Complete Hausa Novels

Fareedah Nabeel Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Fareedah Nabeel Complete Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 1 of 2

[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹
*FAREEDAH NABEEL*
🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL✍🏻*

*EDITED BY UNCLE YUSEEPA* NADABO

*WANNAN PAGE ƊIN NA SADAUKAR DASHI GARE KA, UNCLE YUSEEPAH NADABO,THANKS FOR HALACCIN KA AGARE NI ALLAH YA BAR ZUMUCHIN MU FATAN ALKHAIRI A GAREKA ALLAH YA ƘARA MAKA BUƊI DA ƊAUKA KA, FATAN ALKHAIRI NAKE MAKA A DUKKAN RAYUWAR KA,UBANGIJI ALLAH YA KAREKA DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKA HASSADA, ALLAH YA ƘARA MAKA BASIRA DA ƊAUKA KA INA MATUƘAR GODIYA*

*FAREEDAH NABEEL DEDICATED TO :- ƘAWATA WATO XAYYNEB💤💤(XEXEN FASAHA)*

*SAKON FATAN ALKHAIRI ZUWA GARE KI ƘAWATA WATO XAYYNEB 💤💤 (XEXEN FASAHA) ,THANKS FOR KULAWARKI AGARE NI ALLAH YABAR KAUNERH ,FATAN ALKHAIRI NAKE MAKI A DUKKAN RAYUWAR KI,UBANGIJI YA KAREKI DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKI HASSADA, WALLAHI ALLAH INA KAUNAR KI HAR CIKIN RAINA, ALLAH YA ƘARA MAKI BASIRA DA ƊAUKA KA KANA ALLAH YA ƘARA MA MAMAMU LAFIYA TARE DA NISAN KWANA*

*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I'm
selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951

Bismillahirrahmanirrahim

Da sunan Allah mai rahma mai jin kai
dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah mai kowa mai komi sarkin daya halicci sammai da kassai batare daya kwaikwaya awajen kowaba madaukakin sarki me kowa mai komai

Wannan littafin ƙirƙirar ren labarine. banyi shi dan cin mutuncin wani ko wataba.
so idan yayi shige da halin mutum yayi hakuri nayi ne domin fadakarwa da kuma nishadantarwa, badan cin mutunci ko izgili ba
yadda na fara wannan sabon littafin da Bismillah inna rokon ALLAH yasa in gama da ALHAMDULILLAHY

*🌺chapter 1-2🌺*

*MINNAH*

Wani katafaren gida ne da yake dashe a unguwar shiroro road
na hango!
tsarinsa da kyawunsa ma Abin kallo ne.wanda idan har bakasan a inda kake ba .baza ka iya tantance wace ƙasa kake ba
kai Daga gani kasan Allah yayi baiwa ga dukkan wanda Ya mallaki wannan gidan,

_____________________________
*GIDAN NABEEL KENAN*
_____________________________

kyakkyawar mace ce Ta bugawa a jarida na hango,doguwa mara jiki shape d'in bakin ta gwanin ban sha'awa gashin girarta ta cika sosai .gashinta na ido zara-zara ,hancinta dogo ne de-de masali dan bai yi tsayi dayawa ba, Kuma bai Yi gajarta ba,
fuskarta it'a ba Mai fad'i ba ,kuma ba mai tsayi ba ,idanuwanta de-de Misali dan suma basu yiyawa ba Kuma basu yi ƙanana ba ,duk da cewa ba fara bace chocolate colour ce hakan ba zai sa ace ita ba kyakkyawa bace ba dan ta haɗA dukkanin abubuwan da ake bukatar agani wajen y'a mace
bata da jiki Kuma ba siririya bace Dan babu wani mahaluk'in É—a namiji da zai ganta bai ji ya yaba da irin tsarin halittarta ba,

*FAREEDAH KENAN*

shekarunta basu haura shekaru ashirin da bakwai ba ,ko murmushi tayi sai ya ratsa ko inna na jikin É—a namiji bare kuma kallonta
mai cike da birgewa...

Zaune take a saman one seat a gaban dressing mirror ,tana shafa turaren jiki wato humra , kasancewar ta Mace ce mai son k'amshi , tana shafawa ne a duk bayan lokacin da ta kammala yin kwalliya, domin kuwa a yanzu ma kwalliyar ta kammala dan har ta saka kayanta ,
fuskarta babu wani makeup sosai daga powder sai jagira da tayi da kuma É—an lipstick da ta shafa a labb'anta , tayi kyau matuka musamman Irin tsarin shigar da tayi na riga dogo ,haka kalar kayan blue da yellow abin gwanin birgewa,
tana gama kammala shirin ta ,sannan kuma ta ƙara kallon madubi sannan ta juya ta nufi hanyar fita daga cikin ɗakin cikin salon takun tafiyar ta mai
matukar É—aukan hankali,....

Ahankali take tako steps din benen tare da saukowa daga saman upstairs, kana jin karar takun takalmanta kas kas kas cikin natsuwa

tana gama k'arasowa cikin tsakiyar parlourn ,daidai lokacin ne kuma wata matashiyar yarinya ta fito daga cikin kitchen,
K'arasowar ta Cikin tsakiyar parlourn yayi de-de da fitowar Azmerh daga cikin kitchen , É—auke da faranti Ahannuntah ,wanda ta É—aura masu food flask flask d'in abinci asama Tare Da plate and spoons and forks,
daga ganin alamun abincin dinner su na dare ne, haka zalika yayi de-de da kai dubanta zuwa ga kofar fitowa kitchen a de-de Lokacin ne kuma idanuwanta suka sauka a kan Azmerh,

Tsayawa FAREEDAH tayi turus atsakiyar parlourn tana kallon Azmerh,cikin ranta tace son maso wani koshin wahala , Allah dai ya kyauta wa wasu masu matattun zuciya ,musamman marasa zuciya Irin su Azmerh ,tana gama k'arasa maganar zucinta ,direct inda Azmerh take tsaye atsakiyar parlourn tana jera abinci asaman center table É—in dake tsakiyar parlourn FAREEDAH ta k'araso gunta cikin fara'a FAREEDAH ta kalli mumunar fuskar Azmerh Kafin cikin murmushi FAREEDAH ta buÉ—e bakin ta tace"
Azmerh kenan ,..
Agaskiya kina matuƙar ji da yayan nan naki,yau tun daga safiya zuwa dare hidimarsa kike!...

"D'agowa. Azmerh tayi tare da mik'ewa tsaye ,kallon banza ta aikawa FAREEDAH Dashi HaÉ—i da gallamata Harara kafin ta haÉ—e rai, Cikin daka mata tsawa Azmerh ta buÉ—e bakinta tace "kinsan shi doki girmansa da haniniyarsa sune suke nuna kasaitar shi..
"Dariyan dole FAREEDAH ta kyalkyale dashi cikin dariya FAREEDAH tace" gaskiya ne kam ,wannan haka yake, kin yi gaskiya yan mata

Duban Azmerh FAREEDAH tasake yi dakyau tukun Kafin daga bisani cikin tsananin farin ciki FAREEDAH ta buÉ—e bakinta ta É—ora da cewar"Ni dai fatana Allah yasa ki samu abunda kike nema....cikin fusata! Azmerh ta katseta ta hanyar fad'in "....

"Bangane abunda kike nufi ba?

"Tsayuwa FAREEDAH ta gyara tukkun Kafin Cikin smiling FAREEDAH tace"ina nufi Allah yasa wanda kika yi domin sa yayi masa maganin yinwa da zai kwaso

"Cabd'ijam inji cewar Azmerh tana fesar da wani irin huci!

Sannan cikin tsananin masifa haÉ—i da bala'in da suke cinta ta cigaba da cewar" ai ko ya zama dole gyaÉ—a tayi mai ,idan taki tasha matsa,
tun daga safiya zuwa dare in bata lokaci na ina abu guda É—aya,tabbas yau makwabta suma sai sunji k'amshinda basu taba jiba

"Haha haha haha FAREEDAH tasake fashewa da dariya har da zubar da hawayen dole sabida tsabar shan dariya
Cikin dariya FAREEDAH tace"hmmmm nidai bari inje in k'arasa yin aiki na kar cikina ya fashe,. .
"Kutmar bura uban aiki ɗin da zakije k'arasa ta ɗura ashar, ba aiki ba ubanki dai, shegiya yar gidan bokaye, Yar matsiyata kawai. ke har wani aiki kika iya! .in banda shirme da jagwalgwalo ,shashsha kawai yar matsiyata ,,,,,kuma bari kiji , idan ma baki sani ba to yau kisani insha Allahu yau idan yayana yadawo daga gun aiki yau dolenshi ya amince da maganar auren mu,kuma duk maitarki da bin malamanki akan kar maganar aure na da yayana kada ya yiwu, insha Allahu wataran Kamar anyi an gamane, dan ni nasan ta hanyan da zanbi in shawo kan abuna,so daga yau ina son kirubuta ki ajiye muddin ni Azmerh na shigo cikin gidan yaya NABEEL a matsayin matarsa tofa shakka babu sai nasa shi ya sake ki , kai wataran sai nasa kin bar gidan nan,dan nina san me na shirya, dan wallahy Allah natsaneki matuƙa, ji nike kamar in shake maki wuya har sai kin mutu kafin nasake, sbd yanda nake bala'in jin haushin ki acikin rai na,

Matsowa Azmerh tayi daf da FAREEDAH kamar zata shige cikin jikin ta ina nufin face to face sannan tasaki wani murmushi irin na mugunta Azmerh ta É—ora da cewar
"baki san ni bane har yanzu dan inda ace
Ƙin san ni, Wallahy zakiyi MATUƘAR jin tsoro na! sai nasa kin bar gidan nan
Taka rasa zancenta
tare da k'wafa

"HAHA haha haha FAREEDAH tasake fashewa da dariya sannan tace"Allah ko yan matah ,.....

OKAY....
Allah yanuna mana lokacin Kawai FAREEDAH ta faÉ—a tana mai É—aga kafaÉ—ar ta alamun ko ajikin ta kenan, kana cikin nutsuwa ta juya direct ta nufi hanyar kitchen Tare Da shigewa
kitchen abinta.
_____________________

Bacin rai mai tsanani ya sake rufe Azmerh cikin ranta tace wai yau ni wannan yar matsiyantan take wa dariya, "ita dai FAREEDAH haka Tabar Azmerh da zage-zage
haÉ—e da tsinewa FAREEDAH d'in Albarka " 'kwafa Azmerh tayi tare da bin bayan ta

Da misalin ƙarfe takwas da rabi na dare....
___________8:30 pm, wani kyakkyawan matashin handsome guy ne ,ya turo kofar parlourn ,sanye yake cikin wasu kananan kaya da suka yi mutukar ansar jikinsa ,kana kuma yakara bayyanar da kyawunsa da kwarijininsa NABEEL ya hadu iya haduwa,kyakkyawane NABEEL asalin kyakkayawa kuwa domin duk inda ake batun kyau to wannan magidancin zai answer first number ,Cikin parlourn
ya shigo tare da furta sallam

"Assalamu alaikum!"

AMIN walkslm inji cewar Azmerh ,"cikin natsuwa NABEEL ya k'arasa shigowa cikin tsakiyar parlourn, samun guri yayi ya zauna a saman two-seater yana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya',',,, kallon kyakkyawar fuskarsa Azmerh tayi kafin cikin kulawa ta buÉ—e bakinta tace"..

"Sannu da zuwa !..
yaya ina wuni!!,.
ya aiki ya jama'a!!! ?..

"Cikin sauri ya jiyo ya kalle ta dan shi baima san akusa da Mutum ya zauna ba,
sabida tsabar gajiyar daya kwaso, shima É—in duban Azmerh yayi dakyau tukun Kafin cikin kulawa ya buÉ—i bakinsa yace"aaa yau kece a gidan?'...
"E Wallahy yaya..
Sannu da zuwa
Ya aiki?

"Alhamdulillahy...

"To madallah

Gyara zama Azmerh tayi HaÉ—i da Washe baki sabida yau taga yadan sake mata fuska, Cikin fara'a Azmerh ta cigaba da cewar"yaya nerh yau girki nayi maka na musamman!"
firgigi NABEEL yayi kamar wanda aka tsikara yasake dubanta kafin cikin É—aure fuska NABEEL ya buÉ—i bakinsa yace"kikai wa gida dai,ai bani kaÉ—ai ne a gidan ba

"To ni dai yaya kai kaÉ—ai na girka mawa, Janyo masa table É—in tayi gabansa kana ta shiga serving É—insa
Ahankali Cikin nutsuwa ya kai hannunsa kana ya debi abinci acikin cokali , yakai bakinsa ai nan da nan fuskarsa tasauya kamar wanda yagumtsi guba
tun kafin ya fara taunawa yaji Abincin tabal ba daÉ—i sai wani uban gishiri, Sannan kuma yaji d'andano ba irin wanda yasaba jiba
,yana tauna abinci yana tabe bakinsa tareda yamutsa fuska,haka ya tauna abinci yana tah yamutsa fuskarsa ."yayin da ita kuma Azmerh ta kafe shi da ido tana mai famar washe baki
, shi kuwa Nabeel sai famar yamutsa fuskarsa yake
Kai Ka rantse kashi yake taunawa, dan dakyar ya iya haɗiye abinchin dake baƙin sa cokalin hanunsa ya ajiye.. ɗaure fuska yayi cikin ɗaure fuska ha'di da bata fuska ya shiga 'kwalawa FAREEDAH kira

"FAREEDAH!
inji cewar NABEEL cikin tsansar
ɓacin rai

FAREEDAH NABEEL!!

NABEEL yasake kwalawa FAREEDAH kira akaro na biyu

"NA'AM .....

Injicewar FAREEDAH tana mai amsa masa kiranta dayayi mata, kana Cikin sauri ta fito daga cikin kitchen

"Mtsww! Wata uwar tsaki Azmerh taja sbd duk duniya ta tsani taji ankira FAREEDAH da FAREEDAH NABEEL

"Ita kuwa FAREEDAH kai tsaye ta nufi inda suke zaune ta k'araso gurinsu, kallon kyakkyawar fuskarsa tayi kafin cikin fara'a HaÉ—i da kulawa had'i da sanyayen murya
FAREEDAH tace"..

Sannu da zuwa!my Prince
Ka dawo!!
Ya aiki ya jama'a?!?..

ÆŠago kai NABEEL yayi tare da kallonta kafin cikin sanyin murya NABEEL ya buÉ—e bakinshi yace "
yawwa sannu
alamu yana cikin ɓacin rai

"Cikin murmushi FAREEDAH tace'kalbinerh yau ka ji É—anÉ—anon ba irin wanda ka saba ji ba ko?

"Kallon kyakkyawar fuskar matansa NABEEL yayi kafin cikin sanyi muryarsa HaÉ—i da tsananin kaunar matarsa ya buÉ—i bakinsa yace"babu wani nau'in abincin da zan ci ko in saka shi abakina har É—anÉ—anonsa ya ratsa harshena, matukar ba hannuwanki suka sarrafa abincinba ,ina nufin matukar ba hannuwanki ne suka haÉ—a mana abincin gida nan ba

"NATSUWA FAREEDAH ta karayi sannan takura
masa idanu
kafin FAREEDAH tace".....

Ban fahimce ka ba?

"FAREEDAH wannan abinci daga ji bake kika yi shi ba, in kuma ke É—in ce To akwai sa hannu wani a ciki,dan haka yi kokari ki kawo min.ko da taliya ce kid'an bararraka min.

"Kan bura uba!!! Azmerh tazabga ashar saida NABEEL da FAREEDAH duk suka waigo afirgice suka dubi inda Azmerh take tareda zaro idanunsu sabida tsananin mamaki.....

Yayinda Ita kuma Azmerh ta mike tsaye tana mai cigaba da cewar"..

Amma NABEEL lallai kai É—an rainin hankali ne ,...

Inji cewar Azmerh cikin tsantsar zafin rai.

Sannan cikin faÉ—a da masifa HaÉ—i da tsananin bala'in da suke cinta Azmerh ta cigaba da cewar...
"In bata lokaci na!
In bata ajina!!
Tun daga safiya zuwa dare, ina Abu guda É—aya, amma daga karshe kayi Allah wadai da bajinta?
kallon Azmerh NABEEL yayi kafin cikin É—aure fuska NABEEL ya buÉ—e bakinsa yace"Azmerh babu wata mace me aji indai har FAREEDAH NABEEL tana nan, sannan kuma kin daÉ—e da sanin sirrina na zama na da FAREEDAH.tun Farkonsa har da karshensa dan haka babu wata mace in ba FAREEDAH ba,..

"Tsawa Azmerh ta bugawa NABEEL cikin k'araji kamar zata dake shi ta furta"
in hakane kuwa wallahi ka zalince ni, kuma zan iya cewa
Allah ya saka min,...

Mik'ewa tsaye NABEEL yayi cikin tsananin ɓacin rai NABEEL bai tsaya wata wata ba ya sauke mata mari" jikake tasssssss amatukar firgice Azmerh ta dafe gefen fuskarta inda taji saukar mari Sannan cikin zubar da hawayen Azmerh tace"...

Yaya NABEEL ni ka mara,?

"Cikin ɓacin rai NABEEL ya daka mata tsawa yace"an mare ki ɗin ko zaki rama ne?

Cikin sauri FAREEDAH ta furta"haba NABEEL bansan ka da saurin hannu haka ba
"Cikin ihu Azmerh tace "Dan Allah gafara can ,munafuka, ke har kina da kalmar da zaki faÉ—a tai tasiri ,ban cin duk maganganun da kika faÉ—a masa akunnensa
"cikin sanyi murya FAREEDAH tace"

"Allah ya baki hakuri Azmerh,ni dai asanin da nayiwa mijina ,baya cin abincin ko wace mace in ba na matarsa ba ,shiyasa na Tanadar masada abincin shi .ba tare da na gaya maki ba .amma saboda alakan dake tsakanin ki dashi ,shiyasa na Kyale .

"Cikin sauri NABEEL yace"me kike wani bata hakuri , hakurin me kike bata,Dan Allah rabu da ita ,kawo min abincina Dan Allah ni yunwa nikeji

"Cikin fushi Azmerh ta É—auki Jakarta da mayafinta ,tare da janmasu dogon tsoki mtswww Kafin ta furta
"Allah ya isa na!
Allah ya isa na!!
Allah ya isa na!!! Har sau uku
sannan ta nufi hanyar fita daga cikin parlourn Tare da ficewar, daga gidan gaba daya

"Cikin daga murya FAREEDAH tace"Azmerh dan Allah kiyi hakuri ki dawo ,"NABEEL yace
"FAREEDAH dan Allah ki kawo min abinci ,ki rabu da 'yar iska, yar rainin hankali kawai
"Cikin sauri FAREEDAH ta juya direct ta shige cikin kitchen É—insu ta debo flasks É—in abinci takawo parlour ta shiga serving É—insa,
Cikin nutsuwa ya shiga cin abinchinsa cikin kwanciyar hankalin su, SBD Abinchi yayi masa masifar daÉ—i sosai.
yanaci itama yana bata abakinta ahaka har suka gama cinye abincin su ,suna kammala cin abincin ta kwashe kayan da suka bata taje kitchens ta wanke su, kana tadawo suka cigaba da hirar su cikin farin ciki HaÉ—i da kwanciyar hankali da kaunar junarsu...

