Complete Hausa Novels

Farar Wuta Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Farar Wuta Book 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 1 of 9

SHIMFIDA.
A lokacin da abinda kake tsoro yake tare da kai...!
Me zai faru a lokacin da abinda kake tsoro yake tare da kai? A lokacin da ka shiga shiga cikin wata duniya da zaka ji baka son barinta? ka bi ahalin cikinta kuna nutsewa cikin ramin da baku san dashi ba? ka shagala da kallon FARAR WUTAR da ta juye tunaninsu, ta wanke kwakwalwar su har kowa a duniyarsu ya manta cewar wuta, WUTA ce! Duk kuwa irin FARINTA.
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.

BABI NA ÆŠAYA.
~~~~~
Wajen karfe goma sha biyu na rana, matar dake cikin kitchen ɗin da aka zagaye da langa-langa daga ɗan madaidaicin tsakar gidan ta kwance wani ɗaurin itace dake gefe ta ƙara a cikin murhun gabanta sannan ta shiga firfita wutar da wani karyayyen mafici dake gefe. Dattijuwa ce mai kyawun jikin da idan ba fuskarta ka kalla ba zaka zabge shekarunta ƙiyasi.
Kayan jikinta riga da zani ne masu kyau da har karin guga zaka hango a jiki, gashin kanta mai laushi ya sirka da kananun furfura da ta fara yiwa kan nata rumfa.
Sai da ta tabbatar wutar ta kama sannan ta mike ta fito, a tsakar gidan ta tarad da babbar Æ´arta mai suna Amina zaune tana tsintar wake a wani katon farantin silver, shekaru ne kawai suka banbanta kamannin fuskokinsu amma kammaninsu daya sak! Har yanayin jikinsu da komai.
Ƴar siririya ce mai yalwar gashi irin na mahaifiyar tata, komai a fuskarta maidaidaci ne mai sanyin kwatance, idanunta ne kadai abinda mai ɗaukar hankali don duk da ba girma ne dasu ba, amma suna da wani kyalli kamar an ɗiga wani abu a cikinsu.
"Yi sauri ki gama Amina, sha biyu tayi gwara muyi sauri a É—ora don yanzu zaki ji su sun dawo."
Amina ta buÉ—a labule É—akin dake bayanta, ta kalli agogon dake kafe a cikin dakin sannan tace.
"Ashe lokaci ya tafi har haka, ban kula ba sam wallahi."
"Garin ne ba zafi ai shi yasa kika kwanta kika yi ta baccinki."
Da murmushi tace.
"Ni ai na gaji da tashi da wurin ne wallahi, da sun tafi makaranta sai inga gwara kawai na kwanta."
Mahaifiyar tasu da suke kira da Amma ta dauki wata tukunya dake gefe, ta nufi wajen ruwa da ita tana fadin.
"Ki cigaba da addu'a kawai, idan da rabon ki a cigaba da karatun nan zaki yi insha Allah."
Amina bata ce komai ba, don Allah ya sani ta fara karaya, shekararta guda kenan da kammala karatun sakandire dinta, kuma sakamokonta yayi kyau duk da cewar an taimaka musu wajen yin jarabawar, amma duk da haka ta san tana da kokarinta daidai gwargwado, shi yasa ko kadan ƙulafucin son cigaba da karatun bai bar ranta ba.
Kuma ba dole sai wani babban karatu ba, don ta daÉ—e da soke Jami'a a lissafinta, ta sani cewa mahaifinta bashi da halin wannan wajen, yana iya bakin kokarin sa wajen kula dasu da É—an abinda yake dashi kuma duk da haka kullum cikin damuwa yake yana ganin kamar baya basu abinda ya kamata, don yasha fadin cewa yayi burin cewar Æ´aÆ´an sa zasu huta da duk wani gata na duniya.
Don haka tunanin ta a kullum na ta samu makaranta ne ƙarama inda zata dan koyi aikin lafiya... Don mahaifiyarta tasha faɗa mata cewa ko allura ta iya yiwa mutane, idan tayi aure hakan zai taimake ta sosai fiye da ace ta zauna bata yin komai.
Zancen auren ya tuno mata da saurayin ta Abdallah, ta san shirye-shiryen komawa makaranta yake yi shi yasa bata ji shi ba kwana biyu, a matakinsa na ƙarshe yake a can wata jami'ar Sakkwato. Abdallah mutum ne mai kirki da kuma hankali, har islamiyyar dare yake da ita a bayan layinsu wanda yasa kowa ke ganin mutuncinsa kamar yadda itama take girmama shi a kodayaushe, tana ganinsa kamar yayanta shima kuma yana taimakon ta a komai kamar ƙanwarsa.
Mu'amalarsu daban take da yadda take ganin tsakanin ƙawarta Fatima da nata saurayin, abubuwa da yawa idan Fatiman ta gaya mata ta kanyi mamakin yadda suke iya kasancewa, don ita ko ɗaga ido ta kalli Abdallah bata iyawa sosai, sau da yawa ma ta kan manta cewa mu'amalarsu aure zata kai.
"Salamu alaikum, wai a bada gullisuwa."
Sallamar wani yaro ta katse tunaninta sanda ya tsaya daga jikin hanyar soro yana miko naira hamsin.
"Ta nawa?" Ta tambaya.
"Ta naira Ashirin."
Sai ta ajiye farantin waken ta miƙe ta karbi kudin, watanni hudu kenan da fara sana'arta ta saida alawar madara, gullisuwa da kuma albishir, kuma ciniki take yi sosai don a kwana uku kawai take sake yin kowannensu na dubu biyu. Wannan shine babban abinda ke ɗebe mata kewa da kuma faranta ranta ganin yadda take iya yin wasu bukatunta da kanta har ma ta taimakawa ƙannenta da ɗan kuɗin kashewa, saɓanin a watannin baya da bata komai.
Lokaci shine rayuwarka ta duniya da kuma lahira, babu amfani ka barshi yana tafiya haka sakaka... Kalaman Ammansu kenan a kullum idan tana bayanin abubuwan da suka dace da rayuwar mutum.
Ta É—ebowa yaron gullisuwar hade da canjinsa, ta fito daga falon nasu da babu komai sai shimfidadden carpet daidai lokacin da Fatima tayi sallama ta shigo.
"Amma ina wuni."
Ta gaishe da Ammar dake wanke bayan tukunyar data dauka.
"Lafiya kalau Fatima, Hajiyan ta fita ko tana nan?"
Hajiya mahaifiyar Fatiman ce, kuma tana zuwa jinyar kakar Fatiman ne da aka kwantar a asibiti kullum.
"A'a bata fita ba, girki take yi tukunna."
"To bari in gani nima idan na gama nawa ko zan iya bin ta, tun jiya nake waƙar ya kamata in koma wallahi."
"Ai jikin nata ma da sauki."
Cewar Fatiman tana nufar hanyar É—akin su Amina rike da ledar hannunta, ganin hakan yasa Amina ta dauko farantin waken da ta gama gyarawa, ta nufi wajen rijiya ta zago ruwa ta wanke shi sannan taje ta zuba a tukunyar dake gab da tafasa.
"Kaya Ahmad ya kawo min jiya da yazo."
Tana bude labulen ɗakin Fatiman ta fada, da fara'arta kuwa ta goge ruwan hannunta a jikin doguwar rigar da ta saka sannan ta ƙarasa gefen katifarta inda Fatiman ke fito da kayan, atamfa ce har guda biyu da kuma farin mayafi ɗaya sai kayan kwalliya.
"Gaskiya ne Fati, wallahi ki gode Allah, Ahmad na ji dake."
Fatima ta juya idanunta alamun dadi tana murmushi. Fara ce ita sosai, farin da take alfahari dashi a kodayaushe, tana ganinshine silar samuwar abubuwa da yawa a rayuwarta, don iyayenta masu ƙaramin ƙarfi ne sosai.
"Ni kaina wallahi na sani Amina, shi yasa nake gode masa kullum."
"Allah kuwa yana da kyauta, Allah ya saka masa da alkhairi... Kai wannan tafi kyau wallahi." Ta fada tana daga wata.
"Kamar kin san nima nafi ganin kyanta, har cewa nayi ko in barta sai Sallah kawai muyi ankonta ni dake."
Amina ta bude kwalin wata hoda sannan tace.
"Sallah fa da nisa, ki É—inka abarki kawai. Ma yi wani ankon idan lokacin yazo."
"To shikenan." Fatima ta gyara zama tana kallon yadda take kallon kayan, sai kawai tace.
"Wai yaushe rabon Abdallah da ya miki kyauta ne Amina?"
Amina bata bar kallon kayan kwalliyan ba tace.
"Shi da yake dan makaranta ta yaya zai iya wata dawainiya yanzu, in dai sallah tazo ai yana min kaya kin sani."
Fatima ta tabe baki.
"Wannan fa daban, kyauta kuma daban. Ni wallahi Amina na sha gaya miki ki ƙyale Abdallah nan, da tuni kin fara ganin wadanda suka fishi, don naga alama yanzu idanunki basa ganin kowa."
Sai a lokacin Amina ta kalle ta.
"Fatee, ke fa kin san ni duk wannan abin ma ba a gabana yake ba, shi yasa nake son mu'amala ta da Abdallah saboda shima yanzu karatunsa yake son gamawa, baya takura min nima kuma bana takura masa."
"Wai har yanzu kina ganin zaki cigaba da karatun ne?"
Ta daga kanta.
"Wallahi ban fidda rai ba Fatee, duk da  na san Baba ba zai iya ba, kuma babu wanda zai yi min bayan shi din.'
"Shi yasa nake gaya miki ki hakura kawai, ba komai mutum yake samu a rayuwa ba, a yanzu auren kawai ya kamata kiyi, ki ragewa su Baba nauyi sannan kema ki sami wajen da zaki iya É—aukar É—awainiyar wasu ma."
Kallonta kawai Amina take tana murmushi don ta riga ta sani cewa ba zata taba fahimtar abinda take ji a zuciyarta bane, sai da ta kai ƙarshe sannan ta shiga haɗa kayan tanafaɗin.
"To shikenan, ki bari sai bayan maulidi, idan mun fara kai ki, sai in fara wannan lissafin.
Jin haka yasa ba shiri itama tayi murmushi tana kara juya idanunta, don kamar yadda aka tsayar da rana, bayan maulidin ne bikinta ita da Ahmad din.
"Baki san wani abu ba ma, wata mata na samu mai sayar da magunguna a can layin..."
Da haka ta shiga bawa Amina labarin da yasa ta bar hada kayan ta zare idanu tana kallonta kafin  ta shiga ɗaka mata duka alamun bata son zancen, ita kuma tana kyalkyala dariya.
Mahaifin Amina mai suna Alhaji Sulaiman dattijon mutum ne mai sana'ar harkar aikin katako, ya samu wadata a da, don gidan da yake zaune da iyalansa na kansa ne, amma a yanzu abubuwa sun tsaya masa ta yadda ya ɗauki hakan ya sanya a ransa har ya zama shine damuwarsa a kodayaushe. Ƴaƴan sa biyar tare da matarsa Halimatus- Sadiya bafulatanar Niger da iyayenta suka dawo Nigeria da zama.
Amina ce ta farko, sai Aminu, Maryam, Adam da kuma autarsu Hafsa. Maryam, Aminu, da Adam suna matakin secondary ne a karatu yayin da Hafsa kadai take Primary, amma da yake makarantar da suke zuwa wata community school ce dake waje É—aya, tare suke tafiya dukkaninsu tare suke dawowa.
Babban damuwar Alhaji Sulaiman a yanzu shine ganin ƴaƴan sa na ƙara tasawa kuma harkar samun sa na ƙara yin baya, karayar arziƙin da ya samu ta taimaka ƙwarai wajen karya zuciyarsa akan komai, kullum cikin lissafi yake da kuma damuwar da ƙarara kowa ke gane ta duk da irin nuni da kuma nasihar da matarsa ke yi masa a kullum.
***
Ƙarfe Biyu da rabi.
"Yaya dan girman Allah zaki bani naira dari? Ƙunshi zanyi."
Maryam ta fada lokacin da take ƙoƙarin cire uniform ɗin ta bayan sun dawo daga makaranta. Amina na zaune tana ninke kayan wankinta tace.
"Ƙunshin me zaki yi?"
"Bikin yayarsu Na'imah fa, kin manta jiya nazo da katin."
Jin tayi shiru yasa ta sake tambaya.
"Zan baki Maryam, Allah ya kaimu gobe."
"Me za'a bayar? Idan ana ƙaunar Allah nima a taimaka mun."
Aminu ya fada yana shigowa cikin É—akin.
"Kaima ƙunshin zaka yi?"
"Me kyau ma kuwa, don kin san sai yafi fitowa a hannu na ma akan bakar fatarta."
Ya fadi hakan sanin cewar shi fari ne, don Æ´an mazan biyu su suka yiwo mahaifinsu sak a kammani da kuma hasken fatan, matan kuma Suka yo mahaifiyarsu, har gwara Maryam ma ana cewa idonta irin na babansu ne, amma Amina da Hafsa babu abinda suka bari a kammanin Amman.
"Wallahi ni ba baƙa bace kaima ka sani, irin wannan kalar fatar sai ka zagaye garin nan kaf baka samu irinta ba."
"To idan ma an samu me za'ayi da ita? Da dai irin ta Amina kika ce sai in yarda, amma ke duk gidan nan ma akwai mummuna kamar ki."
Maryam ta kara haÉ—e ranta tana saka hijabin data É—auko. Amina ta jefo masa wata riga dake hannunta tana murmushi.
"HaÉ—a mu kayi kawai kake zagi Aminu, dani da ita É—in me ya banbanta damu, ka takurawa Maryam wallahi."
"Haba ya zaki hada kalar ki data wannan fingilar? itama ta hakura ta karɓi kanta yadda take ne taƙi, sai faman iyayi fal ciki."
Da ƙunƙuni Maryam ta faɗi wani abun kafin ta tayar da sallarta. Hakan yasa shi dariya don shi kansa ya sani girman dake tsakaninsu ne kawai yasa take raga masa a azababbiyar magana da kuma rashin kunyar dake cikinta.
"Sai yaushe zaka fita yau?"
Amina ta tambaya sanin cewar da ya dawo baya dadewa a gidan yake tafiya can inda yake koyon gyaran mota a can hanyar gidan zoo, har  ma ya fara kwarewa don kusan shekara biyu kenan da Baba ya kai shi wajen.
"Sai na ƙarbowa Baba, kayansa daga wajen guga..." Ya shafo kansa.
"... Tun dazu ma fa ya kamata in je, sun ce sun gama."
Kafin Amina tayi magana, Hafsa ƙaramar ƙanwarsu ta shigo gidan hannunta riƙe da ƙullin farar ledar atturuhun data siyo na girkin dare da kuma takardar yashin madina tana zubawa a ɗaya hannunta tana lashewa. Amina ta ɗaga murya ta kirata ganin bata da alamun shigowa.
"Ki shigo ki cire kayan nan ki saka na islamiyya, ga uku nan har ta kusa, Adam har ya tafi kina nan."
Tana jin hakan Idanunta irin na Amina suka kaÉ—a a take sannan muryarta ta koma ta kuka, ta shigo É—akin da sauri tana faÉ—in.
"Dan Allah kice Ya Maryam ta raka ni, wallahi zane ni za'ayi..."
Kafin Aminan ta amsa, Aminu yace.
"Saka kayan muje in raja ki daga nan sai in wuce.
Ai kuwa da murnarta ta ruga da gudu zuwa dakin Amma inda kayanta suke, ta sani ba wanda ya isa ya dake ta makarantar tunda Aminu ne zai raka ta.
Aminu ya ciro Naira dari biyu daga aljihunsa ya cilla kan sallayar da Maryam ke sallah yana faÉ—in.
"Gashi nan kije a zana miki abinda ba ganinsa za'ayi ba."
Amina tayi murmushi tana godewa Allah a zuciyarta, tana son yadda suke tallafar junansu akan irin ƙananun buƙatun nan.
Hafsa bata dawo ba suka tsinci sallamar mahaifinsu, dukkaninsu suka kalli juna a lokaci guda sanin cewa lokacin ba lokacin dawowarsa bane, ƙa'ida ne sai bayan sallar magriba kullum yake dawowa don har Aminu yana yawan riga shi isowa ma.
"Allah yasa kar ya tambayi kayan nan..."
Aminu ya faÉ—a yana dafa kansa.
Ta tsakanin raga-raga labulen Amina ta hango yadda mahaifin nasu ya dafa kan Hafsa da ta taho ta rungume shi, sannan kai tsaye ya nufi hanyar É—akinsa.
Taga Amma ta fito daga falo sanye da hijabi alamun salla tayi ta bin bayansa tana fadin sannu da dawowa.
"Ke maza ki dauko takalminki mu fita."
Cewar Aminun, sannan ya juyo ya kalli Amina.
"Kice masa tun dazu na tafi karɓi kayan."
Ai kuwa yana sanya kafarsa waje suka ji Baban yace.
"Fita ce ta kama ni Halima, ina kayan da nace a karbo min?"
Basu ji amsar da Amman ta bayar ba sai muryarsa da ta sake dagawo wajen kiran Aminu.
"Aminu! Yana gidan nan?"
"Na shiga uku.."
Cewar Aminun, kuma Amina na kallon sanda Maryam ta murmusa a sallarta don daÉ—i.
"Baba sannu da zuwa, wani abu ne ya faru ka dawo yanzu?"
Ta tsinci muryarsa da yayi sauri ya tsugunna yana shafa kai ganin ya fito.
"Ni da gidana don na dawo sai ka tambaye ni me nazo yi? Ina kayan da nace ka karbo min?"
"To, to, bari aje a karbo."
Ya fada kamar sai a lokacin yace 'je ka karbo din,' kuma bai jira ya sake cewa komai ba ya kama hannun Hafsa da ta gama shiryawa suka yi waje.
Alhaji Sulaiman ya girgiza kansa kawai saboda takaici sannan ya kalli Amma dake tsaye a gefensa.
"Hajiya Kilishi ce yanzun nan ta kira ni tace tana son ganina."
Daga cikin É—akin Amina zata rantse daga ita har Amman a lokaci guda suka yi murmushi.
Hajiya Kilishi ƴaruwar Baba ce, mace ce mai kirki da son kyautatawa, ta taka muhimmiyar rawa a rayuwarsu ta kowanne fanni, tun kafin Mahaifinsu ya rasa arziƙinsa har bayan komai ya cakuɗe musu, don hatta kuɗin rubuta jarabawarta ta fita daga secondary ita ta tallafa aka biya, babban taimakon da tayi musu na kwanan nan shine lokacin da Maryam ta kamu da rashin lafiyar ciwon ciki, wanda daga ita har su kowa ya wahala kafin a gano cewar wani ƙari ne ke fito mata a gefen cikin kuma yayi girman da har sai an cire shi.
A wannan lokacin komai nasu ya riga ya ƙare wajen jinya, don hatta abinci sai daga gidan wan Baban ake kawo musu kullum ko tukunya basa dorawa, ɗan abinda Baba ya samu da kuma na wajen Amman daga ƴan sana'o'in da take yi duk a asibitin suke karewa.
Don haka a dole Baban ya shiga neman bashi ƙofa-ƙofa, ƴanuwansa suka hada masa iya abinda zasu iya amma ko kwata ba'a shafe na lissafin ba, Hajiya Kilishi ita taji labari a danginsu, ta kira Baban har gida ta bashi tallafin naira dubu ɗari uku, kuɗin aikin har da ɗoriya akai, tun daga wannan lokacin zuciyoyinsu suka kara girman darajarta a wajensu.
Mijin ta wani babban mai kuÉ—i ne kuma sanannen mutum ne, itace matarsa ta biyu kuma Æ´aÆ´an ta biyar dukkaninsu mata, amma ance saboda zaman amanar da suke yi da uwargidanta babban É—anta ma a wajen Hajiya Kilishin ya tashi tun yana yaro ta yadda ba kowa ne ya san cewa ba itace ta haife shi ba, Baba yasha gaya musu cewar ko gidan yaje baya iya banbance Æ´aÆ´an ta dana uwargidan.
"Shinkafa da wake kuka yi? A zubo min dan Allah kafin yaron nan ya dawo."
Muryan Baban ta katse tunanin Amina daidai lokacin da Maryam a gefenta ta idar daga sallah, ta sake kallonsa ta cikin labulen sanda da yake cewa.
"Allah yasa Amina ta daka yajin nan nata mai daÉ—i."
A lokaci guda murmushi ya suɓuce a fuskarta, sai kawai ta mike tana faɗin.
"Akwai Baba, Bari in kawo maka."
***
Royal Brompton Hospital.
Sydney St, London SW3 6NP, United Kingdom.
...So I took your hand, back through lamp-lit streets,
I knew,
Everything led back to you
So can you see the stars over Amsterdam?
You're the song my heart is beating to...
Waƙar a hankali take fitowa daga cikin labtop ɗin dake ajiye a wani ɗan ƙaramin tebur da kujerarsa dake can jikin dogon windon ɗakin, ɗakin asibiti ne da banda gadon mara lafiyar da kuma tarin computers ɗin gefe dake auna lafiyar wanda ke kwance, babu komai sai wata drawer daga can gefe wadda aka yi mata ado har da wasu ƴan fulawoyi, ɗakin a gyare yake tas yana kuma ƙamshi mai daɗi, ga room heater dake fitar da wani ɗumi mai daɗi sakamokon sanyin ƙanƙarar snow ɗin dake zuba daga waje.
A hankali idanun mara lafiyar dake kwance akan gadon suka buÉ—e, kuma duk da lumshewar su girman su ya fito a lokaci guda, matashi ne mai siririyar fuska, yana da yalwar gashin kai da kuma na gira kamar yadda na idanunsa suke dogwaye ta yadda idan ka kalle shi zaka ga kamar baya iya buÉ—e idanun nasa ne sosai.
