Diyam Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: DAN DAKO 1.txt
Chapter 1 of 2
D'AN DAKO
NA UMMI AYSHA
MARUBUCIYAR.
AL'MAJIRIN GIDANA
AURAN YARINTA
WAYA CAN'CANTA
AURAN USTAZ
ZAMAN TASHA
TAYA ZAN GANESHI.
AN NOW
D'AN DAKO.
BISSIMILLAHI RAHMANI RAHIM.
YA ALLAH KAMAR YANDA KA BANI IKON FARAWA LAFIYA KASA IN GAMASHI LAFIYA.
NA KUDINE AKAN FARASHI MAI SAUKI.
DARI UKKU KACAL.
KATSINA STATE.
""Katsina garine daya hada jinsin mutane daban daban yan kasuwa da yan boko wayayyi mutane ne ga karatun Addini garine mai yalwar mutane dakuma karrama bako mafarin takenta da KATSINAWA DIKKO DAKIN KARA KUNYA GAREMU BADAI TSOROBA.
Tana da yalwar unguwanni masu dumbin yawa na talakawa dana masu kudi.
G.R.A
Kyakyawar unguwace data tara hamshakan masu kudi yawancin su duk yan bokone sai yan kasuwa unguwace da baka ganin gilmawar mutane barkatai sai dai kowa yazo da abun hawanshi ya wuce sahoda shimfidaddan titine daya wadatu da kwalta da tatafi dodar gefe da gefen titin kuma wasu irin shukokine masu tsawon gaske da sukayima gidajen dake jere reras cikin unguwar kawanya hakan yasa titin yakasance mai masifar kyau da daukar hankali bakajinkomi sai na isakan dake kada shuke shuken .
Tsaye nayi ina karema tafka tatkan gidajen dake unguwar kallo ka na gilgiza tare da cigaba da tagiya ina tinanin kamar bazaa mutuba da mutane ke gina irin wannan katafaran gidajen.
Wani wawan burki naja gajin wani tamfatsetsen gida dayafi kowane gida akan titin kyau da tsaruwa tindaga get dinsi da kalar penti dake garai da irin furanni da aka zagayeshi da su.
Jin ana kakaniyar bude babban get din ne yasa nayi tsaye danba idona abinci.
Wani dattijone mai kimanin shekaru hamsin zuwa da biyar ya wangale get din da kyal .
Inda wata jar mota kirara FERARI ta sheko da gudu takusanyin kan yatsun dattijon nan da gudu ya kauce tare da tsayawa gefe yana maida numfashi.
Ganin motar ta wuce batare da tatsayawaba yasashi gilgiza kanshi tare da bude bakinshi yace Allah ya shiryaki AMNAH yasa kifara ganin daraja manyanki som halinki ba dayaba da mahaifiyarki babu abunda kika rage na mahaifinki.
Dakyal yasamu ya maida get din ya rufe tare da zama akan dan bencin dake gefe yafara saita Radio dake hannushi.
Wata matashiyar budurwa da bazatafi shekaru 17 bace ta fito da sauri daga cikin faskeken gidan ta nufoshi tanafadin .
"Baba Madu wai Amnah fita tayi ne?
Da sauri ya ajiye radio ya mike tsaye yace.
" eh hajiya Amal tafita badanjimawaba ina kwana."
Kanta ta gilgiza tana Aro fararan idanuwanta tace baba da allah kadaina gaidheni nifa jikarkace wallahi mantawa nayi bangaishekaba ina a rudeme tare fa Mamy tace zata aikemu yo sayayya kasuwa wai ita bazatab taita karo da talakawa tafison super market kuma taya za'ayi asaida kayan da Mamy ke rabawa cikin Watan Ramadan super market?
Murmushi Baba Madu yayi yace
"To kuje inda takeso mana Hajiya Amal.
Kanta ta dago ta kalleshi tace baba kayan fa da yawane irinsu masara gero dawa acca Alkama baba kasan sai kasuwa.
Shuru yai sai murmushi dayaketa zuvawa batarr dayace komi ba Dan yana ganin matsalar suce ta guda bai kaqta ta shafeshi ba.
Juyawa tayi cikin gida ranta amatukar bace .
Kallonta yayi ya gilgiza kai tare da cewa allah kenan yayoku ciki daya amma ya bambanta halinku kekuma sai kika rakko na mamanki ita kumabta dauki na babanku.
Kai tsaye babvar kofar dake zagaye da glass din palon ta bude tashiga babban falone sosai yasha blue da gold na kujeru da labulaye da carpet bakajin kominaciki sa karar Ac da wani irin sihirtaccen kamshin tiraran Wuta mai masufar dadi.
Zama tayi tare da dafe kanta tana jin bacin rai na halin da yar uwarta take nunama talakka.
Jin kara tafiya daga saman benen yasata saurin dago kanta inda ta saukesu fess akan kyajyawar fuskar magaifiyarta dake sakkowa fuskarta cike da alamaun mamaki.
Kyakyawar macace fara sol da ita daga ganinta buzuwace ko balarabiya sanye take dawani dakeken lace maroom da kyanshi ya usa fallasa asirin tsadarsa yan kunne gold je akunnanta hannayenta sanye da manya manya zobuna gold maeu masifar kyau da tsada.
Cikin daddadan magaja ta sakko kasa tare da zama kusa ea Amal tasanya hannunta ta juyo da habar Amal din tare da tambayar.
"Lafiya bakuje ba tare bayan naji karar fitar motar Amnah"?
Ido cike da kwallah tace Mamy ta tafi ta barni nason ta tafi yin gaban kanta ne ai dama batayi niyyar zuwa kasuwar nan ba som taya za'ayi tace sai super market abinda in kasuwane da munje layin yan Awo zamu shiga gasunan masu kyau sabbi bana super mariet ba da wasu zakiga sun kwashi shekaru saboda ba acen ne mahallinsu yake ba.
Shuru mamy tayi ranta abace .
Sai da ta nisa kana ta dakko wayar ta ta lallatda ta kara akunne tana huci tare da gilgiza kafarta daya da tasha jan lalle.
Jin an daukane yasata fara magana cikin tsanainin fushi.
"Kin kyauta kinyi abunda Ranki da Zuciyarki suka Raya miki, Amma wallahi kisani kika siyomun tsaffin kayan da Zanyi sadaka dasu sai ranki ya masifar b'aci, Saboda nafiso in'bada abunda zan iya ci, Sakarai kina Mace amma kinkasance mai kyamar talakawa bayan bakison inda Aure zai kaikiba, Shashasha kawai ta tsinke wayar.
Suna zaune kimanin 30mnt sukaji an buÉ—e get din gidan.
TSuke fuska Mamy ta karayi tare da maida hankalinta ga waya tana latsawa
Bayan kamar ten mnt sukaji an'buÉ—e kofar tare da sakin siririyar Sallama.
Sanin muhimmancin sallama yasa Mamy batare da ta dago kai ta kalletaba ta amsa.
Masha Allah itace kalmar dana furta lokacin da idanuwana sukayi tozali da kakyawa budurwa da bazata wuce shekaru Ashirin da biyu ba aduniya, Farace sol irin farin Mamy ,Gawasu mayun idanuwa dake gareta wayanda suketa lumshewa kamar zatai bacci, Daga cikin kwayar idon nata kuwa wata zaiba -zaiba ce ke shinning aciki ,ga wani dogon hanci har baka ,sai É—an bakinta mai Dauke da pink lips,Atakaice Dai kyakwace ajin farko, gata doguwar mai faffadan jiki dai- dai misali ,Tana da wani irin shape mai masifar É—aukar Hankali, Ga wasu cikakkun Brea's da hips É—inta masu tsananin fadi da girma, sanye take cikin wata Abaya brown mai duwatsu tabi jikinta tayi luf sai kafarta dake sanye da coffe din Tom's da yar jakarta data kasance coffe.
Ahankali ta karaso cikin palon Idon'ta naga kan mahaifiyar Tata ,Gudan Hannunta kuma na rike da madaidaiciyar kula.
Waje ta samu gefe da ita sosai ta zauna tare da fadin
"Mamy nah fushi kike dani?
Nifa ba kasuwa naje ba,
Naje gidan Nene ne tayimun Danbun kaji gashi fita zatayi shiyasa kamin Amal ta shirya naje na dawo, Amma sai faÄa kike Mamy babu ko Saurarawa, Halan wannan yarinya ta hadamu takarasa tana sakarma Amal harara.
Baki Amal ta turo tana sake lafewa jikin Mamy'n.
Kai Mamy ta dago jin Abinda tace tare da sassauta fuskarta tace.
Ai'nasa gaban kanki kikayi Amnah,Nasanki sarai wallahi zakiyi fiye da haka!.
Kanta ta shafa tare da yatsina fuska tace
"kema Mamy kibari Abba ya wadata gidan da ma'aikata wayanda zasuna miki komi Amma kinki, Amma kamarmu Ace wai mune zamuje kasuwa muyo wannan sayayya, Inama laifi Ace shinkafane ko drinks Amma kawai sai Aganmu munje yin awo, Som kamanni mu bai dace da hakaba !Takarasa cikin natsuwa kamar ba ita ke maganaba.
Ido Mamy ta tsiramata sosai tana kallonta, acikin zuciyarta kuwa Abubuwa da dama take sakawa game da gudan jinin nata, Kanta ta gilgiza tare da faÉ—in.
"Ki ajiye wanna Kular Naman kitashi kuje, in kuma bazakiba bani kudina ,Ma'aikata kuma banaso so kuke in lalataku sai an'kaiku gidan aure a koroman ku akan baku iya komi ba ko?
Baki Ammah ta turo tace nida gidana nike fatan a wadatashi da kayan more Rayuwa, aƙalla inaso inga mutum sama da goma aƙal kashina suna mun bauta ina biyan su,Ta yanda ko hakki zan ɗauka akwai wanda zayyi saurin mikoman, Saboda abun ya kasance aikin shi ne.
Cike da bacin rai mamy tayi kwafa tare da cije bakinta.
Cukin natsuwa Amnah ta mike tsaye tare da gyara rolling É—in dake kanta ta sargafa jikkarta key din motar ta ÆŠakko ta rike tana gilgizawa Tare da kallon Amal batare da tace komi ba ta sanya kai ta wuce.
Amal tason bazata tankamataba hakan yasa da sauri ta mike tsaye tare da yafa gyalanta tace .
"Mamy nah sai mundawo."
Fatan Alkhairi tayi musu tare da kishin giÉ—awa akan lallasan kujerun palon tana lallatsa waya ta kanga a kunne.
Jim tayi kafin a É—auka.
Ana É—aukar wayar kuma ta sauke ajiyar zuciya Tare da faÉ—in.
""Akwai matsala Haj Lubna, Akwai ga garumar matsala wallahi, Halin Amnah yana masifar bani tsoro da mamaki, ita som batason haɗa jini da talaka ba ina bauta zai mata ba, batason ƙulla mu'amullah da talakka batason shiga inda talakka zaije, Ita kawai ta ɗauki talakka An halitto shine dan Yayi bauta a'sallameshi, Kana ta ɗauki talaka mutum ne mai kasada Akan Rayuwar shi in Dai zaka bashi kuɗi ƙalilan, Tana ganin Talaka mutum ne wanda zai iya bada ranshi da rayuwarshi dan kudi, Hajiya Lubna ina ganin lokaci yayi da zan zaunar da ita ina warware mata zare da Abawa..
Ajiyar zuciya ta sake saukewa akaro na biyu kana tace shikenan sai na ganki ta kashe wayar..
Amnah
Suna fita ta faÉ—a motar ta tare da kifa kanta akai ta sauke ajiyar zuciya, Haka nan take jin wani yanayi marar daÉ—i dakuma bakin cikin da baida musultuwa , Ko kaÉ—an tanajin kamar zatajene inda za'ayan'yanka naman jikinta ,Karshentama tason yanda talakawa basu da hankali suna iya takamata kafarta.
Da sauri ta rintse idonta tare da dago jajayen idonta da suka canza launi ta zubasu ga Amal data buÉ—e motar ta shigo.
Cikin rawar murya mai hade da tashin hankali tace.
"Hankalin ki ya kwanta zaki kaini inda zuciyata bata aminta da zuwa ba ko? Wallahi Amal inajine kamar numfashina zai ɗauke saboda masifar baƙin cikin da nike ciki, Waiku wace irin zuciyace daku keda Mamy Nason shishigema Talakka? Muna da kuɗin da in mutum dubu mukeso mu aje awannan gidan zamu ajeshi kuma zamu kyautata sallamasu, Amal jibi gidan ubanmu jibi irin motar da muke hawa amma ace da ita zanshiga kasuwa takarasa tana dunkule hannunta tare da dukan dayan.
Tsoro furgici ruɗu suka ziyarci Amal lokaci guda,bata taɓa tinanin abun yar uwar nata ya girmama haka ba ,tana ganin da duk abunda take kamar wulakancine sai yanzu ta tabbatar da duk abunda take akan gaskiyarta take yinshi.
Motar ta tada Tare da janta afusace.
Cikin sauri Amal ta kalleta tare da kallon get din.
Ajiyar zuciya ta sauke ganin tini Baba Madu ya bude get din tare da lafewa bayanshi.
Karcet ta fita da motar tare da cillata kan titi.
Cike da kwarewa take murza sitiyarin har suka fara shigowa cikin gari inda Amal ke mata nuni da Hannu inda zata shiga dan ita batama taba zuwa wajen dake da cinkoso ba irin wannan.
Duk inda suka gifta ido ke dawowa kanta, kasancewar motar samanta bude yake.
Siririn tsaki taja tare da furta.
"Jakai kawai motar ma sai ankalla kai talakka baiba."
Ido Amal ta rintse tare da kauda kanta gefe.
Ahankai suka shigo cikin faskeken get din da aka rubuta CENTRAL MARKET,
inda suka dinga wuce wurare har suka bullo ta get DIN yan Awo.
Tsaki ta ƙaraja akaro na ba Adadi Tare da Ɗakko wani brown din glass ta toshe idonta da shi, Tare da kara tsuke ɗan karamin bakinta dake zagaye da pink lips.