_____________Da misalin ƙarfe goma sha daya na dare.....
Kwance FAREEDAH da NABEEL suke a saman bed acikin bedroom ɗinsu, Yayin da FAREEDAH take kwance a saman kirjin NABEEL ,dago kanta tayi ta kalli NABEEL kafin cikin sanyi murya FAREEDAH ta buɗe baƙinta tace"yaya NABEEL meyasa bazak......,in bai bari ta ƙarasa faɗin abunda take son faɗa ba ya had'e bakinsu guri guda yayi, cikin nutsuwa ya shiga tsotsan harshenta da salonsa na janye zuciya gaba daya baya cikin hayyacinsa tsotsar bakinta yake sosai , wani irin dadi yake ji sakamakon tsotsar bakinta, duk Ya sanye mata yawun bakinta, haka zalika ita ma ta dinga kar'bar nasa yawun tana shanyewa,
ya jima yana kissing dinta batare da gajiyawa ba, sai da ya kashe mata jiki da salonsa
yadan gyara kwanciya inda yamaidata kan bed shikuma yatashi zaune tare da mika hannuwansa daidai kan wuyan rigarta ahankali ya tubeta mata Kayan jikinta
harshen sa ya fara yawo a jikinta ,yarrrr taji tsigan jikin ta ya tashi shafa kirjinsa ta fara yi zuwa kasan mararsa.zura harshen sa NABEEL yayi cikin kunnenta tare da faÉ—in"Allah FABEEDAH abukace nake , PLEASE kibar duk wata maganar da zakiyi tukkun please kiji da yaronki haka ya dinga kashe mata jiki da salonsa Ahankali ya ringa gangarowa a sassan jikinta yana bata zazzafar kissing a sassan jikinta har ya gangaro kasanta cikin nutsuwa ya fara fingering É—inta cusa hannuwanta tayi cikin sumar k'ansa tana yamutsawa k
H tayi Tare Da kwantawa a Saman kirjinsa,zuwa can NABEEL ya mike Tare Da É—aukar ta cak sai bathroom suka shige

*_WASHE GARI_*
Da misalin karfe goma na safe da wasu yan mintoci, tsaye FAREEDAH take a dining area, Cikin nutsuwa FAREEDAH take shirya dining table É—in kana ta Kawo wasu abubuwa da ake bukata na karyawar safe harda su drinks Suma duk tajera su asaman dining table, tana cikin haka saiga NABEEL ya sauko daga saman up stairs, direct dining area ya nufa, NABEEL yana Gama k'arasowa dining area É—in tsayawa yayi yana kallon kyakkyawar fuskar matansa,zura Mata ido yayi kamar tsohon maye batare da yace da ita komai ba ..

ÆŠago kai FAREEDAH tayi Tare Da kallon kyakkyawar fuskar NABEEL Kafin cikin tsantsar kulawa FAREEDAH ta buÉ—e bakinta tace"

Har ka fito kenan?

"Murmushi NABEEL yayi tare da rungumota jikinsa na 'yan wasu dakiku ita kuwa kara shigewa jikinsa tayi ta langabar da kanta akirjinsa ayayin daya daga hannunsa nadama yana shafa tundaga tsakiyar kanta harzuwa karshen kitson dake kanta sannan yadagota daga jikinsa yadan ja dabaya kadan yakura mata idanu kamar baitaba ganintaba

sannan cikin murmushi NABEEL ya buÉ—e bakinsa yace"

Eh rabin rai É—ina

HAR na fito,..

Barka da aiki yar aljanna!

"Yawwa ina kwana?

"Lafiya kalau

Cikin nutsuwa NABEEL yah Kai hannun sa ya ja kujera sannan ya zauna a saman kujeran , Cikin kulawa NABEEL ya dubeta
tare da faÉ—in"

Baiwar Allah kenan

kafin na tashi daga... na tabbatar da kin kammala min komai ,...kai tsaye nike shiga banÉ—aki , dan na tabbatar da cewa kin riga kin had'a min ruwan wankah sai dai ince zan watsa ruwa,.ko ince zan yi wanka zance

"Murmushi kawai FAREEDAH ta ke famar sakewa batare da tace masa komai ba

"Yayinda shi kuma NABEEL ya cigaba da cewar"daga na fito parlourn kuma na tabbatar da cewa kin gama komai na karin-kumallo na wanda zan ci insha Kafin in tafi wajen aiki .bazan bukaci komai ba

"Kallon kyakkyawar fuskarsa FAREEDAH tayi Kafin cikin tsantsar farin ciki FAREEDAH ta furta"

Haka ne kalbinerh

To yanzu a nan gurin mai kake so a fara zuba maka?

"Kamar kullum yar aljanna .inji cewar NABEEL sannan cikin murmushi NABEEL ya buÉ—e bakinsa ya É—ora da cewar"nasan kin fini sanin abun da nike fara karin-kumallo dashi,da kuma wanda nike gamawa da shi , cikin nutsuwa FAREEDAH ta shiga serving É—insa

"Cikin sauri NABEEL ya furta"
Aaaa,Ai yayi yawa ,
kice gara dakika ankarar dani badan haka ba da kin zuba min abinci da zan kasa ci
itadai FAREEDAH girgiza kai kurum tayi tana mai famar sakin murmushi

Zaunar da Ita yayi asaman cinyarsa kafin cikin tsantsar farinciki NABEEL yake fad'in "

Allah ya yi maki albarka, mata ta,rabin rai Allah yasa ki gama da duniya lafiya kema Allah ya baki wanda zasu kula da ke kamar yadda kike kulawa dani, Allah ya ƙara miki lafiya Tare Da nisan kwana, FATAN ALKHAIRI NiKE MAKi A DUKKANiN RAYUWAR Ki UBANGIJI YA KAREKi DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKi HASSADA
NAGODE
NAGODE FAREEDAH
NAGODE FAREEDAH
NABEEL TAWA
"Cikin smiling FAREEDAH ta kai hannunta a kansa tare da shafa masa lallausar gashin kanshi kafin ta furta

"AMIN YAH RABBIL A'ALAMIN my sugar baby,nima haƙa ina matuƙar godiya da kulawar ka agare ni Allah ya bar mu tare

Wash nagaji FAN'S
Inason kusani idan har naji shiru banga zazzafar comments naku ba

To shakka babu kuma kunji shiru
Lovers😍🥰😘

HEY
MARAICIN AZRAH FAN'S CLUB
daku nike
Ku tashi daga barci
Wallahy Allah ko
NARUFE gidan
Kuma kusan Wannan ƙaramin aiki nane ehem🤷🏻‍♀️Haba mana malam kullum gida kenan shiru shiru kamar makabarta ko yar Sada zumunci nan bakuyi*

*ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI*

#COMMENT'S PLEASE !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!

*A'ISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹
*FAREEDAH NABEEL*
🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*AISHA FULANI GAL*

*EDITED BY UNCLE YUSEEP NADABO*

*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*

*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I'm
selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951

*🌺chapter 3-4🌺*

BOSSO ESTATE

__________NABEELAH _______

Wata kyakkyawar yarinya ce tabugawa a jarida na hango, fara ce sol kyakkyawar matashiyar budurwa ce, Asalin kyakkyawar kuwa domin duk inda ake batun kyau to wannan matashiyar budurwar zata amsa first number, Sanye take cikin wata koriyar atamfa me ratsin ruwan hanta ajiki É—inki babu karya yayi matukar kyau sosai sai dai anci ma atamfan mutunci sosai riga da sket ne aka yi mata 8piece's kuma ya yi mata kyau dan duk wani kyawun dirin ta yagama bayyana ...

_____NABEELAH KENAN ____
Wanda bata haura shekara goma sha shida...... A duniya ba ta had'u iya haduwa dan komai nata me kyaune, gwanin birgewa,,.. Tsaye NABEELAH take a cikin bedroom d'inta, daga ganin alamunta waya take yi,
wayace kare a kunnenta, , cikin zazzakar muryarta mai matukar dad'in sauraro take magana, "..

Alright to gani nan fitowa

Cikin nutsuwa ta juya kana ta nufi hanyar fita daga cikin É—akin cikin salon takun tafiyar ta mai
matukar É—aukan hankali,....
Acikin parlourn su ta tadda Hajiya Nafisat tana zaune a saman two-seater daga ganin alamunta tana zaman jiran fitowar y'ar tatace,..

Zaune take a cikin hamshakin parlour d'inta, kallo daya zaka mata kasan dukiya sun zauna mata, ga wata Tsaleliyan phone d'inta kiran iPhone 15 agefen tah,.
Ta hakince Sai takama take yi da gadara, yayinda wata Ma'aikaciyar Gidan take ta famar mata fiffita, duk da uban sanyin dake falon kuwa, daga ganin alama ita ko sanyi bataji. a cewa ita zafi take ji,
da sanyi safiyarnan, Cike da izza take kad'a yan-yatsun tah wanda suka sha gwala-gwalai, Saman kyakkyawar wuyanta Shima yasha ado da sarka Mai ban mamaki.
Sannan ta gyara sumar kanta, Sai sheki yake, sannan ta daura mashi, Dan kwali irin daurin ture kaga tsiya nan.

______HAJIYA NAFISAT KENAN, WATO MAHAIFIYAR SU NABEEL D'IN FAREEDAH,

Ita ko Ma'aikaciyar Gidan Tana ganin fitowar Nabeelah ta d'an d'ago kanta,sai da ta d'an kalli NABEELAH tukkun kafin daga bisani cikin girmamawa ta Dan dukar da kanta,tare da furta...

"Barka da fitowa
Karamar hajiya!...
Ina kwana!! da fatan kin tashi lafiya ?..

Kallonta Nabeelah tayi tukkun kafin daga bisani cikin kulawa ita ma ta bud'e bakinta tace..

"Lafiya kalau

Cikin nutsuwa ta maida Kallonta izuwa gurin Mommyn su A inda take zaune.

Smiling Nabeelah tasake tare da fad'in "

Mommy yau kuma sai ina da sassafen nan,halan unguwa zaki?

Mik'ewa tsaye HAJIYA Nafisat tayi cik'e da gadara cikin izza da isa, sannan a hankali ta bud'e bakinta tafara magana, "...

Sai gidan uban ki cewar Mom tana mai d'aure fuska

Sannan cikin d'aure fuska mommy ta cigabada cewar "
Dan Allah ki yi kokari ki shiga kitchen, ki had'a mana abinchin breakfast kafin In dawo,don kema kisan bana iya cin girkin kazamai yan aikina ,saura kuma ki tsaya tsumulmulah da iya yi irin naki..........

"Okay..
To anyi angama yanzu ma kuwa zan shige cikin kitchen d'in Insha Allahu inji cewar NABEELAH sannan ta cigaba da cewar "
Dama na tsaya yin wanka ne shiyasa kikaga ban fito da wuri ba,..

"Cikin d'aure fuska Mommy tace" nizan wuce gidan NABEEL , Dan so nake da sassafen nan naje na ci mutumci matarr sa , Dan nagaji da jiran gawan shanu ba kaho,..." É—aure fuska NABEELAH
tayi kafin cikin É—aure fuska had'i da b'ata fuskarta Nabeelah ta furta"..
Haba mana Mommy wanann wacce irin masifa ce haka
Yanzu ke bakijin kunyar tashi tunda sassafe kije gidan surukan ki neman rigima ba, wannan wacce irin masifa ce haka!
ke kenan kullum cikin masifa da bala'i dan Allah Mommy kibar matan Yaya Nabeel tah huta haka, dan Allah ki sakar mata mara tayi fitsari, ki duba kigani
Sabida tsabar masifar ki ne fa yasa suka bar gidan nan ba shiri.......

Cikin fusata Mommy ta daka mata tsawa tace "..

Ke
Naci gidanku idan baki rufe min bakiba

"Cikin sanyi murya Nabeelah ta bud'e bakinta tace "kiyi hakuri, Allah ya huce zuciyar ki dear Mom, sai kin dawo Allah ya tsare hanya ta k'arasa maganarta tana mai kama kunnenta "batare da Mom tace da ita komai ba tanufi hanyar fita daga parlourn cikin bacin rai mai tsananin gaske
, tana k'arasa fitowa tsakiyar compound d'in Gidan, ta tadda Idi drivern-ta a tsaye yana jiran fitowar ta, ai kuwa yana ganin fitowar Mommy cikin sauri Idi driver ya bud'e mata marfin motah, ta shiga sannan ya rufe, cikin sauri ya zagaya yashiga cikin motar shima, Kallon sa tayi tare da fad'in
"Kai Dan kutumar ubanka baka iya gaisuwa bane!?

Atsorace Idi drive yace.

“Ina kwana Hajiya Nafisat?.

"Mtswww
Batare da Mommy ta amsa masa gaisuwar tasaba taja masa wani dogon tsoki,
cikin sauri Idi ya tada motar kana gate man ya wangle masu kofar gate d'in Gidan suka fice cikin gudu kamar zasu tashi sama Dan yasan halinta yana fara tafiya kadan kadan zata daka masa Tsawa tace masa ya kara wuta

_______*GIDAN NABEEL*____

Bayan 30minutes mommy ta iso GIDAN NABEEL ,cikin sauri MOMMY , ta shigo cikin parlour,tare da furta "

Asallamu aleykum!

Assalamu alaikum!!

Assalamu alaikum....

"Cikin sanyin murya had'i d'an d'aga murya ! FAREEDAH Ta katse Mom ta hanyar fad'in".

AMIN WALKSLM

"FAREEDAH ta amsa ma Mom sallamar tata, cikin sauri FAREEDAH ta fito daga cikin kitchen,Wani irin Dam! Kirjin FAREEDAH ya bada wani mugum sautin na bugu saboda ganin Mommy NABEEL da FAREEDAH tayi atsaye acikin parlourn su kafin kace k'obo tun jikin FAREEDAH yafara rawa sai wani irin mugum k'aduwa sassan jikinta yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,,,
Kai tsaye inda Mommy take tsaye ta nufa ,cikin sauri FAREEDAH ta k'araso gurin Mommy a inda take jikinta sai wani kad'uwa yake sai kace wacce aka tsamo daga cikin ruwan sanyi,
cikin nutsuwa had'i da fad'uwar gaba ta durk’usa akan gwuiwowin ta Wanda suka lume cikin lallausar carpet d'in dake parlourn ,sannan cikin tashin hankali da kuma firgicin da ta samu kanta aciki,murya na rawa tamkar wacce aka jonawa shocking tace.
"Momma Dan Allah kiyi hakuri ina kitchen ne banji shigowar kiba! , Good morning hope kin ta tashi lafiya? bismillah zauna mana..... ....cikin fusata!Mommy ta katseta ta
hanyar fad'in "....

Kin Ci Gidan ku! Tana mai aika mata da dakuwa, nace kinci ubanki Malamin tsubbu shegiya yar matsiyata
.Bakar juya...

Sannan ta buÉ—e baki cikin tsantsar masifa haÉ—i da bala'in da suke cinta tana mai cigaba da faÉ—in"
Da ban kwana ba zaki ganni,nace, da ban kwana ba zaki ganni Nazo Gidan d'ana NABEEL!
Sannan kuma ni HAJIYA Nafisat ban shigo Gidan nan dan in zauna a matsayin gidan surukata ba, tun da kin d'aura Dan-maran zama anan gidan, to ni kuma Sai na tuka miki tuwon kaya. Miyar allurah.. Sannan
Kuma Sai na shimfid'a miki, tabarman kashi. Wanda dolenki ki zauna a sama, ,kuma barikiji... tunda kince ke ba zaki bar NABEEL ya kara aure ba, duk matan duniya nan, NABEEL yace bai-ga kowa ba .Sai .ke. zai Aura.. ga ki nan juya, Wanda ta gaji bakin kishi daga gurin kakanintah, tunda kika hana NABEEL auren Azmerh . Yar kanwar MAHAIFIYAR sa,..
To ke ma Sai kin bar Gidan nan, domin ni HAJIYA Nafisat na koshi. Da bak'in cikinki, abin ya isheni hakanan!

Sabida haka in ya dawo, kice masa Ina nemansa da gaggawa..

Saura kuma ki ki fad'a masa insake dawowa inci mutuncinki, wadda batada wani amfani shashsha kawai mai mugun hali,
Tana Gama ƙarasa maganarta tanufi hanyar fita daga parlourn tare da ficewa daga gidan gabadaya Abinta.

"Na shiga uku
!!! Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un FAREEDAH ta fad'i tana mai fashewa da kuka sannan cikin sheshshekar kuka ta cigaba da cewa "
Sai yaushe ne zan samu sauyin lamari acikin rayuwa ta? , d'a Namijin da nake tattalinsa fiye da komai nawa , haka kuma d'a mijin tilo da nake ji dashi acikin zuciyarta, rayuwarta komai nawa , lallai kam tabbas idan har Mommy tayi nasar raba nida farin ciki na shakka babu mutuwa zanyi Dan tasan nawa yakare bazan iya rayuwa babu shiba,Cikin zubarda hawayen take cigaba da fad'in "I don’t know how to love somebody, but mah feelings for you justified how much I love you, NABEEL Ina MATUƘAR SONKA
Share kwallar dake zuba a cikin idanuwanta tayi haka dai tacigaba da sharara kuka ita dai har NABEEL ya DAWO daga masallacin ya tadda ita ahaka, "NABEEL ne ya shigo cikin parlourn tare da furta "

Asallamu Aleykum!

tsayawa yayi turus yana kallon matarsa, da take Famar zubda hawaye..
Kai tsaye gurinta ya nufa yana mai mik'ar da ita tsaye, suka kurawa juna ido yayinda idanuwanta suke famar zubar da hawaye, fuskarta ya tallafo cikin tafin hannuwansa kafin ya sanya bakinsa saman kumatun yana mai fitoda halshen sa waje cikin nutsuwa ya fara lashe mata hawayen dake zubowa daga cikin idanuwanta , ta rintse ido ta na mai jin tsayawar hawayen ta chak alokaci guda saikace d'aukewar ruwan sama..Jiki a mace ta kwanta a jikinsa ya rungumeta tsam-tsam! a haka suka nufi kujera mak'ale da juna, A sanyaye ya zauna a Saman lumtsumemiyar kujera yana mai zaunar da ita akan saman cinyarsa
Ko yana mai É—aurata akan saman cinyarsa zance
, duban ta yayi tukkun kafin daga bisani cikin sanyin murya ya bud'e bakinsa
yace " FAREEDAH tah damuwar ki. ciwo ne agare ni, Wanda baya warkewa..
Meye ya faru!
Bayan kuma kinsan zubar hawayen ki, sune Abubuwa mafi kona min zuciya, shin meye ya faru?

"Ita FAREEDAH d'in dubansa tayi kafin cikin sheshekar kuka FAREEDAH tace "NABEEL shekara ta biyar kenan a Gidan ka, ko 'batan wata banTaba yiba, bayan kuma Kai nasan mutum ne Maison d'aukan d'a ko y'a.
Bare kuma yan uwanka, da suke son suga sun samu jika.......
kuka ta sake fashewa ,dashi kafin ta gyara zama asaman cinyarsa sannan ta cigaba da cewar "
NABEEL
INA MATUƘAR SONKA! ba zan iya kwatanta maka irin MATUƘAR KAUNAR da nake maka ba. Kaunar Ka da sonka yana yawo a jijiyoyin jinin jikina,NABE..... "CIKIN SAURI NABEEL
ya katseta ta hanyar fad'in "..
FAREEDAH HAJIYA Momma
ta zo Gidan nan ne???..

