah ya tabbatar mana
da alkhairi" Kawai gani yayi marafa ya daga
hannu sama yana fadin, "Alhamdu lillah!" ya
maimaita har sau uku, sannan ya dubi uban
dawaki, "bansan kalmar da zan fada ba alh......."
yayi murmushi, "ai ka fadi alh., tnda kayi godiya
ga Allah". Ya jinjina kai, "haka ne, to mun kara
godiya gareka Allah, ka nuna mana lokacin" duk
suka amsa da amin. Alh. Nuhu ya zarce da fadin,
"yanzu dame-dame ake bukata na gaisuwa da
baiko?" yace, "kar ku damu da wannan, da zarar
mun zauna da 'yan uwana zaku ji bayani insha
Allahu". "to babu laifi, muna saurare. Ina
sakeenar take? A kira min ita mu gaisa, don in
cika alkawarin da na dauko......" "alkawari?"
"kwarai kuwa, har mota ya biyoni yana fadin,
don Allah daddy in kunje ku isar da gaisuwata ga
sakeena, koda mahaifnta bai amince min
auranta ba. To kaji, dole in cika wannan
alkawari. A kira min ita inga farin cikn
al'ameen" Farin ciki ya lullube uban dawaki,
bakinsa har kunne ya mike, "Allah sarki, to tana
zuwa". Yayi ckn gida da hanzari ya sami Hajiya
Halima, "ina mama? Ashe bakin nata ne" tare da
mamaki ta tambaya, "bakinta? Kamar yaya?"
"zan miki bayani, je kice ta shiryo tsaf ta sameni
falon baki". Ya juya ya koma. Ita kuma dakin
mama ta wuce, gaban madubi ta sameta zaune
tana shafe-shafe, fitowarta kenan daga wanka.
Ta matsa gareta tace, "dama kinsan da zuwan
wasu baki gunki?" "baki?" ta kada kai, "daga ina
umma?" "ni zaki tambaya? To kiyi maza suna
falon baki inji abbanki". Ta juya ckn juyayi ta
fice. Mama kuwa kasake tayi tana tunani,
"baki?" Al'ameen ya fado mata a rai, nan da nan
farin ciki ya rufeta, ta mike da gudu ta nufi
dirowar kaynta, ta zuba ado ta rufa mayafi, ta
fito ta doshi falon baki gabanta na harbawa,
amma zuciyarta fara sol! Duk da cewar bata
tabbatar da hukuncin da abbanta ya yanke ba.
Sai dai tana da yakinin akwai alamun nasara,
tnda aka ce taje da gaishe su . Tayi sallama ckn
kunya ta shiga, ta sami wuri gefe ta tankwashe
kafa, "sannunku da zuwa". Kai bakin marafa da
kaninsa kamar gonar auduga, su kansu mama ta
girgiza su, sun tabbatar da al'ameen ya darzo,
fatan da suke yi Ubangiji yasa kyanta har ckn
zuciyarta yake. Cikin ladabi da tsananin kunya ta
gaishesu, su kuma suka amsa ckn farin ciki da
nuna kauna a zahiri. Marafa ya taso yazo
gabanta, ya tsuguna yace, "al'ameen ya zabe ki,
nima haka. Sbd haka sai ku rike juna amana.
Har Allah ya nuna mana lokacin da muke dakon
zuwansa, kin ji?". Ta kara yin kasa da kai,
sannan ta amsa da kai. Yace, "madalla, to mun
gode". Yasa hannu a aljihu ya zaro sababbin
bandir 'yan wazobia ya aje a gabnta, "wannan
kyauta ce don nuna farin cikina gare ki, sbd
zabar dana ya zama mijinki". Kunya kamar ta
nutse, da kyar ta iya fadin, "na gode. Allah ya
saka da alkhairi". Yace, "to me zan ce wa
al'ameen idan mun koma?". Ta yunkura a guje ta
bar falon, suna mata dariya. Shi kansa Uban
dawaki yana mamakin kansa, irin farn ckn da ya
tsinci kansa. Alh. Saifullahi ya mike, "to bari
muyi harama, mun gode kwarai, Allah ya
tabbatar mana da alkhairi". Suka yi musabaha,
uban dawaki na fadin, "amin". Yayi musu rakiya,
sai da yaga tashnsu sannan ya shigo gida.
"Saboda Allah mama haka kuka yi da abbanki?"
ummanta ke tambaya, ta kada kai, "wlh umma
ba laifina bane. Babu abnda ban gaya masa ba,
yaki yarda. Kinga wannan turowar ma ni bansan
da ita ba, kawai ce min yayi shi yasan ynda zai
bullowa al'amarin, don haka in sa masa ido".
Tace, "ke din ma kina sonsa ne, ai nasan halinki
sarai mama, ba don haka ba ko kallo bai isheki
ba. Kin bani mamaki wlh, watau shi yasa jiya
kika ce minna zaki hutu, ashe da manufarki....."
Abbanta ya cafe, "tabbas haka ne....." ya karaso
ciki ya zauna, yana dubanta yaynda gabanta ke
ci gaba da harbawa da sauri. "ya aka yi haka
mama na? Ki turo min babban mutum irin
marafa, bayan kisan zai yi wuya ince a'a ko?".
Hankalnta ya kara tashi, ido tam da hawaye
tace, "wlh abba ba haka bane, hasali ma ni
bansan shine mahaifnsa ba, domin ni bai gaya
min ba, ka yarda dani abba, don bani da nufin
saba maka. Duk hukuncn da ka yanke akan
wannan al'amarin bazan bijire ba". Tasa hannu
ta goge kwallan da suka zubo bisa kuncnta.
Yace, "matso nan mamana". Da rarrafe ta isa
gunsa, ya kamo kafadarta yace, "dubeni nan". Ta
dago manyan idanuwnta da suka fara jirkita ta
kalle shi, "na yarda da ke dari-bisa-dari
mamana, sai dai abnda nake hangowa watakila
ke ba zaki hango shi ba. Bayn aure mata sukan
fuskanci 'yan matsaloli musamman idan Allah
ya kawo rabo ckn gaggawa, wanda idan ba ayi
sa'a ba sai ya jawo koma baya ga komai nata,
ba ma karatu ba kadai. Amma bazan matsa ba
mamana, ya kasance nayi jayayya da shirn
Allah, don haka ina muku fatan alkhairi". Ta rufe
fuska da tafin hannunta, fuskarta na bayyanar da
murmushi. Jiknsa ta langwabe, dadi kamar ya
kasheta. Yace, "ho 'yar nema! Watau kice kina
son al'ameen ko?". Ta tashi a guje ta bar musu
dakin. Uban Dwk ya numfasa sannan ya dubi
Umma to ya kika ce? Kinga dai yanda al'amarin
ya kasance. Fuska sake tace yaya kuwa za'ayi
Alh? Tunda ka amince ai shikenan Allah yasa
hakan shine mafi alkhairi, yace Ameen. Baki ma
sani ba wai shima likita ne mun fito ina musu
rakiya shi baban nasa ke gaya min. Nace itama
abnd take son ta karanta din kenan. A hakikanin
gsky ya tabbatar min babu damuwa I.S.A zataci
gaba da karatunta, kinji inda muka tsaya dasu.
