Wata Kishiyar Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: WATA KISHIYAR.txt
Chapter 5 of 66
Page 5
“Ban gane ba Nafi me kike nufi da ta haqura da binsa ko baki gane halin da yarinyar nan take ciki bane, yarinya na buqatar mijinta a kusa idan kuma ba halaka ake so ta fada ba se naji, nifa dama na gane take takenki kina so ki fifita bare akan yar uwarki ko Nafi. Kuma da kike zancen za’a shiga haqqin Asma’u ita Amirar daba uwace ta haifeta ba ai ba’a shiga nata haqqin bako” Adda Fatu ta fada cike da jin haushin Dada, se Dadar ta gyara zama tareda cewa
“Ni ba haka nake nufi ba amma gani nayi ai tun farko tare suke a can, yanzu ko cewa akayi suringa yi idan wannan ta je ta kwana biyu se wannan taje kinga bame yiwuwa bane tunda Asma’u tana aiki a garin bakuma ze yuwu muce tabar aikin ta ba tunda idan Amira ce a matsayinta muma bazamu bari a mata ba ko?
Ni dai a nawa ganin Adda ayi haqurin shi yafi a zauna lafiya tunda har komai ya daidaita tsakaninsu bana son wata rigima ta sake tasowa kindai san sharadin da Malam ya kafa mun dan Allah bana so ya sake ganin laifina akan lamarin gidan Bashir”.
Se Adda Fatu ta miqe nan da nan ta fara sababi da fadan maganganu ta inda take shiga bata nan take fita ba, ga baqin cikin rashin samun biyan buqata a gurin Bashir gashi da Alamu wannan Karon Nafi na nema ta bata matsala amma ina bazata sabu ba wallahi dole tasan abinyi. Miqewa tayi still tana masifar ta nifi qofa,
“Wato Nafi kina ganin yanzu kinkai matsayin da zaki qalubalance ni ko? Kin manta duk halaccin da nayi miki a rayuwa saboda qasa ta dade da cinye Naman Baffa da Inna dole ki watsar da maganar su tunda kina ganin yanzu kema Kin kawo qarfi. Na gode zan kuma tafi amma daga yau kisa a ranki baki da sauran wata yar uwa data rage miki a duniya tunda kin zabi Matar danki akaina da Yata shikenan Nafi na yafewa Duniya ke” ta qarasa tana rushewa Kukan munafunci wanda dashi take cin galaba akan Nafin.
Ta kuwa samu yanda take so dan nan da nan hankalin Dada ya tashi ta shiga son nuna mata ita fa ba abinda take nufi ba kenan,
“Idan har da gaske kike kuma kina so na haqura nida kawai kiyi yanda zakiyi Bashir ya dauki Amira ta koma kusa dashi, kuma baze yuwu yace Ze kwashe su su dukka ya kai can ba se dai ki saka shi ya dawo da daya ya dauki daya idan kikayi haka shine kadai Ze sa na haqura in ba haka ba wallahi ki saka a ranki baki da wata Yar uwa Fatu a raye”
Ita dai Dada son su rabu lafiya ya saka ta amince mata, dole ta hado yan kudaden hannunta dubu 30 ta bata tace gashi nan ta kaiwa Amirar ta riqe kafin Bashir din yazo se a san yanda zaayi haka ta rakata har get Addan na sake jadda da mata fa akan tana nan tana jiran saka mako da haka suka rabu.
Numfashi ta sauke bayan ta dawo cikin palour ta tazauna, gaba daya ta tasa ina zata kama akan wannan al’amarin. Har ga Allah bata so ta sake yin wani kuskuren akan na baya amma ya zatayi da Adda Fatu yar uwarta tilo a kaf fadin duniyar nan bata da kamarta. Addan tayi mata komai a rayuwa ya kamata ace ita ma ta saka mata da abinda ta mata. A zatonta Auran Bashir da Amira ya isa ga tukuicin kyautatawar amma se yanzu take dana sanin ma aikata hakan domin kamar ta bude wata qofa ce da Addan ta mayar da ita tamkar birin wasanta.