"Eh
Inji cewar FAREEDAH sannan ta cigaba da cewar "

Bata Dad'e da fita ba..

"CIKIN ransa NABEEL yace da sassafe nan! wannan wane i'rin masifa ce Haka!!

Kwantar da ita yayi asaman kirjinsa kafin cikin kwantar mata da hankali had'i da rarrashinta NABEEL ya buÉ—i bakinsa yace
"FAREEDAH rayuwa ta bata da amfani, matuk'ar babu ke atare da ni ,FAREEDAH ba zan iya had'a rayuwar ki da wata y'a mace ba, ko da kuwa zan rinka ganin fuskata a cikin fuskar ta,
FAREEDAH dukan d'a namiji da yace yaji. Ya gani a kan mace, to babu wani iska ko damuwa da zata raba su.
Matukar dai namiji nan saurayi ne. na kwarai. FAREEDAH na d'aukar miki alkawari ,alkawari tamkar buzu da nad'inta , Wanda in kika ga yawarware to ba karamin Al'amari bane.
"Ai kuwa kafin kasani tuni FAREEDAH ta saki murmurshin sannan cikin murmurshi FAREEDAH
Ta buÉ—i bakin ta
tace " NABEEL Ina Alfahari da soyayya da Kake min daga nan har ranan karshe,..
Shima NABEEL d'in cikin murmurshi ya bud'e bakinsa yace "FAREEDAH ni kuma zan ta miki addua daga yau har ranar karshe, Allah ya bar mu tare

_________Da misalin karfe takwas na dare in the evening at 8:pm,
SU FAREEDAH da NABEEL ne, na hango,acikin hamshakin parlourn su, Zaune FAREEDAH take asaman 2-seater a cikin Parlourn ta ,da ita da NABEEL yayin da NABEEL yake a agefen FAREEDAH ,, daga ganin Alamun hiran suke cikin nishadi had'i da farinciki, haha haha haha FAREEDAH ta fashe da dariya cikin dariya FAREEDAH tace"
Allah ko kalbinerh?

"CIKIN smiling NABEEL yace "Eh zumanerh, "
Cikin fara'a
FAREEDAH tace "to yayi,ni dai Bari in kawo maka abinci..... Cikin sanyi ya katseta ta hanyar fad'in "..
Aa
yi zaman ki, mu cigaba da hiran mu, kinsan ni kullum haka nake so. in saki agaba ina baki dariya
Sannann kuma in ta miki hirar soyayya Ina mai kallon kyakkyawar fuskar ki, so nake nayita ganin dariyarki har sai dariyarki ta Kare

""Haha😹 haha 😹haha FAREEDAH ta fashe da dariya sannan cikin dariya FAREEDAH tace " Kai dai ba Ka rabuwa da zolaya

Suna cikin haka.
,.. sai kawai NABEEL yaji wayar sa Tana ringing,wayar sa ce tayi ringing cikin sauri yayi picking call d'in kana ya manna wayan a kunnesa,sakamakon sunar dayagani yana yawo asaman screen d'in wayarsa, cikin sanyin murya NABEEL yace

"....Assalamu alaikum, barka da warhaka HAJIYA Mommah ina wuni ,yayinda gabansa yake fad'iwa..

"A,bangaren HAJIYA Nafisat kuwa batare da ta amsa masa sallamarsa da gaisuwar saba cikin tsantsar masifa had'i da bala in da suke cinta ta bude bakinta tace" kai NABEEL inason maza maza kabar duk wani abunda kake kazo gidana ina son ganin ka
Yanzu yanzu nan

"To Mommah to shikenan, HAJIYA GAni nan zuwa, batare da yajira cewar taba ya katse wayar sa abinsa

"Wani marayan Kuka NE ya subcewa fareedah

Kallonta yayi kafin yace "
"FAREEDAH!

"Na'am NABEEL! Inji cewar FAREEDAH cikin kuka

"Cikin sanyin murya NABEEL yace "

Me yasa kike kuka??

"Cikin kuka FAREEDAH tace "

NABEEL nasan rabuwar mu ta zo !

"Haba FAREEDAH
Inji cewar NABEEL sannan ya cigaba da cewar "wai shin saunawa zan fad'amaki ki daina saka damuwa cikin ranki! sannan kuma inason kisani
Duk ma'kircin Azmerh da magoya bayanta bazasu taba samu naba.kai harta zuciya ta bazasu taba samu ba dan yayi masu nisa,
Inasan kisa aranki cewa ba zamu taba rabuwa da ke ba, daga nan har zuwa aljanna firdausi muna tare insha Allah
So forget about her, batun HAJIYAr mu kuma inason share ta kawai, mu cigaba da shan soyayya mu, damar Nifa yanzu Haka a bukace nake, I need you! ..........
tsintsiyar hannusa yasa kan botir d'in rigarsa, ya soma balle maballin rigarsa, ya zare rigarsa, white single d'insa ta bayyana da gajeren wandon sa,..
Nabeelah ko duk da bata GA kwantacce sumar dake kwance a kirjinsa ba, but Tana iya hango kan nipple d'insa, dake tsaye, ......
Santala santala cinyoyinsa suka bayyana gaba daya jikinsa, kwance yake da lallausar gashin jiki Mai tsuma zuciya,
Wani i'rin masifar shaukinsa ke fizgarta, bata San lokacin da ta hade bakinsu guri guda, bakinsa ta Kai ma cafka a cikin Nata bakin, Ai kuwa damar jiranta kawai yake yajita a cikin jikinsa, Sai kawai jin sa tayi ya bude yan pink lips d'insa, inda ya soma kokarin kissing her, cafkar lallausar harshenta yayi cikin nasa yana sucking d'inta sosai, yayinda ita kuma tayi shiru Sai famar mayar masa da martani take,
Tsura mata ido yayi tare da smiling, yana jin yadda take jujjuya harshensa da Nata Tana tsotsa lallausar harshensa.
Sauke wani ajiyar zuciya a hankali take cikin nutsuwa ta cigaba da sarrafa harshenta a cikin bakinsa tare da zira hannunta a ƙirjinsa tana shafa lallausan gashin dake faffaɗan ƙirjinsa tana sakin wani dan nishi kadan gami da shagwaba ... wani irin sanyi yaji tare da wani irin daɗin dake ziyartar sa a hankali ya fara jin nutsuwa na saukar masa.
A nsa, lumshe idanuwanta tayi duk wani hudi na jikinta na ƙara karɓan saƙon da yake aikamata dashi yayinda hannusa ya cigaba da yawo dashi a sassan jikinta

sai da suka gajiyar da junarsu ko wannen su ya samu gamsuwa sannan suka zube suna mayarda numfashi sai famar sakin murmurshi suke atare a hankali ya É—an mirgina ya koma gefenta tare da rungumeta tsam a jikinsa wani irin numfashi yake fesarwa tare da fad'in

"ALLAH UBANGIJI yayi maki ALBARKA yadda kika faranta min Allah ya faranta miki fiye da haka Baby ke ɗin ta musammance wanda nake da yaƙinin babu wata mace da ta kaiki balle kuma ta fiki keɗin ta musammance My wife! my life!! my happiness!! my word..
My... my ...... my my..... everything …
Ya ƙarashe maganar cike da wani irin farin ciki ji yake mararta tayi sakayau jinsa yake a wata duniya ta musamman kara rungumeta yayi tsam tare da manna mata kiss a saman lips ɗinta da sukayi matuƙar ja sbd tsabar tsotso dasuka sha, a hankali ya miƙe bathroom ya shiga ya sakarwa kansa ruwa wanka yayi tare da wankan tsarki kana ya haɗa mata ruwa me ɗan zafi ya fito.
Su FAREEDAH kuwa da baccin farinciki ya fara ɗaukarta taji an ɗagata chak turo baki tayi cike da shagwaɓa tace
"Ni kam NABEEL ka barni bacci zanyi." Shima NABEEL d'in cikin shagwaɓa yace
"Sorry zumerh kiyi wankan za kiji daÉ—i sai kizo ki kwanta kinji?"
Bai jira cewarta ba ya tsomata cikin ruwan wanka yayi mata sannan yasa tayi wankan tsarki ya naÉ—ota a towel suka fito Kai tsaye ya nufi hanyar upstairs tare da haurawa sama da ita,
kwantarta yayi asaman makeken gadonsu tare da kwantawa a bayanta yarungumeta dakyau sannan ya rufesu da blanket a tare suka sauƙe ajiyar zuciya wanda tuni bacci ya ɗauki FAREEDAH, shi kuwa da gaba ɗaya jinsa yake cikin wani irin farin ciki marasmisaltuwa ji yake ina ma zai samu ya haɗiyeta ko zai samu nutsuwa gaba ɗaya, ƙara rungumeta yayi yana sanya mata albarka
haÉ—i da shashshafa mata sassan jikinnta.
Lokaci ɗaya ya kwaɓe fuska kamar zaiyi kuka sakamakon tunowa da dear mommy dinsa dayayi cikin ransa yace Wallahy Allah narasa meyasa kwata kwata Mommy dina bata Kaunar FAREEDAH! Mommy wanne irin laifi ta aikata maki ne wai kika tsane ta haQa!! Mommy in wani Abu FAREEDAH NABEEL tayi maki Dan Allah kiyafe mata wallah Allah ina matukar son MATA ta FAREEDAH, sannan kuma Wallahy Allah
Mom ban zan iya aure Azmerh ba mommy ki fahimce ni mana wallah ba zan iya karawa FAREEDAH kishiya ba
da wannan tunanin bacci ɓarawo ya ɗaukeshi yana rungume da abarsa.

Da misalin karfe biyar dai-dai
5:00am dai dai a hankali ya tashi daga barcci tare da janyeta daga jikinsa toilet ya shiya yayi wanka tare da ɗauro alwala boxer yasa tare da singlet jallabiya sabuwa ya ɗauko ya zira tare da feshe jikinsa da sassanyan tura kana ya kalleta cike da shauƙi baccinta take cikin kwanciyar hankali yafita ya rufe mata ƙofar a hankali gudun kar ƙarar ya tadata.kai tsaye masallacin ya nufa
Ko da yayi sallah bai fito daga masallacin ba sai bakwai dai-dai sakamakon karatun da ya tsaya yi, kamar KULLUM da sallamasa ya shigo parlournsu
Wani ƙamshi ya shaƙa a lokacin da ya shigo parlourn gaba ɗaya falon ya gauraye da ƙamshi ga ko ina fess.

"ALLAH sarki
Bai war ALLAH
ta tashi kenan?"
Ya faɗa a fili ganin bashi da mai amsa masa ne yasa ya ƙaraso cikin tsakiyar parlourn har zai nufi hanyar upstairs kuwa jin motsin ta da yaji a kitchen ne yasa ya nufi chan, a hankali ya shiga kitchen d'in hangota da yayi cikin wani irin shigane yasa furta
"Ya ALLAH "
"Baby zaki zautar da NABEEL É—in ki"
Sanye take da wata ƴar yaloluwar riga wacce bata huce gwiwarta ba gata shara shara wanda marabarta da babu kaɗan ne ta fidda duk wani shape na jikinta kanta ba ɗankwali sai dai ta tubke gashinta duk da ba wani kwalliya tayi ba amma tayi matuƙar kyau kamar ƴar tsana haka tayi tana aikin tana cin fararta bakinta sai motsi yake wanda yasha lipstick sai motsi yake.
Yarrrrr-yarrrr-yarrrr yaji tsikar jikinsa tana mike'wa tun daga kan babbar yatsar ƙarfarsa har izuwa tsakiyan kansa.
Ita ko da ta ganshi sarai amma tayi kamar bata ganshi ba ta cigaba da aikinta har ta kammala ta juya komai a muhallinsa ta nufo dining haɗa ido sukayi tare da sakarwa juna murmushi 

"Barka da safiya FAREEDAH NABEEL? "

"NABEEL! "
Ta ƙirasa sunansa a shagwaɓe tana mai turo mai karamin bakinta

"Na'am baby"
"Ni wlh ka daina gaisheni ka rika bari ni in fara maka gaisuwa , ba wai kai ka fara ba.
Ta ƙarashe maganarta tare da turo ɗan ƙaramin bakinta.
Murmushi yayi tare da amsar kulan da ta fito da ita suka nufo dinning É—in yana mai faÉ—in.
"Baby nasan kinji zuwana 'fa amma kika bawa banza ajiya ba dole na miƙo gaisawa irin wannan dawainiyar da ake dani .....
"Laaaa banza kuma?"
Ta tambayesa cike da mamaki kalamansa duk da tasan yana wajen kawai sharesa tayi.

"Yesss banza mana kika bawa ajiyata"
Dariya tayi tare da sunkuyar da kanta saving É—insu tayi sannan suka faraci a tare kana kallonsu za kaga tsantsar soyayya, bege, kulawa da suke bawa junansu suna cikin karyawan

"Allah ya miki ALBARKA , ya kuma kula dak'e tamkar yanda kik'e k’ok’arin kulawa da NABEEL d'in ki !”nabeel ya fad'a

# COMMENTS DOMIN ALLAH

#SHARE FISABILLAH!!�#THANKS

#THANKS FAN'S!!!!

*ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI*

#COMMENT'S PLEASE !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!

*AISHA FULANI GAL CE*

*TAKUCE HAR KULLUM B'INGEL FULBE INA MATUƘAR ALFAHARI DAKU MASOYANA ALLAH YABAR KAUNA*

*AISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

*FAREEDAH NABEEL*

🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL*

*🌺 CHAPTER 5-6🌺*

*EDITED BY UNCLE YUSEEP NADABO*

*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*

*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I'm
selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951*

,*SAHIBA, JAMILA, ASMA'U ALIYU, MY DEAR KAWA MAR'ATUSSALIHA 🧕UMMU SAHAD, ZUWAIRA ISMAIL, NO NYM, JUMAI,,, AISHA Ibrahim,, my dear kawa UMMU ADIYYah, Eeshat ina matukar godiya da jinjina agare ku da ZAZZAFAR COMMENTS naku comments kuya na matuƙar burge Ni JINjINA A GARE KU KUNA MATUKAR BIRGENI SOSAI FATAN ALKHAIRI A GAREKU ,,,kuna ina masu min ZAZZAFAR Addu'oi ina matuƙar godiya friends and lovers ina mai maku fatan alkhairi a ko yaushe, to gaba ɗaya ku Masu comments WANNAN page d'in naku kuyi yadda kuke so dashi*

*🌺chapter 5-6🌺*

________Bayan kwana biyu
Zaune FAREEDAH take a Saman lumtsumemiyar kujeran parlourn d'insu, tayi facing d'in T,V wannan time d'in ma alama hankalin ta baya kan TV ɗin parlourn,duk damuwar duniya ta ishe ta motsi kadan tah share kwallar hawaye dake zuba a idanuwanta Wanda a cikin zuciyarta da ranta take cewa Sai yaushe zan samu sauyin lamari da farinchi a cikin rayuwar zaman aure na, ya ALLAH ka AZURTANI da ɗa Namiji ko ƴa mace ko da daya ne mai ALBARKA , ya ALLAH duk wani musulmin da yake cikin hali irin nawa ya Allah ka yaye masa, Ya ALLAH Ina rokon Ka, ka bani ikon cinye wannan jarabawarka ,ya Allah ni baiwar kace mai rauni ya Allah Ka karfafa min zuciya ta ka bani jarinta da juriya. Akan duk wata jarabawarka. tana cikin wannan halin ne ta ji tsayuwar motar mijin a tsakiyar compound d'in,gidan,hakan yasa ta shafa tare da furta" Amin ya RABBILL A'ALAMEEN gami da Mik'ewa tsaye sannan cikin tafiyar ta yanga da yauki ta nufi hanyar fita daga cikin parlourn tana mai ƙarasa fitowa tsakiyar compound ɗin gidan , ta bude mai marfin kofar motar tare da sakin smillig ,NABEEL mijin ta ne kamar yadda tayi tsammanin, , shima NABEEL ɗin cikin tsananin farin ciki ya mayar mata da martani yayi ,cikin smiling yayi hugging d'inta, kafin cikin kasa da murya ya buɗe bakinsa yace "my lovely sweet wife badai kina nan kina Sana'ar da kika Saba ba ko? "smillig tayi sannan ta bud'e bakinta tace "daga dawowar Ka zaka sakani a gaba ko, to ni dai muje kayi wanka Ka Ci abinci
"Haka suka Fara tafiya cikin nutsuwa abin gwanin ban sha'awa, duk Wanda zai gansu Sai yayi sha'awarsu ,domin kuwa yadda suke nunawa junarsu Tsantsan soyayya da kulawa da juna Kai ba zaka ce suna da wata damuwa ba,kai tsaye bedroom d'insu suka nufa, suka shiga a tare suna k'arasawa ya jawota a cikin jikinsa yace "I miss you , Allah Allah nake na dawo gida saboda nayi tozali da my beautiful baby É—ina ..

"Smillig FAREEDAH ta yi gami da zame jikinta ta na mai faɗin " muje kayi wanka, "cikin hanzari ya rike tsintsiyar hannunta gami da juyo da ita tayi facing ɗin sa, Dan kwalin kanta ya zame sannan ya kwance ribbon ɗin kanta, tare da gangarowa wajen wuyanta ya tattara gashin kanta gefe gami da shafa mata kitson kanta , smiling yayi sannan zuwa can ya sake ta ya zauna a bakin bed d'insu yana sakin murmushi, "yayinda ita kuma tah fad'a toilet ta haɗa mai ruwan wanka a cikin bath, tare da ajiye mai towel sannan ta fito gami da k'arasowa inda yake Zaune da computer a gabansa ta matsa ta saka hanuwanta ta rungumoshi tare da cewa "agogo sarkin aiki kana kuma kalbinerh abin alfaharina ina matuƙar sonka my heart please kah tashi kaje ka watsa ruwa,kafin ka fito na gama shirya maka abincinnka kana fitowa sai dai in baka abincinka kaci ka huta domin yau nasan yaro nerh ya ɗebo rana dayawa ko!.."Hannunta ya rike ya juyo ta ta faɗa kirjinsa sannan ya hade bakinsu waje guɗa daya, Sai da ya dau kamar 20minute yana kissing ɗin ta, sannan ya zare baƙin sa gami da sakinta yana mai mik'ewa tsaye kallon ta yayi l kafin cikin kulawa NABEEL yace
"To Sugar baby Bari na yi wanka, muje Gidan Hajiya Nafisat ko Hajiya Mommah na zance ya ƙarasa maganar sa yana mai sakin murmushi "cikin kankanin lokaci yaga launin fuskar FAREEDAH ya canza bai bi ta kanta ba ya fad'a bathroom yayi wanka ya fito, yana fitowa ya tarar da ita Zaune a gefen bed kayan da ta ajiye mai ya dauka Wando 3kwata ne Sai jallabiyar Fara kal wacce aka kayata da ado, yana gama shirin sa, wayarsa ta fara ringing cikin azama yayi picking call d'in kana ya manna wayar akunnesa are da fad'in "

Assalamu alaikum ina wuni
Mommy? "

" A bangaren Hajiya Nafisat batare da mommy ta amsa masa sallamar tasa da gaisuwar tasa ba ta daka masa Tsawa cikin daka masa Tsawa tace"NABEEL Bana bukatar gaisuwa taKa, kayi maza-maza kazo yanzu Yanzu nan Ina da bukatar ganin Ka idan har kanwar uwarka ta yadda, shege wawa mijitace mijin Hajiya shanyayye kawai. Wanda be san ciwon kansa ba.