Sauran maganar gaisuwa da baiko nace su bari
mu zauna da yan'uwana. Ta numfasa gsky ne
hakan kuma yayi kyau saidai kana ganin bazasy
dora wani abu a zukatansu ba? Kasan fa su Ali
sun so ta ka hana kace karatu zatayi. Yayi dan
shiru jim, kafin yace kinyi magana amma ba
komai nina san bayanin da zanyi musu. Tace
shikenan sun dan jima suna maida zancen.
Mama kuwa tana dakinta rayuwa ta zame mata
sabuwa. Duk. Inda tajefa ido Al-Ameen din take
gani kwarjininsa murmushinsa salon maganarsa
da taushin murya mai dadi. Bayan sallar la'asar
lokaci ne da kannen Uban dwk ke dawowa daga
gonakinsu. Yaran nata daukar darasin
Muhammadiyya kamar kullum. Uban Dwk ya tara
kannensa a falonsa ya zayyane musu komai
game da abnd ya faru, nan taje ransu ya sosu ba
kadan ba kallon juna suke cikin al'ajabi suna
tambayar zukatansu. Ina karatun da akace
Mama zatayi? Ya kara gyara zama yace nasan
zakuyi wa zukatanku wann tambayoyu a game da
magana ta, sbd Aliyu da Sa'aeed dama sauran
samarin da suka yo caa akan Mama, suna neman
aurenta amma na hana, sbd dalilin zurfin
karatunta. Wannan magana wllh haka take cikin
zuciyata kuma shine buri na saidai marafan lafai
ya cika min ido kwarai da gaske, banjin kuma
zaku goyi bayan na bada masa kasa a ido ba,
alhalin da kansa yayi tattaki neman alfarmar da
bata fi karfina ba. Abnd nakeso in rokeku shine
donAllah don son Manzon Allah SAW kuyi min
uziri akan wann hukunci dana yanke karku zargi
komai sai alkhairi, ina fatan zaku bani hadin kai
dari bisa dari. Alh Basiru mahaifin su Aliyu kuma
yafi kowa yaya a gidan ya gyara zama yace Alh
ai wann al'amari na Allah ne kuma abin
alfaharinmu ne ace Mama ta sami cigaba domin
cigaba ne samun irin wann hamshakin zuriya ta
marafan lafai. Mama yar mu ce kuma muna farin
ciki tare da fatan Allah ya tabbatar da wann abu
kome kace Adamu? Alh Adamu karamin cikinsu
ubansu Sa'eed yace wann magana haka take Alh
mu munsan cewa Mama bazata auri kowa ba sai
wanda Allah yace shine mijinta sbd haka muna
murnar samun wann babban rabo daga Allah.
Cikin jin dadi Uban Dwk ke magana "godiya ta
tabbata ga Allah da yasa na sami hadin kanku
cikin sauki nayi godiya sosai, abu na gaba shine
sunyi maganar gaisuwa da baiko nace su dan
saurara min muyi shawara da yan'uwana. Me
zaku ce akai? Alh Basiru yace hakan shi ma yayi
kyau sai ta gama sakandiran ne ko kuwa yanzu
suke so? Yace a'a sai ta gama tukunna. Idan
haka ne zaifi kyau a bari ta gama din sai ayi
baiko a sa rana ko kuwa? Alh Adamu yace haka
yayi daidai. Allah ya nuna mana lokacin lfy.
Kowa ya amsa da ameen. Uban dwk ya shaida
musu kyautar kudin da Marafan yayiwa Mama na
tsabar kudi naira dubu hamsin. Aha! Gsky ta
bayyana abnd Uban Dwk yake so kenan ruwan
kudi. Haka zuciyoyinsu suka saka musu, ya
fiddo kudi ya nuna musu kafin yace saidai
maganata gsky wann kudi ko sisi bazan taba a
cikinsu ba zanci gaba da ajiyarsu cikin banki da
dukkan wata kyauta dazata zo daga baya har sai
wann abu ya tabbara iidan kuma an sami akasi
ba fata muke ba sai a mayar musu kayansu. Ko
yaya kuka gani? Sasan alh. Basiru suka tasu da
matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a
falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita
ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu
ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da
gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan
maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali
ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda
ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita
zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh.
Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama
tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi,
burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin
mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka
dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai
shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu
'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba.
Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje
zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani
za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku
wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan
dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da
su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle
kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na
alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi
yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h.
Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane
bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H.
Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda
mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana
nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin
jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an
raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki,
"mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina
wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa.
Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan
kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare
da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina
suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga
sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan"
"dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh.
Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace,
"sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa
sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma
mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to
yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido,
sannan da alama ita ma maman tana son yaron.
'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi
mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H.
Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so
shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne
bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me
kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai
daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har
sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata
ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min
habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace.
Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai
zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi
aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk
fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba.
Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar
sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu
bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h.
Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata
amsa.!
AKIN CIKI 1***4 Sasan alh. Basiru suka tasu da
matansu suka kwnce musu abnda ya wakana a
falon uban dawaki. H. Hajo matar alh. Basiru ita
ta fara tsoma baki, "amma kuwa idan baka mutu
ba zaka ga abin mamaki kala-kala. Ynzu da
gske alh. Babba ne ya iya tararku da wannan
maganar? Ko ya mance abnda yayi a kan su ali
ne?" Alh. Adamu yace, "ya manta? Babu abnda
ya manta. Hasali ma sai da ya kara maimaita
zancn su". "tafdi!" inji h. Gaje, matar alh.
Adamu. "kai dai kaga dan-uwa kawai, ai dama
tun farko na fada, ba wani karatn da ake so tayi,
burnsu mai kudi ko basarake, sbd su ganin
mama tafi kowa kyau a duniya. Shi yasa suka
dauketa a matsayn wani jari gare su. Ai
shikenan, Allah ya bamu lfya. Muma namu
'ya'yan bamu fidda ran Allah zai azurta su ba.
Ba Dai kowannensu ya kama aiki ba? To muje
zuwa wai mahaukaci ya hau kura. Harda wani
za'a tara kudi a banki, don kawai kar ya baku
wani abu ne a ciki, shine yake muku 'yan
dabaru" "ni dama bance a bani ba, me zanci da
su?" inji alh. Basiru. Alh. Adamu yace, "balle
kuma ni, ai tuni na haramtawa kaina komai na
alh, tnda ya nuna mana kiyayya a fili". Ya tashi
yayi waje, alh. Basiru yabi baynsa. Yaynda h.
Gaje ke fadin, "sai musa ido mu gani, da wane
bakin h. Halima zata gaya mana zancan". H.