Ya ɗago da hannunsa dake maƙale da allurar ruwan drip ɗin gefe, ya kalli hannun tsawon wasu sakanni kafin yasa ɗaya hannun nasa ya murza goshinsa alamun takaici, sannan a lokaci guda ya fizge drip ɗin daga jikinsa ya mike zaune, jini ya shiga fitowa daga inda allurar ta fita amma bai ko bi ta kai ba ya kalli rigar dake jikinsa, rigar asibitin ce wadda ake bawa kowanne mara lafiya.
Ya shiga ƙarewa ɗakin kallo a hankali har zuwa kan drawer dake can gefe, a lokaci guda ƙwaƙwalwarsa ta tuna masa da jakar da Ishaq ya ajiye a ciki jiya don haka ya mike tsaye, jiri ya so ɗaukarsa amma ya dage ya tsaya akan ƙafafunsa sannan ya isa ga drawer.
Ya buɗe ciki ya fito da wata baƙar jaka ya shiga fito da kayan ciki, ƙamshin turarensa na 'Dior Sauvage' shi ya tabbatar masa da cewar kayansa ne tun kafin ma ya gane su, kala biyu ne sai kuma wata ƙatuwar rigar sanyi wadda ke zuwa har gwiwa, bai yi tunanin komai ba ya shiga canjawa zuwa kayan, sai da yazo ɓalle maɓallan rigar saman sannan ya kula da jinin dake fita daga hannunsa.
Don haka ya saka rigar asibitin da ya cire ya goge sannan ya ɗora daya rigar, ya kuma jawo rigar sanyin ya dora akai, bai ko ɗauke rigar asibitin dake kasa ba ya saita facing Cap ɗin da ya ɗauko a ciki daidai fuskarsa sannan ya nufi hanyar kofar ɗakin, ya san duka wayoyinsa basa nan kuma Ishaq bai bar tasa a gefen labtop ɗin ba don haka ya nufi ƙofar ya buɗe, dogon korido ne a wajen mai dauke da kofofin ɗakuna da kuma mutane dake ta wucewa ta cikinsa, ya tabbata babu ma'aikatan da suka san shi a cikin waɗanda ke wucewa don haka kansa tsaye ya bi ta cikin mutanen dake tafiya ya saje, yana mai nufar hanyar waje.
Iskar dake kaɗawa a wajen mai tsananin sanyi ta ratsa fuskarsa sanda ya fito daga asibitin gabaɗaya, dare ne lokacin, ga fitulu a koina, na kan titi dana motoci, ga mutane birjik musamman na ƙafa sai faman wucewa suke.
Haka ƙofar asibitin take a kullum, tun daga shekarun da ya fara zuwansa har yau. Sanyi ya shiga ratsa kunnuwan sa dake buɗe sannan a lokaci guda yaji wata irin yunwa ta mamaye shi, sai kawai ya saka tafin hannayensa duka biyu ya gefen fuskarsa lokacin da idonsa ya sauka akan sunan wani kanti daga can tsallake, kantin da yake yawan yin siyayya duk lokacin da yazo kasar.
"24 dollors." (Dubu goma.)
Baturen dake kan kantar ya faÉ—a a lokacin da ya gama lissafa abubuwan daya É—ebo.
Ya kai hannunsa bayan aljihu kamar zai fito da wallet sai kuma ya dawo dashi, ya matso daidai jikin kantar yana kallon mutumin yace.
"You know me right?" (Ka san ni ko?)
Kallon da mutumin yake masa yasa ya cigaba da cewa.
"I used to come around, from that hospital...(Ina yawan zuwa, daga wancan asibitin..)"
Ya juya ya nuna asibitin sannan ya dawo ga fuskar mutumin da bata canja ba, sai kawai ya daga hannayen sa sama alamun sallamawa sannan yace.
"What I mean is my brother is coming to pick me from here... So do you mind If I just wait for him while I eat these? Because honestly I dont have anything with me right now but I assure you he's going to pay when he arrive...."
(Abinda nake nufi shine É—an uwana zai zo yanzu ya dauke ni anan... so ba zaka damu ba idan naci wadannan kafin yazo, don bani da komai a jiki na yanzu amma ina tabbatar maka shi zai biya ka idan yazo...)
Mutumin ya saka hannunsa ya danne kayan da yake shirin É—iba, sannan da sautin muryarsa da yafi kauri a yanzu ya sake maimaita masa adadin kudin.
"24 dollors." (Dubu goma.)
Har ya haƙura ya ɗauke hannunsa yana shirin juyawa sai kawai mutumin dake tsaye a bayansa yace.
"You're holding up the line, man! If you can't pay just leave."
(Malam kana riƙe mana layi, idan baza ka iya biya ba ba ka bar wajen mana.)
A sakannin da mutumin ya rufe bakinsa, a sakannin wani irin naushi ya ziyarci fuskarsa, naushin da ya kusan kaishi har kasa, ya ɗago jini na fara zuba ta hancinsa lokacin da wata mata a gefensu ta ƙwalla ƙara shi kuma ya furta kalmar zagi yana share jinin, kuma baiyi wata-wata ba ya nufo kansa da nasa naushin shima dsya haddasa fada a tsakaninsu ba shiri, kuma kowannensu yaji lokacin da mai kantin ya kwalla ƙara yana faɗin.
"Someone should call the police!" (Wani ya kira Æ´an sanda!)
****
British Transport Police Station
No. 2 Melton St, London NW1 2BW, United Kingdom.
"Kun tabbata dukkan waÉ—annan bayanan file É—in gaskiya ne?"
ÆŠan sandan ya tambaya daga tsallaken teburin da Ishaq ke zaune tare da wani ma'aikacin asibiti a gefensa.
"Da gaske muke ranka ya dade, mara lafiya ne ya fito ba tare da an sallame shi ba, kuma a yanzu haka ma ba'a hayyacinsa yake ba."
ÆŠan sandan ya kalli ma'akacin asibitin da yayi magana, ya kara kallon ID Card É—insa da ya mika masa sannan ya gyada kansa yana sake kallon cikin file É—in.
"Naga dukkan wasu bayanai na cewar yana da matsalar kwakwalwa, amma banga wani bayani ko sau daya na abinda ciwon ke saka shi ba..."
"Ai da yake yallabai, mu  a asibiti cutar kawai muke bayani ba abinda zata haifar ba."
Jin haka yasa Ɗan sandan ya dawo da hankalinsa ga Ishaq dake zaune yana kallon can gefe inda aka ƙulle tarin mutane a cikin wani budadden cell da aka zagaye da karafa kawai.
"Kai É—anuwansa ne ko? Zaka iya gaya mana abubuwan da yake yi, don mu san cewa ba da gangan yayi abinda muka kama shi yanzu ba?"
Ishaq ya gyara zamansa bayan ya dawo da hankalinsa nan, sannan cikin harshen turanci shima yace.
"Yayi abubuwa da yawa yallaɓai, waɗanda suka fi wannan ma, ba tun yanzu ba..."
"Misali..." ÆŠan sandan ya katse shi. "Misali zaka bani ba wani bayani ba."
Jin haka yasa Ishaq haÉ—iye yawu ba shiri, ya juya ya sake kallon idanun da suke kallonsa daga cikin cell É—in sannan ya gyara zamansa kaÉ—an, muryarsa can kasa yace.
"Yallabai, a karo na ƙarshe da ciwonsa ya tashi saura kaɗan yayi kisan kai."
Idanun É—an sandan basu canja ba, ya cigaba da kallonsa na wasu sakanni kawai kafin ya gyaÉ—a kai, sannan ya nuna file din dake hannunsa.
"Zan baku belinsa ne yanzu saboda wannan kawai, amma ku tabbatar bai sake barin asibitin nan ba sai da cikakkiyar lafiyarsa. Idan ba haka ba idan muka sake kama shi, mu zamu riƙe shi har sai ya warke."
Dukkaninsu suka gyada kai alamun sun fahimta kafin ya juya ya kira wani ɗan sanda dake ƙoƙarin wucewa.
"Stone! bring the Black one out." (Stone! Fito da baƙin cikinsu.)
Stone ɗin baya bukatar wani karin bayani don wanda aka nuna masa shi kaɗai ne baƙi a cikin tarin turawan cell din, don haka ya zaro muƙullai daga jikinsa ya nufi wajen.
Ɗan sandan ya sake kallon file ɗin hannunsa a karo na ƙarshe, idanunsa suka sauka akan sunan dake rubuce a jiki.
Ma'aruf Mansour Bakori!
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.
BABI NA BIYU.
~~~~
"Kowanne ɗan adam yana da tarin ƙalubale a rayuwarsa, amma ga wanda suke da cutar 'Bipola disoder' nasu ƙalubalen daban ne. Bipola disoder cutar ƙwaƙwalwa ce dake canja yanayin mutum a lokaci guda, ta canja ƙarfinsa, yanayin tunaninsa har da ɗabi'arsa. Cuta ce dake iya taba rayuwar mutum ta bangaren aikinsa, karatu,  zamantakewa har ma ta iya dakushewa mutum hanyar cigaba a rayuwarsa, don tana yawan tashi ne akai-akai.
Cutar tana farawa ne daga lokacin ƙuruciya, kuma duk da cewar babu takamaimai maganinta ana samun saukinta ko kuma ƙaruwarta idan har ba'a bin ƙaidojin magani daidai. Tana da matakai huɗu kuma na ƙarshen da ake kira da "Mania" shi yafi kowanne hatsari.
A matakin 'Mania' mara lafiya yana jin tsananin ƙarfi da jin cewa zai iya komai, da kuma tsananin fushi da yawan tunanin abubuwa barkatai, wanda ke jawo mutum ya harzuƙa ta yadda babu mai iyawa dashi, mara lafiyar yana samun ƙarancin bacci da kuma rashin nutsuwa sannan wasu ƙwaƙwalwar su tana buɗewa ta yadda za su yi abinda idan a lafiyarsu ne baza su iya ba. Matakin dake bi wa wannan kuma shine 'HypoMania'...."
Duk wannan bayanin yana fitowa ne daga wata Tv dake kafe a saman harabar wajen, ƙaton wajen jira ne na asibiti inda tarin ma'aikata ke wucewa wajen wasu gadaje daga can baya da aka kwantar da marasa lafiya, labulayen da aka sassaka a tsakanin kowanne gado sune kadai abinda ya raba gadajen.
Bayanin dake fitowa daga Tvn, na irin rashin lafiyar ƙwaƙwalwar da ake dubawa a wannan ɓangaren asibitin ne, masu jiran kuma na zaune suna saurarar bayanan da ake yi mai dauke da hotuna don sauƙin fahimta ga marasa lafiyar da kuma masu jinyar, Ishaq yana ɗaya daga cikin masu jiran, yana zaune daga karshen kujerar kamar mai jiran ƙiris! Ya mike, kafarsa ta bangaren dama yake faman bubbugawa yayin da gefen bakinsa yake a cije.
A bayyane yake ga duk wanda ya kalle shi cewa jira kawai yake likitocin dake tsaye a wajen gadon É—an'uwansa su fito daga bayan labulen da aka zagaye gadon dashi. Sun taru kusan su bakwai a ciki har da Nurses don hankalinsu ya tashi jin cewar daga police station aka taho dashi bayan an neme shi an rasa.
Ya sani cewar dukkaninsu tsoro suke yi game da ciwonsa, don Ma'aruf ya riga ya kai mataki na karshe a ciwon ƙwaƙwalwar tasa, ya riga ya kƙure komai a Bipolar Disoder, don idan har akwai wani mutum a duniya da baya taimakon kansa to Ma'aruf ne. A shekaru goma da cutar nan ta same shi babu irin fadi tashin da ba'ayi ba daga kowanne ɓangare na iyaye da kuma ƴanuwansa amma rashin tasa tallafawar ya haɓɓaka ciwon har sai da ya ƙaraso matakin ƙarshe, 'Mania Stage'.
A baya bai fi ƴan awanni ko kwana ɗaya zuwa biyu ba yake yi idan ciwon ya taso masa, amma a yanzu sati guda cur, har suka zo ƙasar nan Ma'aruf ba'a hankali sa yake ba, hakan yasa dole aka kwantar dashi a asibitin da alluran bacci wanda suka taimaka, ya farka cikin hayyacinsa yanzu.
Don duk da cewar a police station suka je suka same shi, idanunsa kawai ya kalla ya san cewar ya dawo hayyacinsa tun kafin likitocin ma su gane, shi yasa ya matsu da fitowarsu a yanzu don yaje ya same shi, ya sauke maganganun dake zuciyarsa tun daga ranar da Mami ta kira shi muryar ta na rawa taje ya taho gida Ma'aruf ya shigo musu da gawar wani.
Likitocin duka fito a daidai wannan lokacin, kuma bai tsaya jiran komai ba ya zagaya ta É—aya hanyar da wandanda ba ma'aikata ba ke wucewa ya nufi wajen gadon.
"Minti biyar! minti biyar kawai na fita Ma'aruf amma kayi tsalle daga asibitin nan zuwa police station!"
Ya faɗi hakan da harshen hausa daidai sanda ya bankaɗa labulen da aka zagaye gadon. Dama abinda Ma'aruf ɗin yake jira kenan, ya riga ya sani cewar ya daɗe a waje yana kaɗa ƙafa yana jira likitocin su fita ya shigo da tarin ƙorafinsa, don haka hankalinsa a kwance ya ɗago da idanunsa ya kalle shi.
"Kaima sani bana iya rike yunwa, na tafi in samu abinda zanci ne and you left me with nothing, ba dole su kaini police station ba."
Ishaq ya girgiza kansa.
"Ma'aruf ba a Nigeria muke ba, ko baka gane bane da ka farka? me kake tunani idan suka kama ka a ƙasar nan?"
Maimakon ya bashi amsa kai tsaye, sai ya koma da baya a jikin gadon, ya zura hannayensa duka biyu cikin gashin kansa sannan yace.
"Na sha gaya maka kana damuwa da yawa Ishaq, kana damuwa akan abubuwan da suke faruwa dama wanda basu zo ba."
"Kuma matsalar kenan, kai da baka damuwar, baka damuwa da kanka balle kuma na kusa da kai, shi yasa har muka zo wannan matakin Ma'aruf! Mania!"
Ya faÉ—i sunan mataki na karshe a cutar da Ma'aruf É—in ke fuskanta, kuma ga mamakinsa, a lokaci guda Ma'aruf É—in ya juyo ya kalle shi, sannan a cikin sakan biyu idanunsa suka haska da wani abu da Ishaq É—in zai rantse da ubangijin dake busa musu numfashi cewar bai taba gani a idanunsa ba. Tsoro da kuma fargaba! Sai kawai ya girgiza kansa sannan ya cigaba da faÉ—in.
"Shekara biyu da suka wuce a asibitin nan ko HypoMania test ɗinka basu kai ba, baka da lafiya amma babu wanda ya sani babu mai ganewa, muna ɓoye komai daki-daki don rayuwarka ta tafi daidai. Amma yanzu ka gaya min me kayi kafin mu taho nan Ma'aruf? Daniel ka yiwa dukan da har ya suma akan baiyi maka submitting takardu a office ba, ka dake shi har ya suma Ma'aruf sannan ka sako shi a mota ka kaishi gida, ka shiga dashi har falon Baffa kana gaya masa wai ka kawo shi ya kore shi daga aiki!" (Mahaifinsa.)
Yanzu ka gaya min a duk kamfanin Bakori da ɗaukacin jama'ar da suka sanka, waye bai san kana fama da ciwon ƙwaƙwalwa ba Ma'aruf?
Yanzu ka gaya min a duk kamfanin Bakori da duk ɗaukacin kewayen da mutane suka sanka, waye a yanzu bai san cewa kana fama da matsala a ƙwaƙwalwa ba? Waye bai san cewa kana da wannan nakasar ba Ma'aruf?"
Muryar Ishaq ɗagawa take a lokacin da yake fadar hakan, sautin ta na fitowa cike da wani irin daci da takaicin duk abubuwan da yake faɗa din, kuma har a lokacin yana ganin adadin kifta idanun da Ma'aruf ke yi alamun cewa kowacce kalma tana bada ma'anar da yake son ya gane a ƙwaƙwalwar sa. Bai ce komai ba ya cigaba.
"Ka san me ya fitar dani É—azu? Ka san abinda yasa na bar É—akin har kaje ka aikata abinda kayi?..."
Ya tambaya kamar yana jiran ya bashi amsa.
"... Office din likitan ka naje, shi ya kira ni personally Ma'aruf! Yayi min dukkan bayanin halin da kake ciki, kuma albishirin ka abinda kake so zai faru, idan komai ya cigaba da kasancewa yadda yake tafiya kana gab da rasa hankalinka gabaÉ—aya Ma'aruf! Kana gab da rasa komai gabaÉ—aya..."
"And so what idan na rasa?!"
Yadda Ma'aruf ɗin ya katse shi a lokaci guda da tasa sautin muryar ya bashi mamakin da har sai da ya haska a idanunsa. Kallonsa yake har a lokacin da nasa idanun da suka canja, yanayinsu na kara lumshewa kamar kodayaushe idan yana cikin ɓacin rai.
"Nace sai me idan na rasa komai? Idan dai har ragowar lokacin da nake dashi zai bani dama na iya cimma abinda ke gabana sai me idan na rasa hankalina?"
Sai ya girgiza kansa kawai yana cigaba da kallonsa.
"Nasha gaya maka Ma'aruf ya mutu shekaru goma da suka wuce Ishaq, kaƙi ka yarda dani ne, amma Ma'aruf ya riga mutu, babu shi anan."
Ya ƙarasa yana nuna ƙirjinsa, daidai lokacin da labulen dakin ya buɗe, wani bature ya leƙo fuskarsa a murtuƙe yace.
"What the in the world are you two talking abou..."
Bai karasa ba sakamakon kallon da su duka biyun suka juyo suna yi masa kowanne ransa a ɓace, sai kawai yayi sauri ya maida labulen ya juya, dukkaninsu suka yi ajiyar zuciya alokaci guda.
Shiru ya ratsa wucewar sakan ɗaya, biyu, uku... kafin Ishaq ya ƙaraso a hankali ya zauna a gefen sa.
"Kwana na nawa a asibitin nan?"
Ma'aruf ya katse shirun da sautin muryarsa da ya koma daidai, mai zurfi dake fitowa can kasa.
"HuÉ—u, you were unconscious for three days a Nigeria kafin mu taho."
A hankali ya haɗiye yawu cikin maƙogwaronsa sannan ya ƙara tambaya.
"Me Baffa yace?"
"Ransa ya ɓaci sosai, ransa ya ɓaci fiye da duk yadda kake tunani, kullum sai ya kira waya ya tambaya idan ka farka, kuma yace da zarar ka dawo hayyacinka mu koma gida."
Yaji lokacin da ya zuƙi numfashi ya fitar sannan ya koma da baya ya jingina da gadon bai ce komai ba, don haka shi ya cigaba da cewa.
"Mami kusan duk bayan awa guda take kira Ma'aruf, suna can ne amma hankalinsu anan yake, kowa ya damu, Hajiya tace hatta Abdurrahim jiya gidanka ya tafi ya kwana, dan Allah Ma'aruf, dan Allah ka taimaka ko don waÉ—annan mutanen ka tallafi rayuwarka, dan Allah."
Kai tsaye maganganun suka shiga har wani waje dake can ƙasan zuciyar Ma'aruf, kuma yana jin yadda tasirin su ya shiga bin kowacce jijiya ta jikinsa yana tafiya tare da gudun jinin cikinsu, sai kawai ya sake cusa yatsunsa cikin gashin kansa sannan ya runtse idanunsa.
Ishaq yana kallonsa, yana jin yadda tausayinsa ke bin zuciyarsa kamar kullum, ba sauki bane rayuwa da irin wannan cutar ya sani, ba sauki bane daurewa irin abinda ke zuciyar Ma'aruf din, ba sauki bane yadda yake iya daurewa abubuwa tsawon shekarun nan, ba sauki bane ba zama Ma'aruf din da yake gabaÉ—aya ya sani... Shi yasa fatansa a kodayaushe bai wuce Allah ya tallafi rayuwarsa ta wata hanya daban da take sabuwa ba, domin Allahn ya sani cewa su sun gwada duk wata hanyar da take a tunaninsu amma babu wani sauki.
Ya haɗiye yawu a hankali cikin maƙogwaron sa yana cigaba da kallonsa yace.
"Nayi mana booking flight, gobe zamu koma."
Kuma ba don kallonsa yake ba ya tabbata ba zai ji sanda ya amsa da 'Allah ya kaimu' ba.
Saboda haka kai tsaye sai ya sake tambaya.
"Yaya kake ji?"
Ma'aruf yasa yatsu biyu ya shafo saman hancinsa har a lokacin bai buÉ—e idonsa ba yace.
"Ina ji ne kamar zan mutu saboda yunwa, nace ka taimaka min da abinci amma kana ta masifa, Idan na sake fita daga nan kar barni kawai kar kaje beli na."
Ba shiri wani guntun murmushi ya suɓuce a fuskar Ishaq ɗin na tabbas ɗin da yake dashi cewar ya dawo daidai, don har abada irin Ma'aruf guda daya ya sani a duk tsayin rayuwarsa.
Ma'aruf yaji lokacin da ya fita amma duk da haka bai bude idanunsa ba, hoto ɗaya ne ke yawo a cikin kansa, hoton ɗakin bincikensa, yana hasko tarin takardu da kuma hotunan da suke cikin ɗakin nan, sannan yana hasko yadda hanya ta ƙarshe da yake tunanin zata kai shi ga nasara bayan shekaru huɗu ta rushe har garinta, wanda takaicin haka shine sanadiyar tashin ciwon nasa da abinda yayi har suka taho nan.
Wata jijiya daga gefen kansa ta bullutso cike da wani sabon takaicin da ya sake ratsa shi, sabon takaici... Don wannan É—auke yake da wani layi na fargaba da kuma tsoro, tsoron da bai taba ji a ransa game da ciwon nasa ba tsawon shekaru goma da suka wuce, maganganun Ishaq suka sake haskawa a cikin kansa.
...idan komai ya cigaba da kasancewa yadda yake tafiya, kana gab da rasa hankalinka gabaÉ—aya Ma'aruf!