Amal tace ga inda zamuyi parking cen kana mufito ba.
Kallonta tayi a kufule kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta tsaya dai dai wajen wasu mutane dake tsaye suna rike da buhun huna gero.
Wani dattijone cikin kamala yace yam Mata gero kike sone.?
Kamar zata kyakeshi kuma ta daure tace
"Eh".
Tare da buɗe jikkarta ta yago wata paper tayi rubutu kadan tare da mikamai dan gani take tsayawa magana da shima ɓata lokacine.
Jujjuya takarda yashigayi dan yakasa fahimtar mita rubuta dan da turanci tayi rubutun.
Kafeshi tayi da ido tana kallo dan ta fahimci abunda yake nufi, tsaki ta saki sosai wanda yasashi juyowa ya kalleta saikuma yafara kokarin magana.
"Babaaaa"
Itace kalmar data ratsa dodon kunnasu ta katsema dattijon magana da yake kokarin yi.
Ahankaki ya juya ga saurayin da yayi shigar buzaye inda ya rufe fuskarshi baki ɗaya da baƙin rawani, Ƙafar shi sanye da slipas masu saukin kuɗi, Baƙin wandone jikinshi sai farar riga ta wani yadi da yasanya ,Baka ganin komi sai kwayar idonshi .
Dattijon yace Yawwa Habu kaimun wannan takarda shagon Mai Shadda kace nace ya fad'amaka Abunda akasanya saika kawoman.
Dan jim yayi kana ya dago ya kalli mutumin baice komi ba kuma yafara tafiya cikin sassarfa.
Anan na karemai kallo dogone sosai gashi da wata irin kira ta karfafan maza ,Cike da sassarfa yake tafiyar har ya shawo wata kwana inda ba yawan mutane sosai Kana yasamu wuri ya zauna ya duba takarda baki dayanta yana gama dubawa ya tashi ya maidata aljihu yayi gaba ya dawo inda dattijon yake.
"Akausashe yace bayanan amma na haɗu da wani na bashi ya dubaman tana bukatar gero dawa masara acca alkama buhu hamsin- hamsin sai kamata lissafin kudin kana Asamata mota,Ya ƙarasa yana kokarin wucewa.
Yalwataccen murmushi ya faÉ—aÉ—a ga fuskar Dattijon yace.
" Kai amma Alhamdulillah dama yau mukayo sabon sari duk zata samu, Kai Habu kaje store ka kwasomata kayayayyakin kana sawa a'mota ko kunzo da motane Hajiya?
Ya tambayi Amnah.
Bakinta ta tabe ta juya kai da sauri Amal tace aa baku da D'AN DAKO ne wanda zai kai a'mota?
Da sauti yace ga Habu nan zai kai maku duk inda kuke so.
Kallonshi Amal tayi sosai tace sai kasasu a'mota kabiyomu ko?
Kanshi ya gilguza batare da yace komi ba.
Cikin sauri yafara tafiya zuwa wani É—an shago dake tsaune da hatsi cike da jarumta yake sabo buhun nan y'ana sasu bayan motar.
Sosai Amna ke kallanshi tanaji inama ace kasanta yake dayasha bauta son rai , Da n daganinshi zai jure wahala .
Saida ya Tabbatar da ya cika bayan karamar mota kana ya koma wajen Dattijo'n cikin wata irin murya da som batai kama da ta buzaye ba yace .
"Baba nagama amma duka buhu hamsin nasanya zanje indawo sai inkwashi sauran.
Da sauri Baban ya daga kai tare da cewa yawwa kaga kana da naira dubu biyar kenan a wayanda ka É—ora, kuma suna son buhu kusan dari biyu kaga yakama zaka samu dubu ashirin yau kenan.
Bai ce komi ba haka kuma babu wani alamun farin ciki a abunda aka faÉ—amai ya juya ya shiga yar gwatsar motar ya tada inda duk ya wuce zakaga hayaki mutane kuma na kiranshi da Bukar Buzu .
Duk uban kiran da akemai sai dai ya juya ya É—aga musu hannu amma babu wanda ya taba cewa ga kalar fuskarshi ko kalar magana shi sai Dattijo.
Tafiye suke har suka shigo cikin gari sosai inda keda cunkoson ababe hawa.
Cikin fushi ta tsaida motar .
Ganin haka yasashi shima tsaida tashi dake bayan tasu.
Afusace Amnah ta fito ta isa wajenshi rai aɓace. "Tace kai wane irin shashashane kidahumi ? taya zaka cikamun kunne da ihun wannan gwatsar motar taka ?Miyasa bazaka bari inyi nisaba kamin ka biyoni? Matsala mu_amullah da jahilai kenan talakawa masu aiki irin na dabbobi,Dan kaja al'umma su raina ajina kaja aga tare muke ,ina mu'amullah da kazami irinka wawa kawai mtssss.
Tinda ta fara magana bai tankamata ba haka kuma babu niyyar tankamata a'tattare dashi.
Afusace Tace kai D'AN DAKO Bakajinane.
Shuru yamata yana kallon titi.
Dogon tsaki taja tare da watsamai yawu ta wuce.
Ahankali yasanya gefen rawaninshi ya share baice komi ba sai Yatsun hannunshi da ya dinga É—aÉ—É—agawa ahankali saman sitiyarin motar.
Motarta ta koma ta tada tare da cillata bisa titi aguje.
Tada tashi yayi yabi bayanta har suka ido kofar gidan nasu.
Hon tayi da sauri Baba madu ya bude ta danna hancin motar ciki .
Ganin haka shima yasanya tashi aciki dai- dai tsakiyar gidan yayi parking bai yarda ya karasa wajen da ta ajiye tataba ya fara sakko dasu cikin Sauri, Cikin ƙanƙanan lokaci yagama yayi tsaye yana jiran abashi cikon da zai kaima Baba kana ya Ɗakko sauran.
Amal ce ta fito da sauri ta karaso wajenshi ta mikamai kudi tace dan Allah kayi hakuri dazu naga kamar Aunty Amnah namaka faÉ—a ko?
Kai ya gulgizamata cike da gundura shi kudin shi kawai yakeso tabashi ya wuce ta tsayamai tambaya.
Kudin ta mikamai tare da fadin munafa jiran sauran yanzu.
Bai cemata komi ba ya faɗa motar yafara ƙoƙarin tadata amma taki tashi.
Ahankali ya sakko Tare da kwanciya ƙasan wajen ya danyi taɓe -tabe 'nshi kana yakoma yatada amma still taki tashi.
Fitowa yayi tare da dafe kanshi yanajin kamar ya saki kuka ga wata mahaukaciyar yunwa da kishi da yakeji , Babu abunda yaci ya fita kasuwar yana zuwa kuma aka haÉ—a shi da wannan aikin.
Tausayi sosai Yaba Amal dake tsaye gashi ya nade fuska duk uban zafin da ake da alama ruwa za'ayi dan garin ya É—auki wani mahaukacin zafi, Cikin sauri ta koma palonsu tare da shiga kicin ta samu wani katon flat tazubo shinkafa da miya da taji naman kaji da coslow gefe ta dauki wani flat madaidaici ta cikashi da Pepe chicken tare da É—aukar kunun Aya mai sanyi ta tsiyaya a madadaicin juk ta É—auki robar ruwa guda daya ta shirya kayan akan babban tire tafito da sauri.
Akan hanyar fitane daga palon sukaci karo da Ammah ta bita da kallo.
Fuska Amal É—in ta É—aure sosai tare da buÉ—e kofa tayi saurin ficewa.
Kai tsaye inda yake ta nufa tare da.
" Cewa sannu kana ta shan rana motar yaki tashi ko?
"Um" yace agajarce.
Dago kanta tayi ta kalleshi ganin yanzu har girar shi ana gani sabanin É—azu da kwayar idon shi ke rufe.
Ganin hakan ne yasa da sauri ya jawo rawanin ya lullube ko in nashi yabar kwayar idon nashi abuÉ—e.
Murmusi ta saki tare da cewa ku buzaye bakwajin zafi bakwajin kuma nawi?
Shuru yamata yana jin ɓacin ran surutunta shidai yatsani atasashi gaba anamai magana .
Abincin ta ajiye gabanshi tace" ÆŠan Allah ka zauna kaci sai in'kiramaka mai mana gyaran mota kaji?
Kai ya gilgiza cikin kuma yanayinshi na sanyi ya bude baki .
Yace nakoshi Allah ya amfana .
Ido ta zaro tare da haÉ—a hannayenta tace dan Allah da manzonsa ka zauna kaci abincin nan, Na rokeka, in'ba hakaba Amnah zatamun dariya wallahi, ka taimaka takaras tana dora kanta akan wuya alamun roko.
Dan jim yayi sai kuma yace shikenan na gode amma kijuyemun aleda kar in ɓata muku kwanikka yakarasa cikin sanyi.
Tausayi yabata sosai wato yana ganin bai kai matsayin da zaici abinci cikin kwanan da zasu ciba kenan.
Cikin natsuwa tace aa mudakai duk yan Adam ne bawani abu kaci kawai.
Jin cikin shi namai wani mahaukacin yatsinawa ne yasashi mika hannu biyu ya É—auki kayan abinci tare da buÉ—e Bayan motar ya ajiye kana yashiga ciki shima yayi shuru yana jiran ta tafi.
Fahimtar hakan yasata juyawa ta koma ciki tana mamakin yanda yake da kamun kai haka da kunya kamar ba DAN DAKO ba dan tason su da fitsara.
Yana ganin wucewarta ya juya ya kalli ko ina ganin babu kowa sai mai gadi da shima ya juya baya yasashi kai hannushi bayan rawani ya kwance tare da fara zagaye fuskanshi dashi har ya kwance.
Ahankaki ya ÆŠago kanshi yana sauke numfashi.
Wani irin tsalle zuciyata tayi da tasani sakin wayar batare da na shirya ba......
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: 🌹D'AN DAKO
MALLAKI
UMMY AYSHA🌹
3ï¸âƒ?&2ï¸âƒ?
""Masha Allah itace kalmar da ta samu fitowa daga cikin baki na.
Wani irin haɗaɗɗan saurayine fari sol irin farin larabawa, ga wata tausassa sumar da tayima kanshi ƙawanya, ga sajenshi da yayi ma sumulmula fuskarshi kyau yayi shar sakamakon zufa da fuskarshi tayi, Wani irin dogon hanci gareshi da yatafi D'oɗar har baka, ga wasu jajayen lips da suka dace da kyakyawar fuskarshi, yana da idanuwa masu masifar kyau da ɗaukar hankali.
Ahankali yaja hannun rigarshi sama kutt na furta lokacin da idanuwana sukai tozali da kyawawan hannayenshi da suka kasance farare sol, Ga galgasa da tama hannu rumfa irin dogayen nan mai tsananin sheki da sulɓi.
Robar ruwan ya É—auka tare da fidda hannunshi waje ta window mota ya fara wanke hannun shi.
Yana gamawa yaja kwanikkan tare da buÉ—e su.
Idon shi ya lumshe dan yaushe rabon da yaga abinci mai kyau kamar wannan.
A'hankali yayi Bissmillah tare da fara tsakurar abincin kaÉ—an -kaÉ—an yana ci.
Baiwani ci da yawaba ya ture tare da turo hannun shi still ya wanke ya É—aga cup din Kunin Ayar yasha sosai saida yayi rabi kana ya ajiye.
A'hankali bakin shi ke motsawa alamun Addu'a yake ta bayan gamacin abinci(ALHAMDULILLAHI LAZI AÆŠÆŠA'AMANI HAZA, WARA ZAKNIHI MIN GAIRI HAULIN MINNI WALA KUWWA)
Idon shi ya lumshe tare da jingina kanshi da motar.
Dai -dai kuma lokacin ne aka fara iska mai tsananin karfin dake nuni da ana gaf da sakko da Ruwan sama.
Idon shi ya lumshe tare da shaƙar kanshin ƙasa dake tasowa.
Da kallon gefen da kayan daya ajiye musu yake wanda ya tabbatar da in ruwa ya safka akansu sun gama yawo.
Cikin natsuwa ya maida rawanin fuskar shi tare da fitowa yafara tsakula motar dan yasamu ta tashi yakara gaba kar ruwan ya safko amma motar taki tashi.
Tsananin fushi yatasomai wanda yasashi kaima motar wani wawan dukan dayasa marfin ɓallewa ya fita.
Aƙufule ya kwaso tiren kayan abinci tare da ajeshi cen gefe inda za'a iya gani kana ya dawo yana ɗaga kanshi sama ganin yanda garin ke rinewa sosai.
Tsaki yasaki tare da fara kokarin tafiya.
Dai -dai lokacin ne kuma Amal da mam6y da Amnah suna fito cikin sauri Amal tace .
"ÆŠan uwa dakata mana."
Shuru yayi batare da yatsayaba kuma bai fasa tafiya ba.
Yana gab da cimma get Amal tace katsaya Dan Allah.
Cak yatsaya batare da yajuyo ba.
Rai ɓace da ganin yanda yaketa izza Amnah da tasha wasu riga da wando da suka masifar yimata kyau rigar orange mai ratsin Black sai wandon kuma daya kasance Black mai ratsin orange kanta sanye da wata Black din hula data ɗan turata baya yalwataccen gashin goshinta duk yafito, daga Baya kuma foygon gashinta ya bazu akafaɗata sai sheki yake,Cikin isa tafara tako cike da izgili har zuwa inda yake.
Cikin tsananin ɓacin rai tace.
"Mene Acikin Tumbi banda kashi,Ina ɗan burburi ina niganci,Ina talakka ina girman kai,Ina D'AN DAKO ina iskanci da har za'adinga kiranka amma kayiwa mutane banza ka kyalesu kai ga shashasha ko? Wawa baƙauyen da yakasa gane gabas da yamma, Kayi maza kaje anason ganin ka koba sallamaka za'aiba da kake nunama mutane iko, Takarasa tana nunamai inda su Mamy suke tsaye akan Bagala..
Da zata lura baki dyayan jikinshi kyarma ya d'auka kyarma da rashin ganin fuskarshine yasa aka kasa ganewa...