Hajo tace, "kema dai da son jin baki kike. Tnda
mijnta ya furta, ai ba sai ta maimaita ba, tana
nan tasa ido muje mata murna 'yarta tayi farin
jin". Tayi 'yar shewa, "Allah mai iko, kiri-kiri an
raina mana wayau?". H. Hajo ta ja tsaki,
"mtsww! Kina mamaki kenan, dama kin daina
wlh, domin an jima ana ruwa kasa na shnyewa.
Ba girin-girin ba dai, tayi mai. Ba auran gidan
kudin ba, kwancyar hnkali!" Tana rufe baki tare
da sallamar umma, suka amsa suna wani yatsina
suna yarfarwa. Ta zauna tana fadin, "na shiga
sasanki yara suka ce kina nan" "uhm! Ina nan"
"dama maganar 'yarku ce, ban sani ba ko su alh.
Sun gaya muku halin da ake ciki?". H. Hajo tace,
"sun gaya mana, yanzu haka ma shirn zuwa
sasan naki muke, sai kuma gaki. Ashe kuma
mama an fasa karatu aure za'ayi?" Tace, "to
yaya zamu yi, mutane sun cikawa alh. ido,
sannan da alama ita ma maman tana son yaron.
'ya mace kuwa idan ta nuna tana son aure, to yi
mata auran shine mafi alkhairi ga iyaynta". H.
Gaje tace, "gaskya kuwa, gidan hutu ai dole a so
shi. Ai kinga wadancan da yake ya ku bayi ne
bata ce tana so ba". Umma ta dube ta sosai, "me
kike nufi gaje?" tace, "me kuwa? Ita gaskya ai
daya ce, sannan arziki na Allah ne. Daga ali har
sa'eed bamu fidda masu rai ba". Ta tsura mata
ido cike da mamaki, kfn tace, "na wuce kiyi min
habaici gaje, domin ni ba sa'arki bace.
Kasancewar ali da sa'eed 'yan uwa ga mama bai
zama dole wani a cknsu ya aureta ba, domin shi
aure nufi ne na Allah. Shi ke kullashi, kuma duk
fassarar da zaku yi man kun dade ba kuyi ba.
Allah yasan zcyrmu akan komai". Ta tashi ta bar
sasan. Wata uwar shewa suka kwasa hannu
bibiyu suka tafa, "tabarmar kunya....," inji h.
Gaje, "da hauka ake nade ta!" h. Hajo ta bata
amsa.! Umma na shiga sasanta ta iske baraka,
shigowarta kenan suna murnar ganin juna ita da
mama. "a'a baraka ce?" "nice umma, ina yini?"
"lfya kalau. Ya babanki da innar taki?" "duk suna
lfy. Tace a gaisheki. Wai dinkunan sunyi miki
kuwa?" "wle sunyi kyau" Mama ta cafe, "baki ga
ta cabawa abba ado ba yau tun safe?". Ta yo
mata dakuwa, "gidanku!". Ta wuce suna mata
dariya har da tafawa. Janye ta mama tayi ckn
daknta, "kamar kinsan ina nemanki kawata"
tace, "nima haka kawai naji ina son ganinki,
nacewa inna zanzo nan. Har tana min tsiya, wai
anyi hutun kenan, bama gajiya da bin hanya".
Suka yi 'yar drya, kafn mama tace, "kinsan wani
abu?" ta kada kai. "kawai dazu da rana sai ga
mahaifn al'ameen........" ta katseta ido waje,
"don Allah? Sai aka yi yaya?" tace, "uhm! In
gaya miki Abba ya amince! Kimji ynda nake ji
yau a duniya?". Ta cika da mamaki, "tafdi! Allah
ya saka masa da alkhairi" "ameen ke dai. Ni
ynzu al'ameen din nake son gani, idan yaji
wannan albishir din. Kinsan Allah, da ni duk na
hakura ina 'yar dabara inje hutu minna, idan
Abba ya hana ma rika gaisawa a can" Tace,
"amma idonki ya rufe, wa ya gaya miki a minna
yake da zama?" "nasan a zariya yake, amma
dole yaje minna, musamman idan yasan zai
ganni a can". "ke mama......" "meye?" "meye
kuwa? Allah dai ya nuna mana lokacn lfya". "to
ynzu zaki je hutun ko kin fasa?" "Gobe insha
Allahu zan tafi, amma dole in dan saurara in ga
ko zaizo goben" Tace, "kema kinsan dole gobe ya
dauko hanya, wannan babban albishir ina zai
tsoma ransa, idan bai zo ya ganki ba?". Suka
tafa suna 'yar driya. Har gab da magariba suna
tare, sannan mama tayi mata rakiya ta koma
gida. Inna saude kanta tayi farin cikin jin
wannan labari.! Duk da cewar maganganun su
Haj Gaji sun bala'in batawa Umma rai sam bata
gayawa Uban dwk ba gudun tashin hsnkali da
sabani, hakan yasa bata kwana da zancen cikin
ranta ba taci gaba da sabgoginta kamar ba abnd
ya farau. Mama kuwa ta kintsa kayanta a jaka
tare da sakonnin Umma wanda zata tafi dasu
don yin tsaraba, Abba da kansa yake gaya mata
kar tayi gaggawar tafiya watakila Al-Ameen
yazo kada suyi sabani, ya wuce gona da kazzin
idan har ya dawo daga goba bai zo ba shi zai
kaita, ba karamin dadi Mama taji ba sbd a zahiri
Abbanta yana nuna jin dadinsa da sauyin da
Allah ya kawo musu a lokaci guda. Mama ta
caba kwalliyar mamaki irin wacce take gigita
samarin gidansu duk sanda sukai tozali da ita
duk da cewar basanan Ali yana aiki da karamar
hukumar birnin gwari shi kuwa Sa'eed dan-
sandan-bada-hannu ne a Kd. Shi Sa'eed
Mamansa ce ta dauki abin da zafi tuni ya gane
ta wuce ajinsa ya fara neman wata anan Kd. Can
sassan ta shiga don gaishesu tare da shaida
musu zata tafi hutu kamar yanda ta saba idan
zata tafin. Tana shiga danlami ta samu yana
wankin kayansa ya zura mata ido harta iso
gunsa tana murmushi duk da cewar shi tasa
fuskar a daure take "wanki kakeyi?" "Uhmmn.....
Kuma a zaune don lalaci yaushe zai fita.. Yace
ni banson iyayinki.. Tace iyayi?? Wai naga sai
wani cin magani kakeyi baka koshi bane halan?
Ya dubeta sosai Yace Eh yunwa nakeji.. Saiki
kawo min abinci matar masu kudi! Baki sake
take kallonsa "matar masu kudi? Ban gane
nuffinka ba? Yace jeki abnd ya kawoki karki
hanani aiki na.. Ta gyara tsayuwa tace
maganarka tana da manufa danlami me kake
nufi da matar masu kudi? Sai taji magana daga
bakin Haj Gaje ai ba karya bane yaga kinyi kalar
matar masu kudi ne shiyasa ya fadi haka ai
kinga masu kudin suna zuwa aure ya tabbata!