***
Alhaji Muhammad Mansour Bakori, sanannen mutum ne wanda yake da babban Kamfanin yin robobi a garin Kano tare da ƙaninsa Alhaji Usman, wanda su biyu ne kacal a wajen iyayensu, mahaifinsu ya rasu shekaru da daɗewa amma mahaifiyar su tana raye.
Alhaji Mansour Bakori yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha ɗaya, yayin da Alhaji Usman bai taba haihuwa ba tsawon shekaru talatin da aurensa, wanda hakan ya faru ne sakamakon wani hatsari da yayi tun kafin tun yana saurayi har ya zame masa sanadin hakan, shi yasa kowa a danginsu yake girmama matarsa Hajiya Madina da kuma jinjina mata na zaman da take dashi a duk shekarun nan alhali ita lafiyarta ƙalau.
Matan Alhaji Mansour biyu, Uwargidan itace Hajiya Maimuna, wata mata mai kirki da kuma alkunya, É—anta na farko Jamal ya rasu shekaru goma da suka wuce, daga shi sai Ma'aruf wanda shi a wajen kishiyarta ya girma, sai Shukra, Munaya, Abdurrahim wanda shi tun yana shekaru biyu a duniya ya kamu da matsalar rashin magana amma yana ji kamar kowa, sai kuma autarsu Zahra.
Hajiya Kilishi itace mata ta biyu a gidan, wata mace ce mai tsananin kirki da kyautatawa, don faɗa ko da na rana guda bai taɓa haɗa su da Hajiya Maimuna ba tun zuwanta gidan, wani irin zaman lafiya da mutunta juna ne a tsakaninsu tun farkon zuwanta gidan, hakan yasa basu kaɗai ba ko wanda yake nesa ba zai taba cewar su ɗin kishiyoyin juna bane idan ya gansu tare.
Ita ta raini Ma'aruf tun daga watannin da aka yaye shi har zuwa girmansa na yanzu. Hajiya Maimuna, mace ce mai hali irin na mutanen da, tsananin kawaici akan abinda suke ganin shine daidai, don haka tun daga ranar da Hajiya Kilishi ta karɓe sshi bata ƙara nuna cewa shi nata bane, a suna kawai Ma'aruf ya santa a matsayin mahaifiyarsa, amma a wajen Hajiya Kilishin da suke kira da Mami ya samu dukkanin wata kulawar da ɗa ke samu daga mahaifiyarsa.
Ita ta raine shi da ƙarfin jikinta da kuma na zuciyarta, har zuwa girmansa kuwa ya zama tsakaninsa da Hajiya Maimuna gaisuwa ce kawai amma Mami ce komai nasa, duk da ƴadda wasu daga cikin ƴanuwan Hajiya Maimunan suke nuna rashin jin daɗin su akan hakan a yanzu da ya zama shine kaɗai namiji babba a gidan.
Ƴaƴan Hajiya Kilishi biyar ne, dukkaninsu mata kuma dukkanninsu harafin sunansu ya fara ne da harafin S, Safiyya, Salma, Surayya, Samira da kuma Sahla kamar yadda take so, don a wajen Daddy babu ruwansa da raɗin suna, duk wanda iyayensu mata suka zaba shi zai saka ba ruwansa. Zahra ce ma kawai taci sunan Inna Danejo 'Fatima' kamar yadda Hajiya Maimunan ta nuna tana so a saka.
Hajiya Maimuna ta sami matsalar shanyewar ƙafafu bayan ta haifi ƴarta ta ƙarshe Zahra, kuma babu irin maganin da ba'ayi ba a ƙasashe daban- daban amma ba nasara, don haka a dole yanzu sai akan Wheelchair take yawo.
Gidan Alhaji Mansour dake unguwar NNDC quarters a garin Kano, ƙaton gida ne mai ɗauke da bangare-bangare, akwai ɓangaren iyalansa guda biyu wanda kowanne iri daya ne, ƙaton falo da ɗakuna hudu kowanne da banɗakinsa a ciki da kuma sauran wajaje irin Kitchen, store, courtyard da dai sauransu, sai bangarensa inda shine waje na farko a gidan mai ɗauke da ɗakuna biyu da falo da kuma wajen meeting ɗinsa inda yake ganin baƙi a gida.
Akwai bangaren boys quarters inda masu a gidan suke zaune sai kuma wajen Inna Danejo kakar gidan, wato mahaifiyarsu Alhaji Mansour inda itama take da ƙaton falo, ɗaki ɗaya da kuma toilet, sai ɓangaren ƴan aiki, sai kuma bangare na karshe daga gefen hagu na harabar gidan, wato bangaren Alhaji Usman da suke kira da Alhaji Baba, wanda shima da a gidan yake tare da matarsa daga baya sai ya siyi wani gida gaba dasu kaɗan ya koma, don haka wajen a ƙulle yake babu kowa.
Ishaq abokin Ma'aruf ne kuma É—an'uwansa, don da Mahaifiyar Ishaq É—in da Hajiya Maimuna iyayensu É—aya, asalin mahaifinsa É—an Kaduna ne kuma shi kaÉ—ai iyayensa suka haifa, mahaifinsa ya daÉ—e da rasuwa amna mahaifiyarsa sai da yazo matakin shiga Jami'a ne sannan Allah ya É—auki ranta, don haka da shawarar Mami, Hajiya Maimuna ta tambayi Alhaji Mansour da kowa ke kira da Baffa, Ishaq ya dawo gidansu da zama daidai lokacin da Ma'aruf ke kokarin shiga Jami'a.
Mamin tayi haka ne don ganin ta samowa Ma'aruf sauki akan halin alhinin ɗanuwansa da har a lokacin bai gama warkewa daga ransa ba, don haka tare da Ishaq ɗin Baffa ya ɗauki nauyin karatunsu a wata Private University dake London har suka kammala, kuma hakan ya sanya shaƙuwa sosai a tsakaninsu duk da cewar ɓangare daban-daban suka karanta. Ma'aruf ya karanci harkar Kasuwanci ne yayin da Ishaq ya karanci ɓangaren aikin lawyer kamar yadda yake da buri tun yana yaro.
***
Washegari...
No. 58 Mafara Street, NNDC SharaÉ—a Qauters.
.07:30 Pm.
Tun daga ƙofar gidan zaka gane cewar anyi wani taro ne a gidan an watse, don hatta gate din a bude yake gabaɗaya sannan ga motoci daga ciki suna kokarin fitowa.
Idan ka biyo ta cikin mutanen, zaka wuce ko'ina hanya ta kai ka har ɓangaren Hajiya Maimuna inda taron mutanen yafi yawa musamman a ƙaton falon ɓangaren da zaka tarar wanda yake cike da tarin mutane gabaɗayansu mata, kowa na zaune da abokin hirarsa yayin da ƙamshin turarukansu ya haɗe da ƙamshin daddaɗan abincin da aka gama ci a falon, don ga tarin plates nan wasu ma har da ragowar abincin sannan kuma a can gaban Tv stand na ɗakin akwai wasu manya-manyan flasks cike da snacks kala-kala ga duk wanda yake so ya diba.
Sai dai duk wannan ba shine abin kallo a dakin ba, tarin akwatunan dake zube a makeken carpet din tsakiyar falon ne, an buÉ—e kowannensu dake cike da kaya fal.
Lefen Babbar ƴar Hajiya Maimunan mace da suke kira da Shukra ne, amma ba zaka banbance adadin yawan ƴanuwan Hajiya Maimunan ko kuma na Hajiya Kilishi a falon ba, sun riga sun zama ɗaya dukkanninsu don ko a sati biyu da aka karbi lefe biyu na ƴaƴan Hajiya Kilishin Safiyya da Salma, duk sune dai a wajen, shi yasa a yanzu ma rabi hirarsu ta shirye-shiryen  bikin da aka saka nan da wata guda mai zuwa ce.
Hajiya Kilishi ta ratso ta cikin mutanen, sanye take da wata doguwar rigar lace daya sha adon stones sai wulgawar kyalli yake a cikin hasken fitulun dakin, ta karaso inda Hajiya Maimuna ke zaune akan kujerar Wheelchair dinta tana hira da wata Æ´aruwarta, ta sunkuyo daidai saitin fuskarta sannan tace.
"Hajiya su Ma'aruf sun iso, yanzu na tura Malam Sani (direba) ya É—auko su daga airpot, mukullin store dinki zan karba na ajiyemusu abinci É—azu, Hajiya Madina ce tace zata tafi nace idan direban nata ya sauke ta sai ya karasa ya kai musu abinci don na san baxa su shigo yau ba."
"Toh Alhamdlilah, Muƙullin yana hannun Sameera ita ta karba dazu wai sun ajiyewa ƙawayenta abinci su ma."
Hajiya Maimunan ta amsa a hankali itama. Dukkaninsu sun sani cewa a duk tarin jama'ar gidan babu wanda bai san abinda Ma'aruf ɗin yayi ba da kuma cewar baya ƙasar don labari baya taba ɓuya, amma duk da haka gwara ace basu fallasa zancen ba duk kuwa da cewar duk ƴanuwa ne a gidan, amma hakan ba zai hana cece-kuce ba.
Daga nan ɓangarenta ta nufa, inda babu mutane sosai, kuma ƴanmatan gidan da wasu kawayensu suka tare suna ta hayaniyar da jiran a ragu don suma suje su buɗe nasu babin kallon kayan. A falo ta tarar da Zahra da Sahla ƴan autan gidan kuma sa'annin juna sun baje litattafansu suna ta aiki kamar basu san da bidirin da ake yi a gidan ba, dama yayyensu sun riga sun manna musu sunan Allazi boko 1 da kuma Allazi boko 2, don mayun karatu ne kamar ba gobe, yanzu suka shiga SS1 amma abinda suka sani ko Abdurrahim da yake SS3 bai sani ba, kwanaki har Surayya dake level three suka koyawa wani abu a Biology.
Har Hajiya Kilishin zata yi musu maganar abinci sai ta kula da plate din snacks dake tsakiyar litattafansu, ta sana aikin Mama Rabi ne hakan, wata dattijuwa ma'aikaciyar gidan da har yanzu bata daina kula dasu ba kasancewar ita ta yaye su tun suna ƙanana.
Don haka ta amsa sannu da shigowar da suka yi mata kawai ta wuce. Ta nufi kofar dakinsu Salma inda Æ´anmatan suke, hayaniyarsu tun daga falon zaka ji ta, cike da raha da kuma nishadi kamar an fara bikin, kuma duka hirar da suke ta tsare-tsaren bikin ce da suka daÉ—e suna yi tunda wannan shine karo na farko da za'a aurar da mata a gidan, kuma har guda uku a lokaci guda.
"A'a ranar kunshi ne fa za'ayi style iri daya, ranar Kamu kamar kowa zaiyi style dinsa ne ko?"
Muryar Munaya ta tambaya cikin hayaniyar.
"Ranar kunshi fa shi babu anko Munaya kin manta ne kowa kayansa zai saka, da Kamu ne za'ayi har style É—aya."
Wata kawar Salma, mai suna Aysha ta bata amsa.
Hajiya Kilishi ta buɗe kofar dakin daidai lokacin da Munayan ke gyara glass din idonta tana kallon wayar Sameera dake hannunta inda take ƙoƙarin banbace tarin atamfofi da kuma lesukan da zasu yi ankon dasu.
A ƙaton gadon ɗakin gabaɗayansu suke a baje dasu da tarin plate din snacks din da suke ci, sai wadanda basu sami waje bane suka zauna daga kan bedside drawers.
"Ni fa wallahi gani nake kamar wata É—aya ba zai isa duk wannan shirye-shiryen ba."
Shukra ta faÉ—a tana danna tata wayar.
"What?!" Salma ta mike daga kwance tana kallonta.
"... Ai Ya Shukra kar ma ki fara wannan zancen don wallahi Imran ba zai taɓa yarda a ƙara mana ko sati ɗaya ba."
Salma ta faɗa wanda hakan yasa dukkaninsu yin shewa a lokaci guda, don duk cikin amaren tafi kowa ɗokin bikin, yayarta Safiyya ba ruwanta don ita dama ba mai magana bace tun farko, kuma wanda zata aura mai mata ne da ƴaƴan sa biyu duk da cewar ba wani manyan ta yayi ba. Shukra kuma dake kan matakin masters dinta a bayyane yake cewa hankalinta yafi tafiya ga Project work din da take kan gaɓar yi fiye da bikin, duk kuwa da irin rawar kafar da  Suraj ɗin da zata aura ke yi shi, wanda dan wani abokin aikin Baffa ne.
Har Salma zata sake cewa wani abu Sameera dake gefenta ta daka mata duka, wani duka da idan zata yi ɓaram-ɓaramarta Mamin tazo wucewa suke yi mata shi, don haka a lokaci guda ta juyo ta kalli kofa inda Hajiya Kilishin ke tsaye tana kallonsu da murmushi.
"Mami ina wuni..."  Duka kawayensu na ɗakin suka hada baki wajen gaishe ta don tun zuwansu basu ma ganta ba.
Da murmushin ta amsa musu sannan ta kira Sameera.
"Ina muƙullin store dinsu Munaya? Yayanku sun dawo yanzu, kizo ki tayani mu debo abincinsu a saka a motarsu Hajiya Madina."
Da wani irin murmushi mai faɗi Sameeran ta amsa, don Allah ya sani duk da kowanensu yayi waya dashi tun a jiya, da kuma hayaniyar gidan ta yau, suna cike da tunanin halin da Ma'aruf ɗin ke ciki, don abinda yayi wani abu ne da basu taɓa gani ba tsawon rayuwarsu duk da sun san cewa kuwa yana da wannan cutar.
***
Mallam Aminu Kano International Airport 
08:30 PM.
"Wata nawa aka saka bikin yaran nan ne Malam Sani?"
Ishaq ya tambaya a lokacin da yake kokarin saka jakar kayansu cikin boot É—in motar da Malam Sanin ya buÉ—e.
"Wata É—aya aka saka wallahi, ai gidan ma har yanzu yana nan a É—inke, shi yasa Hajiya tace ba sai kunzo ba, kawai in wuce daku gida."
Ishaq ya gyaÉ—a kansa yana rufe boot É—in.
"Ai dama bamu da plan din zuwagidan nan yau, amma Lallai su Baffa sun shirya, har su uku ne fa a wata É—aya kawai."
"To ai rufin asirin Allah ake ciki kullum kuma shi ke rufawar." Cewar Malam Sanin yana dariya.
Duk maganar da suke yi, Ma'aruf na zaune a cikin motar daga baya, wayarsa na riƙe a hannunsa haskenta na haska siririyar fuskarsa da a cikin ƴan kwanakin ta ƙara ramewa, message ne kawai ke tururuwar shigowa da kuma tarin emails tunda ya kunna wayar har zuwa yanzu, ya lumshe idanunsa kawai sai kallonsu yake a lokaci guda kuma yana jin hirar su Ishaq ɗin daga waje.
Allah ya sani gabaÉ—aya ya manta cewa shirye-shiryen bikin akeyi sai a jiya da Mamin ke tuna masa cewa yau ne za'a karbi lefen Shukra, kuma jin cewa gidan a cike yake yasa shima baiyi tunanin ya kamata su je É—in ba, amma kuma ya kamata yaga Baffa a yau, idan yana gidan kuma fa? Sai yasa yatsan sa É—aya ya share dukkan messages É—in sannan ya lulubo nambar mahaifin nasa amma sau biyu ya buga bata shiga ba, don haka ya nemo ta Mami.
Bugu É—aya kuwa muryarta ta shiga kunnensa.
"Mai gaskiya na, kun taho?"
Ta kira shi da sunan data laƙaba masa tun yarintarsa.
Sai ya sake lumshe idonsa ya koma da baya jikin kujerar lokacin da Ishaq da Baba Sani suka buɗe ƙofofin motar suka shigo.
"Eh Mami, Baffa yana gida kuwa?"
"A'a yana office shima har yanzu. Na bayar direban Hajiya Madina zai kawo muku abinci yanzu, wataƙila ma kuyi daidai dashi."
Wani abu ya motsa a kirjinsa, don yayi kewar irin wannan kulawar tata a Æ´an kwanakin nan, sai dai kafin ya saurari abinda ta cigaba da cewa hankalinsa ya kai ga abinda Ishaq ke cewa cikin wayar sa da aka kira ya amsa.
"To shikenan gamu nan insha Allahu..."
"... Akwai maganar da zamu yi Ma'aruf, nima nafi son ka samu hutu sosai zuwa goben."
Sauran maganar Mamin ta shiga kunnensa bayan Ishaq ya kashe wayar da yake yi."
"Ma'aruf, kana jina kuwa? Da kaci abinci ka sha magungunan da aka baka "
Yaji ta sake faÉ—a lokacin da Ishaq ke cewa Malam Sani...
"Sakataren Baffa ne yakira, wai Baffan yana son ganinmu a office É—insa kafin muje gida, ka juya ta wanna U-turn É—in sai mu koma."
Ba shiri Ma'aruf yaji wani abu ya zarce cikin maƙogwaronsa, don tun bayan farkawar sa sau ɗaya kawai yayi waya da Baffan, a jiya daya kira ta wayar Ishaq, ya tabbatar masa da cewar lafiya yake jin kansa shikenan bai kara nemansu ba, amma ko Baba Usman ya sake kira a safiyar yau kafin su taho.
Yana jin yadda Mamin ke cigaba jero masa tarin tambayoyi ta cikin wayar amma hankalinsa sam baya kanta har Malam Sani yasha kan U-turn din da Ishaq ya nuna wanda zai komar dasu baya zuwa hanyar Office ɗin Baffan, wani ƙaton branch na kamfanin su inda iya ma'aikata ne kawai a wajen.
"Muhammad..."
Muryar Baffan ta kira shi kuma a lokaci guda amonta ya ratsa har cikin kansa bayan sun isa Office ɗin, bayan sun shiga ciki kuma Baffan ya sallami wasu mutum biyu da yake tare dasu a lokacin, sannan bayan Ishaq ya dauki wata wayar ƙarya ya fita don dukkaninsu sun fahimci cewa dashi kadai yake son magana. Don haka ba shiri Ma'aruf yaji maƙogwaronsa ya bushe a lokaci guda, saboda Baffa baya taɓa kiransa da wannan sunan sai idan har wani zance mai muhimmanci zasu yi, kuma rana ta karshe da zai iya tuna ya kira shi da hakan shine ranar da aka daura auren sa.
Ya gyara zama a hankali yana jin yadda Baffan ya cika masa office din ta koina saboda kwarjini.
"Sun turo min da takarda wadda take bayanin ciwon naka."
Ya san takardar shima, sun tura ta email É—insa sannan sunyi printing É—inta a cikin tarin takardun da aka sallamo shi dasu.
"Sun ce a cikin shekaru biyu kawai ciwon ka ya kara haɓɓaka har ya kai matakin karshe, shi yasa abinda kayi ya faru..."
Baffan ya faɗi haka sannan kuma yayi shiru, wannan dai al'adar ta manya. Ƙarar sautin shigowar saƙo daga wayar dake aljihun Ma'aruf ya cika shirun dakin kafin ya cigaba.
"Ko zaka iya gaya min a shekaru biyun baya kana ina Ma'aruf?"
Sai ya gyara zamansa a hankali, yana tuno ranar da Baffan ya naÉ—a shi a matsayin manajan kamfanin 'Bakori Enterprises' ranar da burinsa na farko ya fara cika a duniya.
"Baffa... Shekaru biyu baya shine lokacin da ka bani matsayin manaja a kamfanin nan."
Bai kalle shi ba, amma yaji sanda ya girgiza kansa.
"Ba wannan ba, rayuwarka personally Ma'aruf, kana ina?"
A yanzu ya rikice, yana jin kamar ma bai warke ba gabaÉ—aya, kamar ya sake bin jirgi ya koma asibitin nan ya kwanta.
"Ka manta?"
Ya tambaya amma bai bari ya amsa ba ya cigaba.
"... Bari ni na tuna maka, shekaru biyu baya kana tare da iyalinka Ma'aruf, shekaru biyu baya kana tare da matar da naje na karba maka aurenta har ma da yarinya, a shekaru biyu baya kai cikakken mutun ne mai kamala da mutunci a idon mutane, kuma a tsawon shekarun da kayi cikin wannan mutuncin,  hankalinmu da naka bai taba tashi kamar yadda yayi a yanzu ba."
Wani abu ya zarce a maƙogwaron Ma'aruf, yaji wani ɓangare na ƙwaƙwalwar sa na gaya masa cewa wannan ce damarsa, yau shine lokacin da zai gayawa Baffa abinda shi da ishaq suka dade suna ɓoyewa, yau ya kamata ya gayawa Baffa cewa ba haka bane, abinda ya faru a zamansa da Ruƙayya har zuwa rabuwarsu ba yadda suke tunani bane sam.
"Na san da wannan tunin da nayi maka ka fahimci abinda ni dama duk sauran al'umma suka fahimta Muhammad, don haka kaje ka fara shirye-shirye, nan da wata guda zan karɓa maka wani auren tare da na ƙannenka."
Sai da aka shafe sakanni kafin maganar ta shiga cikin ƙwaƙwalwar Ma'aruf, da wani irin ƙarfin da sai da yayi da gaske kafin ya iya jawo iska ta shiga ƙirjinsa, sannan a karo na farko tun bayan fitar Ishaq ya ɗago idanu ya kalli mahaifin nasa.
Sai dai me? Maimakon fuskar Baffan, sai hoton wajen ya canja a idonsa da wani lokaci da ya faru a shekaru biyu da suka wuce...
Lokacin daya shaƙe wuyan Rukayya da duka hannyensu biyu, yaji ƙarar sautin karkarin da take fitarwa a lokacin da kuma yadda hawaye ke zuba daga idanunta yayin da take kallon ƴarsu da bata fi watanni shida a sannan ba... Babyn da ya karɓe daga hannunta ya wancakalar da ita a cikin falon, kanta ya bugu da kujerar gefe ta shiga ƙwallara kukan daya karaɗe gidan gabaɗaya, wannan sautin kukan da a kowanne daren duniya, dashi yake kwana a kunnuwan sa!