Amal tace Mamy kije da kanki kartamai wani abu fa.
Cikin amincewa da maganata Mamy ta tattako cikin dattako har inda suke tsaye.
Sallama tayi tare da cewa bawan Allah munata magana amma shuru .
Baice komi ba sai juyo da kanshi da yayi ganin Babba maca ce cikin mutunci ya buÉ—e bakin shi ya gaishe ta .
Amsawa tayi cikin fara'a .
" Tace dan Allah ko zaka iya zuwa ka kwashemun kayan nan, Naga kamar za'afara ruwa kuma munan bamu da masu kwashewa wancen Tsohon bazai iyaba saboda halin girma ta nuna mai gadi.
Kai ya jinjina batare da yace komiba yayi gaba cikin sassarfa.
Yasa hannu zai É—auki kayan kuma yayi tsaye yana tinanin ta ina zai dosa dasu ga bakin shi yayi Nawin da bazai iya magana ba.
Mamy takatse mai tinani da faÉ—in ga inda zaka ajiyesu acen, Wancen store É—in dake kusa da dakin Baba Madu.
Baice komi ba sai kwasar kayan da ya fara cikin jarumta yana kaiwa kamar ya d'auki kwali.
Yana gab da gamawa akafara iska mai matsanancin ƙarfi.
A'hankali ya duƙa yakama kowanne buhu da hannu ɗaya yazamana buhu biyu ke ahannunshi yafaraja da sauri.
Suduka kallo suka bishi dashi inda Mamy jarumtar saurayin ta burgeta, Hakanan taji sha'awar samunshi amatsayin wanda zai dingamata hidimar gida koda kuwa aikin kula da get ne, Dan taga dakyal Baba Madu ke buÄeshi yana rufewa.
Zai kai buhun karshe cikin sauri jin ana yayyafi gefen buhun ya fashe wanda yasa Dawar dake ciki fara shatata.
Saurin ajeshi yayi cikin zafin nama ya sungumi É—aya'n yayi É—aki.
Dawowa yayi ya kai wanda ya fashe tare da Sunkuyawa yana kwashe wadda ta zube.
Fararan ya tsunshi yasa yana tattarawa yana tsaka dayi Saiji yayi an takemai su da ƙarfi da tsinin takalma.
Wanda hakan yasashi saurin juyowa da karfi ya sauke kwayar idon shi cikin ta Amnah.
Bin dogayen yatsunshi take da kallo ganinsu wasu irin farare tass har wani jaja sukeyi ga tsintsiyar hannu A yalwace da galgasa..
Ido takashe tanamai kallon kurullah tare da kara É—aro idonta a murzazza fatar shi datayi lumi.
""Kai ÆŠan Dako ne kuwa? In har takasance haka miyasa kamuna asara? Kana aiki da hankali kuwa? Kai da kake Talakka kai ya kamata ace kafin kowa iya tattali, Amma saboda ba gidan Tsoho bane sai a wifintas?
Shuru yayi har lokacin kanshi a sunkuye yake sai hannunshi data danne da takalma da yake kallo wanda still tana akai taki É—agawa shima bai motsa ba..
Mamy takaraso wajen tare da dakamata tsawa da ta sata matsawa.
Kuɗi mai yawa Mamy ta ƙilgo tabashi tare da cewa.
"Dan Allah kayi hakuri kaji ko,Yarinta na damunta ,Ƙarɓi wannan maza katafi kaga am'fara yayyafi wannan kabarshi ba damuwa ko Baba ya ba tsuntsaye.
Mikewa tsaye yayi tare da Ƙarɓa kudin ya kilga ya dauki dubu biyar yace.
Ga sauran nan na kilgi abunda ke hakkina .
Mamaki sosai yaba Mamy wanda ta bishi da kallo na ganin yanda yabata maƙudan kudin da ita kanta batason adadinsu ba.
Murmushi ta saki tare da cewa" ka rike nabaka ai.
Kai ya gilgiza alamun a'a...
Tsawa Amnah ta dakamai tare da faɗin basu kazo nema ba? Kuma zaka tsaya kana ja'inja da ita munafuki ka Ƙarɓa ka wuce daga nan ka cikamu da warin talauc....
Tass!Tass!Tass!!!
Haka Mamy ta wanketa da kyawawan maruka guda ukku wanda sukasata Tuntsirawa.
Kamin mamiu ta juyo har yakai get cikin sauri tare da kwance rawanin kanshi yafara tafiya.
Kiranshi mamy keyi ko tsayawa baiba.
Cikin ikon Allah yana fita yaga mai Machine ya. Haye tare da" faÉ—in ya kaishi kasuwa.
Ganin mai machine na kallon shine ya sashi tunowa da ashe fuskarshi ba É—aure take ba, Da sauri ya naÉ—e fuskar yabar kwayar idon shi.
Cikin rawar jiki da son samun shiga mai machine yace
"Wallahi Dan uwa kaman kama da wani Soja mai suna Sadeeq daya ƙasance Ɗan Gidan Matawalle...
Tsawa sosai ya daka mai tare da faÉ—in saukeni! Dan na hau machine É—inka shike nuni da kasamu damar da zakamun tambayoyin da Ranka keso ?Maza saukeni anan kamin in maka abunda bakai tinani ba, Duniya ba akamane da zaka tsareni da tambayar banza yakarasa cikin sauti da rawar jikin da ta furgita Mai Machine.
Cikin Rawar ɗari mai machine yace "Kayi hakuri Wallahi nima cewa nayi kamace saboda na taɓa ganin shi so ɗaya gidan da nike kai yaransu makaranta Lokacin ma da kek....
Kan ya ƙarasa ya saki wata gigitatta tsawa da tasanya mai machine saurin yin parking tare da direwa ya yanka da gudu..
Tsaki sosai ya saki tare da sauka yafara tattakawa da sauri dai-dai lokacin ne kuma aka tsuge da ruwan sama sosai.
Babu abunda yashamai kai tafiyar shi yake cike da zafin nama sa hannayenshi da yasa ya tare Duka aljihun shi saboda wayarshi da kuma kudin Baba daya karb'o.
Abangaran Mamy kuwa afusace ta kalli Amnah tace ke da kinson Asalina da naki da kuma wahala rayuwa danasha Wallahi da baki kyamaci talaka ba , Saboda...Sai kuma tayi kwafa tare komawa ciki tana share Kwallah a fakaice.
A ɓangaren Amnah kuwa.
Kyarma sosai jikinta ya É—auka akan talakka yau aka mareta aka kaskantar da rayuwar ta agaban wanda baida matsayi.
Jin ruwa ya kaule da karfi yasata tashi jiki asanyaye tayi É—akin ta tare da É—aga waya ta Daddana.
"Please Abbah ka dauka"
Tafada tana yarfe hannu tare da matse Kwallah.
Jin ta kase bai ɗaga ba yasata hakura sai kwanciya da tayi akan makeken gadonta ta saki wani mahaukacin kuka mai tattare da ƙunar zuciya..
Aɓangaran Mamy kuwa tana shiga ɗaki ta dyauki ƙaramar wayar ta tare da kiran Mijinta Alhaji Isa mai Zinarai da number shi ta sirri da bakowa yason shi da itaba sai amintaccen shi.
Bayan ya É—auka suka gaisa .
mamy take tambayar yaushe zai dawo sunyi kewar sa?
Murmushi ya saki tare da faÉ—in nima haka amma next week ina nan dawowa insha Allah ina Yara na?..
Farin ciki sosai Yakamata inda tace" To Allah yakawoka lafiya zanma tarba ta mussam man .
Murmushi yasaki mai sauti yaire da faÉ—in nasani matata nason zakimun fiye da haka .
Dan jim tayi batace komi ba dan gane da yabon da yamata.
Daga cen ɓangaran yace. "Are you ok Sweetie?
ÆŠan nisawa tayi kana cikin raunatata murya mai haÉ—e da roko tace Hubby wallahi alfarma nike nema awajenka.
Ajiyar zuciya ya sauke tare da faɗin Alhamdulillah da awajena kike nemanta ba awajen kowa ba, indai har kinsanni kinsan waye ni to kinson babu Abinda zan gagara yimiki, Dan haka faɗi buƙatunki kai tsaye nida abunda kikeso duk mallakainki ne ...
Wani irin sanyi ya ratsata cike da kwarin gwiwa tace "Hubby agasjiya ina da bukatar sabon mai aiki , Saboda Baba ya manyanta, Ga rabon nan da zanyi bazan iya cewa komi sai su Amnah zasuyiba kadai son halinta zamuyita samun matsalane da ita.
Shikenan Tsadadda "Matata duk abunda kikeso haka za'ayi insha Allah zanyi ƙoƙari sosai wajen samo miki wanda ya dace.
Da sauri tace ''Am nace ba ...
Nan ta kwashe duk abunda ya faru game da wanda yama su Amnah Dako tare da jaddada mai cewa zai iya dayuke duka ragamar gidan baki É—aya, Fatan ta dai ya bata izinin zuwa nemanshi wajrn mahaifinshi dan taga alamar yayi fushi da abinda Amnah ta mai duk da ba komi ta fad'amai ba tana ganin sirri ta ne tsakaninsu da Yar ta. ..
Cike da fahimta haÉ—i da kwarin gwiwa yace "Na amince miki Hajiyata duk abunda kikeso ina sonshi, Ke kinson matsayinki awajena sannan kinson burina da farin cikina inga kinsamu abunda kikeso.
Fira suka shiga yi cike da shauki kana ya kashe wayar.
Ganin babba wayar shi Amnah ta kirane yasa da sauri ya maida mata kira.
Cikin shagwaɓa take faɗin
"Abbana bakasona yanzun kwana nawa banjika ba?
Murmushi yasaki tare da cewa "Amnah nah in bansoku ba wazan So?
Cikin jin dadi tace babu Abbah .
Dama faÉ—a ma zanyi Mamy ta mareni akan ÆŠAN DAKO ko,kuma Abbah agabansa fa,Basai ya rainani ba ya raina ajina?takarasa tana sakin kuka mai sauti.
Take muryarshi ta canza cikin byacin rai yace Mamy taku ta mare ki akan wani banza barni da ita anjima zamuyi magana yakashe wayar yana Huci.
Lokaci guda kuma ya É—auki wayar shi Afusace ya kira Mamy da dai-dai lokacin ta fito daga toilet ta É—auro Alwallah.
Mamaki ya kamata ganin wayar shi bayan yanzu suka gama waya.
ÆŠauka tayi tare da yin sallama......
Amsawa yayi.cikin ɓaci'n rai yace mi"Amnah ta miki da kika Mare ta akan wani Ɗan Dako..
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO🌹
MALLAKI🌹
UMMY AYSHA🌹
🅿ï¸5ï¸âƒ?&6ï¸âƒ?
"" Shuru tayi ba Tare da ta ta kaba.
Cikin fushi yasake cewa "kina fa jina Fulani!
Nasha faɗamiki ban yarda da abunda zai shafi ɓacin ran Yarana ba, Akan wani sakarai zaki zauna ki Mari yarin yata ,in kika mata illah fa, mizakice ,Ki kiyaye daga yau ya kashe wayar...
Shuru tayi ranta na ƙuna akan bin bayan rashin gaskiya da yayi.
Sai da ta bada kamar ten mint kana ta É—auki wayar shi tamai Text kamar ''haka."
""Hubby Kayi hakuri banyi wani abu dan ɓata ranka ba Amma ni nason som Amnah halin da take ba mai kyau bane amatsayinta na ya mace, Amma in maganata tamaka zafi kayi hakuri ka yafeni kason fushinka masifane akaina, Har kullum fatan neman yarda Allah da taka nike saboda aljnnata na kasan tafin kafarka, Ina sonka sosai mijin marainiya(SUNAN DA TAKE KIRANSHI KENAN IN TAGA YANA CIKIN FUSHI SABODA YAKAN KARYA MISHI DA ZUCIYA) ta turamai.
Cikin kankanan lokaci wayar shi ta shigo wayar ta.
Murmushi ta saki tare da É—aukar tace'' Ka sirace Hubby..
Murmushi ya saki yace kiyi hakuri da abunda ya faru kinji sweety ,kinson bana iya control din kaina akan soyayya yarana, É—an allah ki daina cewa kedin nan marainiyace bayan kina dani ga kuma NENE ..
Murmushi tayi mai sauti ta ce" shike nan yanda kace.
Daganan sukai sallama ta ajiye wayar tare dayin Sallah.
Bayan ta gama ta É—aga hannu sama tana kwararo Addu'a da hawaye jage- jage a fuskar ta wanda banson na minenen ba.
Aɓan garan Habu Ɗan Dako kuwa cikin sauri yake tafiya baki ɗaya kayanshi sun jike inda suka lafe jikinshi suka fiddo kyakyawan zatinshi na zama cikakken Namiji mai zarra.
Bayyi wata tafiya ba ya ƙaraso kasuwa saboda dama sun kusa.
Koda yazo kai tsaye Rumfar da Baba suke yashiga ya samesu tsaitsaye suna É—aure Buhun hunan hatsin su.
Sallama ya musu suka amsa ya koma gefe tare da kwaso Damen kuÉ—in yaba Baba.
Murmushi yayi yace "Habu ka kasa hakurin ruwa ya É—auke ka taho cikin su.?
Kamar bazai magana ba kuma ya nisa cikin ƙasa da murya yace" Motar ta lalace bata tashi shiyasa na barota acen .
Ido Baba ya zaro cikin ɓacin rai tare da cewa" Wai kai wane irin mutum ne, Haba ina dalili nan da G.R.A din amma sai da kamun asara ɓatamun mota, To da ubanmi zan koma gida ?Habu kana da matsala wallahi badan Amanar kaba da tini na rabu da kai ,kai kason kaf ɗin kasuwar nan babu wanda ya rufama asiri kamar ni ɗan kwal uba har yau banson fuskar kaba na yarda dakai na sakar ma dukiyata na baka Amintatta motata da ba kowa nike ba 'ba , Amma saboda Ƙaton banzane kai sai da ka lakata to Wallahi sai kabiyani yaƙarasa yana neman yin kuka saboda tsananin son motar da yake...