Gaba daya ta daburce ta rasa ina wann magana
ta dosa ba shiyasa tayi tsaye tana kallon Haj
Gaje. Tace ki daina kallona idan baki gane ba ki
tambayi mai hankali yayi miki bayani. Ta wuce
abin ta cikin daki. Take nan ran Mama ya baci.
Ta juya cikin sauri ta bar sassan, kicibis sukayi
da Salisu ya dubeta da kyau yace ashe dama duk
abun yaudara ce koda yake dama kin gaya min
su Ya Ali basa gabanki, ta kalleshi tace kwarai
haka ne ko akwa me yi min dole? Sannan yin
kwadayi ma ai dace ne wani idan zai like yayi
kwadayin ma bai samu mtsewww... Taja dogon
tsaki tabar gurin yayin da Haj Hajjo ta tsaya
gabansa amma kai sakarai ne tsayawa kayi tana
gaya maka magana son ranta? Kai tsaranta ne?
Sakarai kawai. Itama taja tsakin ta wuce shi.
Haushi kamar ya hadiyi zuciya cikin sauri ya
fice kofar gida. Gaban Ummanta ta zube idanuwa
cike da kwalla tace Umma meke faruwa ne cikin
gidan nan ake yada habaici? Tace shine zakiwa
kuka? To ina ruwanki da abnd ke faruwa? Tunda
ba matsalar mu bace. Umma kinsan ban son
abin haushi idan su salisu sukaci gaba da yi min
habaici wllh zan basu mmk gara ki gayawa Abba
yayiwa tufkar hanci tun kafin gidan nan ya
yamutse. Ta zura mata ido kinga babu abnd ya
shafeki da surutunsu domin ba shi zai hana abnd
Allah ya shirya ba, biye masu zakiyi duk ku
haukace gaba daya? Ina so ki dauke kanki daga
gare su tamkar yadda nayi. Ta goge kwalla tace
kema sunyi miki ne? Tace tun jiya iyayensu suka
fara amma bai dameni ba don nasan wann abu
bani na shkirya shi ba ba kuma Abban ki bane
balle ke. Shiyasa ko shi Alhajin ban gayawa ba
sbd bana son hayaniya kin gane? Ta dan yi jim
sannan ta amsa da ka tana goge kwalla. Tashi ki
je ki wanke fuskarki. Ta mike zata wuce yaro
yayi sallama yace wai ance Sakeena tazo Al-
Ameen yazo. Gabanta ya yanke ya fadi ta zurawa
yaron ido ta rasa me zatace? Umman ce ta bashi
amsa to kace tana zuwa. Ya juya ya fita, kin
tsaya ki kam kije ki shiryo mana. Ta shige
dakinta sanyi na kwarar zuciyarta. Ta tsaya
gaban mudubi ta gyara fuskarta ta suro gyalenta
ta yafa tayo waje. Umma na tsakar gida ta mika
mata makulli tace ki kaishi falo karku tsaya a
waje. Fuska sake ta amsa ranta ya kara sol. Tayi
kofar gida cikin sauri amma cikin sanda ta leko
yana tsaye jingine da motarsa ya zurawa zauren
ido shiyasa tayi arba da idanuwansa masu haske
da girma. Sbd haka kunya ta lullubeta ta koma
zauren ta lafe tana maida numfashi kawai
muryarsa taji bisa kanta yana fadin sallama
gareki ma'abociyar kyau! Jim tayi shiru kamar
ruwa ya cita hannunta daya rufe da fuskarta
haka shima ya tsaya ya zura mata ido dauke da
murmushi mai isar da sako barkatai. A nutse ta
bude fuskarta ta dubeshi "sannu da zuwa"
taushin muryarta yasa jinin jikinsa ya tsinke yaji
son Mama ya kara malale kowane lungu cikin
zuciyarsa tamkar ya hadiyeta yakeji kai bai
tabajin azababben so irin wanda ya kama hsi ba,
ya numfasa yace gimbiya ta kenan. An fito lfy?
Tace kalau ya hanya? Yasu Baba sukaje gida?
Ya amsa duka lfy lau, tace mungide Allah. Yanzu
ka ban minti daya zan bude maka inda zaka
zauna, yace ni kadai? Gsky ban yarda ba! Tayi
dan murmushi to inda zamu zauna. Yauwa yanzu
naji batu gara da kika gyara. Ta wuce tana 'yar
drya. Shi kuma yayi wawan ajiyar zcya, ya dawo
jkn motrsa ya harde. Jimawa kadan ta budo
babban kofar get da ke can wani bangare na
katangar gidan, ta fito tace dashi, "bismillah!".
Bai yarda ta tsere masa ba, jerawa suka yi suna
tafe yana fadin, "ga Amarya ga Ango!". Ta ballo
masa harara, fuskarta kunshe da kyakkawan
murmushi, har suka shige falon. Ta nuna masa
kujera ya zauna, ita ma ta koma gefen damarsa
ta zauna, suka sake gaisawa. Yace, "to Alhamdu
lillah, godiya ta tabbata ga Allah wnda ya nufi
al'ameen ya zama angon sakeena. Ko kinsan
cewa jiya banyi barcin kirki ba?". Ta kada kai,
"me yasa?" "ban taba zaton abba zai saurari
kukana ba, shi yasa na kasance tamkar maraya,
ni kadai cikn daki, bana aikn komai sai na
addu'a, idanuwan nan sun fidda hawaye gaban
Ubangiji don neman biyan bukata. Beliete me ma
jinina ya hau kfn dady ya dawo......." ta katse
shi, "amma da ya dawo fa?" yace, "albishir din
da ya dawo min dashi ya hana min barci sbd
tsabar murna da farin ciki, cnt explain sakeena"
tace, "ka mamayi abba, kuma ni kaina nayi
mamakin amincewarsa, koda yake abba mai
saukn kai ne, kuma bai cika jayayya ckn
al'amarn rayuwa ba" "na yarda da ke. allah ya
sakawa abba da alkhairi, domin ya ceci
rayuwata. Ko har da taki?" Ta dube shi suka
hada ido, ta dan kauda kai. Tayi 'yar drya. Yace,
"ban damu ba, tnda ni nayi nasara". Tace, "ni
kuma bazan yarda da kai ba, sai naga alkawari
na". Ya zuro mata ido, "a tunaninki zan manta
ne? No sakeena, kece komai nawa, bazan taba
mantawa da wani abu wnda ke alaka da ke ba,
balle kuma ace alkawari ne......," Ya tura hannu
aljihu ya dauko wani dan karamin mazubi ya
bude, ya nuno mata wani gangariyan zoben
zinari yace, "ina jin wannan shine alkawarin ko?"