***
Me ya faru shekaru goma da suka wuce?
Wane bincike Ma'aruf ke yi da har ya kai ga tashin ciwonsa?
Wacece Rukayya? Me ya faru da ita da kuma Æ´ar ta?
Sannan wacece amarya ta huÉ—u a bikin iyalan gidan Alhaji Mansour Bakori?
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.
BABI NA UKU.
****
A wannan daren...
NO. 38 Ramie Street, Nassarawa GRA, Kano.
.
A cikin ƙawataccen ɗakin, wata yarinya ta buɗe ƙofar ta shigo, ba zata fi shekaru uku da kaɗan ba, tana sanye da irin kayan yara kamarta, wani ɗan gajeran skirt kalar lemon greeen, (lemon tsami) sai farar rigar da itama akayi mata da ado da irin kalar, gashinta da ba wani yawa ne dashi haka zalika tsawo ba an tufke shi cikin kalba guda biyu da ribbon masu kalar kayan.
Ta karaso cikin ɗakin daya gauraye da sanyin A.cn da aka kai maƙurarta, akwai wani tebur irin na ado dake gaban hadadden gadon dakin, ta kansa ta taka ta isa kan gadon, ta hau tana bi ta kan ƙafafun wadda ke kwance har ta isa daidai fuskarta da ta rufe da bargon data lulliba gaba ɗaya.
"Mammy Mammy Mammy...."
Ta kira ta na bubbuga daidai kanta da Æ´an hannayen nata, a lokaci guda mahaifiyar tata ta yaye bargon daga fuskarta ta buÉ—e idanunta da kyar tana kallonta.
"Menene Hameeda? Me ya kawo ki?"
Ta tambaya ranta a ɓace.
"Mammy I'm hungry. (Yunwa nake ji.)"
Taja tsaki a hankali.
"Ina Nannynki?"
Sai kawai ta miko mata takardar hannunta, kamar ba zata karba ba sai kuma ta yatsunta  biyu ta sakala ta cikinsu sannan ta buɗe ta.
'Ajiya I'm sorry Oo, dey don call me now say my mother dey hospital. I'll return tomorrow by God grace.'
Ta sake jan wani tsakin mai tsayi, bata san sau nawa take gayawa Mary cewar ta daina yi mata pidgin a gida ba, amma don rashin mutunci shine har rubuto mata take yi a takarda.
Ta juya ta sake kallon yarinyar data tsura mata idanu, dogwayen gashin idanunta sun kusa haÉ—ewa da juna, yadda take lumshe su ya tuna mata da fuskarsa a lokaci guda.
...idanunka kake gani ko Ma'aruf? Irin naka ne sak!
Muryar Mami ta haska a cikin kanta ranar farko na zuwan Hameedan duniya, ta tuno fuskarsa, yadda ya kalmashe ta cikin hannunsa, lumsassun idanunsa na haskawa da tarin ƙaunar da kamar wani abu ba zai taɓa giftawa a cikinta ba.
Ruƙayya ta sake yin wani tsakin da ya riga ya shiga cikin dabi'arta kafin ta ture bargon gadon ta miƙe, wata lallausar doguwar rigar bacci ce a jikinta da idan ka kalle ta zaka ga kamar tana zamewa ne tsabar santsi da kuma kyallin da take yi.
Ta kalli agogo wajen karfe bakwai na dare.
"Baki ci abinci bane da rana?"
Ta tambaya tana daure gashin kanta da za'a kwana a yini ana musu da wani akan cewar nata ne, don human hair ne (gashin mutum) da aka dinka mata shi cikin nata ya saje tsaf!
"Mami tun da na sha tea, Mary bata bani komai ba. Waya take ta yi."
Gwarancin yarinyar mai daÉ—i ya fito tana kallonta. Wani tsakin ta sake ja kafin ta dauki wayarta sannan tace.
"Oya, taho muje to."
Da sauri yarinyar kuwa ta sauko tabi bayanta, suka fita daga É—akin zuwa wani dogon korido daya hada fuskokin É—akuna, suka isa wani rantsatstsen falon da komai na cikinsa kalar ruwan gwal ne da kuma makuba, a gefensa akwai matattakalar bene, suka sauka har kasa zuwani falon da yafi wannan girma, ta jikin dining area suka shiga wata kofar da take ta kitchen ce, wani katon kitchen da yake a gyare tas.
Babu ko tukunya guda daya akan gas don haka ta san babu wanda ya dawo a cikin kannen nata uku maza, suma can yawonsu waye ma zai gansu yanzu da magaribar nan? Dama Ashraf mai bi mata ne idan ya dawo daga aiki sau da yawa zai shigo ya dafa abincinsa tun bayan da suka rasa Josh (mai yi musu girki)  yanzu kuma yayi aure sati uku da suka wuce don haka babu mai shigowa kitchen din.
Hameeda ta ɗane kan ɗaya daga cikin kujerun da suka zagaye worktable din kitchen din sannan ta zuba mata idanun tana jiran taga me zata yi, Allah ya sani ita bata son wani girki yanzu, da safen nan fa dawowarta kenan Nigeria daga ƙasar Paris inda suka tafi ita da mahaifiyarta, shi yasa ta kwanta take ta sharɓar baccin ta kuma yanzu ta tashi ta kama girki?... sai kawai ta dago da wayarta ta shiga nemo nambar Mariya, babbar ma'aikaciyar gidan.
"Hajiya barkanmu da safiya. Ina kwana." Muryar dattijuwar ta cika kunnenta, bata ko amsa ba tace.
"Mariya, abinci zaki kawowa Hameeda yanzu, a dafa mata duk abinda zata iya ci kawai."
Daga cikin wayar Mariyan tace.
"Hajiya ai bana gidan, yau kwana na uku a madobi, mahaifina ne ya rasu wallahi, amma su Jamila da Aisha suna nan."
Ta ɓata rai a lokaci guda don ta manta lokacin da suna can taji mahaifiyarta ta na fada, sai kawai tace.
"Allah ya jiƙansa." sannan ta kashe wayar.
Ba zata yarda ƴarta taci abincin waɗannan kazaman yaran ba su tsaya a iya gyaran gidan da suke yi kawai, don ko Mama Mariyan ma da suka saba da ita tun yarintarsu ba kowanne girkinta suke ci ba, tunda Josh ya mutu shikenan kowa ya ta'allaƙa akan siyan abinci a waje tunda dama gidan ƴan maza ne ita kadai ce mace.
"Hameeda me zaki ci?"
"Mammy banda indomie." Ta fadi hakan alamun da gaske ta gaji da cin indomien, haka yasa ta gane cewar Indomie kawai Maryn ke É—ura mata da basa nan don haka ta gyaÉ—a kai kawai.
Ta ajiye wayar akan table din sannan ta juya ta shiga store, ta fito da kwai guda uku a hannunta, ta kunna ruwa a kettle sannan ta fasa kwan ta soya shi cikin ƴan mintuna, ta haɗa mata tea da ruwan zafin da yayi sannan ta ɗauko biredi a fridge ta saka mata kwan a tsakiyar, ta zauna a kusa da ita tana kallon murnar dake kan fuskarta sanda ta fara cin ƙwan, har yanzu bata kai shekara hudu ba amma tsaf ta iya cin abinci da kanta, sai kawai tayi murmushi sannan ta janyo wayarta.
Ta shiga whatapp tana fara ganin yadda messages ke tururuwa har da sababbin nambobi, sai da suka gama tsaf sannan ta danna kan sako guda É—aya mai sunan Jawad da mintuna biyu kawai akayi da turo shi.
"Baby kin dawo ko? I'm badly missing u here... Zanzo anjima kinji." (Ina mutukar kewar ki anan.)
"Mammy nayi missing dinki."
Muryar Hameeda ta katse ta daga amsar da take shirin rubutawa. Ta juyo ta kalle ta, tana ta cin biredin da sauri alamar da gaske yunwa take ji. Itama tayi kewarta da gaske shi yasa ma ta kasa jiran Maamah ta taho. Bayan bikin Ashraf ne suka tafi Paris É—in ita da mahaifiyarta don medical check-up kasancewar hidimar bikin ta wajiga su da yawa, kuma satinsu É—aya acan ta gaji ta taho don ranar da suka tafi ma Hameedan na bacci a hannun Mary ko sallama basu yi ba.
Allah ya sani ta fara gajiya da wannan rayuwar,  ba haka take hango ta ba sam, ba haka ta dinga hango abubuwa ba lokacin da mahaifiyarta dama kawayenta suka bata goyon bayan kashe aurenta ba, Maamah cewa tayi...
"Idan baki fito daga gidan nan ba kin kusa kashe kanki ki tsufa a banza Ruƙayya, ta yaya zaki zauna babu wani isasshen hutu sannan kuma ki fara tara ƴaƴa bi da bi? Yanzu kika fara rayuwar ki fa, kina da dama mai yawa a gabanki Rukayya."
Haka take gaya mata kullum, shi yasa ta rufe idanunta a wancan lokacin ta danne zuciyarta tayi abinda ya fito da ita ɗin, kuma har bayan aurenta da Alhaji Ahmad, tafiya take akan wadannan kalaman na mahaifiyar tata, takunsu take bi har ya kai ga mutuwar aurenta da Alhaji Ahmad ɗin shima, kuma ko a yanzu ma bata fasa gaya mata cewar komai kaddara ce ta cigaba da cin ganiyarta ba, amma ita ta sani cewar bayan wannan ƙaddarar har da ƙaddarar zuciyarta akansa shi ma.
Ta san duk irin halayen da zuciyarta ta shiga a gidan Alhaji Ahmad, ta san duk irin wahalhalun data fuskanta a kowanne lokaci na zamanta a gidan yadda ta dinga kwatanta abubuwa a gidanta na farko da kuma nasa tana ganin bambanci su a baiyane har suka kai ga matakin ƙarshe na mutuwar auren, don Maamah bata taɓa sani bane, amma MA'ARUF shine sanadiyar mutuwar aurenta da Alhaji Ahmad.
Kuma ko a yanzu da kowa ke kwaɗaita mata auren Jawad, ita ta sani cewar abinda ya faru shi zai sake faruwa, babu wanda zai taɓa iya cike gurbin Ma'aruf a ranta, ta so shi tun bata ma san kanta a duniya ba balle ta san menene son, ta so shi da dukkan kowanne bangare na ruhinta, don rayuwarta ma gabadaya tare dashi ta gina ta.
Iyayensu maza abokan juna ne tun da dadewa, saboda haka ba zata taba iya cewa ga ranar data san Ma'aruf ba, tayi wayo ne kawai a duniya tana iya lissafo shi a cikin abubuwan da ta sani na rayuwa, don haka kowa ya sani cewar tsananin kulawar da take yi masa shi ya janyo hankalinsa akanta shima har ya kai ga soyayyar su.
Sai dai a lokacin da ta aure shi, ta auri wani Ma'aruf din ne daban saɓanin wanda ta sani, ta san hakan don yasha gaya mata cewa Ma'aruf din data sani ya mutu babu ko da digonsa a cikin zuciyarsa, amma ta rufe idonta daga komai tace taji ta gani har aurensu ya tabbata.
Auren da tun a darenta na farko a gidan abubuwa suka yi juyin waina daga yadda take hasko su. Ta rufe idanunta a hankali tana tuna dukkan abubuwan da suka faru a waÉ—annan shekarun, irin wahala da barazanar da rayuwarta ta fuskanta, sai dai ashe bata san gwara su sau dubu akan abinda zata je ta tarar a gaba ba, don a yanzu ta gane abinda taso ta manta a baya, cewar duk duniya Ma'aruf ne kadai namijin daya tattara duk wasu halayen da take so a wajen namiji. Shi yasa bata son sake maimaita kuskure na uku a yanzu, bayan guda biyun da tayi a baya na fitowa daga gidansa har kuma da auren Alhaji Ahmad.
Ta riga yankewa kanta shawarar cewa ba zata sake biyewa kowa ba, ra'ayin zuciyarta kawai zata bi, zata samo yadda zata koma cikin rayuwar Ma'aruf kotawacce hanya kuwa, kuma bata ma tunanin cewa hakan zaiyi mata wuya tunda tana da abinda daga shi har iyayensa zai kassara su. Hameeda...
Tayi murmushi tana sake kallon yarinyar, lokaci yayi da a yanzu zata san waye mahaifinta!
***
A wannan daren....
Na baki amanar rai na, daiman
Yau zaki ceton raina, abadan
Kin ƙulle mini kwaɗon raina, da'iman
Ki taho, raina yana sururi numfashina kece abadan dai'man!
"Maryam dan Allah ki kashe waƙar nan, dan Allah."
Amina ta faÉ—a tana hararar rediyon da Maryam din ta kunna, ta jingina ta da langa-langar langar kitchen É—insu yayin da ita take ciki tana girki.
"Haba mana Yaya, kin san yadda nake son irin waƙoƙin nan fa, kuma yanzu zasu cire ma don wani shirin zasu fara."
Maryam É—in ta faÉ—a daga cikin kitchen É—in, kuma jin tayi shiru yasa ta kara da...
"Idan ana yi wallahi ji nake kamar in tashi sama don dadi, da wayarki android ce ai da har sai kin gaji da jin su ma."
Amina ta girgiza kanta daga kan tabarmar da take zaune Hafsa a kwance akan cinyar ta tana tsefe mata kalbar da ta baÉ—e ta tsaf da wani sabon yashi da aka zube a layin nasu inda yara kamarta ke tururuwar wasa.
"Ni basu dame ni ba sam, kawai a yanzu ne ban ga amfanin jin waƙar ba tunda kin san abinda yake faruwa."
Jin haka yasa Maryam ɗin tayi shiru tana cigaba da yanka cabbage ɗin dake hannunta, kuma a daidai lokacin ma suka cire waƙar, muryar wani ma'aikaci daga gidan rediyon ta fara gabatar da shiri na gaba a jerin shirye-shiryen su, amma tuno abinda ke faruwar kamar yadda Amina tace, yasa Maryam ta ajiye wuƙar hannunta ta taso ta kashe rediyon gabaɗaya.
A jiya da Baba ya fita zuwa kiran Hajiya Kilishin da yace, bai dawo ba sai wajen sha ɗaya saura na dare har su Hafsa da Adam sunyi bacci a sannan, wanda hakan wani abu ne sabo a wajensu, wani abu daban, saboda ba don sun kira shi a waya har ya ɗauka ba ma, Amina ta san tsaf Amma zata iya saka hijabinta a daren  ita da Aminu su fara tafiya nemansa.
Shi ba mutum ne mai dadewa a waje ba musamman idan dare yayi, abubuwa da yawa komai muhimmancin su in har dare ya raba to zai ajiye su ne sai zuwa gobe, ko hirar maza irin ta daren nan Baba baya taɓa zaman yinta, tun suna yara sun taso da sanin cewa lokacinsa da daddare nasu ne, a cikin iyalansa zai zauna ayi wasa da dariyar da a cikinta zai fahimci dukkan matsalolinsu.
Don haka a jiyan da ya kai goma sha ɗayan dare dole zuciyoyinsu suka kasa nutsuwa sai lokacin da suka ji ƙarar shigowarsa da kuma rufe kofar gidan da yayi, babu wuta a lokacin, sannan Aminu ya fara tararwa jingine da bango yana danna wayarsa.
Kuma ta cikin É—an hasken fitilar tsakar gidan da batiranta suka gama yin sanyi, Amina ta hangi fuskarsa tattare da dukkan wani nau'i na damuwar dake fitowa har a cikin sautin muryarsa sanda yake amsa gaisuwarsu, gaisuwar da daga ita bai sake cewa komai ba, ya nufi hanyar É—akin sa kawai ya shige.
Amma ta ɗebi kwanukan abincinsa ta bishi dasu yayin da suma kowa ya kama hanyar makwancinsa, Aminu yayi hanyar soro inda ƙofar ɗakinsu shi da Adam take, su kuma suka dauki Hafsa suka shige nasu dakin, kuma ba sai ta tambaya ba, Amina ta sani daga ita har Maryam da Aminun babu wanda yayi baccin kirki a ranar. Kuma babban abinda ya ƙara tsurar dasu shine na yadda har a yau basu ji komai ba, ko daga bakin Amman kuwa.
Baban bai ko je aiki ba a yau, tun safe ya fita zuwa gidan wansa da suke kira da Kawu mallam kuma bai dawo ba har yanzu, Amman ma kusan a daki ta yini tun bayan fitarsa, ita kadai tayi ta kai kawo a gidan bayan sun tafi makaranta, tace mata wai gyaran durowarta take yi, amma tsaf Amina ta sani cewa kayan nata data barbaza akan katifar ɗakinta ba don ninki ta fito da su ba saboda yanayin dake fuskarta kusan iri daya ne da wanda ke kan fuskar Baba tun a jiya da daddare, kuma wajen la'asar sai ga kiran Baba a wayar Aminan cewa Amman taje ta same shi a gidan Kawu mallam ɗin, wanda hakan shine abinda ya ƙara ɗaga hankalinta, da ƙyar Aminu ya shawo kanta bayan sun dawo daga makaranta kafin ya tafi wajen aikinsa shima.
Sai dai kafin ta bawa Maryam amsa, Adam yayi sallama yana shigowa.
"Salamu alaikum, wallahi Yaya yarinyar nan ƙarya take, babu wanda ya ture ta, wasan banzan su kawai suke yi, ga sauran ƙawayen nata can ma har yanzu a  kusa da yashin."
Ya zayyano dukkan wannan bayanin daga tsaye kasancewar shi yaje ya zaƙulo ta tsakiyar masu wasan yashin. Da jin haka kuwa Hafsa tayi narai-narai da muryarta ta shiga rantsuwa tana faɗin da gaske ture ta akayi ta faɗa kan yashin, wanda kowa ya san ƙarya ne wasanta tayi daga yadda baƙin gashin kan nata ya burɗine tsaf da ƙasa.
"Ko baki ɓata kanki ba meye amfanin zuwa wajen yashi da magriba Hafsa?"
Amina ta faÉ—a a hankali tana kama wata jelar, don ita ko kaÉ—an ba ta fadan nasu take yi ba, jikinta ne kawai zaune a gidan amma hankalinta ruhinta zarya kawai suke a hanyar gidan Kawu mallam kamar tururuwa, shi yasa ko girkin daren ma tace Maryam tayi.
Allah ya sani abu na ƙarshe da zata so a yanzu shine wata matsala ta sake gifta musu, rayuwarsu ta haska da kaloli mabanbanta a shekarun baya, sun fuskanci abubuwan da ko a labari basa son tunawa, kuma har yanzu ƙoƙarin tashi suke, ƙoƙari Baba yake don ganin rayuwarsu ta daidaita ko da ba kamar a baya ba, don haka ta yaya zasu taɓa son ace sai sun sako daga farko idan wani abu ya sake gifta musu ya a yanzu...
Har sai da ta gama wankewa Hafsa gashin nata da karkashi sannan Amma ta dawo, Baba kuma bai shigo ba sai bayan sallar isha, wanda kafin ayi hakan har Aminu ya riga su dawowa, a tsakar gidan ya tarar dasu tana sake yiwa Hafsa wata kalbar bayan ta wanke matta kan, yayi wanka yazo ya zauna a cikinsu shima yana ta mita da tsokana akan girkin da Maryam É—in tayi, jollof din shinkafa da taliya ce da ko a ido tayi kyau, amma tunda ya zauna yake sukar abincin yana kuma kai loma.
"Wallahi akayi miki aure kika je kina irin wannan abincin sati daya zaki yi ya koro ki, ace jollof amma ba mai sa faman kora ruwa nake kamar dambu nake ci."
An kawo wuta a lokacin don haka tsakar gidan yayi tar da wasu sababbin ƙwan fitilar da ya haɗa da kansa ya saka musu. Maryam da a lokacin take wanke uniform dinta daga can bakin famfo tace.
"A haka babu man kake ƙoƙarin tayar da plate din ai."
"To idan ina jin yunwa ya zanyi? rufa miki asiri kawai nake ma wallahi, don yanzu ina tafiya wajen Isah (mai shayin layinsu) kowa sai ya gane cewar a gidanmu ba'a iya girki ba kenan, kinga masu kokarin zuwa nan gaba ma sai su fasa. Kuma Amina ita ta riga ta samu kece a ruwa."
Maryam ta juya bayanta amma yana ganin adadin yadda gefen fuskarta ke juyawa wajen murguÉ—a baki tana faÉ—ar wasu abubuwa da ba jin su yake ba. Yayi murmushi yana sake faÉ—in.
"Hotonki zan nemo a wayata in maida shi fari da baki in rubuta ga matar da akan girkinta aka ƙirƙiri sunan abincin 'Ci kar ka mutu, 1987.'"
Bai saurari abinda take cewa ba ya juya ya kalli Amina da bata sanya baki a hirarsu har yanzu ba, ganin damuwar dake kan fuskarta har a lokacin ya dawo da hankalinsa kanta sosai.
"Wai har yanzu damuwa kike? Nace miki fa ki kwantar da hankalinki tun dazu. Ni alamar ma da na gani kamar wasu maƙudan kuɗi Baba ya samo shine aka tafi gidan Kawu mallam ɗin ake ta faman lissafi."
Ba shiri dole Amina tayi murmushi tana kallonsa.
"Aminu Allah ya shirye ka, komai sai ka maida shi wasa wallahi."
"To me yasa zaki yi ta damun kanki akan abinda bai ƙaraso ba tukunna."
Ya faÉ—i hakan sanda ya juyo, idonsa ya kai kan hannun Maryam dake ta cuÉ—a kayan wankinta.
"Ke, idan kinyi ƙunshin nan ma haka zaki cigaba da irin wannan wankin? Kwana biyu ya goge? Kuɗina zaki taso ki dauko min Allah indai haka ne."
"Kudin ka ai sun riga sun shigo kenan wallahi baza su dawo ba, sai dai idan nayi ƙunshin ka kankare shi."