Duk da Habu na cikin ɓacin rai hakan bai hana kwayar idonshi ta kasa fallasa yalwattace. Murmushin dake rufe da fuskar shi ba.
Kallonshi Baba yayi baki asake yake karema idonshi kallo.
Kuka yasaki yace "Habu ni kake ma dariya?Ni ka É—auka mahaukaci ka sacemun mota kuma kazo kace lalacewa tayi Habu ni????
Dakyal ya gimtse dariya dake tasomai yace.
"Baba zaka iya bina muje kaga motar ka tana cikin aminci , Sai dai na ɓalle murfi ɗays data batamun rai yakarasa hankali kwance cikin kuma tabbatar da gaskiya....
Salati Baba yasaki yana zama ƙasa tare da ɗora hannunshi akai yasaki kuka mai karfi da yasanya matasan wajen kwashewa da dariya dan kowa yason yanda yakeji da motar shi da Abun hannushi ,Baya tauyema kowa hakki amma kuma bayasoAmishi asara kota kwabo, Mafarin ko tukin motar bai yarda kowa yayi ba sai shi sai ko Habu daya Amincemawa gashi kuma yau ya zalunce shi...
Cikin shasheka da rikicin tsufa yace" Habu ka cuceni ka zalinceni bansonkaba na baka amana kayi ha'inci Allah yasakamun kuma ba zan bika ba kaje ka saidani babu ni babu kai har abada, Kaje na koreka kai
Iro bishi ka karɓomun motana yafada yana nuna wani matashi.
Dariya Iro yayi yace walkahi bazan bishi ba nima fa ban sonshi ba kawai kai dai ka aminta dashi ya zauna cikin mu.
Duk kan maganar da suke Habu na jinsu kuma yason Gaskiya sukai su kadai suka aminta dashi batare da sun taɓa ganin fuskarshi ba yazama dole ya cire musu kokwanto a ransu! A'hankali yasanya hannun shi yafara warware Rawanin shi har ya gama tass.
Wata irin zabura Baba yayi tare da ƙoƙarin shiga cikin buhun geron dake gabanshi da bai wuce kwano goma ba.
Iro da jikin shi ya É—auki rawa shida wasu samari guda biyu dake cikin shagon yakamo hannu Baba ya makalkale yana zare ido.
Ihu Baba yasa tare da faÉ—in" DAGA TAIMAKO Ashe aljani muke tare da shi tsawon wata shidda, Wayyo ni Audodo naga ta kaina nashiga ukku na lalace Zai kasheni yau namai faÉ—a, Wayyo Allah na yakarasa cikin kyarma.
Kyakyawar fuskar shi ya ÆŠago ya zubama su Baba ita tare da cewa" Ka kwantar da hankalinka Baba ni mutum ne bawai Aljani ba, Kuma ni ba Macuci bane dole tasani rufe fuskata bawai dan ra'ayina ba , Amma namaka alkawari daga yau bazaka sake ganin fuskana arufe ba amma kataimaka ka barni bakin aikina kai kaÉ—ai kamun halaccin ÆŠaukana.Sama da wata biyu ina cikin kasuwar nan ina yawo lungu da sako dan samun wanda zai taimakamun da aiki amma haka nike gama yawo na inkoma inda nafito bansamu komi ba, Saboda mutane naganin cewa ni wanine ko kuma kyan da Allah yamin yafi karfin ace ina neman Aiki DAKO, bayan Allah shike tsara halittar bawan shi ba wai bawa ke tsarama kanshi halitta ba , Shikenan sai ace gidan talakawa ba zasu samu yara masu kyau ba ko me? Halitta" Ubangiji ke yinta yayi Æaki acikin fari haka yayi fari acikin baÆ™i, Da haka ka daina mamaki inka amincemun zan zauna da kai ,in kuma baka amince ba kana ganin babu yarda zan fita in samu wani aikin..
Illahirin jikin Baba rawa yake jin yanda yake rattafo zance da halshen hausa dan ko makaho yaga Habu yason ƙaryane yace shi bahaushene, Dan ko kaɗan shi bai kama da hausawa ba sai dai ko kasashi cikin jinsin Larabawa ko indiya wa....
Cikin Rawar murya yace Habu kaga dai da gaskiya na rikeka ko? To Dan Allah karka cutar dani ka kama gabanka Dan Allah nagode kuma kamun kwatance inda gidan yake a'ida kai masu kayansu in ÆŠakko motata.
Murmushi ya saki mai ciwo tare da kwatan tabmusu cikin fahimta ya tashi ya musu bankwana da godiya akan Alkhairi da sukaimai na rikeshi tsawon kwanaki.
Cikin sauri Baba yace bakomi bakomi jeka ga hakkinka ya bashi dubu biyar.
Karba yayi tare da turawa aljihu yafita daga rumfa yafara takawo cikin ruwan da basu da niyyar tsayawa.
Gabaƙi ɗaya'n masu shagunna kasuwar kallo shi ake wasu harda fitowa bakin rumfunan su suna leken baturen da yashigo kasuwa yana tafiya da kafa ganin irin cikakkiyar sumar shi tayi linkim da ruwa duk ta balbaje tayi masifar kyau.
Sosai ya tsargu da irin kallon da ake binshi dashi hakan yasashi fara tafiya da sauri cike da sasarfa da kuma ɓacin rai.
Dan kallo na É—aya daga cikin abinda ya tsana arayuwar shi ya rasa ubanda yasa mutane ke kallonshi haka kamar sun samu Tv.
Gabaki É—aya ya fita kasuwar yana fitowa ya tare keke napep ya shiga.
Tinda yashiga napep din kaɗan kaɗan mai napep ya juyo ya kalleshi amma bai ce komi ba shikuma tinda yaga haka ya ƙara haɗe fuskarshi tamau.
''yallabai wace unguwa zan kaika?
"Tudun wada.*
Yabashi amsa agajarce.
Kai tsaye suka nufi unguwar ahaka ya dinga nuna mishi har suka karaso wani dan matsakaicin gida da ƙofar ke saye.
Sauka yayi ya bashi kuÉ—in tare da kutsa kai cikin gidan ya tura kyauran yashiga da sallama.
Yason ruwan da ake bazai ba na ciki damar jiba kamar yanda bazai bashi damar jin ko an amsa ba.
Ɗan ƙaramin gidan nasu yatsaya karema kallo da keda Ɗakuna ukku biyu ajere sai daya dake kallon su sai dan karamin tsakar gida da baifi zaman mutum biyar ba sai toilet da karamin kiching.
Ba laifi tsakar gidan nada kyau dan ashafe yake tas ga pent da yasha komi a'killace yake ba wasu hayaniya.
Dayan É—akin da ke aware yayi saurin turawa tare da shiga ya maida kofar ya rufe tare da danna Sakata
Babu komi.acikin É—akin sai wata tabarma da kuma karama katifa sai Alkur'ani sai wani truly babba guda É—aya ..
Yana shiga yabi É—akin da kallo jin yanda yake ta busa kamshi tsintsiya da akasamai gashi agyare tsaf.
Cikin natsuwa ya fara cire kayanshi tare da sasu awani babban boket dake bayan kyauran, Yana gamawa ya É—aura wani HARAMI akugunsa tare da É—aukar É—aya'n ya yafa akafaÉ—ar sa.
Wani irin mahaukacin kyau yayi kamar wani Balarabe dake filin Arfa.
Soso da sabulu ya É—auka tare da boket din dakayanshi ke ciki ya fita dasu .
Ajiyesu yayi tare da faɗawa toilet din dake tsakar gidan ɗan madaidaici ba laifi yana da kyau akwai shower da toilet sit da ƙaramin pampo ciki.
Wankan ya faɗa tare da murzar jikinshi sosai cikin lokaci ya fito tare da duƙawa ya wanke kayan daya cire tass ya shanyasu akan igiya.
Alwallah ya É—aura saboda Al'adar shi ce zama da Alwallah yana gamawa ya nufi É—akin shi ya zaro wata tattausa brown din jallabiya dake linke mai gajeran hannu ya sanya.
Wani irin mahaukacin kyau tamai gashi ta sake fito da Hasken farar fatar shi da kuma zatin shi da murzazza fatar da Allah yamai mai kama data ya'yan hutu.
Kai tsaye ya fito tare da nufar É—akin dake kallon nashi ya tura guda da salllama a'
bakin shi.
Wata murya ce mai sanyi ta amsamai sallama tare da bashi izinin shigowa.
Shiga yayi cikin ɗakin yana takawa A'hankali kamar wanda ke tsoron ƙasa.
Wata farar matace dake hakim ce akan kujera hannuta rike da littafin Adduo'1i tana dubawa ,hukunta sanye da wani kace mai kyau da tsada.
Kai ta ÆŠago ta kalleshi tare da fadin.
SADEEQ Kadawo?Sannu ya aikin naku?Ina fata komi yana tafiya yanda ya dace? Da fatan dai bakajin yunwa ko? tamai tambayoyin duk ajere.
Wani kyakyawan murmushi ya sakarmata tare da Duƙawa kasa ya ya dafa gwaiwar ta yace. "Ammina Barka da gida kin cikani da tambaya waccen/ kikeso in am'samiki? ya ƙarasa yana turo baki cike da shagwaɓa .
Murmushi Ammi tamai mai tsananin kama dashi ta ya mutsa sumar kanshi tace duka nike so ka amsamin,Saboda É—an jarumi ne ,kuma Nason in akwai wadda tafi wannan zaka amsamun.
Hannunshi da Amnah ta rike ya ɗaga yana murzawa A'hankali saboda yana tinanin tamai rauni, cikin Raɗaɗin da zuciyar shi kemai yace" Ammi nah komi lafiya klau Alhamdulillah , Sai dai inaso kisani Addu'a da bakin ki mai Albarka, wanda nike ƙasan shi sama da wata shida yau ya koreni tinda yaga fuskana yana ganin kamar cutar su zanyi kuma na fahimtar dasu sun kasa ganewa yakarasa cikim.ƙuna rai da taune jajayen lips ɗin shi.
Shuru matar tayi batace komi ba sai kanta da ta sadda ƙasa cikin kankanan lokaci ta fara kwallah masu tsananin zafi da ƙuna rai.
Saurin Ɗago kanshi yayi arikice tare da karasawa wajenta ya rike gwaiwarta illahurin jikinshi rawa yake idonshi yayi jawur cikin ƙanana lokaci,Murya na rawa yace.
"Ammi Dan girman Allah da manzon sa karkimun kuka na rokeki Ammi, ku kanki shine zai raunata zuviyata inkasa zama Namiji na ,Ke kinson waye ɗanki Ammi akan ki zan iya ɗauke komi amma banda ganin hawayen ki, Bani da mafita shiyasa na zaɓi faɗamiki saboda ko ba komi nason zakimun Addu'a kuma addu'arki gareni batada hijabi karbabiyane muyi hakuri mu fauwalama Allah,Domin shi ne zai kawo muna mafita, in kuma kina ganin in dingama fuskana penti kamin in fita sai inyi Ammi, Amma wallahi ni kaina abun na da nike naɗawa na matukar damuna Ammi kinson Ni banason zafi da abu mai nawie...
Hawayenta ta share cike da tausayin yaron nata.
Rungume shi tayi sosai tare da sakin wani mahaukacin kuka taf ara kiran shi da Sadeeq!Sadeeq!!Sadeeq!!! Munga rayuwa, Rayuwa tamuna juyin waina a Tanda, Sadeeq yanzu kaine wai....
Saurin rufemata baki yayi tare da gilgiza kanshi idonshi jawur yace" ki daina wata magana Ammi abunda ya wuce ya wuce munma rasa mahaifinmu mun hakura ballantana wata rayuwa cen ,karki damu Ammi nah ina Hamrat?
Hawayenta ta share tare da nunamai inda wata kyakyawar yarinya ke kwance akan katifa da ba tafi shekara goma ba, Bacci take cikin jin DaÉ—i da kwanciyar hankali.
Cikin natsuwa ya zare jikinshi daga na Ammi ya ƙarasa wajen yarinya ya aza gwiwowayin shi ƙasa tare da riko hannunta ya Ɗan murza ahankali yana kallon fuskarta da ke tsananin kama da tashi...
Kanta yafara shafawa A'hankali yanajin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa game da yarinya,baison dalilin da yasa duk sadda zai kasance da yarinya ba yakejin wani tarin rauni dakuma matsanancin tausayin ta ,ƙanƙanuwar yarinya ke cikin wannan rayuwa da suke ciki fatanshi ya nema dan ya wadatasu amma yau gashi an koreshi akan abunda bai kai ya kawo ba.
Amma ya tabbata babu wadda ta jamai kamar wannan yarinya da som batada É—a'a da tarbiyya.
Hannu shi ya kalla inda ta takemai har ya fashe gashi yayi jawur.
Lips ɗinshi ya ƙara taunewa akaro na ba a Dadi..
Mamy ta katsemai tinani da faÉ—in ga abincin ka nan kazo kaci.
Cikin ladabi yace"Ammi minene kika dafa muna?
Murmusi tayi tare da faɗin"Wakene sai shinkafa da salad harma da ƙwai na siyo nasamaka takarasa tana Murmushi.
Tausayi tabashi sosai ganin yanda take farin cikin ta Da ɗaɗamai ta hanyar samai kwai duk da cikin shi a'cike yake amma bazaiso ɓata farin cikinta ba,Haka ya zuba kaɗan ya fasa kwan yaci yanata mata santi ita kuma tana tajin daɗi tare da mai kallon tausayi.
Gidan su Amnah kuwa Baba Habu yaji anama gidan wani mahaukacin bugun da yasashi Ɗakko Sanda da yar ƙaramar wuka ta yanka albasa yafito tare da buɗe kyauren cikin kasada ba tare da ya tambaya ba ya lafe baya.
Iro ne ya turo kyauran da karfi wanda yasashi matse Baba madu .
Ihu ya saki tare da watsar da Sanda da wuka .
Cikin furgici Iro ya juyo tare da fadiyn lafiya malam kake ihu munzo É—aukar mota ne muna tare da Bakanike ba masu Sata bane..