Baknta yaki rufuwa, ya matso gabnta ya
tsugunna ya miko mata, tasa hannu ta dauka ta
zurawa yatsanta. Wayyo! Al'ameen zuru kawai
yayi yana kalln zara-zaran yatsnta, zoben nan
ya zauna kamar da shi aka halicce ta. "tsarki ya
tabbata ga Ubangijn da ya halicce ki sakeena".
Ya dago ido ya dubeta, "kiyi min alkawari har
abada ba zaki daina sona ba". Tace, "insha
Allahu zaka sameni mai cika alkawari komai
wuya, komai tsanani zan jure akan alkawarinka.
Har abada kai kadai ne, ba wani sai kai"
Idanuwnsa suka kawo kwalla, murya sanyaye
yace, "na gode sakeena" tace, "kar ka damu". Ya
mika mata gidan zoben ta karba. Ya koma
mazauninsa ya zauna, abba ya gaya wa dadyna
kema irin karatu zaki yi, kinga ta kwana gidan
sauki, wai matar likita ta haifi panadol" Ta fara
drya, "oh, drya na baki ko? To shikenan, ai ba ke
matar likitan zaki haifi panadol din ba........"
tace, "au son kai ne abin?" "eh mana. Nawa
bouncing baby ne, baby boy ko girl? Zabar min".
Ta mako masa harara, ya hau drya. "well, daga
nan idan na tashi zariya zan wuce, sai kuma nxt
week zan dawo in sake ganin gimbiyata" tace,
"Allah ya kaimu lfya, nima anjiman zan wuce
minna wajn yayana zanyi hutu" Ya bude ido,
"owk, kuma shine tnda nazo baki gaya min ba, ai
sai in juya in kaiki, daga can in wuce". Ta kada
kai, "bana son ka wahala, ka wuce wurin aiki
abinka. Babu komai". Yace, "uhm...... To na
gode, amma ina fatan akwai phon number a can,
kin ga sai mu rika gaisawa ko?" tace, "eh akwai
land-line zan baka" Yayi ajiyar zuciya, sannan
yace, "yanzu ki bani labari, ku nawa ne a
daknku?" tace, "mu hudu, yaya abdul-kadeer
soja, shine babba, sai yaya abdul-kareem yana
CBN Minna, shine zani hutu gunsa, then yaya
Abdul-rahman yana kadna, lst year ya fara aiki
da ma'aikatar kimiyya da fasaha ta jiha, shi
kadai ne bai yi aure ba......" "sai kuma ke ko?".
Tayi 'yar dryar nan da yake so. Yace, "kun
burgeni, Abdul 3, ni kuwa tilo ne ckn gdnmu,
bani da yaya balle kani. Kadaicn yayi min yawa
sakeena". Tace, "kamar ynda gata yayi maka
yawa ba" "haka kike gani? No ba zaki gane ba,
naso ace akwai wasu, musamman kanne, na rika
yi musu 'yan mazurai ina cewa, kai ku bari
mana! You knw, smthn like that dai. Amma ka
zauna shiru babu mai maka fada, babu wnda
zaka yi wa? Babu dadi abin". Ckn tausayi tace,
"ai shirin na Allah ne" yace, "yes haka ne, na
yarda. Amma very soon zan samu many babies,
su zagayeni, dady kalla! Dady bani wannan!
Dady sa min riga! Kin gane? Ina son hayaniyar
yara sosai" Tana drya tace, "kana da aiki" "come
on, muna da aiki dai. Ai mu biyu ne muna
tsakhya, sun zagaye mu, na 6 can 6. Wuu!
Confusion! Wa zai gane min ke?" Hannunta
tallafe da kunci, ta zuba masa ido tana kallnsa
yana ta zuba bayani, idanuwanta suna nuna mata
yaran zagaye da shi. Shi yasa yana sa aya ta
fashe da drya. Yace, "drya ma na baki ko?
Yarnya gudu zanyi in kyaleki dasu" Ta dan tabe
baki, ta tashi tsam! Zata bar falon, yace "ina za
ki? Har kinji tsoro ne?" tace, "tsorn me? Ruwa
zan kawo maka, kaji dadin santin". Sosai yayi
drya, har ta bar falon. Ya koma a hnkali ya
jingina bayansa da kujera, ya rufe ido tamkar
mai barci. Wani kasaitaccen taro yake hangowa,
wnda cikarsa baya misaltuwa. Jimawa kadan ya
keto taron rike da hannun sakeenarsa, da ka
dube su kaga amarya da ango. Jama'a na musu
tafi, su kuwa baki yaki rufuwa. Bisa wasu
kasaitattun kujeru suka zauna, ta tsiyaya lemu a
kofi ta mika masa a baki, ya dauka zai fara
sha...... "Assalamu alaikum!". Ya bude ido a
hnkali, tana tsugunne gabansa rike da kofin
ruwa. "barci kayi? Lallai na dade da yawa, ayi
min afuwa". Ya saki wani wawan numfashi, ya
girgiza kai, "dogon tunani ne ya dauke ni. A
duniya bani da wani burin da ya wuce aurenki
sakeena.....". Yayi dan shiru jim! Yana kallnta,
ya kada kai, sannan ya karbi kofin hannunta, "na
gode". Ya shanye ruwan, ta zuba masa lemu, ta
koma ta zauna, ilahirin jiknta ya mutu. Wane irn
so al'ameen ke mata? Ta tambayi kanta. Tana
ganin ita ma irnsa take yi masa, domin itama
burinta ta zama mata a gareshi. Ko don ita
kunya na maida ita kurma, shi yasa yake ganin
shi kadai ke da buri a kanta? Zurun da tayi masa
a rashn sani, shi ya jawo hnkalnsa ya daina
kurbar lemun. Ya matso gabnta yasa mata kofn a
baknta, ta sha kadan ta dube shi, "ba kai kadai
ke da buri ba Dr., sanin kanka ne mu duka muna
da bukatar kasncewa tare. Idan baka sani, ynzu
na gaya maka ka sani, don ka daina damuwa".
Ya numfasa yace, "Allah ya tabbatar mana da
wannan buri" tace, "amin". A natse suka zauna
suka ci gaba da faranta wa junansu rai da
dad'ad'an kalamai. A nan yayi sallar azahar, ya
ci abnci, sannan yayi shirn wucewa zrya. Ita ta
jagorance shi ya shiga ya gaida umma, don ya
matsa kwarai yana son kai mata gaisuwa. Ta
kuwa ji dadi, ta kuma yaba da tarbiyyar sa,
yanaynsa da alkunyar sa.! Suna tsaye jikin
motarsa sallama taki karewa Ya Ali ya danno
kofar gidan da jakarsa akafada, bakinta har
kunne ta tarbeshi Ya Ali! Sannu da zuwa, ya
kalleta ya kalli wanda take tsaye dashi kafin ya
amsa. Ya mikawa bako hannu tare da sallama
(Allah Sarki ubana akwai jarumta!). Ita kuma
tana fadin Ya Aliyu kenan cosin dina ne, Allah
sarki inji Al-Ameen an dawo lfy? Yace lfy lau!