Ko da yaushe cikin daga mata hankali take tunda akayi wannan auran da ita dai bata ga amfaninsa ba in banda bacin rayuka da ya janyo da yawa, shigowar Nazir Autan ta ya sakata dagowa ta kalle shi
“Yanzu na hadu da fitinanniyar yayar ki a hanya seda tayi mun fashin 10k wallahi, gaskiya Dada ki ringa yiwa Adda fada abubuwan da takeyi basa dacewa. A yanzun fa ga kudi a hannunta amma ta tsaya suna fada da Dan Napep dan yace a 200 ze kaita gida”
“Hmm Allah ya rufa asiri kawai Naziru amma ni lamarin Adda ya fara bani tsoro, yanzu ma fa kaji abinda ya kawo ta” tiryan tiryan ta labarta masa yanda sukayi.
“Wallahi Dada ki kiyayi matar nan, ni dai ina ga Asiri take yi miki ma kike wasu abubuwan idan ba haka ba dan ta riqe ki ai ba baiwarta bace ke da kuma zata ringa juya ki yanda taso. Tun farko abinda muka guda a hadin wannan auran kenan amma kika rufe ido kika ce se anyi zumunchin ku ya qara qarfi ko ai gashi tun ba’aje ko ina ba kinzo kina dana sani. Shima Yayan banga qaddarar daya gani a jikin wannan mara mutunchin yarinyar ba daya yarda ya aure ta”
“To Naziru yaya zanyi Adda yar uwata ce da bani da kamar ta ka sani kuma farincikin Yayanta shine nata idan banyi mata ba a rayuwa ta wa zan yiwa?”
“Ai kuwa gashi nan, kafin da ki sake yanke wani hukuncin se ki tuna cewa Auranki kema yanzu lilo yake yi a garin faranta mata kuma baza muso ace Uwar mu ta shiga zawarci a wadan nan shekarun ba” ya fada ya miqewa dan ya fita dan dagaske Bala’in haushin Adda yake ji har ma da Dadan da yake ganin tana biye mata ne.
“Allah ma baze sa ba Naziru zan lallabata insha Allahu babu abinda ze faru ma” Dada ta fada itama tana miqewa dan neman abinda zata ci, ko karyawa batayi ba Adda ta doko mata sammako.
ADDA FATU
Bayan barinta gidan Dada gaba ta qara dan kuwa bazata koma gida yanzu ba dan tuni Amira ta gaya mata matar tazo karbar kudinta gata nan a tsakar gida tana ta zuba Rashin mutunchi akan Adda ta fito ta bata kudin ta sunce mata bata nan amma taqi yarda, gara ta qara gaba ko Allah ze sa ta dace ta samo wani abun koda taimakon da zesa Bashir ya turo musu kudin ne. Gidan Aminiyarta Haj Balaraba ta wuce, ta sami Balaraban a qofar gida an kira mata me Napep zata fita unguwa.
“Fatu daga ina da safiyar nan haka” ta fada tana qoqarin rufe gida.
“Ke zan tambaya Balaraba keda nasan se ki kai 12 ma baki tashi ba”
“Hmmm ta ina Kishiya na neman sabautani ina naga ta bacci, kinga yanzu ya akayi dan ni a tafe nake neman taimako zan tafi” Balaraba ta fada tana jefa muqulli a cikin jaka.
“Ai kawai muje dan nima matsalar ce ta kawo ni ma tattauna a hanya” nan suka fada Napep Balaraba ta fada masa inda ze kaisu. Suna tafiya Adda Fatu na jerowa Hajia Balaraba matsalinta.
“Ni na rasa wane irin shegen yaro ne Bashir wallahi naje gun malaman naje gun Yan Bori amma an kasa cin galaba akansa, ke har fa nafi ganin aikin kissa idan tayi masa akan na asirin nan wallahi dama Da Nafi nake samun yanda nake so a gurinsa to itama naga alamar tana so tayimun Bore. Ga shegiyar me kayan can da kika hadani da ita bashi kamar na masifa na kasa biyanta”.