Ajiyar zuciya Baba Madu ya sauke tare da É—aukar waya Yace" Dama Hajiya tace in anzo É—aukar motar a'mata magana Bari in fad'ama ta.
Tsaye sukayi suna jira har ya mata waya ya fad'amaka sai gashi tafiyo ita da Amal suna sanye da hijjob.
Ƙarasawa tayi tana binsu da kallo ganin bataga buzun da ya kawomata kaya ba.
Cikin dube -dube tace yo ina ÆŠAN DAKO kayan yake?
Cikin matsananci Ɗumi dake cin Iro ya fara magana" Ai Hajiya ɓarnar da yama Baba mu ta mota yau shiyasa aka koreshi , Saboda Baba bayaso amai ɓarna ga mota, sabodama yarda da shine yasa ya bashi to amma kinga harda marfi ya cire mata uwa uba kuma Baba baison fuskar shiba tsawon watanni shidda sai ɗazu ya buɗemuna ita, Wallahi Hajiya abun mamaki ashe Bature ne shegen aka turoshi ya ga asirin Dukiyar Baba Dan yaje ya faɗama yan uwanshi azo ayi KIDGWASHIN ɗin Baba asaceshi, Aiko Baba ya korai tin ɗazu ba mu son inda yake ba...
Wata ityin dariya Amal ta kwashe da ita ganni yanda yaketa rattafa zance harda ambatar sunan kidnapper's da kidgwashin ..
Sosai jiki Mamy yayi sanyi hakanan taji yaron ya shiga ranta cikin sauri tace" Toni yanzu wazai ida kawoman sauran kayana, Gashi gobe zanyi rabon nan, Kana dan Allah inda hali ni ku nemomanshi inason ganin shi .
Iro Yace" Ga sauran kayanki nan cikin babbar mota wasu suzo mukama dan gaskiya ni ko Rabin buhu ban iya dakkowa, Saboda Hakarkarina ciwo suke banima da isasa lafiya.
Cikin bacin rai "tace to ina wancen yake ku kiraman jarumin mana sai aturoman lusari irin ka mizakaman wannan ma ai haukane inane gidan su?
Iro yace wallahi bansani ba Hajiya.
Mamy tace "number wayar shi fa?
Iro yace" eh ina da ita gatanan ya faÉ—a yana nuna mata wayar shi.
Karba tayi ta kwafe awayar ta tare da kangawa a'kunne.
Shi kuwa Habu dake É—akin Ammi suna fira yaji wayar shi na Ring. Ganin bakuwar number ne ke kiranshi hakan yasa ya É—auka tare dayin sallama.
Daga ɓangaran Mamy amsawa tayi cikin Dattaku tare da mai bayanin kanta akan tanaso ɗan allah ta Ɗaukeshi aiki duk wata zata biyashi dubu ɗari in ya amince zai dinga kulawa da wasu hidimar gidan sauran bayani dai in yazo yaji.
Shuru yayi kan shi a'kasa saima wani irin ɓacin rai dake tasomai akasan zuciya "Dubu dari yasake maimaitawa akan laɓɓanshi tare da taɓe bakinshi ya saki wani murmuahi Mai ciwo.
Ammi dake jin duk abunda suke faÉ—a ta É—agami kai alamun ya amince..
Bazai iya tsallake umarnin taba duk da baisoba saboda Yarinya gidan amma bazai iya fad'amata ba.
Cikin dusashiyar muryarshi yace" Na amince.
Farin ciki sosai mamy taji inda ta hau zubamai godiya kamar yamata wani abu.
Idon shi ya limshe batare da yace komi ba.
Cikin É—oki tace to kazo yanzu.dan Allah akwai aikin da zakamun.
Uhm yace yana kashe wayar shi.
ÆŠago kan da zayyi yaga fuskar mahaifiyarshi ayalwace da farin ciki.
Hakan yashi tsiramata ido ko kyaftawa bayayi aduniyar da suke ciki yana fatan yagan ya zama farin cikin iyayen shi, Yana so yaga mahaifiyar shi ta samu gata ta dalilin shi da yar ƙanwar shi da baida kamar ta da ta taso cikin halin Rayuwa.
Murmushi ya saki Dan ƙaramata kwarin gwiwa, murmushin daya bayyana asalin kyanshi da kwarjinshi gawata siririyar wushirya data bayyana a tsakiyar fararan jerarun hakoran shi.
Mamy ta É—aga hannu sama tace" Allah nagodemaka daka kawomana mafita cikin gaggawa, Allah ga bawanka ka saukaka mai wahalar da yakesha ubangiji ka jibanci lamurran mu.
Ameen ya amsa yana mikewa ya tsaye yace "zanje in dawo.
Mamy tace "Yanzu Sadeeq haka zaka dinga fita ko kuwa zaka dinga sanya Rawanin?
Shuru yayi yana nazri saikuma yace" Bari in maida wayan cen kayan kawai inkuma sanya rawani inyaso gaba in naga sun aminta dani sai in daina sawa.
Cikin Amincewa tamai fatan ALKHAIRI da kuma fatan nasara a'rayuwar shi.
Ameen ya amsa yana juyowa ya shafi Fuskar Hamrat ya ficce.
Sauri -sauri ya sanya kayan da basu gama bushewa ba ya naÉ—a Rawanin tare da fitowa yana duba lokaci yaga biyar da rabi, Cikin sauri yamata bankwana ya fita tare da tare Machine ya faÉ—amai inda zai kai shi.
Tinda suk shigo layin yaga babba J5 yason aiken su aka kawo shiyasa ta nemeshi.
Siririn tsaki ya saki tare da karasawa wajen ya sallami mai machine É—in.
Ana ya gansu tsaitsaye yakarasa tare da cema Mamy" Barka da marece Hajiya.
Tace yawwa Habu ko kaifa, Naji daÉ—in zuwanka yanzu ga kaya nan ashigo dasu asasu inda yan uwansu suke zuwa gobe za afara rabasu zansa akawoma mota.
Kai ya jinjina tare da cema Iro daya saki baki yana kallon shi "kashigo da motar ciki.
Bakaniken yace ai ta garejin muce bari ashigo da ita.
Wangale musu get din Habu yayi cikin kuzari suka shigo da motar ya nunamus inda zayyi parking dinta kusa da D'AKIN.
Anan sukayi kam cikin jarumta ya fara kwasar kayan akafaÄar shi yana shiga dasu.
Cikakken mint talatin baiba ya tsauna su cikin Äakin.
Iro ya saki ihu tare da fad'in Hokai jarumi Jarunaj wallahi dole Bab yayi misir (Missing)dinka saboda samun jarumi yanzu kamarka babban aikine ,wallahi Allah yasa inyi K'arfi irin naka.
Baice komi ba haka kuma bai amsa ba.
Ita kanta Amal ya masifar burgeta dan ta yaba da zaɓen Mamy tasu da tace tanaso yazamana mai aikin gidan su...
Bayan sun gama mamy ta cema su Iro zasu iya tafiya ta gode.
Bankwana sukai sukaja motacin sukayi gaba ..
Wata kyakyawar Bukka da akayita saboda hutawa tace ya biyota.
Binta yayi har zuwa wajen inda ta samu wuri ta zauna shikuma yayi tsaye kanshi a sunkuye...
"Ina son ganin fuskarka Habu saboda inson da wa nike zaune, in'yaso daga yau saika cigaba da lullube abunka ba damuwata bace mamy tafad'a cikin natsuwa...
Baitsaya gardama ba ko wani fargaba a'hankali ya since rawani..
Tin kamin yagama amal ta mike tsaye jikinta na rawa tana nunashi da yatsa......
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO 🌹
MALLAKI 🌹
UMMY AYSHA 🌹
🅿ï¸7ï¸âƒ?&8ï¸âƒ?
"""Fitunannu idon shi ya watsamata tare da kauda kanshi gefe yana sakin ƙaramin tsaki.
Cikin tsanani ruÉ—u Amal tace" da gaske kake kai ÆŠan Dako ne?
Kai ya jin-jinamata batare da ya kalle ta ba.
Ita kanta Mamy saida taji zuciyar ta ta buga da karfi ganin kyakyawan saurayi kamar shi wanda som babu alamun da suka nuna yayi kama da ÆŠan Dako , Dan ko kayan sa fess suke babu wata lalacewa babu kuma faci jiki...
Amal zatai magana Mamy tace zauna ya isa haka kaima zaka iya zama.
Cikin girmamawa Yace" Aa Hajiya basai na zaunaba ina sauraran ki dai...
Mamy tace shikenan. "Dama inaso gobe zansa akawoma mota zan haÉ—aka dasu Amal ku kaimun kaya cen gidan mahaifiyata, Zaka tsaya ta lissafamaka duk wanda za'aba ,zaka É—auka ka kaima mutane, Bayan angama inaso ka dawo gidan nan da zama kana É—an kama ma Baba Madu aikin bude get din cen , Naga ya fara manyanta, Sannan yan aike -aike da suka dace zaka dinga zuwa kana muna, Wannan shine kawai aikin ka, inaso ka haÉ—o kayan ka ka dawo gidan nan ,ga É—aki cen daka tsauna kaya idan ka kwashe zaka sanya naka a'ciki, Ina fatan tsarin yamaka haka?
"Bai manba Hajiya.
Ya bata amasa cikin Natsuwa..
Kallon mamaki suke binshi dashi ganin irin gatan da akaimai amma babu wata shakka yace tsarin baimai ba.
"Komi yasa kace haka "?
Mamy ta furta.
Saboda ina da mahaifiya da ƙanwa da nine jigonsu, Ni suke gani suji daɗi, Ni mike zama muyi fira dasu in maye musu kewar mahafina! Wannan shine kawai.
Murmushi Mamy ta saki tare da cewa indai wannan ne karka damu zaka iya maidosu gidan nan da rayuwa suyi zaman su ,Nidai na aminta dakai, Bana tinani wata cutarwa daga gareka, In ma mahaifiyar taka zata iya sai ta É—an dinga kamamun wasu aikace -aikacen nan part É—ina.
Wani kallo ya mata da yasata shan jinin jikinta, ta rasa miyasa take shakka yaron da baifi shekara 30 ko Da 31 ba, Yana masifar yimata kwarjini tana jinshi kamar É—an da ta haifa..
Cikin fushin da yatasomai murya a'kausashe yace mahifiyata bazatai aiki ko inaba,In hakane haihuwata batai mata rana ba kenan,Ayanzu data ajiye kamata tafi bukatar hutawa fiye da da,in dai har zanfita ta fita to menen ribar haihuwar tawa ma Hajiya? Ina son Ammi na bana fatan ace wai tayi wani aikin wahala Dan zata samu abunda zataci,Nidai da nike namiji Zan iya iya aikin karfi wanda yafi Dako wahala dan sama mata farin ciki, In zaki amince ma zuwana karfe 8 na safe in tafi bayan isha to shikenan, In kuma bazaki yarda ba to gaskiya asamu wani saboda nima inaso in samu lokacin da zan tattauna da mahaifiyata inji matsalarta data Ƙanwata data ragemun,Dan nine garkuwan su .
Ya faÉ—a cikin gaskiyar shi tare da tsuke baki dan ya daÉ—e bayyi irin wannan dogon sharhin da wani ba sai da mahaifiyar shi ko sst shi....
"KAIFI ÆŠAYA"Mamy ta furta ,Dan ta fahimci yana da tsatstsauran ra'ayi sosai..
Tace shikenan na amince ma hakan, Ina fatan ka rike amana shiga da ficen gidan nan .sannan miyasa kake son rufe fuska? Ko buzayene ku..
KafaÉ—ar shi ya É—aga.
Tare da faÉ—in ko É—aya, kawai Bakowa ke yarda dani ba idan yaga fuskana shiyasa,Suna ganin kamar zanzama É—an leken Ashirin su..
Amal da ta ke binshi da ido cike da burgewa tace.
"Ai kana da kyau sosai Wallahi kamafi Aunty Amnah kyau ba kaÉ—an ba Shiyasa ake kin yarda..
Kallonta yayi tare da kauda kanshi gefe.
Mamy tace sunan ka Habu ko?
Yalwatacciyar sumar shi ya murza tare da cewa. "Sadeeq ne sunana, Tsohon da nike aiki dashi yasamun Habu, Saboda bazai iya faÉ—in sadeeq ba.
Mamy tace shikenan daga yau zamuna kiran ka Sadeeq dan yafi daÉ—i.
Amal tace yamafi dacewa dashi.
Wayar shi ya zaro tare da cewa zan je Sallah Hajiya..
Mamy tace akwai masallaci a'kofar gidan nan kaje ka dawo zan baka sako.
Yace ok tare da nufar wajen mai gadi ya gaisheshi amutunce tare da fita daga gidan .
Harya fara tafiya ya juyo tare da cewa Baba ba zaka Sallah bane?
Baba Habu ya rike baki yace "Yaro Hajiya Amnah tazo bana nan aini nason dubu hamsin din da suke bani zatabi Ruwa, Anan nike kayana..
Cikin ƙanƙantar da ido yace akan duniya Baba da shekarunka zakayi gudun zuwa masallaci dan kar ka ɓatama wata rai?Wai miyasa mutane ke ɗaukar raini akan wasu yan canji da ake basu,Danmi zaka saɓama mahalicci ka
Akan abokin halittar ka,Baba kasamu kwaÉ—o kasanya kawuce muje sallah ,Sallah cikin jam'i tafi lada, Baba kaji tsoron Allah kaida ka fara manyanta ma ...
Jikin Baba yayi lakwas kamar an'watsama kaza gishiri.
Yace shikenan yaro bari in rufe.mutafi Nagode da tinatarar wa.
Ido Sadeeq ya lumshe batare da yacekomi ba.
Baba ya ÆŠakko kwado ya dannama gidan tare da faÉ—in muje.
Fita sukai suna fita saiga masallacin jere da gidan.
Sadeeq yace kenan ma masallacin na gidan ne kawai fita ne bakayi.
Baba Madu Yace_ Wallahi" Yaro ina tsananin tsoron Yarin ya abun har mamaki yake ba'n, Dan Akwai Hannatu jikata na tabbata ta girmeta, sai dai in nayi duba da kasansu nike sai inga wajibine in mata biyayya.