"Cikin sanyin murya NABEEL yace
"KIYI HAKURI
Momma dama yanzu.,,..

Cikin fusata! Mommy ta katseshi ta hanyar fad'in..

"Rufe min baki! Wawakawai

"Kafin ma NABEEL yace zai yi wata magana tuni Mommy ta katse wayar, ta,..

FAREEDAH ko yana fitowa daga bayin, ita ma É—in ta shige cikin bayin tayi wanka kana ta fito cikin kankanin lokaci ta kammala nata shirin, cikin doguwar rigar ta atamfa wacce ta sha aikin ,stone's work har kasa ta yi mutukar kyau mayafin ta da takalminta kalar blue and white Sai tai kalar stone's work d'in jiki kayanta Shima blue and white ne, ta fito parlourn ta same Shi a Zaune yana zama jiran fitowar ta tunda take saukowa yake binta da kallo zuciyarsa na Kara kayata mai tsantsan kyawun da Allah yayi mata don tayi masa matukar kyau.

Mik'ewa yayi ya Kama Tsintsiyar hannunta , suka fito tsakiyar compound d'in, suna k'arasawa bakin kofar motar, ya bude mata motarsa ta shige sannan ya rufe murfin motar, yakoma .........mazaunin driver ya zauna ya tada motar suka fice daga gidan ,tuking yake yi a hankali ,hankalin suke tafiyar yayinda kowa da tunanin da yake a zuciyarsa cikin 30minuts suka shiga cikin Anguwar su Hajiya Nafisat Mommah dinsa, bosso estate Gidan hajia nafisa tasa, direct ya nufa, yana zuwa bakin gate É—in Gidan, ya Danna horn da gudu gate man yazo ya wangale masu kofar gate É—in, Gidan, direct motar su ta shige tsakiyar compound d'in Gidan Allah sarki baiwar...Allah..

"Tunda suka shigo cikin Gidan FAREEDAH ta ji gabanta na fad'uwa, lura da yayi da yanayinta hakan yasa cikin tsansar tausaya mata ya zagayo yabude mata marfin motar, sannan ya Kama hannuwanta kafin cikin sanyin murya had'i kwantar mata hankali NABEEL ya bud'e bakinsa. Yace"
Haba FAREEDAH Dan ALLAH
ki kwantar da hankaliki kidai na tsaka damuwa a cikin ranki,kinji ko!...

"Dan razana FAREEDAH tayi kafin cikin tsananin fad'uwar gaba ta buÉ—e bakinta tace"..
Babu komai kalbinerh kawai dai tsoro nake ji , saboda nasan rabuwa mu tazo, ko?
,, share ta yayi batare da yace da ita komai ba sukanufi hanyar nufi hanyar da zai Sada sa da babban parlourn Gidan.wao part d'in Hajiya Nafisat NAFISAT ,..
A tare suka
shiga cikin Gidan,...

Zaune Mommah take a cikin parlourn tare da Azmerh da NABEELAH yayinda Azmerh take zaune agefen Mommy haka zalika itama NABEELAH sun saka Mommy
a tsakiyar su, ..

Mtswww

Azmerh Tana ganin shigowar su NABEEL da FAREEDAH ta ja masu tsaki
tare da kauda Kai ......

Gaba dayansu su FAREEDAH da NABEEL suka zube bisa Saman lallausar center carpet din Falon suna kwasar gaisuwa ,"cikin kasaita da isa da nuna izza Momman take ansar gaisuwar tasu, kallon FAREEDAH tayi sannan cikin dak'awa FAREEDAH Tsawa Mommy ta bud'e bakinta
tace tace"Ke kuma bakar juya. Babban munafuka diyar bokaye, maza maza ki tashi ki bani waje zan yi magana da É—ana munafuka annamimiya algugunmah
shegiya bakar juya..

"Jiki a sanyaye FAREEDAH ta mik'e ta nufi dakin NABEELAH yayin da ita kuwa Mommy sai da taga shigewar FAREEDAH sannan ta maida kallon izuwa gurin NABEEL cikin tsansar bacin rai had'i da d'aure fuska Mommah ta cigaba ......da cewa, " NABEEL shin a duniyar nan kana da wacce ta fini? "

Shi ko NABEEL da kansa yake aduke cikin ladabi da biyayya
ya bud'e bakinsa yace
" Babu Mommah
"To me yasa ka ke kyamar abunda na kawo maka, bayan kasan cewa shine mafi kusan Chi a gare Ka inji cewar mommy..

Cikin sanyin murya NABEEL yace "
Mommah Bana kin Azmerh amatsayin kanwa amma huja daya ne na baki ,to kiyi hakuri gami da uzuri kasan cewa mu tare da FAREEDAH shin ne burina "

"To shikenan Inji cewar mommy..

Sannan ta buÉ—e baki cikin tsantsar masifa haÉ—i da bala'in da suke cinta tana mai cigaba da faÉ—in"
duk Wanda ka ga ya kona rumbunsa yasan inda toka take tsada ne,...soboda dan ya sayar ,ya samu riba,... to Kai a cikin wannan wane riba kasamu a tsawon wannan lokachin da Kake tare da ita,?"cikin fad'uwar gaba NABEEL yace "
Momma ba zan dai na baki hakuri ba domin babu jayayyah atsakanin ni da ke ,amma Dan Allah kiyi hkr kibar magana Azmerh "

Kallon mamaki Nabeelah yake ma mommy kafin cikin tsananin bacin rai NABEELAH tace "haba momma
Dan Allah ki....
"Ke NABEELAH Dakata
Mommy ta daka mata tsawa ta hanyar katseta, sannan ta cigaba da cewar "Kuma ki tashi ki bar wajen nan kafin in karkarya maki kasusuwa..

Ay kuwa kafin kace k'obo cikin tsananin jin tsoro kar tasha duka wajen Mommah NABEELAH miƙe tsaye kai tsaye ta nufi bed room d'inta ......Acikin d'akinta ta tadda FAREEDAH tana zauna a saman gadonta ta had'a Kai da gwiwa duk abin duniya ya isheta, kallon tsatsan tausayawa take ma FAREEDAH kafin cikin ranta tace Allah sarki rayuwa, Allah sarki baiwar Allah Allah ya isar maki, Allah ya kareki daga sharrin makiya da masu son ganin bayan aurenki,,,,, Mommy wai wanne irin laifi FAREEDAH ta aikata maki ne wai Kika tsane ta haka!kwata kwata narasa mesu FAREEDAH da NABEEL suka
tsarewaa tsohuwar banzar Nan datake so taga Bayan auren su, tsanar tayi yawa wai wannan wane irin masifa ce haka!,.

Dafa kafadar FAREEDAH NABEELAH tayi yayinda FAREEDAH ta dago Kai a razane!!!
Kallon FAREEDAH NABEELAH tayi Kafin Cikin sanyin murya Nabeelah tace" Dan Allah aunty FAREEDAH
kiyi hakuri da abunda Mommah take yin maki..

"FAREEDAH ta dube ta sannan tace "wallahy Nabeelah ban taba ɗaukar abinda Mommah take yi min amatsayin wani Abu ba saboda aganina ta damu da halin da nake cikine Kuma tamkar uwa nake ɗaukar Mommy agurina saboda Haka kada ki damu ta ƙarasa maganar tana mai sakin murmurshi dole.

"Momma ba uwarki bace suka jiyo murya kamar daga sama Azmerh ce ta cigaba da shigowa dakin sannan ta cigaba da cewar "nace Momma ba uwarki bace domin kuwa inda ace Mommah uwarkice ba zaki mallake mata É—a ba, Kuma ina son ki saka a cikin ranki cewa ni baby Azmah yaya NABEEL Sai ya aure ni ko yana so ko baya so, kuma ni nan da kike gani na lafiyayyiya ce, ba kamar keba bakar juya "smiling kurum FAREEDAH tayi ba tare da tace da ita komai ba ...

Bangaren su Mommah kuwa cikin daka masa Tsawa mommah tace "ba damuwa zan baka zabi Abu uku ,na daya Ina son Ka rabu da FAREEDAH har Abadah kwata kwata baka ba ita, na biyu Ina son Ka Kara aure, cikin two weeks...cikin daga murya ta cigaba da cewar "......na uku , ko ka bani nono na... da... na baka... kasha ....

A matukar razane NABEEL ya d'ago kansa ya kalli mommy sannan yace "Dan Allah Mommah kiyi hakuri ,ba zan iya rabuwa dake.ba ko dana wuni daya, kina nan aMatsayin uwa agare ni ,but Mommah kiyi hakuri ba zan iya yi ma FAREEDAH kishiya ba,... Cikin tsananin bacin rai Mommy ta d'aga hannunta ba tsaya wata wata ta sauke masa zazzafar mari tare da fad'in " Ni zaka gaya wa zancen banza! To Bari kaji yau nake bukatar answer nan, ba Sai tomorrow ba ,Dan Haka meye zabinka? "Mommah na zabi hakuri agurin ki , ki yi min alfarma kasan cewa zama na da FAREEDAH ..

"Inna lillahy wa Ina ilaiheem rajioun inji cewar Mommy shikenan ta gama mallake min É—a murmurshi dole tayi kafin cikin tsananin bacin rai ta bud'e bakinta ta cigaba da cewar
"NABEEL tunda nariga na rantse cewa baza ka zauna da wannan matsiyaciyar yarinya nan ba,......to ku je gida duk wani abunda kasan tazo maka dashi Gidanka ,to ta kwashe Shi ta tafi ..in Kuma ba Haka ba duk abinda ya faru da Kai ,hmmm Kai Ka so ,Tana gama maganarta Mik'e, tsaye kai tsaye ta..nufi hanyar upstairs tare da haurawa sama.

NABEEL kallon photo mahaifinsu yayi, Wanda yake manne a jikin
bango parlourn ,..

*Division tuni NABEEL ya shiga *TUNA BAYA*
wani kyakkyawar Alhaji me matukar kama da NABEEL sak👌🏻 ne na hango,suna tsaye da Shi da hajiya nafisat a cikin tsakiyar parlour su,kallon Hajiya Nafisat Alhaji yayi sannan tsansar farinciki Alhaji yace "hajiya ni zan wuce gurin aiki" cikin sanyin murya Mommah tace "Alhaji maganar da mukayi jiya da kai Kuma fa, bamu k'arasaba kace min Sai yau .Kuma yau gashi zaka fita ,kar... Cikin daka masa Tsawa ya katseta! ta hanyar fad'in "..
Hajiya Nafisat muyi magana dake jiya,jiya maganar da muka yi dake biyu zuwa uku, cikin daka mata tsawa haÉ—i tsananin bacin rai ya cigaba da cewar "wace magana A ciki kike nufi?..

"To Ina da maganar ne da wuce magana NABEEL da Azmah Inji cewar Mom.

"Hajiya ke ma wani lokaci. fa kin fiye rigima, wannan Abu ai ba namu bane ,tunda yarinya Tana so, Shima ai NABEEL É—in Sai atambaye Shi in yana so ,meye na wani wahala a ciki.

NABEEL ne ya shigo cikin parlour tare da furta ".

Assalamu alaikum! .

Cikin fara'a mahaifinsa yace "Amin Wlkslm yawwa gama NABEEL É—in yazo, ..

Kai tsaye ya nufi inda suke tsaye cikin sauri ya ƙaraso gurin su a inda suke tsaye yana mai dubansu cikin tsansar kulawa ya buɗe bakinsa yace "..

Ina kwana Abba? Good morning Mom?

"Lafiya my dear son
Inji cewar Abba yana mai kallon É—an nasa sannan ya cigaba da cewar "Kai ya maganan yarinya nan Azmerh yar Gidan Hadiza??.

"Abba ni ai ba magana kowa atare da ni ,.
Inji cewar NABEEL sannan ya cigaba da cewar "Abba jiya ba mu gama magana dakai ba. a Hanyar mu ta dawowa daga office ba Jiya ba!..

"OK natuna Inji cewar Abba
Sannan ya cigaba da cewar "
FAREEDAH NABEEL É—in ka ko?,yar Gidan Malam SANI ko,?
"Eh Abba Inji cewar NABEEL yana mai washe baƙi sannan cikin fara'a ya cigaba da cewar " ita fa, Abba ita nike son ita nake matuƙar kauna..

"kai Masha Allah,yana mai washe baki shima inji cewar Abba tare da kallon mommy sannan ya cigaba da cewar

"To ke kin ji...

"Agaskiya bazai yiwu ba,
Inji cewar Mom tana mai kallon su kafin cikin masifa da bala'i ta cigaba cewar "haka kawai aje aÉ—auko na waje abar na gida! Wallahy Allah bazai yiwu ba,kuma wannan yarinya ai tayi gadon tsiya Æ´ar matsiyata ne kuma ba ahalinmu bace..Wallah bazata sabuba...

"OK Inji cewar Abba sannan ya cigaba da cewar "kina da wani tsari naki kenan Wanda kike so ki nuna mana, to Bari in gaya maki, ni har abunda yaro yake so ayi .shine zanyi anan ba naki tsarin ba ...

"Abba! NABEEL yakira sunar mahaifin nasa cikin fara'a.

Batare da Abba ya amsa ba ya dube ɗan nasa "yayinda shi kuwa NABEEL cikin tsansar farinciki ya cigaba da cewar "yaushe zamuje muga iyayen nata ?"ai NABEEL ko yau Kake so,zan tura baban ka alhaji Rabi'u, jeka na sallameka," ihu mom ta kurma kafin cikin ihu mommy NABEEL tace" ni Gaskiya wannan abun bazai taba yiwuwaba ! haka kurum aje auro mana diyar mayu., shi yasa tun tana ƴar karamar ta nayi masifar tsanarta , haƙa kurum yarinya tun tana yar kankanuwarta ta makalewa ɗana, harda Wani canzawa sunarta suna wai FAREEDAH TA NABEEL shi yasa Ni wallahi tun tana ƴar karamar ta natsane ta nace na tsane ta natsane ta, FAREEDAH aduk inda kike Allah ya tsine maki ALBARKA
ƙarasa maganar ta cikin ihu.

"Mtsswww
tsaki Abba ya ja mata
Tare da furta "mahaukaciyar mata,
shashsha kawai sannna suka nufi hanyar fita daga parlourn suka bar ta tsaye sai famar surfa masifa take ita dai

*WANENE NABEEL!*

Sunar mahaifinsu Alhaji Suleiman Sai mahaifiyar su Hajiya NAFISAT , su FULANI ne daga yola, Balaguru Sukai daga garin su ,suka sauka a Minna,damar can suna da yan'uwa a cikin jahar minna mahaifinsu harkar kasuwanchi yake, Kuma Allah yasa masa albarka, Dan har kasa waje yana zuwa, Alhaji Suleiman yana da Æ´aÆ´a biyu, babban sunar sa NABEEL sannan Sai da Hajiya Nafisat tayi shakara biyar sannan ta haifi kanin sa wato Ahmed , Ahmed yaro ne kyakkyawah,..

Zaman lafiya suke ba Mai jin kansu ,bayan wasu shekaru, watarana mahaifinsu yayi tafiya ,ya tafi, metting a Abuja, akan hanyarsa ta dawowa Allah ya aiko masa da hatsarin inda anan take Allah ya amsa abunsa, Sai dai muce may your soul rest in perfect peace Alhaji ,..

Tunda Abban su ya rasu NABEEL shi yake kula da kaninsa Ahmed, domin kuwa yanzu Haka Ahmed ya tafi karatunsa a can kasan waje, AHMED kuwa yana can yana Ta karatunsa,...
Cikin kwanciyar hankali..

Su NABEEL yara ne kyakkyawai kana ganin su kasan sunsha nono Fulani, yanzu Haka NABEEL Shi yake kula da. company. mahaifinsu
SULEIMAN SALIHU COMPANY NIGERIA LIMITED sunar *company*,, . ****

*CIGABAN LABARI* *
Cigaban labarin NABEEL Sauke ajiyar zuciya
NABEEL yayi

*"INASONKA ABBA NA INA MATUƘAR JIN KEWAR KA"*

Ya fad'i hakan acikin zuciyarshi yana mai sake jin tsananin shaukin son mahaifin nashi na ratsa zuciyarsa
cikin zubar da hawayen yace ".Abba!!!Innalillahi wa inna ilaihirraju'un yau nasan da ace kana raye hakan bazata faruwa ba Nabeel ya faÉ—i cikin shesh shekar kuka sannan ya cigaba da cewa "Allah yaji kan ka da rahama Abba Allah yasa can tafi maka nan,,,,,,,

*_ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI_*

#COMMENT'S DOMIN ALLAH !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!

*Ni dai TAKU HAR KULLUM B'INGEL FULBE INA MATUƘAR ALFAHARI da ku MASOYANA ALLAH YA BAR KAUNA*

*AISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

*FAREEDAH NABEEL*

🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL*

*🌺 CHAPTER 7-8🌺*

*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*

*🤝 SDEENDTM DATA SERVICES🤝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = N300. 1GB = N300
2GB = N600. 2GB = N600
3GB = N900. 3GB = N900
4GB = N1200. 4GB = N1200
5GB = N1500. 5GB = N1500
*GLO* . *9MOBILE*
1.5GB = N500.
2.9GB = N1200. 1.5GB = N1100
4.1GB = N1600. 2.9GB = N1400
5.8GB = N2100. 3GB = N1650
7.7GB = N2700. 4GB = N2100
*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
For more information call or whatsapp me
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
🪀08066268951

*🌺 CHAPTER 7-8🌺*

*🌺 CHAPTER 7-8🌺*

__________*NABEELAH* __________

__________Bayan sati biyu
kyakkyawan matashin ne na hango, janye yake da trolley É—in sa, ya shigo cikin tsakiyar compound É—in Gidan hajia nafisat , AHMED Kyakkyawa ne haÉ—e da iya shiga ya tsaru iya tsaruwa .sumar kansa ya wanda ya tarashi luf dashi baki ga tsantsi da laushi ,ita ka dai ma abun kallo ce. da burgewa. É—an gemu nan tare da É—an saje KaÉ—an Sai sheki suke yi suna walwali, fatarsa kadai ita ma abun burgewa ce Sai ka rantse yanzu aka fito dashi daga cikin engine, farine irin tas É—in nan, sannan Kuma yana da wani irin kyau da Karin kwarjini,Ba Sai na faÉ—a ma ba kasan naira da Hutu tare da jindadi, sun ratsa shi ,sanye yake cikin kananan kaya white and blue color kamshin daddadar turaren jikinsa gaba daya ya mamaye compound d'in Gidan, shi dogo ne amma ba zankaleleba de-de ne ,Shi, ba ramanme ba Kuma shi ba me kiba ba atsakiya yake kirjinsa me ÆŠan faÉ—i normal, eye's d'insa Dara Dara suna lumshewa, face d'insa Tana da Dan tsayi Kuma Tana da Dan fadi normal face, hancinsa dogo Dan chib baiyi tsini da yawa ba, bakinsa Dan karami pink lips dashi, yana shinning, fatarsa Fara ce tamkar bature Haka ma sumar kansa take unique ce kamar ruwa two Haka yake, tafiyar sa kamar ta basarake ta maza masu ji da kansu, AHMED ba zai haurawa 25years ba, domikuwa yana ji da kuruciyar a lokacin sa.
Cikin wani irin taku dake nuna zallah kwarjininsa ya nufi hanyar da zai Sada sa da babban parlour Gidan. part d'in Hajiya Nafisat ..