To madalla. Aliyu yace dauke da matsanancin
kishi da mamaki a ransa. Al-Ameen kuwa fadi
yake kuna satar kama da juna da an ganshi an
ga dan'uwanki, tace ko? To ai da Baban shi da
Abba duk dakinsu daya. A Birnin gwari yake aiki.
That's gud' ina ganin ya kamata in lallaba in
barki ku wuce ko? Kar dare yayi. Tace hakane,
kai din ma bana son dare yayi maka. To
shikenan karfe tara ISA zakiji wayata. Allah ya
yarda a sauka lfy. Ameen. Ya shiga mota ta rufe
masa tana kara fadin kayi tuki a hankali, yace
thank U. Ta juya zata wuce yayai kiranta
Skaeena! Ta juyo tare da murmushi yace "I love
you!" Ta kara fadada murmushinta ta rausaya kai
ta juya zata wuce Sakeena! Ta sake juyowa. I
love u! Tayi jim kafin tace I love U too! Ta ruga
cikin gida ya rakata da kallo bakinsa kamar
gonar auduga kasala ta rufe ya kasa tada motar.
Ta sake lekowa tayi masa bye-bye shima ya
daga mata hannu sannan ya sami karfin tada
motar yayi ribas yai kwana ya fada hanya ya
kara dago mata hannu ya wuce cike da begenta
tamkar yadda takeji a ranta. Tana shiga cikin
gida muryar Ya Ali kawai ke tashi yana
bambamin fada "ai dama haka rayuwa take
kiri'kiri jininka saiya wulakantaka don baka da
kudi! Muma muna kan hanya indai arzikine
abuna Allah! (Kana da gsky Baffaba!) Mama tayi
tsaye jikin kofar sassansu tana saurare haj Hajjo
tace nace dai kayi shiru haka ko? To kaci gaba
idan hakan shi zai sa a baka ita. Mama dai ba
saurana mata tafi ba ga yanmata nan bila adadin
duk wacce ka zaba sonka zatayi idan ita ma ba
kwadayi tasa wa ranta ba. Sbd haka kar in sake
jin wata magana ta fito daga bakinka akan wata
Mama! BARKA DA SALLAH
HAUSA Novels BOOK
BAKIN CIKI 1****5 H. Gaje ta cafe, "ki kyale shi
ya amayar da bacin ransa, kar ya zame masa
ciwo! Da wanne zai ji?" yace, "ai inna ba zata
gane ba mama gaje, wannan rainin arziki ne a
ckn gida. Uwa daya uba daya? Haba! Ya kamata
a duba!". H. Hajo tace, "wa zai duba? Lallai
ranka zai fita idan har zaka kwallafa wa kanka
wannan maganar!" Tana sa aya daidai da
sallamar uban dawaki, yayi tsaye yana kalln
mama na zubda kwalla, yaynda yaji muryar h.
Gaje na fadin, "babu wnda zai duba wannan
al'amari, tnda dai shi da kansa alh. Babban ya
ya yamutsa al'amarin!". Kalaman da suka fada
kunnuwan uban dawaki tare da bugun zcy, ya
zurawa mama ido tamkar ynda take kallnsa, "me
ke faruwa?". Bai gama rufe baki ba yaga Ali ya
fito a fusace, idanuwnsa na tsatso kwalla. Shi
kansa gabnsa yayi mugun faduwa, kasala ta
kama shi, ya rage sauri, "kai ali lfy?". Ya gnge
fuska, ya dan rankwafa yace, "sannu abba!"
"nace me ya faru?" "babu komai" "ina wasa da
kai ne? Kake gaya min babu komai!". Mama
tace, "abba tun jiya gidan nan a yamutse yake,
ana ta habaici tare da yada magana akan zancen
al'ameen. Umma taki gaya maka ne sbd gudun
fitina. Amma kowa gani yake yi sbd kudi ne yasa
ka amince inyi aure, bayn ka hana kowa kace
karatu zanyi. Me yasa za'ayi mana mugun
zato?" Nan da nan ransa ya baci, yayi fushi
sosai, ya kwalawa umma kira. Ta fito ta samesu
ransa bace. Ckn fushi yace, "kira min matan
gidan nan!" "lfya alh?" yace, "ban son jin wata
magana". Tace, "alh ka kwntar da hnkalnka kayi
hakuri har zuwa lokcn da mazajnsu zasu dawo.
Zai fi kyau duk abnda zaka fadi ka fada a
gabnsu. Ina rokn wannan alfarmar don girmn
Allah!". Alh. yayi jim! Shiru yana kalln umma,
kafn ya dubi mama yace, "kin shirya kayanki?"
tace, "eh" "to kwaso ki zuba a mota maza mu
tafi". Ya wuce da sauri daknsa, kowa ya kama
gabnsa, har da ali ba tare da wani ya kara cewa
komai ba. Kayn jiknsa kawai uban dawaki ya
canza, yayi rawani kamar ynda ya saba, ya fito
lokacn mama na tsakar gida da jakar kaynta tare
da tsarabar da umma ta bayar a kaiwa yara.
"Baki kai kayan motar ba?" inji abba. Tace, "ai
basu da yawa, su kenan" "wuce muje". Umma
tace, "Allah ya tsare, a sauka lfya". Ya amsa da
amin, yayi waje. Mama ta biyo baynsa. Ali na
zaune bisa dakali tmkar yayi bindiga sbd tsabar
fushi da kishi, domin sosai yake son mama.
Kuma yayi wa ransa alkawari zai ci gaba da
farautarta, sai yaga abnda ya turewa buzu nad'i.
Shi yasa ya aje wa ransa zai iya jiran ta gama
karatnta. Shi kuma zai ci gaba da gina kansa da
duk wani tanadi wnda zaizo daidai da jin dadin
rayuwr aurnsu. Ina zai sa ransa yau yaji dadi?
Yana ganin mama ta shige mota idanuwnsa suka
yo tam! da hawaye. Musamman wannan zuwan
ita yazo gani, sanin cewa sunyi hutu. Kamar ya
kwarma ihu. Ya mike ya sake fadawa ckn gida.
Alh. Ya bude mota, kalla ya matso, "ranka ya
dade tfya za kuyi?" yace, "ai tare zamu tafi da
kai, taso ka shiga mota. Minna zan kai mama
na" yace, "to shi kenan". Ya mika masa makulli,
"ka tuka motar kalla, bana jin dadin jiki na". Ya
amsa yana fadin, "assha! Allah ya sauwake"
"amin". Ya bude gidan baya inda mama take,
shima ya shiga. Jikn mama ya kara sanyi, tasan
abbanta ya kanso suyi tfya su 2 kacal! Suna tafe
yana bata labarin duniya. Ta tabbata bacin rai ne
yasa ya gayyato kalla ya tuka su, gudun afkuwar
wani abu. Sun mika tfya shi babu mai magana,
shirun sam baya mata dadi, sbd haka tace,
"Abbana kayi hakuri don girman Allah, kar
hnkalnka ya tashi akan wannan maganar". Ya
dubeta sosai yace, "dole raina ya baci, sbd an
zarge ni akan abnda ba shine a ckn zcyata ba.