Amina ta kalli yadda yake murmushi yana kallon Maryam din, ta san shima ya damu, watakila damuwar ma har tafi tata, amma haka Aminu yake a kodayaushe, shi mutum ne da zai sa kaji kamar baka da wata matsala koda kuwa kana nutsewa a cikinta ne tsamo-tsamo. Lokacin da Baba ya shiga tashin hankalin karayar arziƙinsa, Amma tace Aminu shi ya ɗauki kaso mai yawa bayan addu'a wajen dawo dashi daidai.
A daidai lokacin Amman tayi sallama ta shigo, kuma kallonta kawai Amina tayi taji gabanta ya faÉ—i duk duk da cewar yanayin damuwar fuskar tata ya ragu akan da safe.
"Haba Amma kun barmu sai kace marayu a gidan nan, ko shirin yaƙin duniya kuka tafi yi yaci ace kun gama."
Duk da yanayin Amman sai da tayi wani guntun murmushi tana girgiza kai sanda suka shiga yi mata sannu da zuwa, don ta saba a irin lokutan wasansa, Aminu ya riga ya mayar da ita kamar kakarsa.
A lokaci guda sai komai ya dawo daidai a gidan, da duk yawansu ji suke kamar a cikin wani fanko suke, Adam ya dawo daga siyan wainar fulawar da Maryam ta aika shi, Aminu ya kafa ya tsare cewar sai yaci rabi don wai ya san da kudinsa ta siyo, duk dauriyar Maryam sai da ta rufe idaninta ta fito da duk masifar dake cikinta wanda dama abinda yake jira kenan don haka shi da Adam suka dinga kyalkyala mata dariya.
Sannan a ƙarshe bayan sun shiga falo, wani film din indiyan da ake yi a tashar Bollywood ya ɗan daukewa Amina hankali daga wannan damuwar ganin cewar Amman ma har ta sake tana kokarin sakawa Hafsa maballi a wuyan rigar makarantar ta, tana yi tana mitar yadda Hafsan ke yawan yar da maɓallan rigar.
Falon ya É—auka da sautin wakar film É—in da ake yi lokacin da take ke kallon fuskar kowa tana murmushi, yadda Hafsa ta zuba manyan idanunta tana saurarar kashedin da Ammar keyi mata akan maballin, da yadda Aminu da Adam ke cigaba da dariya tsokanar Maryam da bata ganewa ta daina biye musu, har ma da idanun Maryam É—in da suka cika da haushi fal! Haka take so... Haka take so rayuwa ta kasance musu a kodayaushe.
Sai dai rayuwar bata taɓa biyewa muradan zuciya, ita da zuciyar ma sunyi hannun riga, ƙaddara take kallo a kodayaushe tana bin takunta, don a lokacin da Baba ya dawo bayan sallar isha a lokacin komai ya ruguje, zuciyar Amina ta sake ruftawa cikin ramin da yafi wanda ta fito daga cikinsa zurfi. Su Hafsa suna makarantar dare a lokacin, Aminu kuma ya fita wajen abokansa sannan Maryam da wata ƙawarta sun tafi bakin titi wajen mai yin zayyanar allo kasancewar suna dab da yin sauka a islamiyya, gidan ya rage sai ita kaɗai, kamar dama ƙaddarar ta zaɓi wannan lokacin ne don ita kadai ɗin.
Amma ta kira ta zuwa É—akin Baba lokacin da take kokarin haÉ—a kan kitchen É—insu, kiran daya tabbatar mata da cewar abinda take jira ne zai kasance kuma a hanyar zuwan tunanin ta ya É—an É—aure don a zaton ta ita da Aminu ya kamata su zayyane wa komai.
Ta shiga ciki lokacin da Baba ya rufe flask din nasa abincin da ya gama ci, ta zauna a daidai saitin Amma da har a lokacin ta kasa tantance yanayin fuskarta.
"Amina jiya da naje gidan Hajiya Kilishi aurenki na bayar ga É—ansu."
Maganar ta fito daga bakin Baban kai tsaye ba wane shamaki balle kewaye kewaye, kuma ta tafi kai tsayen har zuwa cikin ƙwaƙwalwar ta, sai dai bata nutse ba, zagaye kawai ta dinga yi a zaman kan nata kamar mai jiran a buɗe mata ƙofar shiga.
Shiru ya ratsa ɗaukacin dakin, shirun da a cikinsa Amina ta kasa ko zuƙar numfashi, kuma bata damu da tsayinsa ba don har a lokacin bata gane maganar da Baban ya faɗa ba, shiru kawai tayi kamar bata ji shi da farko ba a yanzu take jira yace wani abu, sai da shi da kansa yaga bata da alamar magana sannan ya sake kiran sunanta.
"Amina.."
Ta kuwa É—ago ta kalle shi, da idanunta dake haskawa a cikin hasken fitilar É—akin, sai ya cigaba shima kamar bai fadi maganar farko ba.
"Jiya da naje gidan Hajiya Kilishi da mijinta nayi magana ba da ita ba, kiran nasa ne ba nata ba, don da na isa gidan mota kawai tasa aka É—auke ni aka kaini har ofishin mijin nata.
Acan na tarar dashi tare da ƙaninsa, mutane ne manya-manya Amina masu mutunci da kuma kwarjini, kuma kai tsaye suka shaida min cewar aurenki suke nemawa ɗansu, yace min Hajiya Kilishin ita da kanta ta roƙe shi alfarmar hakan saboda yarda da hankali da kuma tarbiyar da muka baki. Al'amarin ya girgiza ni kamar yadda kika ji shi a yanzu kema, amma wallahi a wannan lokacin ba zan iya kallon idanun wadannan mutanen ince musu 'A'a' ba don bani da wata hujja ko dalilin da zai sa in faɗi hakan..."
Ba fahimtar abinda yake faɗa Amina take ba har a lokacin, kallonsa kawai take tana jin yadda muryarsa ke karyewa da kowacce kalma daya fada, mahaifinta mutum ne da ta sani jajirtacce, ko a lokacin da yake cikin tashin hankalin karayar arziƙinsa, baya taba fasa binsu da alkawuran cewa zai inganta rayuwarsu don kar su karaya da komai. Amma a yau kiri-ƙiri take jin duk wata amon karaya a muryar tasa, amon da take ji yana bin jijiyoyin ta yana tayar da tsigar jikinta bi da bi ta kowanne ɓangare.
"Na san karatu ne a ranki Amina, kuma na san ba sau daya ba sau biyu ba na sha yi miki alƙawarin cika miki wannan burin amma a kullum abinda muke tsarawa daban, wadda ƙaddara ta tanadar mana daban, kuma na san ba sai nayi miki bayanin wannan ba don a ƙananun shekarunki kin gan kalolin ƙaddarar mabanbanta, shi yasa nake son ki kalli wannan ɓangaren ƙaddarar ma, ki kalle ta idanun rahma Amina, Allah ya sani a zuciyata na yarda cewa ban miƙa ki inda zaki wahala ba, don komai halin da zan shiga a duniya ba zan yarda da duk abinda zai cutar daku ya matso kusa ba balle har in kai ku da hannu na.
Kin san Hajiya Kilishi kin san kirkinta, kin san yanayin gidanta, ina ga kinje kusan sau biyu ke da mahaifiyarki, saboda haka Amina wallahi zuciyata bata bani cewa zaki wahala a wannan wajen, damuwata kawai shine yunƙurin rushe miki burin ki da nayi da kuma cewar na yanke hukunci a lokaci guda."
Yayi shiru a lokacin, Amina ta haÉ—iye wani abu a makogwaron ta da bata san sunansa ba, maganganun Baba a gefe suke daga cikin kanta, har a yanzu damuwar dake cikin muryarsa itace a gabanta, ita take lissafawa tana son kirga adadinta. A hankali ta juyar da idanunta kan Amman dake zaune a saitinta, kuma a hankalin idanunta suka fahimci abinda ta kasa ganewa a fuskar tata É—azu, damuwa ce fal ke yawo a cikin nata idanun!
Wani abu da ya ƙara rikita tunaninta a lokaci guda... Don bata taba tunanin cewa irin wannan maganar ce zata saka Amma cikin damuwa itama ba, idan har zata iya tunawa tun farko dama ita tafi son zancen aurenta akan karatun da take naci, kawai ganin cewar daga ita har Baban akan son karatun suka tsaya yasa ta sallama itama, amma duk da haka tasha gaya mata cewar ba ba lallai sai ta gama karatun zata yi aure ba, to me yasa wannan maganar zata dame ta?
Sai ta sunkuyar da kanta ƙasa sannan ta gyara zamanta a hankali, tana jin nauyin idanun iyayen nata biyu dake kallonta, so take tace musu in har wannan ne abinda ya tashi hankulansu a gidan tun jiya to su kwantar dashi, don a cikin aure da zancen rashin karatun tana jin ba wanda na zata iya daurewa ba don farin cikinsu.
"Baka ƙarasa zancen naka ba ai Mallam, baka gaya mata abinda yafi komai muhimmanci ba."
Kamar saukar ruwan sama a lokaci guda muryar Amman ta faɗa, kuma a lokaci gudan Amina taji gabanta ya faɗi, abu muhimmanci tace, kenan wani abu ne daban, wani abu da yafi girman abinda ya faɗa, wani abu da wataƙila shine dalilin damuwar dake kan fuskar Amman da ma zuwansu gidan Kawu mallam a yau.
Taji Baba ya sake gyara zamansa sannan ya kira sunanta.
"Amina..."
Ya kira kamar tayi nesa dashi, kuma ta san me hakan ke nufi saboda haka da sauri ta ɗago idanunta daga kan ƴan yatsunta ta kalle shi, ƙaguwar ya furta abinda zai faɗa na haskawa tar a cikin idanunta.
"Kiyi hakuri Amina, amma sun shaida min cewa yaron yana da matsalar taɓin hankali!"
A daidai sanda ya rufe bakinsa, a daidai lokacin aka haska wata walƙiya har da tsawa a cikin ɗakin!
***
A wannan daren....
Wajen ƙarfe tara saura a lokacin da wata mota ƙirar kamfanin 'Elantra' ta shigo cikin layin, ƴan yara maza dake wasa akan hanya suka dinga darewa da gudu cikin wasansu suna bawa motar hanya kasancewar faɗin layin ba zai yiwu ta wuce kuma suna wajen ba. Ko'ina yayi tar da wutar nepar da aka kawo don gaka ƙyallin sabubtar motar haskawa kawai yake yi a idanun mutane kamar an shafe ta da maiƙo.
A cikin motar saurayin dake zaune a kujerar gefe mai suna Jamilu ya nuna ƙofar wani guda inda hasken jan kwai ke ci a samansa.
"Wancan ne gidan yallaɓai, in dai gidan Alhaji Sulaiman ɗin daka kwatanta min ne to shine gidan."
Ma'aruf dake rike da sitiyarin motar a gefen sa ya gyada kai a hankali yana kallon ƙofar gidan shima.
"Nagode sosai kaji."
Saurayin ya washe baki.
"Ah haba yallabai ai ba wani abu wallahi. A sauka lafiya."
Ya faɗi hakan da tsantsar murna yana ƙara rike sababbin kudin da Ma'aruf ɗin ya danka masa tun lokacin da ya shigo motar, a can farkon layin ya dauko shi, cikin dandazon wasu samari a inda ake sayar da rake. Kuma duk yadda ya kai ga kwatanta musu gidan Alhaji Sulaiman ɗin da yake nema, saurayin ne kaɗai ya gane don haka ya roƙe shi yazo ya ƙarasa dashi.
Saurayin ya rufe ƙofar motar daidai lokacin da kira ya sake shigowa a wayarsa, tun dauko shi dama ake kiran wayar kuma daga nambobi biyu kawai Ishaq da Mami, yana kallon yadda saurayin ma ke ta kallon wayar tun da ya shigo idanunsa na haskawa da mamakin cewa me yasa ba zai ɗauki kiran ba.
Ya ƙyale wayar yayi gaba a hankali zuwa daidai kofar gidan da yake kallo ya tsayar da motar daga gefe sannan ya janyo ta.
"Ma'aruf kana ina? Ina ka tafi?" Muryar ishaq ta fito a lokaci guda da ya amsa, sai ya koma da baya ya jingina kansa da kujerar motar sannan yayi murmushi.
"Kana magana kamar kana neman wani yaro É—an karami, sau dubu nawa a rayuwata na É—auki mota na fita da daddare Ishaq?"
Yaji yadda Ishaq din ya fitar da numfashi cike da takaici.
"Wai ka haukace ne gabadaya Ma'aruf? Yanzun nan fa muka dawo ƙasar nan, minti biyar kawai kayi a gida kayi wanka ka fito! Yanzu ƙarfe nawa? Tara fa ta wuce, ta yaya zaka ɗauki mota ka fita a halin da kake ciki?"
Ya sanya ɗaya hannunsa ya cusa yatsuntsa cikin gashinsa yana tuno abinda ya faru bayan barinsu Office ɗin Daddyn, tsaf ya zayyanewa Ishaq abinda Daddyn ya shaida masa tun a hanya kafin su ƙarasa gida, kuma zai iya rantsewa kamar yadda maganar ta tsorata shi haka ta daki Ishaq ɗin shima, amma duk da haka ya boye ta hanyar gaya masa cewa ya kwantar da hankalinsa kawai insha Allah zasu daidaita komai a hankali, wasu maganganu da jinsu kawai yayi a lokacin da yake furtawar.
Don suna shiga gida wanka kawai yayi ya shirya cikin wasu riga da wando duka kalar baki sannan ya dauki wata rigar mai hula (hood) da dogon hannu ita kalar ruwan toka ya dora akai, ya rufe kansa da hular amma duk da haka ana ganin sumar kansa data taru itama baƙa wuluk da ita kamar kayan.
Lokacin da ya fito falo Ishaq ya shiga wanka shima, don haka wayarsa kawai ya dauka da muƙullin motar Ishaq ɗin yayi waje, don shi tasa motar tana can gida ba'a dawo da ita ba tun ranar da al'amarin ya faru (lokacin da ya ɗauko mutumin da yayi wa duka daga Office ya kaishi wajen Daddyn.)
Ya tabbata Ishaq yaji lokacin da maigadi ya buɗe masa gate ya fita, don bai ko bar kan layinsu ba kiransa na farko ya shigo, amma bai dauka ba, sai da ya katse sannan ya lalubo nambar Sameera a cikin wayarsa ya kira. Sameera itace kusan komai na gidan nasu don itake kula da kusan harkar komai a gidan, shi yasa duk wanda zaiyi wani abu sai ya neme ta, saboda haka ya sani duk wani information in dai ya taɓa ratsawa da gidan ba lallai ne taƙi samunsa ba.
Daddy ya gaya masa cewa mahaifin yarinyar da suke zancen zata shigo rayuwarsa É—an'uwan Mami ne kuma sunansa Alhaji Sulaiman.
Don haka kai tsaye bayan Sameeran ta gama murnar dawowarsa da kuma shaida masa cewar ai direban Hajiya Madinan da yayi clear dashi kafin ya fito titi zai kawo musu abinci yanzu, sai ya tambaye ta.
"Waye Alhaji Sulaiman a Æ´anuwan Mami?"
Shirunta ya nuna alamun tambayar ta bata mamaki amma duk da haka mamakin nata baiyi tsawo ba tace.
"Ko wanda yazo jiya? ÆŠan'uwansu Hajiyar Mami ne, yana É—an zuwa dai ba sosai ba."
Ya cije gefen lebbensa kafin ya sake tambayarta.
"Da yazo jiyan me yayi?"
"Bai wani daÉ—e ba Yaya, Mallam Sani ma aka saka ya tafi dashi office É—in Daddy wai zasu yi magana."
Da jin haka ya tabbata shine wanda yake nema don haka kai tsaye ya sake tambayarta.
"Kin san gidansa?"
"A'a, amma Mami tace a Gadon ƙaya yake wai wajen layin transformer."
Ya gyada kansa.
"Kin san sunan Æ´aÆ´an sa?"
"Eh, Babbar dai kawai na sani sunanta Amina."
Ya riga ya gama samun abinda yake so don haka ya gyada kansa kawai yana gode mata sannan ya kashe wayar, kwatancen daya kawo shi har kofar gidan kenan a yanzu.
"Ina Gadon ƙaya."
Ya bawa Ishaq amsa ta cikin wayar.
"Gadon ƙaya? Wajen wa? Me zaka yi?"
"Ni da kai mun sani cewa abinda Daddy ke shirin ba ƙaramin hadari bane Ishaq, don haka zuwa nayi na warware komai tun kafin lokaci yaja da abinda ba zai taba faruwa ba."
"What?" Ƙarara mamaki da kuma fargaba suka fito daga muryar Ishaq ɗin, kuma Ma'aruf zai rantse ya shiga girgiza kansa lokacin da yake faɗin.
"Kar kayi haka Ma'aruf dan Allah, ka juyo ka dawo. Zuwa wajen mutumin nan ba shine zai kwance komai ba..."
"Ba wajensa nazo ba don dashi da Daddy duk abu É—aya ne. Ita nazo gani Ishaq, saboda a yanzu maganar ta koma ni da ita kawai."
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un... Ma'aruf me zaka yi?"
Salatin ya saka shi sake yin murmushi yana cije lebbensa.
"Nuna mata zanyi irin ramin da ake shirin jefa ta, nuna mata zanyi da gaske bani da hankali."
"B, tsaya kaji..."
Dib. Ya katse kiran ya ma kashe wayar gabaɗaya. Idonsa ya sake kallon ƙofar gidan yayin da zuciyarsa ke zana masa dukkan hotunan abinda zai faru kafin ya kashe motar ya fito.
Ya sake janyo hular rigar yana ƙara rufe fuskarsa daidai lokacin da wasu yara biyu mace da namiji suka zo shiga gidan idanunsu akan shi da kuma motarsa. Da sauri ya yafito namijin alamun yazo.
Ya kuwa taho yayin da macen ta tsaya tana kallon su hannunta rike da wani abu da take ta lasa.
"Bigboy ya sunanka?" Amon muryarsa mai zurfi da taushi ya tambaya sanda yaron ya ƙaraso.
"Adam."
Ya gyada kansa yana murmushi lokacin da ya zaro wata sabuwar ɗari biyar daga aljihunsa yana miƙo nasa.
"Idan ka shiga gidan nan Adam kace wai Amina tazo."
"Toh."
Ya amsa da nasa murmushin shima sannan ya juya, idanunsa ko kaÉ—an bama su ga kuÉ—in da yake bashi ba.
Da murmushin da bai san dalilinsa ba Ma'aruf ya maida kudinsa cikin aljihu yana kallon tafiyarsu zuwa ciki, Æ´ar yarinyar har sai da sake juyowa ta kalle shi lokacin da Adam É—in yaja hannunta zuwa ciki.
A hankali ya dawo da fuskarsa kan katangar gidan, idanunsa na hasko masa dukkan abinda zai faru nan da mintunan dake shirin tahowa!
***
Me zai faru??
Me zai faru??
.
.
.
Me Ma'aruf zaiyi??
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.
BABI NA HUDU.
~~~~~
"Kiyi hakuri Amina, amma sun shaida min cewa yaron yana da matsalar taɓin hankali!"
A daidai sanda ya rufe bakinsa, a daidai lokacin aka haska wata walƙiya har da tsawa a cikin ɗakin! Kuma bayan walƙiyar ta ɗauke a idanun Amina, Baba ya cigaba da maganarsa.
"Wannan maganar ita ta sanya a safiyar yau dana shaidawa Kawu mallam dukkan abinda ya faru ya tara meeting din da ya sanya yinin mu a gidan, don har su Kawu Ibrahim da Kawu Hamza sun zo a yau..."
Ba shiri tasirin sunayen ya sanya Amina ta sake ɗago da idanunta ta kalli mahaifin nata, yayyen Baba hudu ne kuma shine ƙaraminsu, Daga Kawu mallam sai Kawu Abubakar da suke kira da 'Baban kurna' sai kuma Kawu Ibrahim da Kawu Hamzan da dukkansu biyun suke zaune a garin Abuja tare da iyalansu, don haka bata san adadin mamakin da zata iya kiyastawa ba na cewar saboda maganarta Kawu mallam ya taso su a yau tun daga can suka zo, ganin yadda Babn ke kallonta yana son fassara yanayinta yasa ta maida idanunta ƙasa a hankali yayin da hannunta na dama ya kamo karshen skirt dinta da ƙarfi.
"Amina a jiya babu irin boren da mahaifiyarki bata yi min ba akan maganar nan, dukkan ku shaida ne cewa Halima mace ce mai biyayya gare ni, don tun daga ƙuruciyarku har yanzu babu ranar da ɗayanku zai ce kunji kanmu ni da ita game da wani al'amari a gidan nan, duk abinda na fada ko nayi daidai ne a wajenta, amma a karo na farko jiya mahaifiyarki ta bijire min akan wannan hukuncin, tace bata yarda ba, tace ba ni kadai na haife ki ba itama tana da nata haƙƙin akanki don haka ba zan siyar dake ga wasu mutane ba kamar yadda ta fassara al'amarin.
Kuma bayan zuwan su Kawu Ibrahim a yau sai suma duk suka goyi bayanta, da ni da Kawu mallam da Baban kurna Amina mune kadai muka hango wannan al'amarin ta fuskar alkhairi da kuma cigaban ki wanda su basa gani. Don haka na san a shekarunki da kuma hankalin yabzu zaki iya banbance daidai da akasinta, don haka muka yanke cewar matsayar tana gare ki yanzu, duk ɓangaren da kika zaɓa shi zai fi rinjaye kuma maganar ta zauna kenan har abada, kar ki ga cewar na amsa musu acan, ki faɗi ra'ayinki Amina babu wanda zai taɓa ganin laifinki don rayuwar ki ce, mu duk ƴan kallo ne kawai.
Don haka kije kiyi tunani daga yau zuwa gobe, saboda idan har ɓangaren mahaifiyarki kika ɗauka, ina so ne muje mu sami mutanen tare da su Kawu Ibrahim kafin su koma kuma kafin wani abu ma daga ɓangarensu yayi nisa. Kije kiyi tunani Amina."