De-de lokacin NABEELAH ta fito daga cikin bed room d'inta,A hankali ya murda handle d'in kofar parlour , da sallama ɗauke abakinsa,ya shigo ,shigowarsa cikin parlourn yayi de-de da fitowan NABEELAH daga cikin bed room d'inta, haka zalika yayi de-de da Kai dubanta zuwa ga kofar shigowa parlour, a daidai lokacin ne kuma narkakkun idanuwansa suka sauka a kanta..Tana sanye da 'kananun kaya wanda suka matse ta riga da wando tight! hattar da shatin nipples ɗinta sai da suka fito, wandon ya manne a jikinta ya fito da sharp din jikinta ,tsayawa Ahmed yayi yana kallon ta daga sama har ƙasa,Sakamakon yanayin kayan dake sanye a jikinta kananu ne masu matukar fitar da sura.shigarta tafi da imaninsa ,kai daga shi har ita tsayawa sukayi suna kallon junarsu, yayinda ko wanne su yake kallon Ɗan uwan nasa daga kasa har sama ,sukai Kusan minti ashirin haƙa zuwa can
Sai naji NABEELAH ta buɗe bakinta Cikin zazzakar Muryar mai matuƙar daɗin sauraro tace ...

"Sannu da zuwa "cikin ranta take cewa da gani wannan kyakkyawan matashin yaron nasan shine Autah Mommah da take yawan bani labarinsa , ashe wannan masifafiyar matar ta iya haifuwan kyawawan yarah ,domikuwa shakka ba nayi wannan matashin saurayin yafi yaya NABEEL had'uwa Nisa ba kusa ba, wow he's so cute so sweet so Handsome ,duk
wannan magana a
Cikin ranta take yi shi ..

Hajiya Nafisat ce ta fito. daga cikin kitchen,cikin murna ganin Autanta had'i da washe hakworai kai tsaye inda suke tsaye ta nufa cikin sauri ta ƙaraso gurinsu a inda suke kallon AHMED Mommah tayi Kafin cikin murna had'i da fara'a farinciki
ta buÉ—e bakinta tace..

"Oyoyo auterh nerh, ...
sannu da zuwa ,kai Masha Allah bakon turai kenan, aaa sannu da zuwa
ya hanya? ya karantu? ,da fatan ka kammala karatu naka lafiya ? Shi AHMED É—in rungume ta yayi kafin cikin Dadda'dan Muryar sa mai cike da kasaita
had'i da farinciki
ya buÉ—e bakinsa yace..

Alhamdu'lillahy Mommah
Mun same ku Lafiya?

"Alhamdu'lillahy inji cewar Mommah ,"To Masha Allah inji cewar AHMED yana mai zare jikinsa daga nata..

Kallon Mommah tayi Tare Da faÉ—in "amma meyasa da jirginku ya sauka, ba kira ni .,na turo maka Idi driver yazo yayi picking É—in ka ba? "no Mommah ba zan iya jiran har sai Idi driver yazo ya yi picking ÆŠina ba "to Masha Allah sannu da zuwa "yawwa dear Mommah" dama duk na kosa kayi ka dawo"smiling AHMED yayi Kafin cikin kulawa ya buÉ—e bakinsa yace"kisan wani
Abun ne mommah?"
A'a inji cewar Mommah
Tana Mai kallon sa ".

Wallahi cikin Abokai na. kullum hiran ki nake yi Sai kace masoya irin na soyayya . inji cewar AHMED yana mai sakin murmushi.

"Murmushi Mommah ta yi Kafin cikin smiling tace "AHMED kenan, banda Abinka ai soyayya uwa da ɗa ta wuce wasa. Kuma bata taba kwatantuwa da soyayya ta ƙarasa maganar ta Mai kallon NABEELAH
NABEELAH! Mommah ta kira sunarta.

"Na'am NABEELAH ta amsa

"Je ki É—auki akwantinsa ki kai masa part É—insa kinga ya dawo ko " batare da ta ce komai ba ta É—an duka ta É—auki akwantinsa sannan ta fara tafiya hankali,Jan akwatin sa NABEELAH tayi ta fara tafiya a hankali tana tafiya a hankali sannan kumaTana kallonsa har ta fita daga cikin parlour ,
Haƙa zalika shima Ahmed ɗin dan sai da yaga fitar ta tukkuna sannan ya mai da kallon sa izuwa gurin Mommah Tare Da faɗin....
"Mommah wannan kyakkyawar yarinya fa?" NABEELAH ce Ai inji cewar Mommah sannan ta cigaba da cewar",yar kanwata Amina ne wanda ta rasu, Daman ina so ta dawo nan wurin da zama, ikon Allah kuma sai gashi mahaifinta Allah yayi masa rasuwa Shi ma ,shine kawai sai nace ta dawo nan gurin da zama kawai Gaba Ɗaya"to shi kenan ni bara in ƙarasa part ɗina in samu in yi wanka in huta "To abinci fa? "A'a Mommah na ci abinci a cikin jirgi "to Masha Allah
Allah yayi maka albarka É—a na kaina "AMIN inji cewar AHMED gami da nufa hanyar fita daga cikin parlourn,

AHMED na zuwa bangaren sa ,ya iso parlourn sa a buɗe agyare Sai zuba uban kamahi take haƙa ma bed room d'insa , ma tasha gyara AHMED kai tsaye bathroom ɗin sa ya shiga ya had'a ruwan dimi ya cika bath, sannan ya cire kayan jikinsa, ya shiga cikin ruwa sosai ya gasa jikinsa da ruwan dimin yana gama wankar ya daura towel da karami a hand d'insa yana goge kansa ya fito ,gaban katon dressing mirror ya nufa yana goge jikinsa, AHMED ya shafa jikinsa lotion me masifar kamshi ya gyara sumar kansa da sajen fuskanshi, ko kayan bacci bai saka ba yabi lafiyar bed ......

Da misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare AMATUƘAR razane NABEELAH ta farka daga nannauyan bacci take sakamakon mumunar mafarkin da tayi , lokacin ɗaya taji duk jikinta ya soma Bari sai wani kaduwa sassan jikin ta yake sai kace wacce aka tsamo daga ruwan sanyi hannayenta dake rawa tasa ta dafe de-de saitin zuciyarta dake bugawa da karfi, yanayin yanda jikinta ke rawane yasata cije labbanta, tare da lumshe sexy eye's d'inta kam-kam, tabbas ta yi matuƙar tsorata da wannan munannan mafarkin da tayi akan su Mommah da yaya AHMED ,Ahankali tadan soma jujjuya kanta da taji yayi mata nauyi sosai, da sosai, mafarking da tayi ya tada mata hankali matuƙa ya Kuma hautsuna duk wani tunaninta, yayinda wani irin tsoro me ɗauke da zallah fargaba ya lullubeta, kwata-kwata bata jin zata iya jurewa, domin kuwa zuciyarta ta karya sosai, tsoro take ji kada dreaming ɗin ta ya zamanto Gaskiya, hakan yasa Ahankali ta zuro da kafafunta ƙasa tare da saukowa daga kan bed ɗin ta kallon agogon dake sakale ajikin bango dakin tayi, duk da cewar cikin tsakiyar dare ne sosai bata tunanin akwai wani Abu da zai hanata zuwa garesa, fitowa tayi daga cikin bed room d'inta, Ahankali take tafiya, yayinda kuma zuciyarta ke cike da tarin tsoro, domin kuwa babu wani Abu dake motsi a cikin Gidan ko Ina ta dau shiru..
Kasancewa a wannan lokacin da yawan mutane sunyi Nisa a cikin baccinsu. Sam bata damu da duhun da ya mamaye parlourn ba kai tsaye ta nufi hanyar fita daga cikin parlourn,tana fita, Kai tsaye ta nufi kofar da zata Sada ta da part É—in AHMEDh ,duk da cewa a yanzu zuciyarta ta Fara kawo mata wani Abu me Kama da tsananin tsoro Sai dai Sam bata jin akwai Abun da zai hanata zuwa garesa a wannan dare, dan ita bata kan Mommah take ba dan ita ma Allah yasa Yan fashin su kashe Mommah ita meye ruwanta , babban burin ta kawai ta isa garesa domin kuwa zuciyarta cike take da son ganinsa, saboda ba kadan ba mafarkin da tayi akansu ya daga mata hankali. Tana isa daidai part d'insa, d'aura hannunta akan handle d'in kofar parlour tayi tare da tura kofar cikin Ahankali ,ta shiga cikin parlournsa,sassanyar kamshi da kuma sanyi A/C ne suka daki kan fuskarta. Wanda hakan ya tilasta mata lumshe beautiful eyes d'inta, tare Kuma da buÉ—e su alokaci guda , ayanzu kam ta fahince cewa shi É—in mutum ne me mutukar son kamshi. Ahankali ta shiga dan sai yau take Kare parlour nasa kallo, Wanda komai dake cikin sa yake nit babu alamar datti ko akasin Haka, duk da cewar babu yalwatacce light a cikin parlourn ,,,Dan blue light ne kadai ke kunne, amma hakan baisa ta daina ganin tsarin parlourn sa ba,
Gaba daya zuciyarta ta Riga da ta karye da tunaninsa, hakan yasa kaitsaye ta nufi daya daga cikin kofar dake cikin parlourn ,Wanda Kuma anan bed room d'insa yake,
Bata ko tashi jin fargaba da matsanancin faduwa gaba ba, Sai da ta k'araso jikin kofar bed room d'insa ta tsaya, dan lumshe idanuwanta tayi Tana me sauraran yanda zuciyarta take bugawa da sauri-sauri, nan take wani irin tsoro ya lullubeta, Abu guda biyune aranta Wanda na farkon shike Kara karya mata zuciya, domin kwata-kwata batason ace mafarkin da tayi akansu ya tabbata musamman shi..

Dan koda da second daya ne bata jin zata iya jurewa cutuwarsa, Saboda lokaci daya zuciyarta ta kamu da soyayyar sa, lokach daya taji ta Tana matuƙa son sa
Idanuwanta da suka cika da kwallar ta lumshe, lokaci daya mafarkin da tayi ya shiga dawowa cikin kanta, wanda hakan yasa ta rike kannata da sauri, yayinda idanuwanta ke yi mata imagine d'insu suna kwance a cikin jini dashi da Mommah kamar yadda ta gani a cikin dreaming Nata, ai kuwa cikin sauri ta murda handle d'in kofar, tare da tura kofar cikin.. take kuwa kofar ta bude, Ahankali ta Dan tura kanta cikin bed room d'in, take kuwa taga duhu ya mamaye ganinta, kasancewar ko d'igon haske babu acikin d'akin, Ganin duhun ne yasa ta jin wani irin faduwar gaba, tare Kuma da tsinkewa zuciyarta, domin kuwa hakan Alamace dake nuna mata cewa babu kowa acikin bed room É—in , Dan da akwai mutum to da dole zai bar light É—in akunne komin kankantarsa ,samun kanta tayi girgizawa kanta cike da fargaban abun da zuciyarta ke kokarin Rayamata ......
bazata iya jurewa ba domin kuwa taji zuciyarta ta kasa samu nutsuwa, duk kuwa da yanda zuciyarta ke sanar da ita cewar baya cikin d'akin bata amince da hakan ba Ahankali ta...Ta soma Ɗan bin jikin bango bed room d'in, tare da soma lalube ko zataji makunnin light, sanin da tayi cewa Dukan dakunan Gidan makunnan wutansu suna kusa da kofar ake saka su, ne, yasa ta bin jikin bango kofar Ahankali ...Cikin sa'a kuwa taji ta d'aura hannunta akan makunnin light d'in, idanuwanta ta rumtse da karfi, sakamakon yanda zuciyarta ke cike da fargaba, Had'i da tsananin jin tsoron Abun da zata gani bayan ta kunnah light, tabbas Tana matuƙar jin tsoro, domin kuwa tasan acikin biyu dole ne daya saiya faru, maybe kunna light d'in da zatayi yasa mafarkin ta ya tabbata, wata kila Kuma akasin Haka, shine baya cikin bed room d'insa, rumtse idanuwanta tayi kam, lallai tabbas tasan cewa acikin biyu za 'ayi daya, zuciyarta cike da tsoro da fargaba ta Danna makunnin light d'in bed room din, take kuwa gaba daya dakin ta gauraye da haske...Atsorace tasoma Dan ware idanuwanta dake akulle, inda ya sauke ganinta akan hadadden gadon dake cikin bed room d'in, gani da kuma nutsuwarta ne suka sauka akansa, inda yake kwance anan saman tsakiyar bed ɗin sa, yayi kwanciyar nan irin ta rub da ciki, yayinda kuma yake sanye a cikin gajeren wandon ajikinsa, Kasancewar bashi da Riga NE yasa faffadar surar bayansa dake ɗauke da yan tsirarun tattoo ya bayyana, sauke idanuwanta akansa da tayi ne ya sanya ta sakin wata ƙatuwar ajiyar zuciya, Wanda karfin da Kuma sautinta ya bayyana, Wani irin matsanancin farinciki ne ya shiga zuciyarta, yayinda take jin wani irin daddadar sanyi na ratsa ta har izuwa tafin kafarta,jingina bayanta da jikin bango d'akin tayi, tare da lumshe sexy eyes d'inta, Wanda hakan yasa Ahankali wasu tsiraran hawaye suka silalo daga cikin eye's d'inta,""Alhamdulillah Allah na gode maka Allah ka ƙare min shi "ta fad'a cikin wata sassanyar murya dake ...... Bayyanar da zallah abun dake ciki zuciyarta,
Ahankali ta kuma bude kyawawan eyes d'inta, tare da saukesu akansa wani irin matsanancin farinciki take ji yana ratsa ta, sanadin hakan kuwa yasa bugun zuciya da fitan numfashinta daidai
,a Hankali Ta sauke idanuwanta akansa da ta yi ne yasata jin wani i'rin matsanancin shaukinsa na bin jikin ta da jininta,ahankali cikin nutsuwa ta shiga takawa zuwa jikin bed din sa, ......'a yanayin yadda take jin zuciyarta ta tsumu da matsanancin shaukinsa, bata jin akwai wani Abu na daban da zai kawar mata da tunaninsa ......Samun kanta da tayi abakin gadon nasa ne yasa Ahankali ta zauna abakin gadon ,still beautiful eyes d'inta akansa yake,
idanuwanta ne ta sauke su akan Zanen tattoo d'in dake bayansa, tsaida ganinta tayi akan wani Zane da akayi masa me kamar butter flay, sosai Zane yayi masa kyau hakan yasa taji gaba daya ta kwadaitu da son taba zanen, batare da tunanin komai ba Ahankali ta Kai hannuwanta dake rawa kan fatar bayansa, de-de,inda zanen butter flay d'in yake,
Saukar hannunta akan fatar bayansa ne yasa tajin wani irin Abu me karfi ya shiga jikinta ......Yayinda time daya tsikar jikinta suka mimmike, saidai Kuma taushin skin d'insa da taji ya shigeta ne yasa ta kasa É—auke hannunta daga jikinsa,ahankali tadan lumshe idanuwanta tare da sauke ajiyar zuciya ...
Ahankali cikin murya dake Bayyanar da tsananin rauninta tace "Alhamdulillah "Allah Nagode maka, da baka Bari mafarkin na ya zama Gaskiya ba, cikin da son bayyana da abun dake cikin zuciyarta ne yasa wasu hawaye masu sanyi suka zubo daga cikin idanuwanta, take kuwa suka diga akan fatar bayansa, saukan hawayen Nata akan fatarsa ne yasa taga gargasan jikinsa sun mimmike, "yaya AHMED tana mai cigaba da shashafa masa bayan sa,sanin cewa bacci yake hakan yasa batasan aranta cewa zai answer mata ba, jin bai amsa mata bane haƙan yasa Ahankali
Ta cigaba da wasa da yar yatsunta akan fatar bayansa, kana Kuma cikin wani sabon yanayi ta soma zagaye zanen tattoo din dake jikinsa ...Gaba daya ta shagala kan abun da take yi masa din, wanda har hakan yasa ta soma sakin smillig batare da ta sani ba, Ahankali tadan lumshe idanuwanta yayinda take jin wani irin Dadda'dan sanyi na ratsa ta, sassanyar ajiyar zuciya take saukewa tare Kuma da shakan, numfashi turarensa, Wanda dadinsa ke Kara kashe mata jiki, a kasalance ta soma yawo da yatsar hannunta har zuwa tsakiyar bayansa ...Zubawa shining skin d'insa idanu ta yi Dan har acikin ranta Tana mamakin yanda skin d'insa keda kyau da kuma laushi, ganin yanda gargansansar jikinsa Ke mimmike wa ,ne yasa taji kirjin ta ya buga, domin kuwa bata fatan ace ya farka ya sameta Haka, kasancewar kansa na facing d'in kofar NE yasa Ahankali tadan rankwafo,kansa Dan so take ta duba ko bacci yake ,ko kuwa idanuwansa biyu ......
Rankwafowan da tayin ne kuwa yasa jikinta gogan nasa jikin, yayinda tausasan breast d'inta suka gogi bayansa, Dan leka, beautiful face d'insa.tayi, ganin beautiful eyes d'insa arufe ne Hakanyasata sauke ajiyar zuciya, idanu ta ta zubawa fuskarsa Tana kallon Ahankali ta sauko da beautiful eyes d'inta zuwa kan dogon hancinsa, da Kuma Dan karamin bakinsa, Wanda ke dauke da pink lips masu sheki, Ay kuwa batason lokacin da tayi kissing, d'in labbansa ba, harshenta tasa, ta dan lashe Samar lallausar labbansa , sannan ta d'aura bakinta tadan tsotsa lallausar labbansa,tana mai cigaba da sucking É—insa har da lumshe idanuwanta. Sannu a hankali ta zare bakinta akan labbansa,
Lokaci daya taji duk jikinta yayi weak, yayinda kasala ya saukar mata, cikin muryarta daya zama very silent voice tace"kana da kyau sosai yaya AHMED, ban taba ganin hadadden gaye irinka ba you AR so so so beautiful""''so cute so sweet so handsome "tafada hakan Tana me sake ninkaya acikin wani sabon shaukinsa da ta samu kanta, sake kallon fuskar sa tayi , ganin yanda yake fitar da numfashi Ahankali ne ya sata Dan lumshe ido cikin sanyi da kuma sweet voice d'inta tace "have a sweet dreams yaya AHMED, "Tana gama da maganar zata fad'a ' ne yasa,,,
Ahankali ta zuro da kafafunta kasa,sannan ta sauka a Saman bed d'insa, cikin takunta me dauke da nutsuwa ta nufi hanyar fita daga dakin, domin kuwa Sam Ta ma manta da batun kashe light din dakin Haka tayi ficewarta..