Hanci Sadeeq ya hura tare da cika baki shi da iska, Tura hannayen shi yayi cikin aljihu tare da fadin muje.
Shiga sukai sukai sallah ana sallamewa Baba yafara kyarma tashi.
Sadeeq ya kamo hannushi Yace" Karka tashi mana Baba, Ya kamata ka nemi gafara Allah, kayi karatu koda aya gomane, in san samune ma katsaya ayi Isha kana ka koma,Saboda Lahiraka tafi duniyar ka faÉ—i..
Baba Madu ya koma ya zauna dan yasha alwashin gyara goben shi kodan samun rabauta, kwara yasama ranshi zamanshi da ƙorar shi duk Allah ne zai tsara su acikin ƙundun ƙaddara shi.
Suna zaune suna lazumi har akayi isha kana suka fito.
Suna fitowa suka koma gidan ya buÉ—e masu suka shiga su duka suka zauna akan bencin dake wajen.
Baba ya'ce" yaro ya sunan ka.
"Sadeeq" ya bashi amsa atakaice tare da danna ma Mamy kira yace" na dawo.
Amal ce ta fito da kayan abinci niki -niki tayo wajensu tarr da cewa "Yah Sadeeq ga abinci inji Mamy.
Da sauri ya kalleta yana mamakin sunan da ta kirashi da shi ''Yayah'' yasake mai maitawa tare da taɓe baki .
Atakaice yace ki mayar nako shi Alhamdulillah, Sai dai ko Baba amma ni kamin in fito naci Abinci wajen Ammi nah..
Cikin langwabar da kai a:lamun bataji daɗin yanda yamata ba tace. "Dan Allah kaci wallahi saboda kai na girkashi fa Takarasa cikin yanayin shagwaɓa...
Kasa yayi da kanshi akaro na farko yace. "Amalll banajin yunwa nace ki mayar ba.
Wani sanyi dadi ya ziyarce ta jin yanda yakira sunan ta da wani kala jan baki da bata taba jiba, Ita batamason sunan ta yana da daÉ—i ba sai yau da tajishi abakin ÆŠAN DAKO Gidan su.
Baba dake kallonsu Murmushi yasaki ba tare da yace komi.ba.
Amal tace shikenan. Mamy tace kashiga ciki. Ta faÉ—a tana ajiye tiren wa Baba madu.
Tashi yayi yace "muje.
Tafiya ta fara yana biye da ita har suka ƙaraso palon da Sallama, Inda suka iske Mamy zaune cikin kwalliya .
Cikin yan second ni ya karema palon kallo tare da samin kujera dake nesa da ita kaÉ—an ya zauna.
Kai ta ÆŠago ta kalleshi tare da sakin murmushi dan gabatar shi na burgeta da alama bayason raini,Koda kasancewar shi talakka Annabi bai yarda mutunci da Allah yayi Mashi ba ya zube, Da wanine ta tabbata zai zauna akasan kujera in yaga tana sama.
Barka da dare yakatse mata tinaninta tare da Turɓune fuska dan bayasan acika kallon shi ana nazari abun na sosa ranshi...
Tace yawwa "Sadeeq Zaka iya tafiya yanzu Baba sai ya dinga kwana gobe da safe zakazo kamar yanda kacemun karfe takwas .
Yace baki da matsala indai wannan ne insha Allah.
Mikewa tayi sai gata da wasu ledoji manya guda biyu da ta zuba Kaji, kifi ,Naman rago.
Cikin É—aya'n kuma kayan fruit ne ta zuba akai tace ka kaima Ammin ka ina gaisheta sosai wannan kuma albashin kane na farko ta Damkamai dubu dari da hamsin.
Ledar ya karaba tare da cewa Allah ya ƙara arziki Nagode sosai, Amma albashin dubu dari kikace naga nan kuma akwai karin hamsin?.
Murmushi tayi tace'' saboda zaka sha wahala sosai ne wajan raba kayan abinci shiyasa namaka ƙari, Kuma akwai bukatar kasai kaya masu kyau dan ni ba matsayin bawa nikeson rikeka agidan nan ba inajinka ne kamar kanena, Kana ga Amanar Amnah da Amal nan ka kula da lafiyansu da kuma tarbiyyan su, Mahaifin du bai kasance ma'aboci zaman gida ba,inaso katayani saka ido ga tarbiyya yarana saboda shi namiki jigone agida.
Kanshi ya jinjina cike da tsare gida da kamun kai yace "shike nan na amince , Allah ya sadamu da alkhairi natafi nagode Allah ya amfana.
Sosai taji dadi dan harga Allah ta aminta dashi tace" Nagode Sadeeq Nima.
Yace ba komi tare da mikewa.
Amal tace yah sadeeq agaida Ammi da kanwar mu.
Murmushin gefen baki yasaki tare da furta" insha Allah yasa kai ya ficce.
Yana fitowa yaga Baba madu nata kwasar gara tare da ƙulla wani ga leda.
Sallama yamai ya wuce.
Fitar shi bada jimawa ba Amnah ta fito cikin wasu mahaukatan riga da wando da suka masifar yinata kyau kasancewar su read color, kanta ko É—an kwali babu sai parking din da tayi tsakiya ta tufkeshi da read din bant ta sakeshi yana Lilo,,Kunnata toshe da read din Bluetooth don da ya haska farar fatar ta.
Bakinta ta turo tare da kallon Mamy da som hankalinta bai kanta.
Cikin shagwaba tace "Mamy ina Namana ?
Kallonta mamyy tayi batare da race komi.ba sai tashi datayi ta haye sama tana latsa waya dan tana so taga Amnah ta gyara halin ta.
Amal ta kallah tana lumshe ido kamar mai jin Bacci.
Da hannu Amal É—in ta mata nuni dakan dinning da aka ajiyemata .
Cikin natsuwar tafiyar mai jan hankali ta mike tana juya.manyan hips dinta wanda wasu suke tinanin tsabar gayune kesata haka , Amma som ba hakaba ne yanayin tane haka.
Fridge ta Bud'a ta Äauki Hollondia yoghurt tare da karasa wa wajen dining ta zauna.
Naman ta zuba kaÄan
Ta tsakure shi ta zuba yoghurt din taci tare da mikewa tsaye ta nufi hanyar d'akin ta.
Kallo Amal ta bita dashi tare da cewa "Aunty Amnah wai kinga wannan mutumin ashe mahaukacin kyau ne dashi, Wallahi kamar Balarabe, Allah kika ganshi sai ya ruÉ—aki, bakiji yanda naji ina son shi ba, kema Wallahi inkin ganshi zakice kina son yazama YaÆ´an ki, nidai daga yau yazama Yayana kema...
"Ya isa!!!
Takatseta cikin daka tsawa.
Ke in'banda kina wawiya talakka har kyaune dashi, shashasha, insoshi!insoshi kike faÉ—a!!
To bakin banzanki ya faÉ—a miki, Amma nida wancen talakkan sai na azabatar da shi wallahi, ai naji duk kullin da kukai na kawoshi gidan nan, kuma hakan yamun daÉ—i, kana da kanshi da kafarshi zai bar gidan nan, Tinda har yayi sanadin da aka mare ni ni yar gidan .mtsss ta watsama Amal yawu ta haye sama..
Kukan takaici Amal din tasa tare da diddire kafa tace Wallahi nidai ina sonshi wallahi..
Rai aɓace amal ta haye sama itama..
Æangaran sadeeq kuwa yana fita yasamu acaÉ“a ya hau tare d kaishi unguwar su da shatara ta Arziki ,Sosai ya yaba da karramawar matar dakuma halaccinta gareshi.
Yana shiga gida da sallama ya iske Ammi da Hamrat waje sun shinfiÉ—a Tabarma suna shan iska , ga kuma karamar fitila data haska gidan maici da battery.
Oyoyo Babyyyy..
Hamrat tace cikin ihu tare dayo wajenshi ta faÉ—a kanshi.
Da sauri ya ajiye ledojin hannunshi tare da cewa oyoyo Baby'n Babyyyyy. ya faÉ—a yana rungumeta tare da daygata sama yana juyi da ita cikin tsanain farin ciki.
Dariya suke sosai cike da shauki .
Ammi tace nishikenan bakwa tani ko?
Sauke Hamrat yai tare da sumbatar hannunta ita kuma ta sumbaci goshin shi.
Tare da cemai i miss you so much Baby.
Yave.mee too Baby'n Baby.
Tashi tayi tsaye tayi cikin jindaÉ—i ta nufi É—akinsu tana ta dan tsalle tsallanta da rigar jikinta mai kyau sosai.
Kallo ya bita dashi har ta shiga kana ya maido hankalinshi ga Ammi Ya gaisheta yana sakin murmushi..
Hararashi tayi tare da cewa bana amsawa sadeeq kaga Hamrat mantawa kake dani dan haka nayi fushi..
Kyakkyawa sumar shi ya turamata tare da faÉ—in" kaina bisa wuya Ammi nah, Lefa ta daban ce, kinson dole muyi kewar juna yau banganta da rana ba.
Sumarshi ta shafa mai tsananin taushi da yawa tace hakane "ina jin daɗin Alaƙarku Allah ya dora da zumuncin ku har jikoki.
Ameen-Ameen ya amsa tare da janye ledojin da yazo dasu wanda baiso ko na miye ba .
"yace gashi hajiya tace akawo maki kana ya kwashe komi yanda sukai ya fad'amata..
Hamrat ta.fito tare da wani dan cup mai kyau ta bude Randarsu mai sanyi ta ÆŠebomai ruwa tace Baby gashi kasha ruwa.
Ƙarɓa yayi yace yawwa Baby'n Baby Allah yabar k'auna.
Idonta ta juyamai masu kama da nashi "tace Amin tana bashi hannu suka kashe ..
Yana gama shan ruwan ya juyo ya fuskanci Ammi tare da buÉ—e ledojin yace "Ammi kinga ashe Nama ne ma bansani ba ga kuma fruit.
Godiya da Addu'a tashiga yima Allah da kuma Mamy data kyautata musu yau daya taɓasu abunda suka kwana biyu basu ciba.
Kudin da aka bashi ya fiddo ya gwadamata tare da faɗin Mamy inaga silar warakamu tazo yakamata muyi amfani da damar muyi.abunda mike buƙata inaga zansiyo muna fridge D'an madai daici dan mudinga samun abun sanyi,kinga Zafi ake sai kuma in siyo kayan abinci masu yawa a ajiye in sai miki gas ki huta kunna icce ko Garwashi.
Idonta dake cike da hawaye ta ÆŠago tace hakan yayi sadeeq ubangiji Allah yamaka albarka yabaka lada yasa kagama da duniya lafiya.
Ameen ya amsa tare dashafar kan Hamrat yace 'Baby zanje indawo mizan siyo miki?
Cikin jin dadi tace ka siyomun Baru(Tantabara) Sai ka siyomun sweet mai daÉ—i...
Dariya ya saki daba koda yaushe yake yin taba yace insha Allah" wai miyasa kikeson Tantabara ne?
Murmusi tayi tare da cewa Baby ya sayyadi ke cemuna muna karatu in mundawo gida?
Sai muce "eh."
Sai yace muzama masu cika Al'kawari muyi halin tantabaru, Dansu akwai amana da cika Al'kawari, wanan dalilin ne yasa nike sonta Baby.
Kanta yashafa yace angama zan siyo miki Amnah sai gobe insha Allah
Ihu ta saki tare da rungumeshi.
Fita yayi sai gashi da kayan masu yawa ya siyomusu fridge madaidaici buhun shinkafa taliya.maca kus- kus semo da yan kaya masu sauki ya siyoma kanshi.
Farin ciki sosai ya bayyana ga Ammi tai tamai Addu'a tare dacewa naga mutun cin matar nan Sadeeq, Daka bari nima na dinga mata aikin in tana da bukatar hakan..
Take fara'a fuskarshi ta Äauke yace ""Ammi na ke zakiyi aiki da raina da lafiyana zan barki kihi aikatau? hmm Allah ya kiyaye kima daina wannan tinanin keda akaima...
Ya isa sadeeq jekayi wanka ka huta. ta katseshi da hanzari akan magana da yakeson yi..
Shuru yayi tare da leka
ÆŠakin ta ya ajiyema Hamrat kayan da ya siyo mata gefen ta ganin tayi bacci.
Kai tsaye yashige nashi É—akin bayan ya fito ya shirya cikin wasu kayan bacci farare sol masu tsanani taushi da kyau.
Babbar jikkashi ya bude tare da fiddo wata computer mai kyau ya fara dudduba wasu sakwanni na abubuwa da sauri.
Tare da É—aga wayar shi yafara kofe wasu number da banson na minene ba.
Yana gamawa yasaki wani mahaukacin tsaki tare da jinjina kai.
Take jijiyar kan shi ta mimmike idon shi ya canza launi.
Cikin sautin dake bayyana bacin rai yace Rana DUBU TA BARAWO DAYA TAK TA MAI KAYA...
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO 🌹
MALLAKI 🌹
UMMY AYSHA 🌹
9ï¸âƒ?&🔟
""Cikin yanayin na fushi ya rintse hannushi tare da kaima jikka dake kusa dashi duka.
Saida ya kwashe sama da awa biyu kana ya jonata charge yatashi yayi addu'a ya kwanta.
Bacci ya ƙoso ya zomai amman yakasayi ,saboda tinanin inda rayuwa tamayar dashi ayau daya ya tashi daga Ɗan Dako ya koma mai gadi, koda yake bazaice hakan ba tinda cenma DAK'ON zai dinga musu.
Tsaki ya saki yana taune jajayen lips É—in shi.
Ahanka bacci ya yi nasara kwashe shi.
Washe gari da asuba ya tashi tare da walwatsa ruwa dan garin akwai zafi, Yana fitowa yayi shiri cikin farar tattausa jallabiya data mishi kyau sosai ta fiddo zatin shi kamar wani balarabe..
Masallaci yaje yayi Sallah.
Bai shigo gidan ba sai Bakwai, yana shigowa ya iske Ammi kiching tana mishi breakfast dan tason da wuri zai fita .