“Tab ai seda na gaya miki daman ita fa Indo in kaci bashin ta wallahi toshe maka hanyoyin samu yake kika ce bakomai shiyasa kika ni kudi hannu muke sabga da ita gata bata san sabo ba akan dubu daya seta keta miki rigar mutunchi”
“Ai na gani kuwa yanzu haka fa tana can gidan tana ta tijara nidai na ce su Ummi su kulle qofa kar su bari ta shiga bare ta daukar kun wani abun, kudinta Dubu dari biyu yai saura da Mun samu kan Bashir zan tattara na biyata mun rabu kenan”.
“To ai shi wannan yaron fa se kin dage masa gaskiya amma bari muje nan gurin, Maman lurwanu ta kwatantamun tace aikinsa sha yanzu ne dan shi yai mata aiki akan Isah ya saki Kishiyoyinta dukka biyun rana daya yanzu bakiga yanda take shanawa a cikin gidan nan ba ita kadai” cewar Balaraba
“Kice Allah, ashe gara da nayo nan Allah yasa qarshen wahalata kenan (ko kuma farkon wahalar ki ba) in samu ina kafa Amira da kyau sannan in waiwayo kan nawa qananan kwarin ko da yake ni da zaman su da babu duk daya ai kin sani” haka suka ci gaba da tattauna wa har suka isa unguwar da aka mata kwatancen sedai ta kasa ganewa, sunyi tambaya kowa yace be san mutumin da suke nema ba kuma ta kira Number Maman Lurwanu a kashe.
Kamar Adda zatayi kuka ta kalleta tace “yanzu Balaraba ya zamuyi dan Allah wallahi na gama saka ran waraka ta zo” kafin ta bata amsa Me Napep da tunda ya dakko su bece komai ba, tsaf ya gama nade hirar su ta hanyar voice note daya kunna tareda fahimtar matsalar ko waccen su se ya kashe mashin din yace musu bari ya kama ruwa kafin su gama yanke shawara.
Can Nesa dasu yaje ya zaro wayarsa ya shiga kiran abokinsa aransa yana ayyana Banza ta fadi daga can bangaren aka daga wayar ana cewa “ungulu baka jewar banza da alama ta samu”
Dariya yayi kafin yace “yi maza ka shirya area, ka duba whatsapp na tura maka saqo nan da minti Ashirin zan qaraso idan ta saitu”
Dayan ya bushe da dariya yace”an gama kwaro kamar kasan wallahi dama ina ta lissafin ta inda zam samu kudin yiwa Latifa Anko gashi ta matsamin kwana biyu babu kasuwa, Allah dai yasa ta waru, se kun qara so toh” sukayi sallama.
Gurinsu ya dawo harda karbar pure water a wani shago ya fasa ya zubda rabi ya taho yana wanke hannunsa,
“To hajia ina muka nufa yanzu” ya tambaye su bayan ya kunna Mashin.
“Maidamu inda ka dakko mu kawai” Balaraba da abun duniya ya ishe ta ta fada, se ya cilla suka dau hanya yana jin yanda suke ta jimami. Daidai wani gidan mai ya tsaya ya sha, seda ya dan bata lokaci sannan suka ci gaba ya gama shirya abinda ze gaya musu se yayi gyaran murya.
“Am nace Hajia kuyi haquri fa dukda ban gane kan damuwar taku ba amma idan kuna so akwai wani guri da wancan satin nakai wasu passengers, can na jirasu suka gama gaskiya daga yanda naji sun fito nasan sun samu biyan buqatar data kai su, kun gama saqon daya daga cikin su daga Kano tazo ashe suka karbi Number dazu naje na karbo zan saka mata ta tasha akai mata” ya fada yana bude dan gurin da suke zuba kudi ya zaro baqar leda, basu san mene ne a ciki ba gadai shi harda suna da Number waya an rubuta ta wanda zaa turawa saqon. To wanda kwakwalwar sa ta toshe ai se a hankali ba tareda tunanin komai ba suka ce ya kai su, a ransa ya ayyana “Madallah” ya cilla kan mashin suka dau hanya dan yasan zuwa yanzu an kimtsa komai dukda haka seda ya sake yi masa text ya tabbatar masa komai is ready su taho.