Shikenan! Shikenan sai duk bayanin ya ƙare da wannan jimlar, lokaci kuma ya fara bugawa da adadin awannin da zasu tadda goben, goben da Baba ta furta kamar tsawonta na shekara guda ne.
Taji lokacin da ya miƙe ya zo ya wuce ta, taji shi ya zura takalmansa daga waje sannan taji ƙarar takunsa na nufar hanyar soro, sai kawai ta rufe idanunta gabaɗaya tana hadiye wani abu da bata sanshi ba a maƙogwaron ta.
"Duk abinda mahaifinki ya fada haka ne ya faru Amina, kuma ba komai yasa nayi hakan ba sai don nemar miki Æ´ancinki..."
Da wani sassanyan amo muryar Amma ta maye gurbin ta Baban tun kafin ta bude idanunta
"... Ƴancinki nake nemar miki Amina, don ni na hango abinda mahaifinki ya kasa ganowa, mutanen nan masu kudi ne da gaske, kuma duk tsananin kirkin mai kuɗi a zaune yake cewar baya taba son mu'amalar rayuwarsa da talaka kamar mu, zasu taimaka, zasu yi zumunci kamar yadda ita wannan Hajiya Kilishin ke yi amma aure Amina, aure babban abu ne da shine linzamin rayuwarka ta duniya har zuwa lahira, don haka kowa ya sani cewa hakan ba ƙaramin abu bane ga rayuwar mutum da zai haɗa shi da kowa.
Da ke muka je auren wani ɗansu a shekarun baya da suka wuce, kinga matar daya aura ai, kinga irin tarin dukiyar ubanta da danginsu, don ba a banza bahaushe ke cewa 'ƙwarya tabu ƙwarya ba... Kowa daidai dashi yake nema. Saboda haka Amina ko makaho yaji wannan zancen ya sani cewa mu ba daidai da mutanen nan muke ba, sun nemi aurenki ne kawai don son zuciyarsu..."
Sai tayi shiru kamar tana kokarin haɗewa wani abu da ya taso mata ƙirji yayi sanadiyar canjawar muryarta.
"Amina, ciwon yaron nan na 'Hauka' ne na tabbata suka yi masa ado da matsalar ƙwaƙwalwa kawai, kuma kin san wannan ba ƙaramar magana bace, kowa ya sani, su ma sun sani shi yasa basu tunkari kowa da wannan zancen ba sai mu, mu talakawa da aka mayar kamar ba mutane ba, mahaifinki dasu Kawu mallam suna ta danganta al'amari da ƙaddara, alhalin basu ƙara binciken komai akan yaron nan ba, amma ni nace idan har ƙaddarar ce me yasa basu kai ta ga irin ƴaƴan masu kudin da ɗaya ɗan nasu ya aura ba? me yasa sai a yanzu ne irinmu zasu yi musu amfani... Na sha gaya miki masu kuɗi basa kallon kowa sai kansu, suna ganin talaka kamar shi ya zaɓawa kansa rayuwar sa, kamar dama Allah ya halitto shi ne kawai don ya kawar musu da matsalolinsu.
Rayuwarki zaki sadaukar musu idan har kika zaɓi tafiya Amina, don aure ba karamar gwagwarmaya bace ko da mutum mai hankali kuma wanda kake so balle babu duk biyun a naki, rayuwarki zaki sadaukar musu a banza, dukkan wani mafarki da burinki sai ya mutu wajen yi musu bautar da baza su san kina yi ba, don wannan sigar auren a wajensu, bata da banbanci da cewar siyen ki suka yi..."
Ta sake yin shiru sakamakon yadda Aminar ta runtse ido da tasirin maganar, amma duk da haka sai ta cigaba.
"...Annabi yayi gaskiya da yace kudi sune masifar ƙarshen duniya, a karo na ba adadi wallahi na sake yarda da hakan, don ban taɓa tunanin cewa mutum kamar mahaifinki zai iya faɗawa cikin tarkonsu ba..."
Wannan karon kalaman suka daki zuciyar Amina da tasirin da yasa a lokaci guda ta ɗago ta kalle mahaifiyar tata tana girgiza kai. Ta sani dukkan abinda ta faɗa gaskiya ne, amma ba ta yarda da wannan hasashen nata na ƙarshe ba, ba zata taɓa yarda cewa kuɗi zasu rufewa Baba ido har ya mika ta ga inda zata cutu ba, haba mana! ta manta ne? Ta manta duk wannan tarin ƙaunar tasu dake tare dashi? Ta mata tarin sadaukarwar da yayi a rayuwarsa saboda su kawai?
Sai dai kallon da Amman ke mata yasa ta sake sunkuyar da kanta a hakali tana rufe idanunta da ƙwalla ta taru a cikinsu, dukkan maganganun da Amma ta fada gaskiya ne ta sani amma har a lokacin ta kasa gasgata zancenta na karshe don ta sani cewa ko da numfashinta na ƙarshe a duniya ne zata yarda cewa ba zai taɓa mika ɗayansu ga inda zasu cutu ba... A kullum shi mai son gyara rayuwarsu ne.
Ta kai hannu tana share idanunta lokacin da Amman itama tace.
"Kije kiyi tunani zuwa goben Amina, ki auna kowanne ɓangare ki ga wanda yafi rinjaye, ni dai a matsayina na mahaifiyarki kuma mace kamar ki na gaya miki abinda nake ganin shine daidai"
Ta rufe bakinta daidai lokacin sallamar su Adam daga makarantar dare ta kwararo a tsakar gidan. Shi da Hafsa ne suka karaso har cikin dakin bayan sun duba falon da babu kowa, da sauri Amina ta saka bayan hannunta ta share hawayenta kafin su ƙaraso da hayaniyarsu.
"Amma kaina ciwo yake yi." Muryar Hafsan ta ambata tun kafin ta shigo ɗakin da kalar ƙorafinta na kullum yayin da Adam shima ya shiga ƙaryata ta.
"Amma wallahi makaranta ce bata son zuwa gobe ƙarya take yi, yanzun nan fa har kusan faɗa fa suka yi ita da wasu a wajen ƴar tsohuwa, ba don nazo da wuri ba da ko kafi-kazan data siya ma baza ta samu ba."
Babu wanda ya lura da yanayin dakin a cikinsu sai bayan da suka ga Amman bata basu amsa ba, tayi shiru kawai tana kallonsu, wanda hakan yasa Adam yasha jinin jikinsa, ya sake kallon fuskar Amman da kuma ta Amina ya tabbatarwa kansa cewa basu yi daidai da lokacin da ya kamata ba, don haka ya nufi kofa, sai dai har yasa ƙafarsa ɗaya a waje ya tuna da saƙon da aka bashi.
"Au na manta wallahi, Yaya in kin fito ana kiranki a waje."
Da haka ya juya yayi hanyar Kitchen ayana fadin zai sake zuwa yaci abinci. Amina ta ƙara share hawayen idanunta, Abdallah ne ta sani, don dama tun jiya take tsammanin zuwansa dama don ta sani lokacin komawarsa makaranta yayi, sai dai yazo a lokacin da take jin bata son ganin fuskar kowa, maganganun Baba da Amma sun riga sun cike duniyarta ta yadda bata tunanin a cikin zuciyarta ma akwai wani waje komai kankantarsa da zai sake ɗaukan wani abu a daren yau.
"Ki tashi kije, ganinsa zai sa ki sake yankewa kanki hukuncin da ya dace Amina, daga daren yau zuwa gobe kawai kike dashi..."
Muryar Amman ta sake faɗa, taji kamar tayi ihu lokacin data ɗago ta kalle ta, Hafsa na tsaye har yanzu sai kallonsu take alamun rashin fahimta akan fuskarta, kuma daga yanayin Amman ta san ko ihun tayi ba zata canja maganarta ba don haka ta sake goge hawayen da bayan hannunta sannan ta miƙe a hankali tana jin yadda kowa ce kalma da iyayen nata duka furta tayi mata tsaye a zuciya bayan nauyinsu da take ji a kafaɗunta.
Akan igiyar tsakar gida ta tarar da hijabin da Maryam ta goge ɗazu don gobe za'ayi musu hotunan photo album ɗin sauka a islamiyyar su, na sallar idinsu ne, dogo har ƙasa kalar ruwan ƙasa, ta jawo shi kamar zata saka amma sai ta fasa, ta nufi ƙofar soron ta tsaya, ziciyarta na ƙoƙarin ƙulla ta yadda zata yiwa Abdallahn bayanin komai, komai ɗin da itama bata gama sani ba, taji ɓangare da yawa a cikin ƙwaƙwalwar ta na gaya mata cewa fitar ta a wannan lokacin ba alkhairi bace, don haka sai kawai ta dawo ta kira Adam dake karo da kwanuka a kitchen.
"Adam zo."
Ya juyo riƙe da plate yana kallonta kafin ya ajiye shi ya biyo bayanta, suka koma har hanyar soron.
"Adam dan Allah kaje kace masa bani da lafiya sosai, ya dawo gobe ba zan iya fitowa yanzu ba."
Kamar ya tambaye ta dama ta sanshi ne tunda bai taba ganinsa a gidan nasu ba, sai kuma kawai ya fasa ganin yadda idanunta suka yi ja ya san ba lallai taso tambaya a lokacin ba, ya juya ya fita, ita kuma ta tsugunna a wajen tana ƙara share hawayenta ba tare da ta fahimci kuskuskuren da tayi ba.
Lokacin da Adam ya fita, Ma'aruf na tsaye har a lokacin kuma ganin tahowarsa yasa ya ɗago da hannayensa duka biyu a hankali yayi baya da hular (hood) dake kansa, fuskarsa ta fito cikin hasken ƙwan fitilar barandar gidan,
"Yaya tace wai dan Allah kayi haƙuri bata da lafiya ba zata iya fitowa ba ka dawo gobe."
Ba shiri wani murmushin ya subuce a fuskar Ma'aruf, For real? Shine ma zai dawo goben? Bata san me ta tsallake bane, sai kawai ya gyada kansa tare da faÉ—in.
"Okay."
Har Adam zai juya yayi saurin tsayar dashi.
"Kana ji ko, É—an tsaya ka bata wannan."
Adam ɗin kuwa ya tsaya, shi kuma ya buɗe ƙofar motar ya buɗe aljihun dake jikin dashboard ya zaro wata jotter da biro daya san Ishaq baya taba rabo dasu motarsa a matsayinsa na lawyer, ya yago takarda guda ɗaya ya ɗora daga saman yayi wani rubutu layi biyu da rabi kawai sannan ya rubuta sunansa daga ƙasa. Ya kalli abinda ya rubuta din yayi wani guntun murmushi kafin ya juyo ya mikowa Adam ɗin
"Nagode sosai kaji."
Ya faÉ—a yana sake yi masa wani murmushin, da fara'a shima Adam É—in ya amsa yana masa a sauka lafiya kafin ya juya, shi kuma ya jefa kansa baya jikin motar yana cusa hannunsa na hagu cikin gashin kansa.
Ba haka yaso ba, amma hakan ma yayi... Ya riga ya gama da yarinyar nan ya sani, don abinda su Baffa ke tunani ba zai taɓa yiwuwa ba.
Aka É—auke wuta a daidai lokacin, unguwar tayi wani irin duhu dinÉ—im kamar yadda yake jin zuciyarsa! Don haka ba shiri ya kunna motarsa ya shiga ya bar wajen.
"Gashi yace in baki."
Adam ya faɗa a cikin duhun soron bayan ya koma, Amina tayi saurin sake goge hawayenta kafin ta karbi takardar ba tare da tunanin komai ba don ta san ba wani abu bane Abdallahn ya iya rubuto mata fatan samun sauƙi dama, ta damƙe ta a hannunta sannan ta miƙe ta bi bayansa. A kitchen suka tadda Amma na kokarin kunna kyandir guda biyu Hafsa kuma na sake zuba abinci itama, kuma bayan ta amsa sallamarsu sai ta miƙowa Amina guda ɗayan yayin da Adam ya shiga fadan cewar Hafsan ta dauki farantinsa.
Ta wuce ɗakinsu kai tsaye, ta ajiyewa Maryam Hijabin akan katifarta sannan ta manna kyandir din akan wata kwalbar magani, a gabansa ta tsugunna hannunta rike da takardar, daga jikinta har zuciyarta daban take jinsu, wucewar awa guda kawai ta tafi da Aminar da take a baya, a yau da safe ma... tana jin zata rubuta dukkan abinda ya faru a daren yau a wajaje da yawa ta yadda ba labarinsa ba zai taɓa gogewa ba.
Ta sake goge wani hawayen sannan ta buɗe takardar a hankali, zuciyarta cike da fatan ta karanta wani abu mai rangwame daga Abdallan ko yaya ne wataƙila ya iya zaftare wani ɓangare na damuwarta, sai dai kuma rubutun da idanunta suka gani a jiki shine abu mafi tashin hankali fiye da duk maganganun da rayuwarta taci karo dasu a wannan daren.
Kar ki yarda da auren nan, da gaske ne abinda suka faÉ—a miki, I'm a psycho, zan kashe ki idan har kika shigo rayuwata. Ma'aruf B.
*****
11:15Am.
"Mai gaskiya kaci abincin kasha magunguna naka?"
Muryar Hajiya Kilishi ta tambaya cikin wayar dake kare a kunnenta, kuma a cikin wayar aka bata amsar data sa ta gyaÉ—a kanta kafin ta sake cewa.
"Zan kira Ishaq, zamu yi maganar komai dashi, idan zaka shigo kawai ka taho da magungunan duka."
Har tayi shiru sai kuma tace.
"Dan Allah Ma'aruf kafin ka shigo kaje ka aske gashin nan dan Allah, ko É—azu da na shiga wajen Inna Danejo abinda ta fara tambayata kenan."
Amsar da Ma'aruf É—in ya bayar mai tsawo ce, don ta dade tana saurarensa kafin tace,
"Shikenan idan ka shigo kayi mata wannan bayanin da kanka, akwai faten dankali a É—aya daga cikin kwanukan abincin nan ka ganshi?"
Ya fadi abinda ya saka ta yin dariya kafin ta sake cewa.
"To aci lafiya, sannan idan ka wuce 1 baka shigo ba, zaka ganmu gabadaya gidan mun taho."
Ya fadi wani abun da ya kara saka ta dariyar da tafi ta farko tana fadin.
"Ai da Æ´anmata zamu zo sai suyi muku sharar."
Da haka suka yi sallama, tana sauke wayar daga kunnenta.
"Wallahi na dade ina gaya miki Hajiya, da irin mahaukatan secret agent din nan na turawa ya kamata ki samu aiki, ko banza dukkanku zaku amfana da juna, ke da kudinsu su kuma da kissa irin taki."
Cewar Hajiya Salamatu, wata hamshaƙiyar ƴar gayu dake zaune daga gefen Hajiya kilishin.
Wajen ƙarfe goma sha ɗaya ne na safe a lokacin, kuma kasancewar ranar ta asabar ce kowa yana nan, gidan cike yake da hayaniya da kuma hada-hadar masu aiki da suka gama abincin safe suke kokarin ɗora na rana.
A cikin ɗakin da suke zaune an ɗage labulayen tagogin dakin guda biyu iska da hasken rana na shigowa yayin da a lokaci guda kuma filutulun ɗakin suke a kunne haɗe da fankar da aka ware har ƙarshenta. Hajiya Kilishi dake zaune itama cikin nata adon daidai misali ta ajiye wayarta a gefe sannan ta kai hannu ga robar ketchup ɗin dake kan katon farantin da aka zubo musu kayan breakfast akai, ta sake zubawa a farantin dankalin turawan dake hannunta ta sannan tace.
"Idan har zaki samo min me zai sa in ƙi sanya hannu Hajiya, kin san ai waje in dai da raɓa da kuma sirri ba na ƙinsa."
Hajiya Salamatu ta sake kai kofin shayinta baki tana girgiza kai.
"Ai kullum ina gaya miki al'amarinki abun mamaki ne Kilishi, wallahi duk yawona a doron duniya ban taɓa ganin mace irinki ba, yadda ba boka ba malam, kike juya komai da ɗan yatsa guda kuma hankalinki a kwance."
Hajiya Kilishin tayi wata guntuwar dariya alamun ta saba da jin hakan daga bakin ƙawar tata.
"Mu bar wannan zancen yanzu Salamatu, mu tafi ga abinda yasa na kira ki."
Sai da Hajiya Salamatun gyara zamanta a hankali tana ajiye kofin daga durowar gefen gadon, idanunta kaɗai zaka kalla ka san cewar da gasken ta tattara dukkan hakalinta ga abinda Hajiya Kilishin ke ƙoƙarin ɗorawa akan tsohon shirin da suka saba.
"Auwalu yana riƙe da ma'aikata har yanzu, sannan wannan auren kamar ya tabbata ne mu ajiye shi a gefe, me kika cigaba da shiryawa daga ƙarshen ƙullin da muka yi wa zaren, me kika tsara?"
"Tsari na da yawa Salamatu, farko dole ne in fara sakin manufata tun yanzu akan ita yarinyar, dole ne ta ɓoyayyiyar hanya in ƙara bincike akan zuciyarta ta yadda zan fara ƙawata tunaninta da miƙakkiyar hanyar da zata ƙulle ta a gaba.
Na biyu, dole ne a yanzu inyi taku mai nisa daga mahaifin yarinyar da kuma maigidana, zan ƙara zame hannuwa daga al'amarin na in zama ƴar kallo ta yadda ko ƙura ba zata hau kan farina ba, balle wani ɗigo na baƙi, amma zan kusanci mahaifiyar yarinyar dole, don haka ne ingantacciyar hanyar da kowa zai kalla a yanzu.
Sannan na san Ishaq zai shaida min dukkan sabon tsarin magungunan Ma'aruf, don haka wannan ma babu matsala, komai zai cigaba ne daga inda ya tsaya. Game da auren su Salma kuma wannan komai tsaftatacce ne don kin san bana taɓa haɗa ƙasa da gari waje guda. Daga Auwalu kuma, mun sake bude wani sabon account zai loda kudaden wancan watan..."
Ta faÉ—i hakan sannan tayi shiru a hankali, ramin bakinta na wasa da wani murmushi mai armashi.
"A yadda lissafin komai yake Salamatu, shekara guda tayi yawa kafin komai ya ɓare!"
Hajiya Salamatun tayi nata murmushin itama yayin da take kallon fuskarta.
"Na fahimta Kilishi nima na lissafa wannan adadin tun a wancan karon. Sai dai kin san a kullum nice mai hasko miki ƙalubalen da ke bakya ƙirgawa dasu. Ƙalubalen da duk zare ɗaya ne ya ƙulle su suke reto a jikinsa, ƙalubalen kuma da shine raunin ki Kilishi, shi kadai ne raunin da na san ubangijin ya halitta a ƙirjinki, Ma'aruf!"
Murmushin da kullum ke sauka a fuskarta duk sanda Hajiya Salamatun ta furta mata magana makamanciyar wannan shi tayi a yanzun ma, tayi shi tana ajiye farantin hannunta, ta jawo tissue a gefe ta goge maiƙon hannunta sannan ta miƙe, ta isa ga makekiyar wardrobe ɗin dake ɗakin ta buɗe waje na biyu, a ciki kayan Ma'aruf ne wanda ya cire daga jikinsa ranar da aka tafi dashi tafi London ba'a hayyacinsa ba.
A gaban kayan akwai dukkan tarkacen dake cikin aljihunsa a wannan ranar, muƙullin mota, chewing gum, chapet, biruka da kuma wallet ɗinsa, wallet ɗin ta dauko sannan ta rufe wardrobe ɗin ta dawo gaban Hajiya Salamatu ta miƙo mata ita.
Sanin halinta sarai yasa Hajiya Salamatun ta karɓa ba tare da ta tambaya ba, ta ware cikinta, kuma bayan tudun kuɗin da taji a ciki da kuma jerin credit cards, wani hoto da aka maƙala a jiki shi ya ɗauki hankalinta, samari biyu ne a jikin hoton wanda kallo ɗaya kawai zai shaida maka cewar wa da ƙani ne, don bayan girman da ɗaya yafi ɗaya, akwai kammani sosai a fuskarsu. Suna dariya mai cike da nishaɗi yayin da babban ke miƙo hannunsa kamar zai naushi ƙaramin.
Ƙaramin Ma'aruf ne Hajiya Salamatu ta sani, babban kuma...
"Jamal..." Sassanyar muryar Hajiya Kilishi ta furta tare da tunanin Hajiya Salamatun.
"Jamal shine ƙalubale na kuma shine rauni na Salamatu, shi yasa na rufe idanuna nayi abinda ya kamata akansa, don haka kamar kullum zan gaya miki cewa ki yarda bani da wata matsala a duniyar nan yanzu idan ba kuma ƙaddarar ubangiji ba. "
Ta fadi hakan yayin da take tsaye akanta, Hajiya Salamatun ta É—ago ta kalle ta, wannan murmushin na baya ya tafi, idanunta sun canja ta yadda ko É—igon raha babu a cikinsu.
"Kar ki ƙara lissafa Ma'aruf a cikin ƙalubale na Salamatu, don kinfi kowa sanin matsayinsa a waje na."
Kuma a cikin idanuwan nata, Hajiya Salamatun ta shiga hango abubuwan da suka faru wasu tarin shekaru da suka wuce!
******
11:20 Am
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Wai baka da imani ne Ishaq? Tun da na tashi kake ta masifa a gidan nan kana mita, nace maka wallahi ko ganin yarinyar banyi ba balle inyi mata wani abu, do I have to bury myself before you believe?" (haƙa kabari zanyi in shiga kafin ka yarda dani?)
Ma'aruf ya fada a lokacin da yake zaune kan dining table din falon gidansu, inda ya samu ya ture wasu litattafai da kuma kayan wankin Ishaq ya dora plate É—in abincin da yake ci.
Ishaq na tsaye daga cikin falon shima rike da nasa kofin shayin da kuma remote É—in da yake kokarin chanja channel daga ta labaran da Ma'aruf ya kai.
"Ka gayawa wani ba ni ba, na san halinka sarai B, hankalinka ba zai taba kwanciya haka ba idan har ba kayi abinda kake so ba. I'm just advising you (shawara nake baka) komai zai iya faruwa idan har maganar nan ta lalace kuma Baffa ya san da saka hannunka."