Suna gaisawa ya shige dÉ—akin shi tare da cire kayan jikinshi ya É—aura haramin shi yafito yayi wanka.
Yana fitowa yazo yashafa mai tare da fesa tiraren E collection mai daÉ—in kam shi da sanyaya rai.
Wasu riga da wandone Black masu ratsin white ya É—akko ya sakama jikinshi tare da murza turare a'hannun shi yasake mulke kan shi take wani daddaÉ—an kamshi ya fara tashi daga É—akin.
Tattasau sumar shi ya gyara tare da É—aukar wata Black p-cap yasama kanshi ya É—auki bakin maks ya mannama dogon hancin shi.
Madubi ya kalla tare da lumshe ido dan shi kan shi ya yaba da shigar tashi duk da duka kayan jikin nashi ko 5k basu kai ba amma yayi masifar kyan da wanda yakashe 100k bazai yi kwatankwacin kyan shi ba, dan kyau ajinin shi yake.
Da sauri ya fito yana kallon agwogo ganin yaci four mint acikin awa É—aya kuma baya fatan karya alkawarin dan ba fatan shi bane kuma baya cikin tsarin shi.
Ammi ya iske zaune tana fiffita mishi tea'n data haÉ—a mai .
Zama yayi ya ƙarɓi tea yasha tare da ɓallar bread da kwan data soyamai kaɗan yakai baki.
KaÉ—an yaci ya aje sai tea daya shanye.
Kallan shi tayi cikin fuskar damuwa tace wai miyasa sadeeq bakason cin abinci ne?kana aikin karfi kana wahala zafi inuwa ƙuna amma baka da lokacin cikin ka miyasa? Takarasa cikin raunin murya.
Kallon ta yayi sosai yana murmushi tare da riko hannunta yace "karki damu Ammi nah kinson duk sadda ka cika cikin ka lokacin rauni da kasala ke kawoma ziyara .
Nikuma bana fatan abunda zai dakushemun kuzarina da rashin cika muradina dare da Rana .
Shiyasa nama kaina wannan sabon kuma yabi jikina .
Amma Ammi kidaina damuwa dan ni ba yaro bane duk sadda naji yunwa zan nemi abinda zanci na barki lfy .
Tsororo tayi tana kallon shi dan tabbas maganar shi akwai kamshin gaskiya.
Addu'a ta mishi dafatan nasara kana ya shiga É—akin ta ya shafa kan Hamrat kana ya ficce da sauri.
Takwas saura minti biyu ya isa kofar tafkeken get din gidansu Amnah.
Bayan ya shiga sun gaisa da baba madu ya É—aga waya yama Mamy waya akan ya iso.
Dadi taji sosai tare da faÉ—in "akwai sabuwar mota na nan compound ka karbi key wajen Baba Madu ka fara shirya kayan aciki kamun su Amnah su gama shiri saiku wuce.
To yace tare da latse wayar.
Key ya ƙarba tare da nufar motar ya jata har wajen kofar ɗakin kana yafara sungumo kayan cikin tsantsar jarumta yana shiryawa.
Cikin kankanan lokaci ya take bayan motar taf da kaya,Kana yakoma wajen Baba madu yana sauke ajiyar zuciya dan cikin kwanakin'nan da yayi aiki da yawa sai yaji ƙasan zuciyar shi namai masifar ciwo da bayan shi,Daure wa kawai yake dan baya fatan yaba gangar jikinshi muhallin hutu har sai ranar da burun shi ya cika.
Kimanin awa ɗaya suna zaune saiga Amal cikin shirinta na atamfa tasanya hijjob madaidaiciya tafito da ƙaton basket a'hannunta shake da kayayyaki.
Kai tsaye ta iso wajensu tana doka murmushi tare da ajiye kayan gaban shi ta tsugunna tana dafe kumatunta ta zubamai ido cikin narkakka murya tace "yah Sadeeq ina kwana, kana lafiya yasu Ammi da sst Hamrat.?
Alhamdulillah ya bata amsa agajarce yana kallon gefe.
Tace yawwa" Ammi tace ga breakfast ka farayi kamin Aunty Amnah ta gama shiri.
"Yace ayyah kimayar kice ngd naci agida kamin inzo Naci.
Kallan shi tayi tana kwabe fuska tare da faÉ—in
"Dan Allah kaci mana miyasa duk sadda zamu baka abu bakaci ko kana tinanin zamu cutar da kaine ?
Murmushi ya saki da bai shiryaba yayi ganin yanda tayi magana kamar zatai kuka .
Yace "A'a ko É—aya kawai naci abinci agida Amma bani ruwa.
Ruwa ya ƙarba yasha kaɗan ya rike sauran ahannun shi.
Baba madu ta turama sauran takoma ciki cikin rashin jin DaÉ—i.
Saida suka shafe kusan awa É—aya sannan suka fito su duka.
Mamy Amnah Amal.
Kai tsaye wajen motar su Amnah ta nufa yayin da Amal da Mamy sukayo wajen shi suka sake gaisawa tare da fad'amai yanda takeso ayi tsarin abun dan washe gari ake sanya ran ganin wata.
Kai ya jinjina tare da mikewa cikin kuzari ya isa ga motar ya ajiye ruwan tare da shiga ya zauna yana lumshe ido tare da wasa da hannunshi daya rike styarin ...
Tada motar yayi dai-dai lokacin da Amnah ma ta tada tata tayo hanyar get.
Shima hanyar get É—in ya nufo tare da kashe motar ya fito ya tura get É—in da hannu daya kan ya koma mota yadosi get din.
Sosai Amnah ta sheko da gudu asan ta samu ta rigashi fita.
Cikin kwarewa ya kaucema motar ta tare da fita yayi parking ya fito .
Cikin bacin rai ta fito tana sanye da maroum din Abaya mai duwatsu kota ina tasha kwalliya data mata mugun kyau.
Wajenshi ta nufo cikin gadara tana zuba yauki kamar sabuwar ƙubewa
"Uban waye ubanka dazan fito kafito bazaka jurema fitana ba kamin kafita É—an talakawa marar tarbiyya? miye ai'kinka inba takemun bayaba ka rikemun jikka amatsayinka na ÆŠan Dako uhum nace waye ubanka?
Wata firgitacciyar tsawa ya dakamata data sata daka tsalle ta koma gefe.
Afusace ya zare hular kanshi kyakyawan gashin shi ya bazu tare da cizge maks din da yasama fuskar shi ya cilla gefe.
Jajayen idanuwan shi da suka cika da ɓacin rai ya dago ya zubamata Tare da nuna kanshi da yatsa cikin ɓarin da jikin shi keyi yace.
" Ni tsaran kine?ke wace irin wawiyar yarin yace marar hankali da tinani,Natabbat nabaki shekara goma a haihuwa,Saboda bakida wadatacciyar tarbiyya ko?ko Dan kinganni agidanku akacemiki kisamu damar wulakantani!To bazan É—aukaba, bazan jureba, tinjiya naga take taken nothing kanki akwance suke.
To Wallahi ni Sadeeq S Sadeeq zan iya saita ki yanzunnan kimatsa kibani waje kamin inmiki abunda baki taɓa tinani ba dakikiya kawai ko Anfaɗamiki kyauta za'asallameni ba sai nayi aikiba, bana tinanin cewa hakana za'kuna ɗaukar kuɗi kubani kyauta, Yajarasa yana sakin siririn tsaki tare da kifa hularshi ya fita cikin kasaita da cikar zati.
Duk abunda ya faru akan idon Mamy da Amal
Sosai abunda yayi ya burge mamy ganin irin furgici da tashin hankali da tsawar shi kadai ya jefa Amnah.
Murmushi tasaki batare da tace komi ba sai ciki data koma waya makale akunnanta cikin farin ciki taci gaba da magana da ƙawar ta Hajiya Turai.
Amal takarasa wajenta cikin rashin jin daÉ—in abunda aka mata ta kama hannunta tace.
Auntu Amnah kiyi hakuri muje kinji ko.
Fuzge hannuta tayi idanuwanta sun cika da kwallah amma taki basu damar zuba dan kar ya gani ya rainata.
Cikin rawar murya tace "agaban Mamy akaiman haka amma tashige ciki tana doka murmushi, D'an Dako yafi dan gida, nida gidan ubana, anya mamy na sona, kodai ba Mamy ta haifeni ba,?
Taƙarasa tana yarfe hannu tare da kutsa kanta cikin mota ta kifa kanta da styari tana sauke ajiyar zuciya, ga mamy ta mata shamaki da kai ƙarartaa wajen Abban ta,kuma tason babu wanda zai goyi bayan ta sai shi.
Amma tayi alkawari koyama wannan baƙauyen hankali.
Tada motar tayi tawani fizgeta da ƙarfi tare da fita daga gidan.
Tsaki yaja tare da taɓe baki ya kunna tashi yabi bayansu.
Duk yanda take tsula gudu bisa titin dan tabashi wahala ta hanyar bacce mai amma abun ya gagara.
Dan yanunamata namiji namiji ne mace kuma macace.
Tafiya mai É—an tazara suka karaso unguwar su Nene.
Unguwace dake da yawan mutane mabuƙata da almajirai, Dan ta tara makarantun allo da dama .
Parking tayi awani gida mai babban get black da yasha fentin lemon green
Hon tayi wani saurayi hannushi rike da Radio ya keto da gudu ya É—an buÉ—e yana faÉ—in.
"Yau sain tsulamaku bulalai yan iska masu kawunan Agwagwa shikenan baku barina in huta masu gida basuce in buɗeba saiku yan banza duk ruwan da aka fidda muku waje amma saikun karbi na cikin gida saboda hassada, Nace uwaku ya saki daƙuwa dai -dai lokacin da idon shi ya sauka kan na Amnah data tsareshi da lumsassun idonta fuska a tsuke..
Salati ya saki yana yankowa da gudu ya zube ƙasa tare da cewa "Dan Allah kiyi hakuri Hajiya Amuna wallahi banyi tinanin ke bace naga jiya kikazo.
Afusace tace zaka buÉ—emun get kosai nabi ta bisa bakaken yatsunka masu kama dana gizo- gizo na wuce?..
Hannunshi ya kalla kana ya tashi da gudu yashiga ya bud'É—e get É—in yana cillama bayan motar harara tare da "fadin wannan mai kama da manja Allah yamamu maganinki fitinaniya ga kyau kamar zoben zinari amma kafurar zuciya gareta kamar ta haÉ—a iri da sheÉ—an..
Yana kokarin rufewa sadeeq ya dallo tashi ciki.
Wait !wait !!! ya ciga da cewa amm ko tsayawa baiba saidai ya samu wuri kusa da motar Amnah yayi parkin tare da zamanshi yana latsa wayarshi hankali kwance batare da yace komi ba.
Su Amnah Fita sukayi suka faɗa cikin gidan inda Suka iske wata dattijuwa da a'ƙalla takai shekaru sittin da biyar tanata faɗa da mai lallaɓe mata kai.
"Haba zulfa sai shafar mun kai kike kamar kwartuwa nace ko dad'i kikeji?Dan masifa kingama kitsemun tin É—azu amma bazaki barni inje inyi walha ba dan dai kisa inmakara ko? Miyasa wai baki da imani da tausayin wanda ya kwana biyu.
Mai kitson tayi murmushi tace" Haba Hajiya Nene tattare miki nike dan karya dameki kin tsufa amma har yanzu kanki masifar yawa ga tsantsi dole sai an tufkeshi gudun karya warware.
Baki ta murguÉ—a tace tubarkallah kali kuss mai bakin banza sala kija ma'askin dare yamun aski tinda kincikani da baki, ni sakeni in sammaki nama dan in banbaki ba nason ba ci kike ba kuma karshenta bala'in bakinki kan kyakyawan gashina zai kare, Duk inkinmun kitso saikinyimun baki.
Dariya makitsiya ta tuntsure da ita harda kwallah tanason Nene sosai shiyasa take jure abunda take mata.
Amal dake tsaye fuskarta cike da murmuahi yayin da Amnah ta zauna ta É—ora É—aya kan É—aya tana kallon mai kitson cike da takaici irin yanda ta samu damar zama tana yanda take so .
Amal tace "Nene mu!.
Afurgice ta É—ago ta kalleta tare da mikewa tana kokarin gudu wa.
Dariya Amal tasa tace ga faÉ—a ga masifar tsoro to nice.
Dariya Nene ta saki tana mikewa ta ƙaraso wajensu ta cire kallabinta ta yarfama Amal din afuska tare da cewa "ja'ira na ɗauka aljannu zulfa ne suka tashi kinson suke gareta kusan buhu goma akai.
Dariya suka sanya Amal da zulfa inda zulfan ta tashi tana faɗin Nene bari in wuce sai da daddare nazo inci tuwo mai sulbinnan in kintuƙa selonita kike cemai komi?
Baki Nene ta saki tace kai kedai wannan kanki kamar na Zabo wlh bakya rabawa" semovita" akecewa wannan tsamin bakin naki yana kasheki da yawa.
Dan ma Allah ya rufamiki asiri bakinki baya wari da babu ni.babu ke kinson ni nafison É—an gayun mutum koya yake kuwa.
Dariya tayi tace shikenn bari inwuce sai nazo.
Tsaidata tayi tashiga ta shakomata kula da naman da fura mai sanyi tabata tare fa sabullan wanka dana wanki dan Nene akwai kyauta.
Godiya zulfa tayi taryr da fita dan atsorace take da irin kallon da Amnah kemata.
Tana fita Nene ta juyo wajen Amnah tare da sanya kafarta ta noshi ta amnah datake kaɗawa cike da ƙasaita.
Da sauri ta É—ago idonta tazubama Nene su.
Cikin bacin rai tace ta sannu hakima!wadda gaba ɗaya zuri'arku babu wanda akaba koda sarauta kwasar kashi ce, Amma in akaga kina abu sai ayi tinani dai- dai da ƙudan gidanku sarkine minafuka.
Kinsha wasu jajayen kayan banza kamar yar shan jini Amnah ki kiyayi duniya wallahi, zulfa ba tsara uwarki bace da ba zaki gaisheta ba ,sai ma hararata da kike kika furgitata kika hanata zama.