'Yan uwana basu yi min adalci ba, na tabbatar
da saninsu mataynsu ke yada habaici da
kananan maganganu. Amma zanyi wa tufkar
hanci. Tnda babu wnda ya haifa min ke". "kara
kayi fada dasu abba....." yace, "ya za'ayi in
tsaya ina fada da kannina? Umarni kawai zan
bayar, kuma dole kowa yabi idan ana son zaman
lfya. A iya sanina na basu hakknsu, na zauna da
su na gaya musu uzuri na. Amma duk da haka
basu gane cewar komai na Allah bane. Ke dai
abnda nake soki dashi, ki rike yarn nan amana,
sannan ki kara kula da kanki, don tsare
martabar gidan nan" tace, "Allah ya taimaki mai
martaba. Mamanka na tare da albarkar umma da
abbanta, da yardar Allah ba zata basu kunya ba".
Yayi dan murmushi yace, "Allah ya kara yi miki
albarka". Tare da kalla suka amsa, "Amin abba
Sun iso minna la'asar sakaliya, shi yasa ruwan
alwala kawai alh. Ya fara tambaya. Yayi sallah a
babban falon gidan, yaynda jerin kayan abincnsa
ke jiransa. 'yan jikoknsa kuwa sai safa da
marwa suke yi. Ya idar da sallar, suna jiran su
tumurmushe shi. Ilai kuwa yana idarwa suka
zube a jiknsa, yana drya ya soma tsokanarsu"
"ameera tsohuwa mai majina" tace, "Allah ameer
ne mai majina" ameer yace, "karya ne abba,
kullum wa ake ba tishu in zamu skul?". Abba
yace, "kyaleta Uwair, waye bai san halima
tsohuwa bace? Mai majina kawai". Ai nan da nan
tayi fushi ta tashi fuu.... Zata fice,suna mata
drya. Sai ga sallamar anti Rabi. "momy kin
gansu ko? Wai nice mai majina". Ita ma dryar
tayi ta wuce ta zube gabn abba ta kwashi
gaisuwa, sannan ta tambayi mutan gida. Yace,
"duk lfyrsu kalau" Kuka ameera ke yi, yaynda
mama ta shigo da ita falon, "ynzu don Allah wa
ya taba min umma na?" yace, "kyale ta mai
majina ce, ni bana auranta!". Ta kara kware
baki, mama ta rungume ta, "kiyi shiru ki kyale
shi, ke ma baki auran. Me zaki yi da shi tsoho?"
ameer sai drya yake mata. Da yaga kukan da
gaske take ynsa sai ya jawota jiknsa, "wanene
ya taba min madam dita? Manta da ameer, tsoho
ne shima. Ina dady bai dawo bane?" ta amsa da
kai tana murzar ido. Anti rabi tace, "bai shigo
gida ba tukuna, amma yana bisa hnya". Yace,
"To Allah ya dawo dashi lfya" suka ce amin..anti
rabi da mama suka bashi wuri yaci abinci tare da
jikoknsa. Yan minticoci bayan kammalawarsa
motar Ya Abdulkareem tayi fakin a harabar
gidan, ganin motar Abbansu yasa ya fito da
sauri kalla ya tarbe shi ya karbi jakarsa yayi
masa sannu da zuwa suka gaisa, tare suka shigo
falon ya zube gaban Alh yana fadin oyoyo
abbanmu! Yace Abdulkareem dan Abba sadauki!
Ya kara fadada dariyarsa domin yana jin dadin
kirarin da Abba yake masa tun yana yaro sbd
tsananin kokarinsa wajen neman duk abnd yake
so musamman ilimi. A yaran gidan kaf! Babu
wanda ya fara sauke Qur'ani da karancin
shekaru sai shi, yana 14yrs yayi sauka kuma
yasan littattafai dayawa. Daka dubeshi kaga
Mama illa dara daran idanuwanta ne kadai suka
banbantasu. Kazo lfy Abba? Yasu Umma? Yace
lfy lau Mamana na kawo maka hutu.....Mama?
Yanzu haka tana ciki? Sai gata ta shigo falon ta
karaso gunsa da gudu ta zube jikinsa Yayana!.
Ya kamo kunnenta ba wani yayankitashi zakiyi ki
koma inda kika fito! Tace Allah sarki yayana dan
Abba sadauki! Ya dada mata duka suna ta dariya
"maras kunya ba Abj kika fiso ba? Ai dama nace
duk randa kikazo yan kafafuwan zan karya..
Tace, "tuba nake yayana, daga yau duk hutu
anan zan yi shi" yace, "naji amma ban yarda ba,
ke da soja ai sai Allah, watakila kema sojan zaki
aura". Ta kada kai ckn shagwaba, "a'a!" Abba
yace, "ai baka ma sani ba? To karkade kunnenka
kasha labari". "ko abba? To bani insha". Abba na
bashi labari, ita kuma mama na boye a bayn
yayn nata. Tas! Ya zayyane masa abnda ke
faruwa. Abdul-kareem ya cika da mamaki, "to
menene abn tashn hnkali a nan?" yace, "nima shi
na gani, har ga Allah zcya ta bata da wani nufi
akan wannan al'amari, amma tnda haka suka
dauko zamu tafi a hakan, kuma mama zata auri
wnda take so". Ya dan kada kai yace, "kayi
hakuri abba, kasan shi mutm a kullm yakan fi
son kansa maimakn neman zabn Allah. Abu
kankani sai a ruruta shi yayi girman da zai
rarraba kan zumunci. Abba ka dauki girma
kamar ynda ka saba, ka dauke kai ga
tsegunguman mata". Ya zura masa ido yana
murmushi, "dan abba sadauki! Duk abnda ka fadi
gskiya ne, shi yasa ma bazan gaya wa yaynku
ba, don nasan halnsa, daga ali har mutn gidan
babu wnda zai kyale idan hauknsa ta tashi".
Yace, "haka ne, kuma nasan ali yana son mama,
dole yaji zafi a rnsa, amma su a matsaynsu na
manya ai bai kamata su rika tnzira shi ba.
Abnda ya dace shine su nuna masa komai na
Allah ne. Amma muna musu fatan Allah ya
ganas da su. Ke kuma mama ki rike amana,
domin duk garin nan babu wnda bai san familn
marafan lafai ba. Babban gida ne masu mutnci.