Jin alamar fitanta daga cikin dakinne ,yasa Ahankali ya bude idanuwansa wanda suka sauya launi daga kalan farin zuwa ja, yayinda kuma suka rikide suka koma zallah sexy eyes wanda suka É—auke da zallah wutar sha'awa acikin su, kana Kuma suka bayyanar da kumaa fallasa asirin dake cikin zuciyarsa,
hanya da tabi ya zubawa ido, Haka yake jin tsikar jikinsa na cigaba da tashi, yayinda kuma gargasansan jikinsa ke Kara mik'ewa, the first time kenan da yaji wata irin mahaukaciyar sha'awarsa na neman fasa masa Mara .domin kuwa tun shigowarta parlourn sa yaji motsin mutum, kana Kuma har ta shigo cikin dakin sa. idanuwansa biyu, duk wani Abu da ta aikata .da wanda ta kuma fad'a yana jinta, Sai dai Rufe idanunsa da yayi yasa ta GA kamar bacci yake yi, tabbas bakaramin juriya yayi ba, domin alokacin da ta d'aura hannunta akan tsakiyar bayansa, wani irin masifaffen shock ne ya shiga jikinsa, take Kuma jarababbiyar feeling's d'insa ta motsa,lallai ya daurewa hakan, domin yanayin yadda take wasa da yan yatsun hannunta akan bayansa bakaramin ruguza masa lissafi yayi ba, Sai dai kuma a zuciyarsa cike yake da mamakin abunda zai kawo ta bed room d'insa a cikin wannan tsohon Daren, sama da 3minute ya É—auka yana ta fama juyi akan bed d'insa duk yanda ko yaso sleep ya É—auke sa .ya kasa, hakika shigowarta cikin dakin nasa yasa yayi losing duk wata nutsuwarsa ,yayinda Ahankali yake jin wani nannauyan kasala na saukar masa, again ga Kuma wani sabon hot feelings d'inta, dake sukar da duk wata kafar sadarwa na jikinsa, wanda Kuma sanadin hakanne ya sashi kasa rumtsawa "yaya AHMED "sautin amon sassanyar murya da takira sunarsa da Shi ne ya shiga dawowa cikin kunnesa, sannan kuma Ahankali ya soma tuna yanda take tsotsa lallausar labbansa ,ai kuwa, wannan yasa batare daya sani. Ko shiryawa hakan ba ya Saki wani kawataccen murmushi daya Bayyana da zallah kyawunsa, Tare Da furta " yanzu aka fara wasan Yan Mata,a hankali ya Dan lumshe idanuwansa ,Dan so yake sleep ya É—auke sa, cikin abun da bai wuce 15minute ba kuwa yayi sa'a bacci ya É—auke sa ,sai dai mu ce Good night, two lover's, AHMED and NABEELAH...

Washe gari ..
Da misalin ƙarfe tara de-de,Ahankali NABEELAH ta buɗe idanuwanta Wanda suke cika da yanayin bacci, Mike tayi tare da yin hamma kana cikin nutsuwa ta zuro da kyawawan kafafunta kasa, Ahankali ta sauko daga kan bed d'inta, tare da mik'ewa tsaye. Yanayin yanda taji jikinta ya zama is very weak sosai ne hakan yasa ta Dan lumshe idanu, tare da sa hannunta ta dafe kanta dake Dan sarawa kaɗan-kaɗan,sabida rashin ishe'shen sleep d'in da bata samu tayi Jiya da daddare ba, kai tsaye cikin bathroom ta nufa Dan tasan idan tayi wanka zata daina jin ciwo kan ta, Ahankali ta murda handle d'in kofar bathroom d'in ta shiga, cikin nutsuwa ta cire rigar bacci dake jikinta ...
tare da k'arasawa gaban shower a kasalance ta sakarwa kanta ruwa. jin saukan ruwan shower's a jikinta ne yasa ta sauke ajiyar zuciya take kuwa ,Moment d'inta na daren Jiya ya shiga dawo mata, tunawa da kyakkyawar fuskarsa da tayine yasa ta sakin smillig,hakan yasa ta yi wankanta cikin nutsuwa, ko da ta kammala wankan wani light peach color din bath robe tasa ajikinta , saboda yanayin wedan garin yasa ana Dan busa sanyi kaɗan kaɗan, wani Dan karamin farin towel ta d'auka tare da nade dogon gashin kanta Wanda yake jike da ruwa, anutse ta k'arasa gaban sink din dake cikin bathroom din, brush tayi hade da sake wanke fuskarta, kana cikin nutsuwa ta fice daga cikin bathroom din, tashigowa cikin bed room d'inta, Tana Gama goge jikinta ta k'arasa gaban dressing mirror, wani body lotion me saukin kamshi ta shafa a jikinta, tare Kuma da feshe jikinta da body spray d'inta me dad'in kamshi, direct ta nufi wajen drawern d'inta Riga da sket din material me colour black ta ciro Wanda aka kawata gaba daya jikinsa da ado white stone's work, a nutsu ta sanya kayan da yayi mutukar amsa jikinta, Dan kuwa bakaramin kyau material d'in yayi mata ba, yanayin yanda kayan ya lafe ajikinta ne yasa cikakkun hips d'inta suka bayyana, dogon sumar ta dake bin bayanta ta tubke da wani babban ribbon, flat shoes masu kalan fari akafanta ta zura, sannan ta murda handle d'in kofar ta fita,ta ƙarasa shigowa cikin tsakiyar falon d'in idanuwanta suka sauka akan sa,,,,Zaune yake a Saman dinning table, yana cin abinci breakfast ɗin sa , Wanda shigowarta cikin parlourn yayi de-de da dogo kansa da yayi, take kuwa ya sauke idanuwansa a kanta ,wani irin kyau da yaga tayi masa,hakan yasa shi tunowa da dare jiya gami da abunda tai masa hakan yasa Shi Dan lumshe idanuwansa tare da sauke ajiyar zuciya,sannan kuma ya Dan ciza labbensa na saka tare da furta " yarinyar zata sani in aikata abinda banyi niya ba.

NABEELAH kuwa ganinsa da tayi ne a dining area haƙan yasa ta saukar da kanta kasa, tare da K'arasowa kan dinning table din ahankali
Tana shirin zama kenan domi kuwa har ta jayo kujeran zama Kamar Daga sama taji ankira sunar ta.

AHMED ne ya ce "NABEELAH! yana mai kallon ta "na'am ta amsa masa "Dan Allah zo mana "asanyaye ta k'araso wajen sa sai dai har yanzu kanta yana kallon ƙasa "Zuba mata kyawawan idanuwansa yayi yana kallon kyakkyawar surar jikinta yana mai sakin murmushi kafin daga bisani Cikin Dadda'dan Muryar sa mai cike da kasaita ya buɗe bakinsa yace
"Jiya daddare mai ya kai ki part Ɗina? Shiru tayi masa taki amsa masa tambayar da yayi mata "tsawa ya daka mata yana mai cigaba da faɗin "nace meya kai ki bangaren na jiya daddare ??"daga kanta tayi ta kallesa kafin cikin shagwaba ta turo bakinta gaba sannan ta buɗe baƙinta tace "dama ...daman .....mafarkin na yi akan cewa da kai da Mommah yan fashi sun shigo mana gida sun kashe ku ,shine ne shine ne Nikuma na kasa jurewa , sbd tsoro nakeji kada mafarkin nawa ya zamanto Gaskiya, Shi yasa na...bai Bari ta ƙarasa faɗin abund take son faɗa ba yayi sauri katseta ta hanyar faɗin
"karya kike yarinya, kawai dai ki ce . ɗan kyakkyawar auterh Mommah ɗin da kika gani ne hakan yasa kika kasa rumtsawa. kika kace Bari ki zo ki gan shi ko haƙan zai sa hankalinki ya kwanta,,yan MATA anga kyakkyawar yaro anƙasa barci dare ko!, anyway sakon da kika zo isarwa ta samu shiga saura ni Kuma na k'arasa aikin da kika fara"ita dai shiru tayi, yayinda kanta yake kallon kasa , sannan kuma sai famar wasa da yan yatsunta take ,yayinda shi Kuma ya zuba mata sexy eyes d'insa yana kallon ta ji yaƙe kamar ya hadiye ta kowa ya huta.Mommah ce ta fito daga cikin kitchen, cikin sauri ƙaraso wajensu a inda suke .dubansu tayi da kyau tukkun kafin cikin
Daga murya tace...

" AHMED lafiya?..
Yaya na gan ku cikin wannan Halin ?? "smiling AHMED yayi tukkun Kafin Cikin Dadda'dan Muryar sa mai cike da kasaita ya buɗe bakinsa yace "lafiya kalau Mommah, dama cewa nayi ya kamata in fara koya mata karatu "cikin smiling Mommah tace "har kasa na ji daɗi ɗan Auterh nerh, to shikenan Ka ga ɗan filin can ya ishe ku .ku zauna kuna karatun d'inku ,kaga ba Hayaniya, "hmmmm inji cewar AHMED sannan ya cigaba da cewar" Ina gani Mommah idan akwai in da ya dace to bai wuce bangarena ba, kinga nan babu abunda zai zo dame mu da Hayaniya "to Masha Allah haƙan yayi kyau inji cewar Mommah tana mai sakin murmushi sannan ta cigaba da cewar"NABEELAH kinga kin samu yaya me kishin ki koh? ""cikin smiling NABEELAH tace "to amma Mommah ki gaya mashi banda duka in nayi kuskure ! " Mommah tace "aa yaya in kinyi kuskure ba za'a dak'e kiba!,ko yaƙe Auterh nerh kai kaji karka d'aketa,...
"AHMED yace "to Hajiya Mommah , kallon NABEELAH yayi Tare Da cigaba faɗin"NABEELAH zuwa anjima sai ki sameni a bangarenah in yaso sai in fara koya miki karatun ko! "alright to insha Allah sai na zo"yawwa Allah yayi maku albarka inji cewar AHMED ,"Amin ya Rabbill A'alamin inji cewar AHMED yana mai miƙewa tsaye sannan ya cigaba da cewar"Mommah Ni na wuce GIDAN yaya NABEEL sai na dawo "mtswww Mommah taja masa tsaki Tare Da nufa hanyar upstairs gami da haurawa saman , murmushi kurum Ahmed yayi kana ya nufi hanyar fita
daga cikin parlourn

*DA DADDARE*
Da misalin karfe goma da minti ashirin na dare, ,...
AHMED ne na hango Cikin d'akin sa ,Zaune Ahmed yake asaman bed d'insa, a cikin bedroom d'insa ,zuwa can Sai ga NABEELAH ta shigo Cikin ɗakin ,da sallama dauke a bakinta, NABEELAH ta turo kofar bedroom d'insa, tare da shigo cikin bed room d'insa Kai tsaye inda AHMED yaƙe zaune ta nufa "AHMED ko yana ganin shigowarta Hakan yasa ya sauke sassanyar ajiyar zuciya Cikin tsananin sha'awarta da yaƙe cinsa ya Ɗan lashi lips d'insa, tabbas yau tarkonsa yayi babban kamu ,tun jiya daddare da tashigo masa dakinsa yake jin wata mahaukaciyar feeling d'inta ,,,burinsa kawai k'arasa aikin da ta Fara anan ya Gama tsara ta yadda zai shigeta a darenan suji dad'in junarsu, yana cikin magana zuci baisan lokacin ta k'araso wurinsa ba "sai kawai ji yayi Tana cewa "yaya gani Na zo "kallon ta yayi kafin cikin sanyin Muryar da tsantsan sha'awar ta AHMED ya buɗe bakinsa yace "NABEELAH Help me please Ina cikin wani yanayi NABEELAH tun Jiya daddare dakika fita daga cikin d'akin na na ƙasa rimtsawa dan Allah ki taimaka min sha'awar ki zata ƙarasa ɗan ki , NABEELAH kece kika tsokano min sha'awa ta da abinda yake damuna, NABEELAH feelings yana neman kasheni ,,,,......
"yaya AH..."in bai Bari ta k'arasa faɗar Abin da take son faɗa ba, ya hade bakinsu guri guda, a matuƙar haukace ya Bakinsa ya ɗora saman Nata cikin wani yanayi mai wuyar ganewa ya cafki lallausar harshenta ya Fara kissing d'inta da salonsa me rikitar lafiyyayen mace, aikuwa ya rikita lissafin NABEELAH gashi ita bakuwa ce a harkar bataba Samun irin wannan kusancin da ɗa namiji ba balle har ya Kai ga tsotsa lallausar harshen juna, duk sai ta daburce ta rasa mema zata yi masa,ya jima yana kissing d'inta batare da gajiyawa ba zuwa can Kuma ya Fara balle maballin rigarsa , ya zame duk wani kayan jikinsa ,yayinda ita mata ya cire mata duk wani kaya jikinta ya cire su tare da jifa dasu ƙasa,Ahankali ya dauke ta cak ya kwantar da ita a Samar bed d'insa, boob's d'inta ya damka da hannunsa tare da Dora bakinsa akai,a tare suka sauke ajiyar zuciya Ahankali ya Fara tsotsar boob's d'inta yana mai lumshe idanuwansa ,yau dukansu sun shiga sabuwar duniya ,Wanda da ko a mafarki ba su taba tunanin zuwanta nan kusaba, ..._*IDAN banga RUWAN COMMENTS NAKU BA ZAKU JINI SHIRU KUMA bansan guntun comment dogon sharhi nakeso*_

*_ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI_*

#COMMENT'S DOMIN ALLAH !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !!!

*Nice dai TAKU HAR KULLUM B'INGEL FULBE INA MATUƘAR ALFAHARI da ku MASOYANA ALLAH YA BAR KAUNA*

*AISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

*FAREEDAH NABEEL*

🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL*

*🌺 CHAPTER 9-10🌺*

*DEDICATED TO :-MY LOVELY FRIEND XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*

*🤝 SDEENDTM DATA SERVICES🤝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = N300. 1GB = N300
2GB = N600. 2GB = N600
3GB = N900. 3GB = N900
4GB = N1200. 4GB = N1200
5GB = N1500. 5GB = N1500
*GLO* . *9MOBILE*
1.5GB = N500.
2.9GB = N1200. 1.5GB = N1100
4.1GB = N1600. 2.9GB = N1400
5.8GB = N2100. 3GB = N1650
7.7GB = N2700. 4GB = N2100
*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
For more information call or whatsapp me
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
🪀08066268951

*🌺 CHAPTER 9-10🌺*

....tureshi ta farayi tana dukan bayansa Tana faÉ—in "wayyo zafi AHMED kabari Haka karka shiga! idan ka cigaba da matsala dan mutuwa zanyi ni dai zafi nake ji na kuma gaji .....ka ...ka barni Haka haÉ—e bakinsu yayi waje guda yana tsotsa da salonsa na janye zuciya kana kuma yana cigaba da kokarin zura gugarsa arijiya

gabadaya baya cikin hayyacinsa, sai wani gurnani yake kamar mayunwacin matashin ZAKI , ita kuma sai kokarin tureshi takeyi tana masa magiya, amma abinka ga wanda yayi nisa bazaiji kiraba , haka kuma kokarin tureshi datake yacitura domin kokusa karfinsu ba dayaba

hakadai har AHMED yayi galaba akanta yasamu nasarar jefa kwallo araga

duk da ba wani dadewa yayi ba amma tajishi kwance sharaf a jikinta, kafin yayi release,
yana sharce gumi

Ahankali tunanin abunda suka aikata ya darsu a zuciyarsa take yaji wani tsoro ya ratsashi, ya janye jikinsa daga nata Ahankali ya koma gefe ya juya mata baya zuciyarsa. najin babu daɗi, baitaba tunanin wannan lokcin zaizo masa a de-de wannan gabar ba tabbas akwai gundumemiyar matsala haduwar farko wannan gingimemen abun da ya shiga tsakanin su gaba Kuma sai ALLAH wasu hawaye ne masu dumi suka zubo masa yaja zuciya de-de lokacin da ta matso ta hade kirjinta da bayansa Tana mai shafa masa boob's d'inta Cikin nutsuwa ta buɗe bakinta tace "Meye kakewa kuka Ahmed? Kana nadama ne na kasancewar mu tare a wannan lokaci, ni kam bantaba nadama ba kuma ba zanyi ba indai da Kai ne please karka ji komai muna tare kaji ko!tayi furucin Nata na karshe da sigar rarrashi haɗe da shashafa masa bayan sa, Haka yasashi juyowa yana mai haurawa samanta ya Kama boob's ɗin ta da hannunsa cikin sanyin Muryar ya bude baƙinsa yace
"NABEELAH
zaki aureni ?
naji daɗin gurin nan bazan iya hakura dashi ba,kuma banason nisanmu yayi yawan da idan munzo tuba zamu samu matsala ,bantaba aikata wannan abin ba,please zaki aureni? "maimakon yaga ta dauki maganarsa seriouse sai yaji tayi smillig sannan ta Mike tsaye ta dubesa kafin cikin kulawa tace "AHMED kenan karfa ka manta kaifa da bakinka kace aikin Dana Fara ne, shine kai kuma kake son k'arasawa,ai bai Kamata ace tun ba muje ko Ina ba ace har ka karaya, haba mana tun yanzu ace har ka karaya tun bamu je ko ina ba haba mana Malam Umaru kar ka bada maza mana, saboda Haka indai wasa ne dani da kai yaya AHMED yanzu muka soma,Yanzu labarin Asalin zai fara ,Yanzu za'a fara wasan , yaƙin Yanzu zai soma , Labarin bai ƙare ba yaya AHMED so idan zaka iya tafiya dani kazo mu tafi muyi rayuwar mu, dan ni nan da ka ganni ban tashi yin aure yanzu ba karatu na zan cigaba da yi,tana kaiwa nan tayi shigewarta bathroom ta Fara tsabtace jikinta, cike da shaukinsa Dan bakaramin dad'insa ta jiba, smillig ta rika sakewa harta Gama gasa jikinta da ruwan zafi, sannan ta fito daure da towel d'insa, ta kwanta a gefensa, Dan kafin ta fito daga cikin bathroom, ta samu har ya sake wani sabon zanin gado, inda shi Kuma har yanzu yake bin ta da kallo yana cewa acikin ransa KADAFA YARINYAR NAN TAIMIN INGIZA MAI KANTU RUWA, sannan ya mik'e kai tsaye yawuce ya shiga toilet.

WASHE GARI da misalin ƙarfe goma na safe
*SULEIMAN SALIHU COMPANY NIGERIA LIMITED,* wata MA'AIKACIYAR NABEEL ne na hango tana tsaye agabon Office É—in NABEEL
kafin daga bisani Kuma Neesah ta shiga zagaye gaban Office dinsa cikin fad'uwar gaba sabida tsabar tsayuwar kafanta har ciwo yake mata cikin tashin hankali ta cigaba da safa da marwa agabon Office É—in NABEEL kana tana mai kallon Kofar Office É—in...
Alhaji MALEEK ne ya nufo inda Neesah take tsaye,ganin Alhajin ne yasa NEESAH tayi sauri ta k'arasowa garesa,tun kan ta gama k'arasowa Alhajin ya kalleta Tare faÉ—in "Neesah lafiya?,......lafiya. NEESAH ya na gan ki kamar hankalinki duk atashe ?......

"Cikin tashin hankali itama NEESAH É—in ta kallesa kafin ta buÉ—e bakinta tace" wallah lafiya dai .ba lafiya ba".