Ma'aruf yayi murmushi a hankali sanda yake jin zafin faten dankalin dake sauka cikin maƙogwaronsa wanda motsawar Adam's apple ɗinsa kadai zai shaida maka hakan.
"Wai ina zaka je ne ma? Yau asabar fa?"
Ya canja akalar zancen nasu ba tare da ya kalle Ishaq ɗin ba, don tun da farko kayan jikinsa sun riga sun nuna masa cewa Office zai je. Babu adadi na lokutan da zuciyar Ma'aruf ke motsawa a duk lokacin da yaga Ishaq na yin wani abu da ya danganci aikinsa, aikin da yake so kuma abinda shine mafarkinsa ya fito dashi zahiri kuma yake yi ɗin. Shi nasa burin da kuma mafarkin sun dade da kaɗewa shekaru goma da suka wuce. Abinda yake yi a yanzu, ba rayuwarsa bace ko kaɗan, wata rayuwa ce da ta zama dole ya ƙarasawa mai ita.
"Thanks to you, nayi missing tarin ayyukan da dole inje in san halin da ake ciki kafin Monday, Idan ciwon ka ya sake tashi Ma'aruf wallahi ka nemi mai raka ka asibiti."
Murmushi Ma'aruf keyi har a lokacin yana cigaba da cin abincinsa yayin da ƙamshin curry da kuma naman dake cikin abincin ke gauraye ɗakin, ya kai hannu yana cusa yatsunsa cikin gashin kansa, wani abu da ya riga ya zama ɗabi'arsa kafin yace.
"Ka san me Mami take ce min yanzu? Wai inyi aski kafin in shiga gida, don Inna Danejo na tashi da safen nan abinda ta tambaye ta kenan."
Ba shiri Ishaq shima yayi nasa murmushin kafin ya gyaɗa kai don har ya hango irin rigimar da za'ayi da Ma'aruf din da ba zaiyi askin ba da kuma Inna Danejon da ba zata haƙura, don kafin tafiyarsu London ta kawo dalilai sun fi ashirin na cewar rashin lafiyar Ma'aruf tana maƙale da gashin kansa ne, Baffa ne kawai bai bada goyon baya ba da tuni sai dai Ma'aruf ɗin ya tashi yaga kansa ɗal!
"Hular sanyi kawai zaka dauka, in zaka shiga wajenta ka saka kace anyi askin ba'a bude kan ne."
Ya faÉ—i hakan lokacin da ya gama neman abinda yake so a jikin Tvn don haka ya ajiye remote din ya juyo ya kalle shi.
"Za'a kawo maka motar ka ne?"
"Eh, na kira direban Office tun dazu nace yaje ya É—auka ya kaita Carwash, I'm sure kafin 12 zai dawo da ita."
Ishaq ya gyaÉ—a kansa.
"Shikenan mu haÉ—u a gidan, nima can na nufa idan na tashi insha Allah."
Ya faɗi hakan yana juyawa hanyar ƙofa, idanun Ma'aruf suka bishi da kallo yana tunanin wani abu, kuma sai da ya isa ƙofar da zata fitar dashi waje har ya buɗe ta sannan yayi saurin kiran sunansa.
Ya kuwa juyo a take kamar shima dama jiran kiran yake yi. Ma'aruf ya girgiza kansa yana kallonsa.
"Wallahi ban ga yarinyar ba Ishaq, kawai dai na bata wani saƙo ne da na san dole ba zata taba yarda ba."
****
11:30Am.
"Na yarda!"
Kalaman guda biyu suka fito daga bakin Amina lokacin da take tsugunne a gaban iyayenta guda biyu da dukkan fuskokinsu ke haskawa da tsananin mamaki.
Tata fuskar fayau take, ba abinda zaka iya tsinta a jiki.
Ta gyara zamanta sannan ta sake maimaitawa kamar wani ya sata.
"Na yarda zan aure shi Baba."
Maimaitawar ta fiyo tare da faɗowar flask ɗin ruwan zafin da Amma ta ɗauko don juyewa Baba ruwan wanka, ya subuce a hannunta ya faɗi har ƙasa, kwalbar ciki ta tarwatse yayin da ruwan zafin ya fallatsa akan dukkaninsu.
*
Me kuke tunani yasa Amina ta yarda da auren Ma'aruf?
Wacece ainihin Hajiya Kilishi?
Me ya faru da Jamaal?
Shekarun cikin labarin sun wuce da wasu abubuwa da zamu fara kwance su daga Babi na gaba insha Allah...☺️
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.
BABI NA BIYAR.
~~~~~
Ana gobe sallah ne ranar, ita da Maryam sun je kasuwa siyayar mayafai da takalmi, tun kusan sha biyu suka fita har mutane suka fara alwalar sallar la'asar basu gama siyayyar ba.
Maryam dake riƙe da ledar kayan da suka siyo kalli tsinken kwakwar da suka auno tsawon kafar Hafsa dashi tace.
"Ai wallahi dama na san takalmin yarinyar nan shi zai bamu wuya, kafa kamar ba ta mutane ba Æ´ar firit da ita."
Amina ta share gumi a gefen fuskarta tace.
Har tunani nake ko ba daidai na auno ba wallahi gashi mun kusa gama siyen komai..."
Bata karasa ba ta tuno da sakon garin da Amma tace su siyo zata yi teba dashi da daddare.
"Kin san na manta da garin Amma... zo muje wancan layin na san zamu samu."
Maryam ta girgiza kanta.
"Mu raba tafiyar kawai lokaci ƙara wucewa yake, ga wani kantin takalma can, bari naje na duba idan ma ban samu ba zan jira ki sai kizo ki same ni anan."
Da haka suka raba tafiyar, Maryam ta tsallaka ta cikin cunkoson mutanen ta nufi kantin ita kuma tabi layin gefensu inda nan É—in ma turuwar mutanen ce wadda dama sun riga sun shirya mata, don tun ana saura sati É—aya sallar suka so zuwa kasuwar amma rashin haÉ—uwar kudin yasa dole sai yau suka samu suka fito.
Ga rana, ga azumi amma yadda mutane suka hargitse baza kace kowa a gajiye yake ba. Da kyar ta samu ta ɓulla layin da masu garin suke, kuma akan ragin naira hamsin ɗin da zasu yi kuɗin mota dashi, sai da ta kusan shanye layin tana tambaya da ƙyar ta samu wani acan ƙarshe yace zai rage mata.
Tana tsaye yana ƙoƙarin auna mata, wani yaron shagon nasa ya shigo, irin samarin nan ne masu magana, yana shigowa ya haye kan ɗaya daga kantocin shagon yana fadin.
"Allah na tuba a yadda ake wannan ranar ga azumi ai wallahi komai talauci na ba zanyi aikin sauke gari ba, don mugunta kaga yadda suke jefo musu buhun nan daga sama, wani har sai ya kai ƙasa wallahi kafin ya ɗago."
Maganar ta É—auki hankalinta, tana hango yadda nauyin buhun gari yake ace mutum ya dauka a wannan ranar.
"Yau ma mota ta sauka ne?"
Mai shagon ya tambaya yana miko mata ledar garin.
"Gata can yanzu ta tsaya, ka san shi Auwalu ko da goma yaga sunyi ƙasa sai yayi aike."
Ta miƙa masa kuɗin tana faɗin ta gode, amma kafin ya karba saurayin yayi saurin miƙo hannu ya karba sannan ya miƙo mata yana mata murmushi, irin halin ƴan kasuwa.
A kofar shagon kuwa tana fita taga motar ana ta sauke garin, tausayin masu yin dakon ya tafi har cikin ranta ganin yadda ko a ido buhun ke da nauyi, tana tafe tana ganin fuskokinsu lokacin da idonta ya kai kan fuskar da ta sa ba shiri hannunta ya saki ledar garin nan... Mahaifinta ta gani dauke da wani katon buhu yana ƙoƙarin kaiwa inda sauran ke saukewa, mahaifinta dai Baba, Baban daya shirya tsaf a yau ya fita suna yi masa a dawo lafiya.
A wannan lokacin yana gaɓar farfaɗo wa daga karayar arzikinsa ne, don duk da kokarinsa wajen yi musu kayan sallah, har saida aka haɗa da kuɗin Aminu kafin komai ya isa, bata san lokacin da hawaye ya fara biyo kuncinta ba, taga ya sauke ya koma sake ɗauko wani... Baba mutum ne mai tsananin son dogaro da kansa kowa ya sani, yayyensa duka sunyi kokarinsu wajen tallafa musu tunda al'amarin ya faru, amma babu wanda ya isa ya ɗauke maka cin yau da gobe sai Allah, don haka ta san nauyin ya cigaba da tambayarsu ne yasa har ya kawo kansa yin wannan aikin don kula dasu.
Hawayen ya cigaba da bin fuskarta yayin da zuciyarta ke rawa a kirjinta, tunanin ta É—aya ne a lokacin, idan har mahaifinta zai iya sadaukar da girmansa yayi wannan aikin don kawai ya fita kunyarsu meye su baza suyi don fita tasa kunyar a duniya da kuma lahira ba?
Ta share hawayenta lokacin da wani mai wulbaro ke miko mata ledar garin da Allah yaso bata fashe ba. Kuma bata fadawa Maryam abinda ta gani ba, bata fadawa Amma ba, bata fadawa kowa ba, don ta san hakan wani abu ne da Baban ba zai taɓa so waninsu ya sani ba.
Kuma a wannan daren sai gashi ya dawo da ledar kaza har guda biyu ta miyar sallah, su Hafsa suka yi ta tsallen murna yana binsu da nasa murmushin shima.
Wajen karfe biyun dare bayan kowa ya kwanta, ta hango shi ta ƙofar ɗakinsu a wajen banɗaki yana miƙe bayansa, kukan da tayi a cikin filonta a wannan daren Allah kaɗai ya san yawansa, abu ɗaya kawai ta sani shine tayi wa kanta alƙawari a wannan ranar cewa ko abinda yafi rayuwarta ne zata sadaukar a duniya don farantawa mahaifinta.
*
"Wallahi gani nake yi kamar zaki ƙyalƙyale da dariya ki gaya min wasa kike yi."
Fatima ta faÉ—a tana kallon Amina data idar da sallah a gabanta.
"Ke ma kin san ai ban taɓa miki irin wannan wasan ba, da gaske nake Fatee, don yanzu haka ma Baba ya tafi gidan Kawu Mallam ya faɗa masa."
"Ya fada masa cewa kin yarda zaki auri wanda yake da matsalar ƙwaƙwalwa Amina...? inalillahi wa'inna ilaihir raji'un Amina kin san Allah ko da nake cewa ki rabu da Abdallah ki samu wanda yafi shi ba irin haka nake nufi ba, ya za'ayi kiyi irin auren da ake bada labarin ire-iren sa a sigogi mara sa daɗi?"
Fatiman ta ƙarashe muryarta na karyewa. Amina ta cire hijabin sallar tana kallonta,
"Ban gane me kike nufi ba?" Ta tambaya tana kallonta. Fatima ta girgiza kai kafin ta gyara zamanta.
"Amina duk wanda yaji batun auren wallahi shaidar da zaiyi miki daban, kowa cewa zaiyi auren kuɗi zaki yi, musamman ƴan unguwar nan da kin san daman ƙiris suke jira akanki."
Amina ta haɗiye wani abu a maƙogwaronta, abinda Fatiman ta faɗa gaskiya ne ta sani, kuma maganar iri ɗaya ce da maganganun Amma na jiya, duka su biyun ƴancinta suke nemar mata, amma a wajenta darajar mahaifinta itace a gaba da ita kanta don haka ta riga ta gama yankewa kanta hukunci, ta gayawa zuciyarta cewa zata tsaya tare da mahaifinta koda zata mutu sau biyu idan ana yi.
"Fatee na tabbata ba fa ba wai matsala ce sosai ba, kawai sun faɗa ne saboda kinga a aure ba'a ɓoye komai, kuma ma Baba yace baza'a bari maganar ta fita ba, kema kin san ba zan iya ɓoye miki bane."
Ta faɗi hakan yayin da idanunta ke hango takardar data cusa cikin kayanta a jiya, babu wanda ya san da ita, babu wanda ta gayawa hatta Amma kuwa duk yadda kowanne abu mai hankali a cikin kanta ya tsorata da maganar dake rubuce, amma ta sani cewar in har iyayenta suka ji hakan dole zai iya sake zama wani ƙalubale musamman ma a wajen Amma don haka ta yanke hukuncin ɓoyewa tunda ba zata taba fatan abinda zai hadassa mahaifinta yaji kunya ta dalilinta ba.
Kuma kafin Fatiman ta sake cewa wani abu suka tsinci sallamar Ummi daga tsakar gida, Æ´ar Kawu mallam wadda suke kusan sa'anni da Aminan.
"Ina amaryar take?" Muryarta ta fito da fara'a bayan ta gaisa da Amma da kuma Maryam wadanda suke kitchen, ta karaso ya É—age labulen É—akin tana kallon Amina bakinta a washe.
"Yarinyar nan da tsinannen wayo, sai dai muji kawai wai zaki yi aure?"
Sai dai Amina tayi wani guntun murmushi kafin tayi mata sannu da zuwa.
"Ni ba zan amsa ba wallahi, tunda sai da muka ga meeting ɗin su Kawu yayi tsawo sannan da kyar muka san me ake ciki, da ake ɓoye mana naga wanda zai raka ki siyayyar kayan bikin ai."
A cikin maganar ta Amina ta tsinci wani abu, cewa da gaske Baba yake a ɗazu daya shaida mata cewar kowa zai ji maganar auren ne ta fuskar alkhairi, babu wanda zai san me ake ciki, gashi kuwa ko iyalan Kawu Mallam ɗin da ake taruwa a gidansa basu san komai ba, zurfin maganar ya tsaya a iyakar Baba da yayyensa ne sai kuma Amma, Fatima, Maryam da Aminu da suka sani a yau. Ance zancen duniya baya ɓuya, amma har cikin ranta tana fatan zancen ya tsaya a iya wadannan mutanen kawai.
"Ai ni ban yi zaton har É—an bokon naki ya gama makaranta ya shirya ba, shi yasa wallahi abun ya bamu mamaki sosai, har su Umma ma cewa suka yi koda wasa Amma bata yi musu zancen a kurkusa ba."
Amina ta girgiza kanta.
"Ai ba shi bane Ummi, wani ne daban."
Sai da Ummin tayi shewa kafin tace.
"Gaskiya ne yarinyar nan, kice da karfinki kika taso, Fatima bani labari don na san zanfi ji a wajenki, wane ne sabon kamun?"
Fatima tana take tace.
"Wallahi kin san al'amarin Allah ai, kawai komai a lokaci guda yazo."
"Eh, amma dai da maiƙon sa ko? Yadda komai ya taso a lokaci gudan ai na san a shirye yazo ko?"
Kawu malam mutum ne malami mai sauƙin sha'ani, amman sai Allah ya bashi matansu duka ukun masu azabar son kuɗi, kuma suka taso da ƴaƴansu ma gabaɗaya akan hakan, gashi mata sunfi yawa a ciki don haka a zaune yake cewa basa auren kowa sai mai abin hannunsa ire-iren ƴan kasuwa, gasu da surutu da kuma kauɗi, hakan yasa duk kusancinsu dasu Amina basu fiye shiga cikinsu sosai ba don halayensu sun banbanta duk kuwa da cewa suna da mutukar kirki.
"Ai kuwa dai yana da kuÉ—i gidansu ma haka."
Fatima ta bawa Ummin amsa har a lokacin tana murmushin yaƙe.
"Kice dole ne mu raƙashe a bikin nan, wallahi azo a saka mana rana ma nan kusa Momi tazo mu fara shirye-shirye, zaki yi anko?"
Amina taji wani abu ya tokare mata a maƙoshi, don ita har ta yanke hukunci bai taɓa zuwa kanta cewar ma biki za'ayi ba, gani take kamar jana'iza kawai za'ayi akaita, kuma sai Allah ya taimake ta kiran Amma yazo a daidai lokacin don bata san amsar da zata bawa Ummin ba.
Amma ta kalle ta bayan ta isa kitchen din, fuskarta fayau tace.
"Kizo ki zuba muku abinci gashi nan an sauke."
Ta haɗiye yawu a hankali tana ƙarasawa ciki, lokacin da flask ɗin ruwan zafin nan ya faɗi daga hannun Amma, sai ya zama kar ya fashe da dukkan irin hukuncin da take tunanin Amman zata dauka akan ƙin bin maganarta da tayi, don a lokacin bata ce komai ba, juyawa tayi kawai ta bar wajen yayin da Baba ke saka mata albarka, kuma bayan taje ta same ta a ɗaki, abu daya kawai tace.
"Rayuwarki ce dama Amina, na nuna miki kuskuren dake ciki ne kamar yadda yake alhaki na a matsayin uwa, kuma tunda har kinga zaki iya dauka, ga fili ga maidoki nan, zuciyata ba zata riƙe ki da komai ba, Allah ya baki sa'a."
Daga haka bata ƙara cewa komai ba, kuma bata yi fushin da Amina tayi zato ba, harkokinta ta cigaba da yi a gidan kamar dama maganar bata taso ba, kamar dai shekaranjiya da Baba bai ko ziyarci gidan Hajiya Kilishi ba, balle su san da komai.
Ta zuba abincin ta kai musu, suna ci Ummi na daɗa bada bayanin yadda abubuwa zasu kasance wanda daga ita har Fatiman yaƙe kawai suke suna amsa mata, wajen la'asar ta tafi, lokacin ma Fatima ta daɗe da tafiya asibiti inda tace yau za'a sallamo kakarta.
Wajen ƙarfe biyar, Aminu ya shigo gidan riƙe da wani flask lokacin da take wanke-wanke ita kaɗai a gidan, don Amma ma ta shirya ta tafi gidan wata ƴaruwarta a Goron dutse ta shaida mata al'amarin.
"Ina yarinyar nan take?"
Ta san Maryam yake nema don haka tace.
"Ta tafi makaranta tun É—azu."
Sai ya ajiye flask ɗin a ƙofar kitchen sannan ya ƙaraso ya tsugunna a kusa da ita, muryarsa ɗauke da nutsuwar da zaka shafe rabin rayuwarka kafin kaji ta a wajen Aminu yace.
"Hukuncin da kika yanke yayi daidai Amina, ba don Amma ba daidai ta faÉ—a ba, sai don kare mutuncin Baba da kika yi, kuma na tabbata Allah zai duba hakan ya kyautata rayuwarki."
Kwalla ta taru a idonta lokaci guda, don haka ta gyada kai kawai ba tare da tace komai ba. Wucewar wasu Æ´an sakanni shima yana tsugunee kamar yana sake biya abinda ya fada a zuciyarsa, sai kuma yayi gyaran murya sannan ya koma Aminun da yake.
"Kin gayawa Malam ne?"
Ta san Abdallah yake nufi don dama haka yake kiransa, saboda haka ya girgiza kanta tace.
"Na san dai zai zo anjima."
"Kice yau Malam zai danɗani baƙin cikin latecomer kenan."
Bata san lokacin da ta watso masa ruwan wanke-wanken ba tana jin wani abu a zuciyarta na fadawa, ya kauce shima yana dariya sannan yayi hanyar fita yana faÉ—in.
"Idan wannan ƙwalamammiyar ta dawo kice mata ga wainar masar da take ƙalata nan na samo mata."
Bayan ta gama wake-wanken ta koma ɗakinsu har a lokacin ƴan islamiyar basu dawo ba balle kuma Amma, a ƙasan kayanta ta sake ɗauko wannan takardar tana karantawa, idanta suka tsaya akan sunan yayin da a yanzu bayan tsoron ma'anar rubutu wani sabon tsoro daban ke shigarta.
Ma'aruf B.
Ta karanta sunan tana jin yadda tsoron harafan kadai ke zanuwa a zuciyarta, ba wai don ta sanshi ta gane waye ba sai don zuciyarta bata cika manta fuskokin mutane ba koda kuwa sau ɗaya ta taba arba dasu, kamar dai shi rana guda ta taɓa ganinsa a rayuwarta kuma bata ƙara ba daga sannan.
Ranar ɗaurin aurensa, ranar da Baba yasa suka tafi tunda sassafe ita da Amma don wai suyi yinin bikin da gaske kamar yadda aka rubuta, a lokacin da ya shigo gidan shi da abokansa da ƴanuwansa bayan ɗaurin auren, ita da Amman suna rakuɓe daga can jikin wata kujerar a falon Hajiya Kilishin, kuma duk da tarin ƴan bikin mata da suka yanyame shi da tsokanar 'ango kasha ƙamshi...' sai da idanunta suka iya hango mata shi yasha farar shaddar dake ƙyalli kamar murmushinsa, yana tsaye daga tsakiyar mutane yayin da masu hoto ke ta yi musu kala-kala.
A wannan lokacin gani take kamar bambancin su ita da Amma da mutanen gidan ya zarta na mutum-mutum, don bayan Hajiya Kilishin da ta amsa gaisuwar su cike da fara'a ta kuma sa aka kawo musu abinci babu wanda ya ƙara lura dasu a gidan, sai wata mace guda ɗaya da tace Amma ta ara mata hijabinta lokacin sallar azahar, itama da alama irinsu ce don ta ɗebo tarin ƴaƴan da ta cika musu faranti taf da abinci suna ta ci. Daga baya ma dole suka bar cikin falon suka zagaya baya can wajen ɗakunan masu aiki, inda anan ne suka ɗan sake har Amma ma taga wata ƴar ajinsu ta sakandire a ƴaƴan dattijan da sune manya-manyan masu aikin gidan.
Don haka kwatanta tsoron cewar a wannan karon ita zata maye gurbin wannan kyakkyawar amaryar da aka shigo da ita gidan wajen yamma abu ne da ta tabbata babu wanda zai iya kwatanta shi a duniyar nan.
Tsaya ma tukunna... Ina matar tasa take??
*****
"Baffa ya gaya maka komai ko?"