So u hv 2 b very carefl, ke ma ki nuna wa duniya
kin fito daga babban gida mai cike da tarbiyya,
OK?" Tace, "insha Allahu yaya zanyi iya kokari
na". Yace, "to da kyau likita matar likita. Abba
kasan wani abu? Ai mu juma munyi bye-bye da
rashn lfya". Suna ta drya, anti rabi ta shigo
itama. Sun jima suna hira, sannan uban dawaki
ya bar garin minna tare da yarnsa kalla.! Anyi
sallar magriba lokacn da suka shigo Fandogari,
don haka a guje uban dawaki ya nemi bada
farali. Bai wani ci abnci sosai ba, sbd abncn da
ya ci da yammacin dazu a minna. Umma ya aika
ta tattaro masa kaf kannensa da 'ya'yan gidan
tare da ali. Duk suka hallara a falnsa, ya dubesu
ya fara magana ckn rashn jin dadi, "abnda yasa
nace a kira min ku, a gskya abnda ya biyo baya
sakamakn maganar da muka yi da ku jiya, sam
banji dadnsa ba. Basiru da amamu kar ku manta
gaba daynmu ciki daya muka fito, babu bare.
Kar ku bari tsegunguman mata su raba kawunan
mu, domin da halima da hajo da gaje tare suka
same mu. Bai kamata in gaya muku uzuri na ba,
ku kuma ku koma kuna min yankn baya wajn
mataynku, har su sami damar yada maganganu
marasa dadi akai ba. Ko ban haifi daya daga
cknku ba, ina zatn ni uba ne a gareku, kuma
daidai gwargwado ban shiga hakkn kowa ba. Ali
da sa'eed a wancn lokaci sun yunkuro,
kowannensu yana son auren mama, a gabnku
yaran nan suka rika rigima a junansu, gaba ta
kullu, babu mai kalln dan uwnsa. Sbd Allah idan
ban ynke wancan hukunci ba me ya kamata inyi?
Shi za'a tsaga mama gida 2 ne, ali ya auri rabi
sa'eed ya auri rabi? A gani na idn aka hana
kowa zai fi mana alkhairi. Ko da bani da ra'ayn
mama tayi zurfn karatu, ballantana ina da shi.
Wlh bani da wani buri akan mama da ya wuce
tayi zurfn karatu ta zama likita gabana. Amma
da Allah ya sauya al'amarinsa, ba zan iya
jayayya ba. Sai dai a cknku laf din nan na bar
muku zabi, idn akwai mai iya yin wani abu bayn
wnda Allah ya zartar bismilla, ina saurarnsa. Ni
kam na yarda nayi gmanin al'ameen Allah ne ya
turo shi, ban isa in koreshi ba. Kuna iya kirana
kuda sbd kwadayi, ba zai sauya komai a jikina
ba, don nasan har ga Allah bana bukatar sisin
kwabo daga al'ameen ko mahaifnsa. Na kare
maganata, idan akwai mai abin cewa yana da
damar fadi". Gaba daya ka rasa mai yin koda
motsi, sbd dogn jawabn uban dawaki ya tattaro
musu kunya ckn idanuwnsu, musamman matan.
Jin sunyi shiru, uban dawaki ya kara da cewa,
"idan babu mai magana kuna iya tfya, shikenan
magana ta kare" Har matan sun mike, alh.
Basiru yace, "ku zauna. A gskya munyi kuskure,
amma ynzu mun gane bamu kyauta ba ko kadan.
Kayi hakuri alh. Da yardar Allah wata magana ba
zata sake bullowa akan mama ba. Ku kuma hajo
da gaje ku ba alh. hakuri, har ma da h. Halima"
Da ganin fuskoknsu kowacce ba akan son ranta
take magana ba. Sun dai bada hakurin, kuma
abba da umma sun yafe, sun maida komai ba
komai ba, a matsaynsu na manyan gida, sun
nada gammo sun dauki girman kamar ynda
hausawa ke fadin Babba juji ne. Aik. Adamu ma
yayi nasa dan guntun jawabin na neman afuwa.
Kowa ya tashi aka bar Ali a zaune, ba tare da
yace wani abu ba. Abba ya dube shi yace, "akwai
magana ne ali?" ya karkada kansa da ke
sunkuye, sai hawaye shar-shar! Suka hau zuba.
Uban dawaki ya sauke numfashi, gaba daya
jiknsa ya mutu. Harga Allah bai taba tunanin
soyayyar mama tayi zurfi ckn zcyar ali haka ba,
wa ke ganin hawayn ali? Da yarntarsa ma ba
karamar azaba ke sanyashi kuka ba, shi yasa
yaci sunansa Gadanga! Domin kaf tsaransa babu
mai nuna masa yatsa. "zo nan ali!" yayi kirnsa
yana nuna masa waje bisa kujera kusa da shi,
"zauna kaji". Ya zauna yana goge kwalla. "abnda
nake sonka dashi ali kayi wa girman Allah ka
dauki imani ckn ranka. Wlh a zatona tuni kun
share maganar mama a zuktnku, ganin na jima
da soke maganar. Amma kayi hakuri, ka dauki
dangana kasa wa ranka, duk abnda Allah ya
hukunta daidai ne" Ya dan gnge kwalla ya dube
shi, "abba sa'eed ne ya hakura, amma ni burina
inyi ta jiran mama har zuwa lokacn da zata
gama karatnta. Kullum addu'a nake yi Allah yasa
a tsayn shekarun nan zcyr mama ta aminta da
ni". Ya numfasa ya kada kai, sannan ya ci gaba,
"bansan yanda zanyi ba abba". Abba ya rungumo
kafadarsa, "hakuri magani ne ali, ban son ka
tashi hnkalnka. Mama 'yar uwarka ce, ka
taimaka ka bata goyn baya tare da addu'ar fatan
alkhairi, kaji? Ka kwntar da hnkalnka, nayi
rantsuwa da mama tana da kanwa da na baka
ita. Amma tnda babu, ina son kasa natsuwa ckn
ranka, ka ji ni?" Yace, "naji abba, kuma na
gode". Umma tace, "nima dai hakurn nan shi zan
baka ali, gaba daya hawaynka sun kashe min
jiki. Amma babu abnda zamu iya yi, sai dai ince
Allah ya musnya maka da alkhairi" yace, "amin
umma". Abba yace, "to tashi kaje ka kwnta, ka ci
gaba da addu'a, komai zai wuce". Ya mike babu
kuzari ya bar falon. Shiru su umma suka yi
tsawn lokaci, kafn abba yace, "Allah ya kyauta!".
Ta cire tagumi tace, "amin. Da gaske ali yake yi"
"mtsw!" yayi dan tsaki ya tashi ya shige daknsa
dauke da tausayn ali, ya bar umma zugum! Tana
tunanin iska. Gidan yayi tsit! Ko da tasa
damuwar. Washe gari da wuri ali ya koma birnin
gwari don kara samun natsuwa. Idan bakwa
comments sai inga kamar littafin ne baiyi muku
dadi ba, na kuma sai inji bana son turowa din.