Tafiyar yan mintina takai su layin gidan har qofar gidan me dauke da shago se kuma soro na shiga cikin gidan. Wasu yan samari biyu ya gani daga gefe kan dakali yai musu sallama tareda tambayar su ko Malam yana nan
“Ai kuwa ya fita amma nasan ba dadewa zeyi ba qilan ma yana hanya.. au ka ganshi ma muna maganar” daya daga ciki ya bashi amsa. Se ya nufi gurin Wizy abokinsa daya sha uwar babbar riga harda wani rawanin iskanci shi a dole ga malami ya miqa masa hannu suka kashe amma se ka zata musa baha sukayi. Cikin daga murya Yanda su Adda zasu jiyo su Wizy yace “Mal Kamar kaine ka karbi saqon hajia Larai dazu ko lafiya dai ko mantuwa kayi”
“Eh wallahi Malam nine ba mantuwa nayi ba wasu iyayen daki na na rako ne”
“Ah to to bismillah ku shigo ka barsu anan kuma kai Iliya me yasa baku bude musu shago sun shiga ba ko ka kaisu cikin gida gurin Maimuna kan nazo” ya fada yana hararar samarin da suke zaune. Seda Iliya yayi dagaske gurin riqe dariyar sa kafin yace “Malam ai ta fita gidan suna itama kuma ka tafi da muqullin shagon ai”
“Anyi haka ya fada yana bude musu kofar suka shiga gaba daya, bayan sun zauna Me Napep yace bari yaje daga waje idan sun gama shima se yazo a bashi taimakon kasuwa.
Malam ya jawo faranti me dauke da yashi ga kuma carbi me dubu ya hau ja yana muimui da baki nan kuma yana faman zane zane sannan ya dago ya kalle su “toh hajia dawa Zamu fara?” Ya tambaye su.
Hajia Balaraba ce ta fara matsawa tace “Malam ni matsalar kaina ce a fara dani dama..” se ya dakatar da ita, “ki bari mu duba abunda bamu fahimtaba se kiyi mana bayani da kuma matakin da kike so a dauka.
Tiryan tiryan ya ringa jera mata zance kamar me gani a film kai har abinda basu fada Me Napep yaji ba seda Wizy ya canka ya fada se kuwa tace kai Malam aikuwa hakane wallahi, yana ta tiqar dariya a qasan ransa to ai labarin duk daya ne dukma wadda tazo indai akan kishiya ne banbancin basu da yawa. Seda ya gama ratta ba mata zance Adda da me gefe ta gama yin Ammana sun zo inda zaa magance musu matsalar su harta gama Ayyano Yanda zasu juya Bashir kaman Tanda a waina.
Tsaf Hajia Balaraba ta gama gaya masa yanda take so ayi nan kuwa ya yanka mata 50k babu neman ragi ba komai ta cake masa su to taji sauqi akan ubannin kudin data ke kashewa babu biyan buqata. Allonsa ya jawo da tawada ya hau rubuta abunda in zaka kashe shi be san menene ba ya gama ya miqa mata da kwano da ruwa yace ta wanke idan taje gida ta guntsi rabi ta fesa a kofar dakin kishiyar ko inda tasan zata taka rabin kuma ta kuskure baki ta zuba a miya kowa na gidan yaci to daga nan babu me jin maganar wani se tata.
Wasu qullin Jan Maganin da kore ya sake dakkowa ya bata su kuma yace ta ringa jiqawa kwana 7 tana sha sannan ya qara mata da wani kuma a jarkoki guda biyu yace ta juye a bokiti ta qara musu ruwa ta ringa sha shima mijin ta san yanda zaayi yasha koda tea ne ta dafa masa dashi sauran aiki kuma karta damu zeyi daga nan shidai idan buqata ta biya kar a manta dashi (kuji dan banza 😂😂Koren Magani na sabara da Jan magani yake ba wa duk wadda tazo se na cikin jarka kuma maganin Basir ne ko banza ai ya temake so ko 😂😂😂😂😂😂).