Meya faru?? inji cewar Alhajin yana mai tambayarta

"Wallahi NABEEL ne kwana nan duk bakin da suke ta zuwa wajen sa, bai ma sake ba ballantana yaje ya gansu, gashi wayan nan bakin na yau dasu kazo important ne agare shi , amma har yanzu bai samu ma zuwa ya gansu ba... banSan me ke damun Shi ba,ta ƙarasa maganar ta Cikin zubar da hawaye.

"Yana ciki? "Inji Alhaji Malik

"Eh yana cikin .
inji cewar NEESAH

"To barin in shiga in gan shi

"Okay "

Alhaji Malik direct office É—in NABEEL ya nufa Alhaji sallama É—auke a bakinsa ya tura kofar office din NABEEL Tare Da shiga cikin office É—in inda Ya tadda NABEEL Yana zaune a saman kujerah kana kuma ya zabga wata uwar tagumi sai famar aikin tunani yake daga ganin alamu yana cikin tsananin tashin hankali da tsantsan damuwa mai tarin yawa 'NABEEL ko yana ganin shigowar Alhaji cikin office D'insa, yayi saurin M'ikewa tsaye kallon Alhaji Malik NABEEL yayi kafin cikin sanyin Muryar NABEEL ya buÉ—e bakinsa yace
"Good morning Alhaji...

"Morning too my son
Inji cewar Alhajin Kafin ya cigaba da cewar

"NABEEL!"

"Na'am NABEEL ya amsa

"Me ya faru na ganka a cikin damuwa , ance mutane sun zo ganinka ma kaki yarda su gan ka "Cikin sanyin Murya NABEEL Ya buÉ—e bakinsa yace" wallah Alhaji
Mommah ce Duk ta takura min wai lalle-lalle sai na saki FAREEDAH ,Kuma sati Uku ta bani gashi yau saura kwana É—aya, Kuma tace lalle sai na sake ta na sake aure, na auri Azmerh yarinyar da kwata kwata bata da kamun Kai, ...Narasa Irin wannan dalilin me Mommah take nufi yakarasa magana cikin tsananin damuwa.
"Cikin kulawa Alhaji Malik yace"Wai meyasa mahaifiyar ku take yin Haka ne ne , ,kwana da kwanaki ta matsu akan magana rashin haifuwan nan ya kamata tayi hakuri ta daina d'aukan irin wannan kudiri cikin zuciyarta, ka bari zan gan ta ,domin kuwa yakamata dai in yi magana da ita yau É—in nan ,ka kwantar da hankalin ka kadaina saka damuwa
acikin zuciyarka ,'.

*GIDAN HAJIA NAFISA*
Mommah ne Zaune a cikin parlour Samar two-seater, tare da NABEELAH da Ahmed suna hiran su cikin nishadi yayinda AHMED d'in yake ba su labarin school d'insu, kallon sa Mommah tayi kafin cikin smillig Mommah tace "Auta nerh kai dai tunda ka dawo Nigeria aikin kenan kullum ciki bamu labari school d'inku Kake,baka gajiya suna cikin hiransu sukaji slm...

Alhaji Malik ne ya shigo
tare da furta"
Assalamu alaikum

"Mommah tace ta Daga kai takallesa Tare Da amsa masa "Ameen Wlkslm inji cewar Mommah sannan Cikin fara'a ta cigaba da cewar"aaa Alhaji Malik sannu da zuwa "Alhaji Malik ne ya ƙaraso inda da suke zauna sannan Cikin kulawa ya buɗe bakin sa yace "yawwa" AHMED budesa Kafin cikin kulawa ya buɗe baƙin sa yace"sannu da zuwa Alhaji "Cikin kulawa shima Alhaji ɗin Yace "AHMED NABEELAH sannunku !"yawwa Alhaji Good morning da fatan ka tashi'lafiya ?
"Alhamdu'lillahy
my children
"Hajiya! Cikin kuwala Alhaji Malik ya kira sunan Mommah" Cikin nutsuwa ta amsa da "na'am tana mai kallon sa sannan ta cigaba da cewar"
bismillah zauna mana sannu da zuwa Alhaji "zama Alhaji Malik yayi asaman kujera Yana Mai kallon ta Kafin Cikin fara'a yace "yawwa Hajiya Nafisat Barka da safiya !"da fatan ka tashi'lafiya! ya aiki?
ya office?.

"Alhamdu'lillahy,............
Sannan ya cigaba da cewar"
Hajiya abunda ke tafe da ni dama nace bari inyi takakkiya inzo in same ki
Mommah tadago kai tadubeshi sannan tace "eh Ina jinka

"Ah akan maganar wannan yaron ne NABEEL da iyalinsa, kawai Haƙa dai ana zaman.lami'lafiya ba a san Hawa ba bare sauka kawai ... Haƙa abu ya zo ya yamutse ya lalace ,
sai naga ya kamata inzo in same ki saboda wancen Kudirin da kike bukata acikin zuciyarki ba halattace bane kumayin hakan bakaramin shishshigi bane cikin lamarin ubangiji, yakamata ki janye kibar ma wannan yaro uzurinsa, ya ƙarasa maganar sa Cikin bada umarni

"Girgiza kai MOM tayi Tare Da furta"Malik kenan

Alhaji yadago kai cike da mamaki sannan yadubeta yace "ah Hajiya Malik ma kawai Haka gatsau ?

"To dan nace Malik meye ? Inji cewar Mommah
Cikin haɗe rai "cikin sanyin Muryar Alhaji Malik ya bude baƙinsa yace"amma Hajiya Nafisat ni mafa gani nake acikin Gidan nan fa kamar nima ina da abunda zan iya faɗi wanda ya kamata asaurare ni saboda ni ma wani Abu ne acikin Gidan nan ...''Mik'ewa tsaye Mommah tayi Kafin cikin daka masa tsawa MOM ta buɗe baƙin ta tace"
"Bari in gaya maka NABEEL dai ÆŠana ne. nina haifeshi duk abunda nake so shi zanyi da Shi saboda nina Haife Shi, ko so kuke abar shi da wannan mata yar iska ?Wanda bata tsinana mana komai ba, bata da abunda take Sai Dai ta Ci tayi kashi ,to ba zai yuwuba ,yanda na haifi NABEEL Haka nake so NABEEL Shima ya Haifa domin in gani inyi Alfahari da Shi sannan kuma inagargadinka akan shiga sabgar dabatakaba.
ta ƙarasa maganar ta
Cikin tsantsan bacin rai

"Shima Mik'ewa tsaye yayi Kafin cikin fusata yace"amma duk da Haka Hajiya Nafisat karki mance ni ma fa NABEEL d'in ÆŠana ne , saboda haka wannan yaron yana da kyau ki bashi
Dama ,a bashi uzuri ,amma bai kamata Kai tsaye Haka kawai ki É—inga wannan.ki É—inga yanke hukunci
da wuri ba ,"""""' Cikin
fusata Mommah tace"
Malik Ai ni naga ya kamata ka tsaya harkokin Ka na office ne, kawai ba Wai sai ka shiga Cikin hurumim Gidana ba ,Saboda haƙa Ina san kasan wani Abu cewa Abokin miji ba fa miji bane.

"Shikenan.naji inji cewar Alhajin Kafin ya cigaba da cewar" amma ya kamata yaron nan aba shi uzuri Hajiya Nafisat bai kamata kawai ki yanke ma kanki hukunci da abunda ba zai yuwuba , yaron suna zaman lamin lafiya da iyalinshi ,aa shikenan Kuma kawai dandai wannan Abu yakawo matsala ace ba zaki tsaya kibashi uzuri ba ?.

"To duk maganar ka Malik ko FAREEDAH É—in ta zauna ko tatafi Saboda haka kaje ka faÉ—a ma NABEEL kace nace na bashi daga Yanzu zuwa yamma ta tattara tsummo-karanta da tasan tazo dashi ta tafi, cikin cikin daka masa tsawa MOM ta cigaba da cewar"nariga na yanke hukunci Kuma babu wanda ya isa ya hanani yin abun da nayi niyya Sai ALLAH ,Haka.
Kawai Kazo ka kawo min wata magana ,maganar banza magana wofi ,Tana gama maganar ta Tare Da galla masa hara sannan ta shige ciki kitchen Tana mita

"Cikin daka Mata tsawa Alhaji yace......"shin bakya tunanin kiyi hakuri Kila ita FAREEDAH kwana nan kiga
Allah ya bata haifuwa

*GIDAN YAYA NABEEL*
Da misalin karfe takwas na dare in the evening at 8:pm,su FAREEDAH da NABEEL ne, na hango,acikin hamshakin parlourn su, Zaune FAREEDAH take asaman 2-seater a cikin Parlourn ta ,da ita da NABEEL yayin da NABEEL yake a agefen FAREEDAH ,, daga ganin Alamun hiran suke cikin nishadi had'i da farinciki, kallon ta yayi kafin CIKIN. SMILING
NABEEL YACE
"Wato idan na Kalle ki sai inga duk kinfi min matan kasa nan kyau, Sai in ganki kamar wata azurfa ce cikin hannuna "haha haha haha FAREEDAH ta fashe da dariya tana mai kallon sa sannan Cikin dariya ta buÉ—e bakinta tace "kaga baka gayamin ya kukayi da Mommah ba naji kace ita ce takira Ka dazun da safe "bar wannan magana jeki kawo min abinci dare yunwa nike ji "cikin smiling Nabeelah ta mik'e tsaye Tare Da shigewa cikin kitchen
Hajiya Nafisat ce ta shigo cikin falon TARE da furta"

Assalamu alaikum

"Cikin sauri NABEEL ya mike tsaye Yana Mai kallon ta kafin Daga bisani Cikin fara'a Had'i da tsananin kulawa NABEEL ya bude baƙinsa yace"AMIN Wlkslm , oyoyo dear Mom sannu da zuwa Mommah "cikin fusata! Mommah ta katse sa ta hanyar faɗin
"ai ba Kai ya kamata kayi min Oyoyo ba ,ya kamata ace yaranka sunzo da gudu sun tare ni cikin murna da farinciki ,Ina matar Gidan take?...... Cikin dak'a masa tsawa Mommah ta cigaba da cewar "nace maka ina matar Gidan take ?...''''Nabeelah ce ta fito daga cikin kitchen É—auke da kulan abincin a hannunta, fitowar ta yayi de-de da Kai dubanta izuwa gurin Mommah a inda take tsaye tana ta famar surfawa NABEEL masifa,..

MOMMAH!!!"
FAREEDAH Ta FAƊA cikin yanayin kid'ima da rudewa, tare kuma da tsananin tashin hankalin daya bayyana akan fuskarta,Wanda har haƙan yajawo faduwar kular abinci ɗin dake hannunta.murfin kular ya buɗe abincin ciki ya watsa,cikin fad'uwar gaba, da tsananin tashin hankali FAREEDAH Ta cigaba da cewar" Inna illahi wa inna illaihim rajiun yau nashiga uku ni FAREEDAH NABEEL
"Kallon ta MOMMAH tayi tana Mai nuna ta kafin cikin tsananin masifa da bala'i MOM tace "Ka gani batasan darajan Shi ba, Saboda bata da maigado ,inda tana da maigado da bazata walakanta wayan-nan abubuwan da take walakantawa ba,"""cikin rawan jiki FAREEDAH Ta ƙaraso Gurin MOM a inda MOM take tsaye Cikin tsananin tashin hankali FAREEDAH ta durkusa har kasa tace"sannu da zuwa Mommah "cikin dak'a mata tsawa Mommah tace"FAREEDAH idan kogi ya kafe asirin kifi ya tonu ,yau kogi yakafe asirin kifi ya tonu, Dan Haƙa yau dole ki zaki bar Gidan nan yau zaki bar Gidan nan zaki rabu da ɗana
"""”"""cikin sheshekar kuka FAREEDAH tace "Mommah Dan Allah kiyi hakuri , ki taimaka min aikata yin Hakan zai iya jefa ni cikin wani Hali
"Cikin faɗa da tsantsan bacin rai MOM ta buɗe bakinta tace"FAREEDAH ai NABEEL ya kamata ya auri Amina yau ga Amina ƴaƴanta uku,......Azmerh Kuma kin shiga kinfita kin Hana Shi NABEEL ɗin ya aure ta ,ya tsani ganin ta aduk duniya bai kaunar ganin Azmerh ta ,yau aurenki shekara biyar kenan da wasu yan watanni .. baki anfane Shi da komai ba ,saboda Haƙa yau makircin ki yaKare .zaki bar Gidan nan ,zaki rabu da ɗana ko kina so ko bakya so ,Kai NABEEL ka sake ta "Cikin zubar da hawaye NABEEL yace"Mommah Gaskiya hannuna bazai iya rubuta saki inbawa Matata FAREEDAH ba, "badamuwa inji cewar Mommah sannan ta cigaba da cewar" nayi maka uzuri ka faɗi mata da baki "cikin sauri NABEEL ya katseta ta hanyar faɗin"Haka wannan kalmar bakina ba zai iya furta taba...
""""Kallon NABEEL FAREEDAH tayi kafin Cikin sheshekar kuka FAREEDAH tace "NABEEL kabi umarni mahaifiyar ka ,kayi mata duk abunda take so Ka bani takadda ta , kuma yau zan bar Gidan ka. ba Sai gobe ba "cikin mamaki NABEEL ya kalli FAREEDAH Tare Da faÉ—in" FAREEDAH da bakin ki kike fad'a na rubuta takaddanki na saki in baki ,!...
Cikin sheshekar kuka ya cigaba da cewar" ke yau kike umartata na in sake ki ? "cikin daka Masu tsawa MOM buɗe bakinta tace" ya isa nace ya isa (ran maza ya ɓace) Cikin tsananin ɓacin rai MOM ta cigaba da cewar" tabjam! ni in maka magana baka saurare ni ba sai da matar ka tai maka magana Sannan zaka saurare ta , to yau dole Sai ka saketa ko kana so ko baka so, maza. Maza ka sake ta, domikuwa ko tare aka Haife ku yau Sai ka sake ta kuma Sai ta bar Gidan nan, sannan yau inasan Inga ni da ke waye yafi mahimmanci a gareshi,inason Ka babban ta min tsakanin aya da tsakuwa yau ɗinga inajira ta ƙarasa maganar ta Tare Da
Ajiye masa farar takadda Samar center table
"Hannunsa dake tsakanin rawa ya kai Bude farar takardan yayi ya É—auki alkalami ya fara rubutu..
"Cikin sheshekar kuka da tsananin tashin hankali FAREEDAH tace "NABEEL sakina Wai zaka yi?wani sabon kukane yasake subce mata "cikin masifa da daga murya Mommah tace " bazai sake kiba tare aka haife ku? Ai ko tare aka haife ku, yau Sai kin bar Gidan nan Kuma Sai ya sake ki, rubuta mata saki Uku in ma ana É—ari kamaka mata maza-maza rubuta mata saki tatashi Ta ba mutane gurin
"NABEEL ko Yana gamawa ya mikawa FAREEDAH farar takaddan NABEEL yayi "Mommahce ta kalleta ganin taki amsa takaddan sakin Haƙan yasa Mommah ta daka Mata tsawa tace" amsa amsa ɗauka ɗauka ,oya tashi kije ki dauko jakar ki .........

LAFANI ORGANIC SKINCARE

Dame akafiki yar uwata?
Kyan fatar ko iya gyaran fatar?,farin fata ko laushin fata
Babu riba ga macen da ta Maida kanta sauran mata?,kazamar gida
Shin har yanzu labarin LAFANI ORGANIC SKINCARE Kike ji ko kike bayarwa?
Hajiyata miye matsalar?
Fatar takice abun se lahaula?
Kingwada kingwada har kin sare?
Tsakanida Allah yaushe daren yayi balle garin ya waye ?

Inbakida labarin LAFANI ORGANIC SKINCARE wacce tasanki tasansu,
Gawurtaccen Kuma shahararren kamfanin gyaran fatane,duk lalacewar jiki,duk hautsinewar fata,duk yenda jikinki yazama abun kunya gareki, Ina tallata maki me gabadaya,

Muntarkato,munwarwaro,munkullo duk wani Abu daze maidaki wanke hannu kataba mun kara a cikin kayayyakinmu,muncire,muntsefe,munfidda,mun tantance mun hadamaku wasu irin hadaddun lafiyayyun kaya masu masifar goge fata,wallahi duk fitinar fatarki inshallah,kinzo bustop,kisiya kiyikyanda ko mace,kan juyo ta waiwayo ta dubi halittar Allah,

In har bleaching ya Bata miki fuska ko ya maida miki jiki aunty rambow ki garzayo ki sai man gyara na LAFANI ORGANIC SKINCARE,kuraje ne ya Bata miki fuska ko stretch marks ne ya Bata miki jiki?,muna da lafiyayyaun mayuka da sabulan gyaran fata da Zaki nemesu ki rasa InshaAllahu hajjaju makkatun

Ga products din kamar

Sabulun amare 5000

Dilka 5000

Tumeric vasiline 5000

Coconut milk cream 3000

Glow oil 2000

Etc

Akwai kananun packaging da manya akwai na matsakaicin kudi iya kudin ki iya shagalin ki

Domin Karin bayani.

Contact:- call or WhatsApp 08167151175

*_ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI_*

#COMMENT'S DOMIN ALLAH !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !

*AISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

*FAREEDAH NABEEL*

🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL*

Alhamdu'lillahy I'm back again lovers

*FAREEDAH NABEEL IT'S FREE BOOK, YOUR COMMENTS AND SHARE KAWAI NAKE BUƘATA, SHAKKA BABU IDAN HAR KUKAJINI SHURU TO RASHIN ZAZZAFAR COMMENT ƊIN KU NE YA JANYO HAƘAN*

*🌺 CHAPTER 11-12🌺*

*DEDICATED TO :-XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA* )

*🤝 SDEENDTM DATA SERVICES🤝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = N300. 1GB = N300
2GB = N600. 2GB = N600
3GB = N900. 3GB = N900
4GB = N1200. 4GB = N1200
5GB = N1500. 5GB = N1500
*GLO* . *9MOBILE*
1.5GB = N500.
2.9GB = N1200. 1.5GB = N1100
4.1GB = N1600. 2.9GB = N1400
5.8GB = N2100. 3GB = N1650
7.7GB = N2700. 4GB = N2100
*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
For more information call or whatsapp me
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
🪀08066268951

*🌺 CHAPTER 11-12🌺*

..D'auka ɗauka ɗauka maza maza kije ki ɗauko jakarki, kisan wani abu ɗaya! uzuri ɗaya zanmaki kishiga ki ɗauko wannan akwatin naki shi kaɗai zaki ɗauko baƙida wani abunda zaki d'auka awannan gidan de-de da tsinke da allurah bazaki fita dashi anan gidanba,jakar nan ma shima dalilin aure yabaƙi shi shiyasa zanbar maki akwatin, maza kije kishiga ki ɗauko jakar ki ,cikin daka mata tsawa ta cigaba da cewar"nace maza-maza ki tashi mana ki ɗauko, kizo ki fita kiba mutane waje
shashasha kawai bak'ar juya
"Hannun FAREEDAH dake tsananin rawa ta ƙarba takardan saki batare da ta buɗeba kai tsaye FAREEDAH ta nufi hanyar upstairs tare da haurawa saman upstairs
Kuka zuwa Wannan lokacin ya 'dauke mata zuciyarta bayan radadi da tsananin kunci babu abinda take mata
dan ahaka ta tattara kayanta da duka abubuwanta ta fito kai tsaye ta nufi hanyar fita daga cikin d'akin tare da saukowa daga saman upstairs,tsayawa tayi tana mai kallon mijin cikin zubar da hawaye "kallo ta Mommah tayi kafin cikin daka mata tsawa Mommah tace"zaki wuce ko kuwa!
'Kai tsaye FAREEDAH tanufi hanyar fita daga cikin parlourn cikin sauri NABEEL mike tsaye da niyar zai bita ,"Ina zaka? inji cewar Mommah cikin fusata sannan cikin daka masa tsawa Mommah ta cigaba da cewar"ai ta gama fita daga hurumimka dan Allah my friend dawo kazo ka zauna fool shanyayye ka tashi zagwayzagway dakai zaka bita to me zakaje kai mata maza-maza fita ki ba mutane waje,kai kuma ka dawo nan ka zauna.kai kana ma bada kanka abanza to me zakayi mata kasake ta babu wani abinda yarage atsakaninku shi dai NABEEL ɗin shiru yayi ƙana kuma har izuwa yanzu kwata-kwata ƙasa cewa komai sai famar zubar
da hawayen dayake,,,,,,,,ɓangaren FAREEDAH ko tana mai ƙarasa fitowa tsakiyar compound din gidan kai tsaye ta nufi hanyar fita daga gidan gaba ɗaya ,tana fitowa bakin titi adai-adai sahu ta samu ta tare ba tare da ta sanar dashi inda zai kai taba ta shige,,,da misalin ƙarfe goma sha ɗaya na dare NABEEL yafito compound din gidansa
NABEEL ne ya fito tsakiyar compound d'in yana k'arasawa bakin kofar motar ya buɗe mata motarsa ya shige sannan ya rufe murfin motar cikin sauri ya tada motar tunkan ya ƙaraso gate man ya wangale masa gate da wata aniyar gudu yafice daga gidan,daga ganin yanayin yanda yake tukar motartasa kasan yana
cikin yanayin tsananin damuwa da tashin hankali sai faman-sharara gudu
yaƙe asaman titi
haƙan yasa cikin minti Ashirin ya ISO babban katafaren Hotel wajene dayake ɗauke da yalwar mutane wasu zaka gansu atsakiyar compound din hotel din yayinda da kuma wasun su kuma zaka gansu a cikin babban parlourn Hotel d'in, duba da irin yanda dayawan mutane wajen keta had'a hadayansu kowa harkan gabansa yayinda Wanda kuma da yawansu samarine da yanmata sannan kuma daga ganin yanayin shigar jikinsu kadai zaka gane ko su ɗin suwaye ne domin kuwa babu wata ƴa mace ko daya awajen da take sanye da shigar mutunci yayinda da yawan mutane dake zaune a cikin babban parlourn wajen suke enjoying cool music d'in dake tashi awajen ta hanyar rawa tare da romancing din junarsu hakika daga ganin yanayin tsarin wajen kadai zai tabbatar maka da cewa ba wajen zuwa kowa da kowa bane sai dai wayanda suke jike acikin nairori musamma duba da irin tsala-tsalan hadaddun maza da kuma yan matan dake wajen saboda da sudin ba Irin gama garin Samari da yan mata nan bane tun shigowar NABEEL farfajiyan waje, da idanuwansa suka sauka akan tsirarun yan mata dake ta shawagi awajen da kuma wasu dake cikin tafkeken swimming pool din dake tsakiyar compound d'in,suna swimming acikin ruwan, Cikin sauri NABEEL yayi ƙasa da idanuwansa tare da kawar da kansa gefe, cikin wani Irin yanayin takun da yake yi ne, cikin kasaita da tabi jinin jikisa ya jawo hankalin mutane da yawa dake wajen ya dawo kansa kasancewa tun shigowarsa wajen hasken fata da Kuma kyawun fuska hadi da murdaddiyar sura jikinsa ya ɗauke hankalin mutane da yawa, shikuma duk da yasan da yawan mutane dake wajen kallonsa suka yi amma Sam bai damu ba, saboda idan da sabo yasaba da irin Haƙa
Kai tsaye gurin da ya zama kaman nanne babban parlourn cikin hotel din ya nufa daya daga cikin hadaddun kujerun dake wajen yaja yazauna asama tare da daura kansa anan kan. Dan table din dake gabansa ... NABEEL kuwa ya sunkuyar da kansa yayi a Samar table din gabansa...ya shiga cikin duniya tunanin da tsananin tashin hankalin da yake ciki, komai yayi masa zafi yarasa Ina zai sa kansa yaji daÉ—i ,wannan wane Irin masifa ce Haka!! Mommy wai wanne irin laifi FAREEDAH ta aikata maki ne wai kika tsaneta haka!!
ɗaya daga cikin masu aikin wajene ya ƙaraso inda NABEEL yake zaune,yana mai Kallon sa kafin cikin ɗan rusunawa haɗi da girmamawa ma'aikacin ya buɗe bakinsa yace"barka da zuwa ranka yadade maiza'a kawo maka? "Cikin nutsuwa NABEEL ya ɗan dago da kansa jin murya mutum akansa yakalli mutumin, yanayin fuskarsa ne ta chanja duk da kuwa bai taba zuwa wajen ba domikuwa wannan ne karonsa na farko, wani abun mamaki ma shi ne kwata-kwata baisan dalilin daya kawosa wajen nan ba, hakanan dai ya samu kansa da shigowa wajen, cikin damuwa gami da tashin hankali NABEEL ya buɗe baƙin sa yace"
Ka bani drinks
'yayin da shi kuwa mutumin dake tsaye kuwa jin NABEEL d'in ya ambaci drinks ne Haƙan yasa shi gane cewa kwata kwata NABEEL din bai taba shigowa wajen ba, domin kuwa duk Wanda ya shigo gurin nan giya yake saye yasha,idan kuma da budurwarsa ce yazo sai sun sha giyan sun shawu Sannan saurayin ya kama masu ɗaki dansu huta su jidadinsu ɗan rusunawa ya sakeyi tare da cewa "I'm am sorry Sir bamu da normal drinks saidai Wanda akayi mix ɗinsa sai kuma alcohol and wine non alcoholic 'NABEEL ko jin mutumin ya anbata masa alcohol ne yasa shi saurin dago kai ya kalleshi saboda shi tunda yake aduniya bai taba shan alcohol ba kai Allah ma yatsare shi dashan giya duniya da lahira cikin sauri ya girgiza kansa tare da kama labbansa a cikin bakinsa ya Ɗan ciza, cikin muryarsa da bata fita sosai ba cikin sanyi da kasa da murya NABEEL yace"kabani wine amma non alcoholic "okay sir inji cewar ma'aikacin yana mai juyawa
cikin sauri ya tafi Dan kawowa NABEEL ɗin wine kamar yadda ya bukatar bajimawa kuwa mutumin ya dawo hannunsa ɗauke da kwalbar wine da kuma Wani glass cup ajiye kwalbarn yayi agaban NABEEL d'in 'tare da juyawa yakoma bakin aikinsa, NABEEL kuwa ɗaukan kwalbar wine din yayi batare kuma da ya duba ko wine din neko non alcoholic bane, yaballe murfin ya zuba wine d'in a cikin cup bai ku ma damu da yawan wine d'in da ya zuba acikin cup din ba sai da ya cika cup din dam sannan ya kafa kofin a bakinsa ya fara sha bai kuma cire cup din daga baƙinsa ba har saida yaga ya shanye gaba daya win din dake cikin kofin, Ahankali ya ɗauki wayarsa dake aje a Saman table din tare da kunnata kifa kansa akan table din dake gabansa yayi, hade da turawa hoton FAREEDAH dake mamaye akan screen d'in wayar idanu, idanuwansa da suka sauka a kan kyawawan lips d'inta yadan lumshe, tare da fesar da wani irin numfashi me sanyi FAREEDAH
INA MATUƘAR SONKI! BA ZAN IYA KWATANTA MAKI IRIN MATUƘAR KAUNAR DA SONKI DA NAKE MAKI A CIKIN ZUCIYA TABA KAUNAR KIDA SONKI YANA YAWO A JIJIYOYIN JININ JIKINA,I CAN DO WITHOUT YOU ,YOU ARE MY HAPPINESS Ahankali NABEEL ya fad'a ta hanyar motsa pink lips ɗinsa
Kwanta da kansa akan table din yayi saide Kuma wani abu mamaki ko mintuna 20 ba acikin da shan wine d'in nasa ba ya ji kansa
Na dan juyawa yayin da idanuwansa ke sake marairaicewa, tamkar Wanda yake jin bacci Haƙa yanayinsa ya dawo musamma ma idanuwansa da suka soma juyewa, haɗi da chanja launi, take kuma cikin mintuna kadan yasake jin duniya tana nema juya masa ganin da yayi cewa da gaske yana neman fita acikin hayyacinsa ne haƙanyasa shi mik'ewa tsaye, tare da ɗauka wayarsa, wallet d'insa dake cikin aljihunsa ya ciro tare da budewa batare da kuma ya dubaba yaciro fararen yan one one thousand ya ajiye musu asaman table d'in,
Ahankali cikin yanayin da yake jin kansa ya fice daga cikin babban parlourn,koda ya fito tsakiyar compound d'in, kansa yadan buga, saboda yanda yake wani jin jiri na nema kai shi ƙasa, a cikin zuciyarsa yake tambayar kansa shin ma Meye kawosa wajen nan? ,gashi sanadiyyar tashin hankali da yake ciki haƙan yasa shi zuwa nan wajen sannan kuma yasa shi shan abunda yake nemar dagula masa lissafi duk laifin kine Mommy kece sila Allah ya isa tsakanin na dake Mommah, cikin dan cijewa ya nufa inda ya ajiye motarsa yana zuwa kuwa ya bude murfin motar nasa ya shiga, ya tada motar sa, da wani irin mugun speed kuwa ya cillah motar kan titi gudu yake yi sosai akan titi
Kai tsaye ya nufi gidan sa, yana isowa gaban makeken Gate din Gidan sa ne haƙan yasa Shi soma Danna wani irin uban horn, yayinda kuma karar horn d'insa kadai zaka ji ka fahinci cewa baya cikin hayyacinsa, da gudu gate man ya fito daga dakinsa ya k'araso, tare da zuwa jikin kofar gate d'in cikin sauri ya wangle masa gate d'in NABEEL kuwa da yakejin kansa asama da wani irin gudu ya shiga cikin tsakiyar compound d'in direct ko Gama de-de ta parking din nasa da kyau kuwa baiyiba ,ya bude murfin motar nasa ya fito, kallo daya zaka masa kasan cewa baya cikin hayyacinsa, maida murfin motar nasa yayi ya rufe,Cikin wani irin taku dake nuna zallah kwarjininsa ya nufi hanyar da zai Sada sa da babban parlour gidansa ahankali ya shige cikin tsakiyar parlour din sa,a Saman two-seater ya zauna hanuwansa biyu yasa ya Kama kansa dake wani irin ciwo, hakanan yake jin kunci da damuwa acikin ransa, lokcin ɗaya. yatambaye kansa, wai ma shin meyasa Ma'aikacin hotel din ya yaudaresa ta hanyar basa wine me alcohol acikin??? Shima bai saniba a
Ahankali ya dago idanuwansa da suka yi jajur ya saukesu akan hadadden Zane photon FAREEDAH wada ya manna ajikin bangon parloursu ,tashi tsaye yayi tare da karasawa wajen da zanen photo Nata yake like Ahankali ya daura hanuwansa akan picture tare da sakin smillig batare da ya yashirye ba"sugar baby
I love you ya furta ba adadi,Zanci gaba da sonki har bada,You are My Everything,My life,my soul mate,My...my....my....my....You are mine Dear I cant do without you My lovely wife....
TABBAS Ni NABEEL ina masifar tausaya wa kaina acikin halin damuwa da tashin hankalin da nike ciki Allah ka bani ikon cinye wannan jarabawarka lafiya, lallai hakika Allah ka aiko min da babban jarabawa rayuwa Allah Kasa in cinye wannan jarabawa rayuwa lafiya Allah ya kawo min mafita cikin lamuran ka,,,
________*FAREEDAHH*______
_____*Bayan sati biyu*_______
BANGAREN GIDAN SU FAREEDAH kuwa
Gida ne mai d'auke da d'akuna uku sai kitchen dake daga bangaren dama sai kewaye dake daga can karshen gidan sai tsakar gida mai dan yalwa, gidan dai kallo daya zakamashi kasan na masu É—an rufin asiri ne
azahar suna zaune atsakar gida cikin yar qaramar rumfarsu
Zaune mahaifin FAREEDAH da mahaifiyar ta suke a samar tabarma
Kallon mahaifiyar FAREEDAH mahaifin FAREEDAH yayi Kafin cikin kulawa ya buɗe baƙin sa yace "
Wai Rabi
"Na'am Malam Maman FAREEDAH ta amsa tana mai kallon mijin nata"cikin sanyin Muryar mahaifin FAREEDAH Yace" wai wace irin tafiya ne wannan NABEEL É—in yayi wanda bazai bar FAREEDAH agidan ba sai ya turo ta nan Gidan ? "cikin sanyin Muryar da mamakin abun mahaifiyar FAREEDAH ta buÉ—e bakinta tace"nima haka nagani kuma ni kasan abunda ke bani mamaki ,FAREEDAH tunda tazo Gidan nan bata wani kazar-kazar shine nace ko dai akwai wani abun ne?
"hakane inji cewar Malam sannan ya cigaba da cewar" to amma kuma ai in baki manta ba yaran nan sun shaku da junarsu kuma suna zaman lafiya da junarsu "amma duk da Haka dai yakamata dai a sake tambayan ta ,inji cewar Mama"yanzu Ina take? "Tana cikin kitchen "kira min ita "cikin daga murya Rabi ta shiga kwalawa yarta FAREEDAH kira "FAREEDAH! FAREEDAHh!!"Na'am FAREEDAH ta amsa kiran da Mamanta tai mata "cikin kulawa Mama ta furta"kizo ana kiranki "
Cikin sauri FAREEDAH ta fito daga cikin kitchen kai tsaye inda suke zaune ta nufa cikin sauri ta ƙaraso gurin su a inda suke zaune tare da rusunawa kallon su tayi kafin cikin sanyin Muryar FAREEDAH ta buɗe bakinta tace"gani Baba "Cikin kulawa Malam ya buɗe baƙin sa yace"FAREEDAHh wai me ke faruwa ne bana son ki boye min komai ki gaya abunda yake faruwa? , Malam ya ƙarasa tambayarta yana mai dubanta "Baba abunda na fad'a maka dazun shine babu abunda ya yafaru,tana cikin magana kenan sai kawai kukan tsananin tashin hankali da damuwa ya subce mata ,..... cikin sheshekar kuka FAREEDAH ta cigaba da cewar "Baba babu abunda ya faru Tana gama magana ta Mike cikin kuka ta nufi hanyar d'akin ta Tare Da shigewa cikin d'akin ta"kallon Malam Mama tayi tare da faɗin
"ka gani ko Malam! in harda akwai wani bakon Abu gameda FAREEDAH ni Ina ganewa " sauke ajiyar zuciya Malam yayi Tare Da faɗin"hakane To kyale ta bari zanzo in kira ta mu keɓance dani da ita insha Allah zata gayamin koma menene ke faruwa"Allah yasa "AMIN YAH Rabbill IZZATI Wai Ina kanin nata ?"Abubakar? "eh "Ina ji yana dakinsa "to maza kirawomin shi yazo ya tayanin rubuta wannan rubutu a jikin allo ",OKAY To inji cewar Mama tana mai mike wa tsaye kana ta nufi
hanyar zaure gidan

*_GIDAN HAJIA NAFISAT_*
A kwance Ahmed yake a cikin bed room d'insa ,da misalin ƙarfe goma shaɗaya na dare Sai famar wani uban juyi yake domin kuwa yana mugun tabawa kanshi damuwa so yaƙe kawai ya Kuma jinshi a cikin jikinta
yana hango kirarjikin ta wani irin tashi da harbawa yaji sandar Shi nayi yayi wani irin nishi tare da dafe ta gam
Yana Kara tuna kirjinta É—in nan masu cika da É—an tauri alamar sai sunji training zasuyi laushi, ya runtse ido yana danna kanshi a pillow, tare da kwance belt din gajeren wandon da bai cire ba yayi freeing d'in jikinshi domin duk .da sanyi AC dake cikin dakin Shi zafi yake ji,,zuwa can Janyo wayarshi yayi tare da nema contact d'inta yayi dialing, lokacin itama Tana kwance tana juyi ji take kamar taje part d'insa, sabida shi is feeling his hands all over her body.
Idan ta tuna yanda yake romancing d'inta Sai tsigar jikinta ta mike har wani irin ruwa taji sunabin kasanta jin karar wayarta yasa tayi saurin picking Tare da manna wayan a kunne ta domin zuciya ta tabbata shine ya kirata, tasan yanda takasa bacci Shima Haka take a wurin shi "Muguwar ajiyar zuciya ya sauke jin murya ta tace hello "baby 'yafada can kasan makoshinshi.Sannn ya cigaba da cewar"me ya hanaki bacci? "Kai nE, ta fad'a Kai tsaye "to me nayi da zan hanaki bacci baby?"turo
Baki tayi cike da shagwaba ta Fara yimai magana, "am feeling ur hand all over me, " me too baby duk da dazun muka rabu but am hungry again.i want you very badly, "come ta fad'a Kai tsaye nima ba zan iya sleep ba i need you sweet Ahmed and I want to sleep in your chest my sweet baby "ahh ya Saki y'ar Kara domin ji yayi ya kwadaita yana mai jin ina ma boob's d'inta a nashi kirjin
"baby idan fa nazo boob's d'in nan zansha sosai har sai sunyi laushi sannan kuma zan buga kwallo har sau biyar "alright to "mik'ewa yayi ya fito daga cikin bed room d'insa, direct part d'in hajiya nafisat ya nufa, yana shigowa ya nufi parlourn ,dan ko da ya shigo cikin tsakiyar parlour yayi Sa'a Mommah bata nan ta tafi kwana direct dakin NABEELAH ya nufa, NABEELAH ko tana ganin shi tana ganin shigowarsa ta sauke ajiyar zuciya, yana Gama k'arasowa direct kan bed d'inta ya hau ,sannan ya haye samata bakinsa ya dora kan nata yana tsotsa sosai ita kuma Tana shafar kansa , sun jima suna romancing din junarsu kafin suka gajiyar da junarsu, kowanne su ya samu gamsuwa sannan suka zube suna mayarda numfashi kwanta tayi ajikinsa kafin kasani tunni bacci
ya sace ta
*_ALLAH YA GAFARTA MANA KURA KURAN MU YAKUMA SA MUCIKA DA KYAU DA IMANI_*

#COMMENT'S DOMIN ALLAH !
#SHARE FISABILLAH!!
#THANKS FAN'S !

*AISHA FULANI GAL CE*
[7/4, 4:42 PM] Fulani Gal✍🏻: 💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

*FAREEDAH NABEEL*

🌹
💖💖💖💖💖💖💖💖
💗💗💗💗
💖💖
🌹

By
*A'ISHA FULANI GAL*

*🌺 CHAPTER 13-14🌺*

*FAREEDAH NABEEL IT'S FREE BOOK*
*DEDICATED TO :- ƘAWATA XAYYNEB💤💤💤(XEXEN FASAHA*)

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.