Hajiya Kilishi ta tambaya tana kallon Ma'aruf ɗin dake zaune a gabanta, a cikin falon ɓangarenta suke su biyu sai Surayya dake can wajen dining tana danne-danne a wayarta, yana zaune a kujerar dake kallon Tv yana kokarin canja channel daga ta india zuwa wata channel da ya san a lokacin ana wani Tv show na likitoci mai suna 'Code Black'.
Sai da ya kai tashar ya karo volume sannan hankalinsa a kwance ba kamar yadda ta zata ba ya juyo ya kalle ta.
"Ya gaya min, and I was surprised har dake Mami."
Tayi murmushi tana kallonsa daɗi na cika kowanne lungu da saƙo na zuciyarta na ganinsa a gabanta, zata rantse da alƙur'ani ko ya'yan da suka fito daga cikinta basa ƙarasawa inda Ma'aruf ke kaiwa a zuciyarta, matsalar ɗaya ce kawai... duk wani ado da zai ƙawata kusancinsu dole ana kaiwa gabar da za'a yaye cewar shi ba mallakinta bane, kuma tana jin cewa da zata iya samun mai gyara mata hakan babu makawa zata bada komai na duniyarta don kawai a wayi gari duniya ta shaida cewa shi nata ne.
"Baffa ya riga ya gama yanke hukuncinsa shi da Alhaji Baba, daga ƙarshe kawai suka tuntubeni Mai gaskiya kuma ka san ba zan iya cewa Baffa A'a ba, shi yasa sai na bada tawa gudunmawar ta hanyar zaɓo maka yarinyar da na san zata dace da yanayinka. Wannan ba irin ba irin Ruƙayya bace Ma'aruf, don nayi Imani yarinyar nan zata baka kulawar da kake buƙata."
Wani murmushi yayi kaÉ—an sannan yace.
"Na dade ina gaya miki kulawarki kaÉ—ai ta ishe ni in rayu Mami, tunda har Rukayya ta kasa bana tunanin akwai wadda zata iya jurewa mess É—ina a duniyar nan kuma."
Maganganun suka taɓo wani abu a can ƙasan zuciyar Hajiya Kilishi, wani abu da sai da ta ji shi har a ƙarƙashin tafin ƙafarta musamman yadda muryarsa ta fito da wannan amon mai  zurfi da kuma sanyi. Kuma sai da ta maida wata ƙaramar ƙwalla a idanunta sannan tace.
"Yanzu dai ka san baza'a fasa ba ko? Don haka zamu fara shirye-shirye, za'a kai musu lefe dole sannan idan kana so ma zaka iya zuwa ka ganta."
Maimakon ya bata amsa, sai kawai ya juyo ya kalle ta, lumsassun idanunsa suka tsaya a nata.
"Wai zaman me Ishaq yake yi ne ma? Me yasa Baffa baice a haÉ—a dashi ba?"
"Sai gida ya koshi ake kallon na waje Ma'aruf, kaine damuwar mu a yanzu ba shi ba."
Kamar bai ji dadin maganar ba, don juyawa yayi yana cigaba da kallonsa ba tare da yace komai ba. Hakan yasa tayi saurin gyara zancen ta.
"Kar ka damu amma, da an gama zancen nan ni da kaina zan saka shi a gaba sai ya motsa."
Murmushin da ya sake yi ya sata jin wani ɗaci a zuciyarta, ba sau daya ba sau biyu ba tasha tunanin kawar da Ishaq daga hanyarta kamar yadda ta kawar da abubuwa da yawa a rayuwar Ma'aruf, don duk wani abu da zai jawo ya raba zuciyarsa da kowa bayan ita, bata ƙaunarsa sam! Amma matsalar shine Ishaq ba ƙaramin amfani yake mata ba, amfanin da shi ta lissafa har ta bada shawarar dawo dashi wajensu bayan ya rasa iyayensa ba don kyautatawar da duniya ke kallonta dashi ba.
"Akwati nawa kake so a haÉ—awa yarinyar?"
Kamar bai damu ba, hankalinsa kwance yace.
"Duk yadda kika yi Mami daidai ne, ni yanzu abinda ke gabana daban harkar Office ce da zanje in gyara, Baffa yace anyi asara da yawa a wannan watan."
Ba shiri maganar ta doka wata tsawa a cikin kan Hajiya Kilishi tana janyo ta daga ramin da zuciyarta ke shirin kai ta, taji kamar ta miƙe tsaye tana karkaɗe raunin daya baibayeta tun bayan data ɗora idanunta akan Ma'aruf ɗin.
"Shikenan, Allah ya taimaka. Ka taho min da magungunan naka?"
Wata ƴar ƙaramar jakar daya shigo da ita a gefensa ya ɗauko ya miƙa mata ba tare da ya janye idonsa daga Tvn ba, kuma da Ma'aruf ya saurara da kyau, zai ji lokacin da ta sauke wata nauyayyar ajiyar zuciya kafin ta buɗe jakar tana nazarin kayan ciki.
A lokacin Samirah ta shigo ɗauke da lemo mai sanyi da kuma cake a faranti, yarinya ce ita mai tsananin kula da son kyautatawa kowa, shi yasa kusan komai na gidan yanzu sai da izininta ake yi, hatta abincin Baffa ta daɗe da karɓar ragamarsa sai dai ko in tana makaranta sai wani a cikin yayyenta yayi, don su Hajiya Kilishi basa girki a gidan. Kuma ko a ɓangaren Hajiya Maimuna akayi baƙi Sameerah ita zata fara tarbarsu da waje da kuma kayan cima kafin kowa, ƙarya ne wani ya shiga gidan nan yace ya fito da yunwa in har tana nan.
"Dan Allah Yaya ka bani kwangilar sati É—aya in cicciko maka da waÉ—annan kasusuwan, wallahi baka ga yadda ka rame ba."
Ta faɗa tana ajiye masa farantin a gabansa. Ma'aruf ya ɗago ya kalle ta yana murmushi lokacin da Hajiya Kilishi ta mike riƙe da jakar magungunan tayi hanyar ɗaki. Kusa dashi ya nuna mata a kujerar yace.
"Zo ki zauna muyi ciniki Please, how much do you need? ( Nawa kike so) coz ƙarfi nake nema nima yanzu."
Ta kuwa ƙyalƙyale da dariya daidai lokacin da Shukra (ƙanwarsa dake bi masa a wajen Hajiya Maimuna) ta shigo daga hanyar wajensu, kuma ganin Ma'aruf ɗin yasa tayi murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau tana fadin 'Alhmdlilah" sannan ta juya da sauri don ɗebo takardun research ɗin da ta tara zai duba mata.
Don haka Ma'aruf bai samu shiga wajen Hajiya Maimuna ba sai da yamma tayi sosai. Kuma a falo ya same ta itama, tana zaune daga kan Wheelchair É—inta tana karatun azkar É—in yamma, yayin da Zahra da kuma Sahla ke zaune suna kallon video É—in wani tutorial daga labtop É—in Munaya da suka aro.
Ya durƙusa har kasa a gabanta ya gaishe ta cike da girmamawa, girmamawar da bayan ita baya taɓa kallonta da wani abu.
"Yaya jikin naka?"  Muryarta mai taushi ta tambaye shi bayan sun gama gaisuwa.
"Lafiya ƙalau Hajiya, naji sauki ai."
"Allah ya ƙara sauki. Kaje wajen Inna ne?"
Ya girgiza kansa.
"Yanzu zan shiga idan na fita."
Tayi shiru yayin da idanunta ke nazarinsa, ya sunkuyar da kansa ƙasa sanye da dogwayen kaya na farin yadin da ko a ido mai laushi ne don ya kwanta a jikinsa sosai ta yadda ya fito da ƙirar jikinsa mai tsari, wani abu dake ɗaya daga cikin abinda ke ƙara masa kwarjini a idon mutane.
A lokacin ne kuna maganar Æ´ar uwarta a kwanakin baya ta haska a cikin kanta.
'Ban ce ki tada hankalin gidan ki ba Maimuna, amma abin yayi yawa, kin rasa Jamal kuma Ma'aruf shine Babba a gidan yanzu, ko yaya ne ya kamata ya dinga tunawa cewa ke kika haife shi ba ita ba...'
Tayi saurin kawar da wannan tunanin tana  haɗiye wani abu da batasan sunan sa ba, a lokainda ƙwaƙwalwar ta ke tuno mata damagaar da Baffa ya yanke taauresa jiya da daddare, sai dai har ta buɗe baki zata yi masa magana kawai taga ya miƙe tsaye yana yi mata sallama, sai ta mayar da maganarta a hankali sannan ta amsa, kuma murmushin da yayi wa su Zahra a matsayin amsa tasu sallamar ya sake ɗago wani abu a zuciyarta da ta daɗe tana danne shi tsawon shekaru. Idanunta suka bishi da kallon da har ya rufo mata ƙofar falon hankalinta bai koma kan karatun da take yi ba.
A falon Inna Danejo Ma'aruf ya tarad da ita tana sallah daga kan sallayar ta da anan take kwana ta yini in har ba tashi ne ya kamata ba, don haka ƙafafunsa suka tako cikin falon a hankali, yana jin kamar zai nutse a sabon carpet din da aka shimfide mata falon dashi, (wall to wall). Ya karaso ya sami waje daga gefenta ya jingina da wasu ƙullin kayanta da ya san na wanki ne sannan ya zaro wayoyinsa daga aljihu.
Tarin messages É—in da har yanzu bai duba ba suka shiga tururuwa akan screen É—insa, sai ya zura hannunsa É—aya cikin gashin kansa kawai sannan ya cillar da ita a gefe ya dauko É—ayar.
A ciki ya lalubo nambar Faruk, aboki É—ayan da yake dashi bayan Ishaq kuma mataimakinsa a wajen aiki.
"Ka gaya min ba maganar aiki bace dan Allah B, don wallahi as we are talking now ina Coldstone ni da yara, kowa yana son hutu a rayuwarsa Ma'aruf."
Faruk din ya faɗi hakan tun kafin yace komai, don shi kansa ya sani ba zai iya kirga adadin wayar da suka yi akan zancen Office ɗin ba tun bayan dawowarsa. Sai dai kalmar yaran da ya furta ta daki zuiyarsa da wani irin tasirin da baya taɓa sabawa dashi don haka ba shiri ya tafi kai tsaye ga abinda yake son tambayarsa.
"Account number Daniel zaka turo min."
"Me zaka yi da ita? Na gaya maka gayen yana can har yanzu da kumburarriyar fuska wallahi."
Ya cije leɓɓensa a hankali yana hango fuskar Daniel ɗin a idanunsa, sanda ya cakumo wuyansa yana kai masa naushin da baya ƙarewa, kuma duk da zafin dukan nan Daniel baya kare ba ko sau ɗaya, kallonsa kawai yake da idanunsa dake nuna tsantsar mamaki da kuma ruɗani har ya fita daga hayyacinsa.
Ya sake tuno yadda ya jawo shi ya fito dashi har waje É—imbin jama'ar Office É—in na kallonsa, da lokacin da ya saka shi a boot din motarsa ya rufe sannan yaja motar zuwa gida, yaje gidan kuma ya fito dashi dashi daga boot É—in motar ya ja shi har falon Baffa a lokacin ma ya riga ya suma...
Sai kawai ya sake mai da kansa baya, yana motsa ytsunsa cikin gashin kansa a hankali, idonsa ya cigaba da hango masa yadda a lokacin duk da baya cikin hayyacinsa amma nauyin idanun Baffa suka sa ya durƙushe akan gwiwoyinsa sanda ya kai Daniel ɗin har gabansa, amma kuma duk da hakan bai fasa gayawa Baffan cewar wai ya kawo shi ne ne don ya kore shi daga aiki ba...
"Just send it Umar..." (Kawai ka turo min...)
Ya faɗa yana katse tunaninsa kuma bai ƙarasa abinda zai ce ba hayaniyar yaran nan ta shiga kunnensa daga cikin wayar, don haka ba shiri ya katse kiran yana ƙoƙarin ture abinda ke ƙoƙarin tasowa daga ƙasan zuciyarsa.
Ya cillar da ita gefen É—ayar itama sannan ya rufe idanunsa yana cigaba da motsa yatsunsa a cikin gashin nasa daidai lokacin da Inna Danejo ta idar daga sallarta.
"Wai rana kika koma bautawa ko me? Wannan wace irin sallah ce bayan la'asar?"
Inna Danejo ta kalle shi zuciyarta fara ƙal! da farin cikin ganinsa lafiya ƙalau, don a cikin addu'inta na tsukin kwanakin bata jin ko kanta ta ambata a cikin addointa banda fatan nema masa sauki, don haka da guntun murmushi a fuskarta ta kai laziminta na sallamar sallah sannan tace.
"Idan ranar na koma bautawa Muhammadu, iyayenku ai su zasu fara biyo ni kafin ku."
Murmushi yayi a hankali sannan ya buÉ—e idanunsa ya juyo ya kalle ta dasu a lumshe.
"Allah yasa da kika dama furar kin rage min, tun da na shigo nake jin ƙamshinta."
Maimakon ta bashi amsa sai tace.
"Yanzu Allah baza ka ji magana ta ka aske gashin nan ba ko? Ko iska ba ka so kaji tana ratsa ka Muhammadu?"
Ba shiri murmushinsa ya karu.
"Saboda me zan so iska ta ratsa ni? Wadda ke shiga hancina ma ta ishe ni Inna... Ki tashi ki É—auko min furar dan Allah."
Ai kuwa kamar ya ziga ta ne akan irin mitar da tayi a duk lokutan da baya nan a gidan, ta faro ta tunda daga farko daki-daki har tana faÉ—in idan ma ba zaiyi askin ba wai ya tsaya ta wanke masa da sabulun salo ta tabbata ranar sai yayi bacci mai daÉ—i, murmushinsa kawai yake yi yana jinta tunda dama ya riga ya shiryawa hakan.
A haka har Ishaq ya shigo ya same su, shima aka zuba masa furar sannan ta tasa su a gaba su duka biyun kuma da zancen aure. A lokacin Ishaq ke gaya mata hukuncin da Baffa ya yanke game da Ma'aruf, don haka bayan ta gama hamdala da mitar cewa Baffan bai zo ya same ta ya gaya mata ba, sai faɗan kuma ya koma kan Ishaq shi kaɗai, tana yi tana zayyano masa jikokin ƴanuwanta na ƙauye, kowacce ta faɗo Ishaq sai ya gyada kai yace "Kuma da alamun tana da hankali."
Ma'aruf na jinsu bai ce komai ba, tunani da yawa ke yawo a cikin kansa game da abubuwan dake gabansa, sai dai ko kaɗan babu batun auren nan a cikinsu, don tunaninsa ya gaya masa cewa ko iyayen yarinyar nan mahaukata ne idan ta nuna musu wannan takardar dole ne  auren ba zai yiwu ba.
A hankali ya sake rufe idanunsa yana tuno dukkan irin matakan dake rubuce a jikin takardun asibitinsa, Allah ya sani a baya baya taba damuwa da ciwonsa, yana ajiye shi ne a can ƙarshen lissafinsa, amma a yanzu... yanzu bai san me yake ji ba, tsoro ko kuma taraddadin cewa abubuwa zasu iya ƙwace masa kafin ya kai ga cimma manufarsa? A cikin duhun idanun nasa ya hango a inda yake manufar tasa, abinda shi kaɗai ne abu guda a duniyar nan da baya taɓa haɗawa da kowa, ɗakin bincikensa yake hangowa, tunda ya dawo bai buɗe shi ba don haka a yadda ya tafi ya barshi yake hango shi... Yadda yayi kaca-kaca da takardu cikin takaicin da shine linzamin dukan da yayi wa Daniel.
"... Kaga Rabi ma Æ´ar wajen BaÉ—É—ejo, yarinya ce mai hankali, ga kyau..."
Muryar Inna ta shiga kansa da wani irin tasirin da ya doka a ƙirjinsa, tasirin da yasa ba shiri ya buɗe idanunsa yana kallon Innar da kuma Ishaq din dake cigaba da gyada kai yana shan furarsa, sai dai ba saurarar abinda suka cigaba da cewa yake ba, muryar Inna ta shekaru goma da suka wuce ce ta shiga haskawa a cikinsa, shekaru goma cikin wannan ɗakin.
Kuma bayan muryar sai hoton ma ya canja a idanunsa, yaga yadda tsufan Inna ke raguwa da shekaru goma da yadda komai na É—akin ke canjawa da abubuwan da suke a mazauninsu a shekaru goman da suka wuce, sannan a lokaci guda Ishaq É—in ma ya bace, siffar Jamal ta maye gurbinsa yayin da yake zaune a gaban Innar yana dariya.
"Ga Halima ma Æ´ar gidan Baffayo, yarinya ce mai hankali, ga kyau, ga kyau..."
Ya ga yadda Jamal ke girgiza kansa yana dariya kafin yace.
"Akwai abubuwa da yawa a gabana yanzu Inna, ki ajiye maganar yaran nan... Akwai abubuwan da nake son daidaitawa a gidan nan kafin ma in fuskanci aikina..."
Kuma a lokaci guda ƙwaƙwalwar Ma'aruf ta tsinto kalamai biyu a cikin zancen...
Abubuwan da nake son daidaitawa a cikin gidan nan... Abubuwan da nake son daidaitawa a gidan nan...
Tabbas! Ya akayi bai taɓa tunawa da wannan lokacin ba? Me yasa ƙwaƙwalwarsa bata taɓa hasaso masa wannan ranar ba? Babu shiri idanunsa suka shiga hasko masa tarin abubuwan dake ɓullewa ga wannan maganar, yaji su suna sauka a cikin kansa kamar zubar ruwan da aka tunkuɗo da ƙarfi.
"B, Yaushe zaka fita?"
Muryar Ishaq ta janyo shi daga tunaninsa, sai kawai ya lalubo wayoyinsa a gefe da mukullin motarsa ya mike tsaye.
"Yanzu." Ya bashi amsa idanunsa na muna tsantsar nazarin abubuwan da shi kaÉ—ai yake hangowa.
Kuma da haka bai jira komai ba yayi waje, yana ji Inna Danejo na ƙokarin tsaida dashi amma bai tsaya ɗin ba, ya fita yana jin tasirin idanun Ishaq da ya biyo da kallo.
A harabar gidan ya gano Munaya tsaye tana waya, duk ta rikice kamar yadda take kullum sai faman gyara glasses ɗinta take alamun bayani ake mata ta cikin wayar, don haka bata ma ganshi ba har ya buɗe motarsa ya jata ya bar cikin gidan, kuma zai iya rantsewa zuciyarsa na lissafa kowanne wucewar lokaci kafin ya isa gida.
A ƙofar gidan ya ajiye motar don ƙwaƙwalwar sa ta gaya masa cewa ba zai iya jira har maigadi ya buɗe masa gate ɗin ba.
Ya shiga har ciki zuwa ɗakinsa, ya buɗe ƙofar da  ko waye ya shigo ɗakin zai ce wardrobe ce. A ciki komai yana nan kamar yadda yake hango shi kafin tafiyarsa.
Tebura ne da duruwoyi masu cike da files É—in takardu da kuma hotuna, ga tarin printers da photocopier a gefe, sannan bayan kayan rubutu akwai allo har kala uku É—aya na rubutu biyun kuma ya manne su da takardu da kuma hotuna. ÆŠaki ne da ko makaho ya shafa zai danganta shi da kalmar binceke balle kuma ga mai ganin da kallo É—aya da zai yi masa zai bashi amsar da ba sai ya tambaya ba.
A jikin allon nan bayanai ne da kuma hotunan mutanen da Jamal yayi mu'amala dasu tun daga lokacin da ya dawo daga karatu har zuwa ranar mutuwarsa, kuma a jikin kowacce takarda da hoto Ma'aruf ya zana tambarin × da jar marker alamun abinda yake nema bai ɓulle ga wannan  hanyar ba, kusan hakan ne ma a jikin kowacce takarda dake barbaje a ɗakin har kuwa da waɗanda aka yayyaga.
A wata durowa daga can ƙarshen ɗakin ya shiga fito da duk takardun cikinta har hannunsa ya kai kan wani file daga can ƙasa.
A cikin file ɗin tarin takardun Jamal ne wanda suka haɗa da duk certificate dinsa na gama makaranta da kuma takardun ɗaukarsa aiki a matsayin sabon ma'aikaci a kamfanin Baffa, takardun ɗaukar aikin ya shiga buɗawa ɗaya bayan ɗaya idanunsa na nazarin komai sai dai har yaje ƙarshensu bai ga komai ɗin da yake nema ba, ya zauna daga tsugunnen da yake, ya sake bin komai dalla-dalla, amma har a lokacin babu komai ɗin.
Hannayensa duka biyu ya cusa cikin gashinsa yana fitar da iska ta hancinsa... Tunani da yawa ke tsere a cikin kansa, yana ji yadda yanayinsa ke ƙoƙarin canjawa, ciwo na harbawa a cikin kansa yana gaya masa cewa zai koma halin da baidade da fitowa ba.
A lokacin ne kuma idanunsa suka hango masa wata ƴar mitsitsiyar takarda da alamun ta faɗo daga cikin file ɗin ne ba tare da ya kula ba, ya miƙa hannu da sauri ya ɗauko ta...
Rubutun Jamal ne, hanwriting É—in sa...
Mamaki ya kama shi tun kafin yafahimci me aka rubuta, don yasha buÉ—e file É—in nan ya zazzage shi amma bai taba ganin takardar ba. Kuma mamakinsa bai karu ba sai da hankalinsa ya gane masa me Jamal É—in ya rubuta a jiki.
Amina Sulaiman.
Gadon ƙaya.
***
Me kuke tunani ya haÉ—a marigayi Jamal da Amina?
Me Hajiya Kilishi ke yi da magungunan Ma'aruf?
Me yasa Ma'aruf baya son hayaniyar yara?
Me Ma'aruf yake son cimma ne game da bincikensa?
Waye ya saka kansa a takalmin Amina?😅
#Aysha Shafi'ee.
#FikraWriters
#FararWuta.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.