Adda ce ta matso aka buga mata nata duban se ya kalleta “Wace Mace ce haka gata nan dai Fara kyakykyawa kamar ma bata da lafiya tana gadon Asibiti”
Ai caraf ta amshe “Asma’u ce ita ce kishiyar yar tawa” gyara zama yayi yana ayyano yanda ze tatsi matan nan yace
“Kamar a kudu take fa wannan kai” se yai shiru kafin ya ci gaba
“Tab di hajia akwai babban aiki a gabanki fa dan koma wacece wannan tasha kan shi wannan mutumin sosai dan kuwa Arnan kan dutse ne suke mata aiki an hada shi da gungun Aljanu suna gadinsa gaskiya wannan aiki yafi qarfina”
“Ai Adda kamar zata rushe da kuka tace “haba Malam ba abinda ya fi karfinka ai (haba Adda Allah ne kadai keda maganin komai) ka duba ka taimakamun nidai a tarkato mana hankalinsa ai ko baya auran yata ni me tsayawa na nema masa taimako ce tunda dana ne ai dan yar uwata”.
Zama ya gyara yace “abinda kamar wuya gaskiya kin san aiki da kafiran Aljanu akwai wahala amma in zaki saki kudi ayi musu yanka kinsan su jini suke so to wala Allah a dace”
“Malam indai zaa samu biyan buqata ba matsaka yanzu kamar me zaa yanka?”
“Gaskiya hajia a qalla za’a yanka musu raguna 20” seta dafe qirji tace Malam ina zan samu kudin nan yanzu fa nake maka bayanin na biyan bashi ma nake nema ni a fara rufemun bakin matar nan ma tukunna ta manta da zancen kudin”.
“Wannan duk ba matsala bane kuma zaki iya ringa bayarwa a hankali ai in kin so ma kiringa yankan da kanki amma akwai kalar dabbobin da ake so da kuma abinda ake fada in za’ayi yankan in kina da wanda ze miki duk sena gaya miki ai”
“Aa malam zaa mata komai anan” Hajia Balaraba ta fada
“To ba matsala”
“Kamar nawa kenan Malam” ta tambaya
“To akwai qauyen dana ke siyo dabbobi ana samun qosashshen rago dai daga dubu Arba’in kinga a qalla guda koma dubu Dari hudu kenan amma zaki iya ringayi a sannu in so samu ne dai cikin wata biyu a kammala aikin”.
Nan dai Adda ta zazzage masa dubu tamanin kudin data harhada zata rage biyan bashi tace in an kwana biyu zata kawo abinda ya samu, ita be bata komai ba se wani abu kamar goro yace idan matar tazo ta saka a bakinta ta ringa taunaqmwa tana mata magana kamar remote haka zata controlling nata aikin Bashir kuma Wannan Ze duqufa yai tayi itama Amira jin tana da ciki ya nemo wani garin Maganin zaqi dana sanyi da aka aike shi ya kaiwa Yayar sa da take da ciki ya bata yace ta kai mata tayi tasha zuwa sanda Bashir zezo daya kwanta da ita anci rabin aiki.
Kamar wanda yai musu kyauta suka ringa zabga godiya ya basu Number wayar sa suka fito Me Napep har ya gaji bacci ya dauke shi fitowarsu ta farkar dashi,
“Gaskiya kun dade hajia yau balance kawai zaku bani na maida Machine din nan na huta dan har na gama gajia” ya kunna suna shirin tafiya har sun ja Iliya ya tsaidasu akan Malam yace ya manta da taimakon kasuwar ne, se suka koma ya barsu a cikin mashin ya shiga.
Be zauna ba 40% 60% suke raba duk abinda suka samu Wizy se dauki 50% ragowar 10 ya bawa su iliya da sauran masu yi musu cover a harkar, cas ya cake masa kudin sa tareda bashi wata qatuwar takadda da aka nade kamar laya yace zasuyi waya ya fito, ransa fes suka kama hanya bayan ya saqala Takaddar a gaban mashin wai ta kiran customers 😂😂 ikon Allah kuwa duk inda suka gifta se an tsaidashi yace drop ne har ya ajiye Hajia Balaraba ya wuce Da Adda Fatu dan tace gara taje ta kai mata ta fara sha tunda yau Alhamis a qa’ida gobe Juma’a ze zo
To se muce Allah kauda tsautsayi da Asara 😂😂😂😂https://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.