Fuska ta yatsina tare da faÉ—in nifa kin cikamun kunne da hayani dan Allah kibarni Nene
Ko infita inbar gidan ki. Haba safiyar fari a cikama kunne da faÉ—a,kina da masifar hayaniya.
Ido Nene ta murza saiga hawaye tace shikenan Amina kici gaba da zagina kina wulaƙantani jiyama kamin kibar gidan nan saida kika kwashemun albarka tass daga kiranki yimakai abun arzi to kisani daga yau babu ni babu ke, Allah kuma ya isa zagina da kikai.
Amalulu muje kici dambun shinkafa yasha kayan dad'i wlh .
Amal tayi murmushi tace to kishare hawayenki kana muna tare da ÆŠan Dako ne zai sauke kaya.
Mamy tace danki samu sauki zai rabamiki iyaka kifita kibashi umarnin inda zai kaisu.
Baki Nene ta washe Tare da faÉ—in kai Allah yama fulanina Albarka ya É—aya tilo mai share ma iyayen ta kuka Allah yajikan Bashari da É—an uwanta,da yana nan da yaga yanda duniya takeyi damu wayyo Allah na mijina ta kece da wani irin kuka zuwa cen kuma ta saki dariya tare da gyara zani tace muje muje Amalulun Nene.
Fita sukai suka doso harabar tsakar gida inda suka iske sadeeq zaune akan motar.
Yana ganin sun fito da yar farar dattijuwar ya tashi tsaye tare da zame hular kanshi .
Daga nesa Nene ke kallonshi tare da É—an lallekawa dan san sanin ina yan uwanshi suke.
Suna gab da zuwa taja wani wawan burki tare da cewa ubnmi akaimka zakazo kaiman tsaye kamar bishiya Dabino, wato shine daga campany suka turoka kenan to maza kabar gidan nan wallahi tin kamin in dakko barkono da mai in laftamaka ga fuska,Dan iskanci banace bana so ba.
Ahankali ya ɗago ƙanshi dan yaga dawa take.
Karaf idon shi ya faÉ—a cikin nata hakan yasa Nene daka tsalle takoma bayan Amal tare da Daga hannu tace Sukusmie(excuse me) tana dagamai hannu alamun yabata waje.
Kallonta yayi sosai tare da sakin murmushi dan yana tinanin shigr da yayi yasa take ganin shi kamar Dan sanda.
Ƙarasawa yayi wajenta tare da duƙawa yace" ina kwana.
Gabaki É—aya idanuwanta ta fiddo tana kallon yanda yayi hausa raÉ—am a'bakinshi.
Amal tace nene gaisheki fa yake shine kuma yakawo kayan daga gidan mu .
Mamy ta sameshi zai dingamata aikace- aikace fa.
Wani irin ƙanƙance ido Nene tayi can ciki tare da fitowa daga bayan Amal tace kina nufin wannan ne Dan Dako? Mike damun Saudat da zata ɗauki wannan saurayin aiki?Lalli kune ya rufema ido amma ninan Nene babu shegen dazaiman rufa ido dagani turoshi akai gidan ku dan ya sace ku, Mussaman waccen mai girman kan bala'i dam ansan in an ɗauketa za akwashi kudi.
Duk maganar da take yana jinta babu abunda yake sai murmushi tare da jingina da motar ya harde kafarshi hannunshi kuma daya sai gilgiza key din yake..
Nene ta matso wajenshi tace kai tsakanin ka da Allah wazaka sace? wa akace kasace kaji tsoron Allah ka fadamun gaskiya? wa akabaka kongila daga acikin zuria ta?
'"Kece''
Yabata amsa agajarce fuskarshi Daure tamau kamar bashi ke sakin Murmushi ba..
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: 🌹 Ɗan Dako
Mallaki🌹
Ummy Aysha🌹
🅿ï¸1ï¸âƒ?1ï¸âƒ?&1ï¸âƒ?2ï¸âƒ?
"" Duk da zuciyar Nene ta buga amma cikin jarumta ta daka tsalle ta iso gaban shi, tare da "faɗin kai uban Turajima yayi kaɗan balle kai, barganinka da kirar samudawa Bashari ya tsumani kamin ya Mace, Dan haka daga yau bana son ƙara ganin ka cikin zuri'a ta, saboda ban'yarda dakai ba.
Yo inbama haukaba irin na Saude taya zata iya zama gida É—aya dakai jibifa nan inka.
Takaima faffaÉ—an kirjin shi naushi.
Idon shi ya lumshe tare da sakin fuskar shi da yalwataccem murmushi yarasa dalilin da yasa tsohuwa ke masifar burgeshi, yana tsananin sonta lokaci guda acikin ranshi.
Ido a lumshe ya fara magana cikin sanyin murya
"Nainahh yaja sunan da wani sauti mai masifar daÉ—i wanda yasa Amal rintse idonta da karfi tare da buÉ—esu lokaci guda ta saukesu akan pink lips dinshi dake motsi A'hankali.
"Nainah bantaɓa cutar waba,duk da ni ancuceni amma kuma hakurina yafi gaban zuciyana,banshigo zuri'a kiba dan cuta saboda bana fatan cutar da Dabba mai tafiya a hanya balle Ɗan Adam da Allah ya karrama, Abu ɗaya nasani tabbas ni ƊAN DAKO ne ,a kasuwa suka ganni nakaimusu kaya mahaifiyar su ta amince dani....
Atakaice yabata labari duk abunda ya faru cikin natsuwa.
Nainah ni maraya ne Baban ya rasu kana ina da ƙanwa da mahaifiya, wayanda sune gatana na duniya kuma nima duk kan wahala da zanyi dan farin ciki'n sune.
Banji haushin kiba dan kin haÉ—ani da mai sace mutane gaskiyan ki saboda rayuwan babu amana aciki.
Amma kisani bawai dan kibarni inyi aiki gidan y'arki ba aa ! Gaskiya ta zanfaÉ—amiki banacin amana amma kuma ina hukunta wanda yaci tawa.
Ya rage naki ki amincemun ko karki amincemun duk É—aya ne awajena, Saboda ita kofofin rahma ta Allah yawa garesu ,
Kisani ranar da nakai kaya gidansu Amall aranar wanda nikema aiki ya koreni , Muna tsaka da magana yanda zan samu wani aikin da zan kula da mu da mahaifiyata naji kiran y'arki.
Zaki iya kiranta yanzu kimata magana kin hanani dan bazan iya tinkarar taɓa gaskiya.
Yakarasa yana É—ago fararan idanuwan shi ya saukesu akan Nene da tinda ya ambaci Maraya ne shi ta É—ora kanta akan motar ta fara kuka marar sauti.
Gaban shi ya faɗi sosai har baison sadda ya ƙarasa wajenta ya ɗagota tare da zube gwiwoyin shi ƙasa yace nine ko?
Kimin hakuri bazan sake ba kiyi hkuri na tafi. ya faÉ—a yan juyawa .
Da wani irin gudu da kuka shaɓe -shaɓe Nene ta kamo hannun shi tare da rikewa gam tace" wallahi kai ba maraya bane, kana dani kana da mahaifiyar ka, Yaro ina sonka zanzamemak a gata kamar yanda allah ya zamemamu a'sadda muma mukayi rashin jigon mu, Dan haka i lovulu wallahi.
Baison sadda dariya ta kwacemai ba sosai yake dariya harda wasu kwallah da suka masifar mai kyau.
Nena ma dariya tayi tana jin tsananin tausayinshi har cikin zuciyar ta.
Tace muje palo na kaci abinci, ya sunan ka?
"Sadeeq" yabata amsa atakaice.
Hannu ta tafa tace sunan ƴaƴan Saudat Wallahi shine ya ɓata tin yana karami ta faɗa tana share hawaye.
Cikin jimami ya mata jaje tare da faÉ—in ina za asauke kayan.
Mai gadinta takira tare da cewa" ÆŠan larai kama mashi mana ya saukesu.
Da" to" ya amsa ya samu ya kinkimo buhu guda ya ajiye yana mayar da numfashi.
Sadeeq ya tattare hannayen rigarshi ya fara saɓosu akafaɗa yana direwa gaban Nene, sadda ya kusa gamawa kana Ɗan Larai ya ajiye buhu ukku.
Tsaki Nene tayi tare da cewa" Huhulahun banza huhulahun wofi, Duk uban abincin da kake ci amma ji abinda kayi .
Cikin nishi yace "Hajiya Nene kowa fa da aikinsa yafi kwarewa, Dan haka aikina buÉ—e get bawai DAKO ba, shikuma aikin sane karshenta kiga inzai bude get har kuka sai ya fashe dashi.
Murmushi kawai sadeeq yayi yana gamawa ya hango pampo ya karasa ya wanke fuskar shi tare da zama kasan wata bishiya Mango dake gidan yayi shuru.
Nene tace to ai yayi mai wuyar dan haka É—akko Baro kazo ka kaima kowa tinda kason inda ake kaiwa shiÉ—in ya kula da get din.
To yace yana sakin mika.
Nene ta koma ga sadeeq ta tsuramai ido cikin tausayi tace" Sadidi in'kawomaka abinci anan .
Kallonta yayi tare da kaÉ—a kai alamar aa.
Amal tace Nene bayacin abincin ko inafa wallahi saina Ammin sa,Ban sani ba ko yana zargin zamu masa wani abune.
Cikin tausasa murya yace babu wanda ya isa yayi sai da yarda Allah, ni bana zargin ku sam kawai ra'ayinane haka,nason duk inda Ammi na take yanzu tanacen tana bukatar taga tamun abinda zanyi farin ciki, to nafito kuma nacika ciki waje kinga bazataji daÉ—i ba taga na koma nace banaci ko?
Yakare magana awahalce dan matsanancin ciwon da yakeji a ƙasan zuciyar shi.
Nene tace" kai Saddi wallahi na fita iya girki, Sala katafi kana tsinemin albarka da zagina akan namaka tayin rowa ko?
Amalulu É—eboman abinci kihaÉ—o da ruwa da kaina zanbashi.
Da sauri ya É—ago kai ya kalleta tare da kawar dakai gefe yana motsa baki.
Cikin hanzari Amal takoma ta jero komi ta kawoma Nene .
Nene tayi zaman dirshan gabashi tare da cewa kadaiga ni "Tsohuwace inka wahala dani allayh zai Sakaman Saddi kaci ko in baka.?
Ganin mutuncin Tsohuwa da kulawa da take nunamai yasashi ƙarba cokalin yayi Bissimillah yafara ci cikin natsuwa.
Ido ya lumshe danjin yanda Danbun da yasha zogala da kayan lambu ya ratsa bakin shi.
Bai an'kareba saida yaci rabin flat kana yaji ya koshi.
Nene ya kallah tare da É—an fiddo ido yace shikenan" Nainah yau babu ni babu cin abincin Ammi nah, kincikamun ciki da girkinki mai daÉ—i ya yfada yana lumshe ido.
Dariya jin DaÉ—i Nene tayi tace" kai nifa gwanace a girki dan shekarun baya har Matar Masari saida taso É—aukata aiki saboda yanda nike baÉ—e kofofin hancinta da kamshi da kuma labarin iya girkina da Bashari ke bata .
Cikin rashin fahimta inda ta dosa ya kaÉ—a kai baice komi ba.
Nene tace to taso muje ciki.
Yace aa zanje in É—akko sauran indawo.
Tace yawwa Saddi maza.
Tashi yayi cikin jin kwarin jiki yafaÉ—a mota ya fita.
Me gadin Nene yadawo da almajirai sunkai talatin.
Azabure Nene ta mike tana faɗin ƙudira sama Liman da wawan zama, Ɗan Larai uban minene haka? mizasuman .?
Yana nishi yakaima kirjin wani dake kusa dashi naushi yace kingansu nan kullim da kinkawoman abinci zakigansu kamar jamfa a jos sun taso suna buÉ—e hancina kamar kofar guga, Suna ya bayin Allah, Minafukan Allah dan suja in'masu rowa Allah yakamani tinda sungani.
To abun yazamemasu jiki kullim saina basu loma É—aya shiyasa da naga zanyi wannan aikin wahala naje na gayyatosu dan karsuci banza , dan haka kowane shege shi zai É—auki na gidajen da ake kaiwa.
Nene tace kamun dai _dai dan Larai wani lokacin fa akwaika da hankali , Dan haka basu suci gaba da kaiwa kana tsaremin get.
Ahaka duk suka karar dana wajen yayin da Nene ta koma ciki.
Anan suka iske Amnah zaune cikin wasu riga da wando gabaki É—aya'n su pink sunmata kyau sosai tayi parking É—in dogo'n gashinta tsakiya ,ta kunna kayan kallon tasa kida mai taushi yana tashi ahankli sai kaÉ—a kafa take tana latsa waya.
Koda suka shigo basu kalletaba itama bata kalle suba.
Saida sukai alwallah sukai sallah Nene" tace amalulu waccen kota hada iri da kafuraine da bata sallah.
Amal tace aa Nene yau batayi fa.
Fusk Nene ta yamutsa tare da cewa kazamar banza kawai dole taita shiga jajayen kaya ashe cikin jini take.
Dariya Amal tayi ta linke abun Sallah tare da mikewa tace" Nene wallahi yunwa.
Tace kije kici abinci ni banaso tuwo zanyi.
Zuwa tai ta zuba abinci ta dawo palo tace" Aunty Amnah in zubo miki!.
Akasalance ta kalleta tana lumshe ido kamar yar maye dan Abinda take gani awayata yana masifa tayar mata da hankali.
Kai ta kaÉ—a mata tare da faÉ—in naci nawa kuna waje.
Nene ta kalleta tace ke" Amina ubanwa ya baki izinin zuba Abincina, ke waima tsaya ke zuwafa yanzu yakamata a'miki aure naga sai wani iskanci kike kina ganin mutane É—ai-É—ai.
Cikin natsuwa ta muskuta ta gyara zamanta tare da fuskantar Nene.
Cikin taushi murya tace "Nima inason kumun auran amma kaf faɗin katsina banga wanda yadace da rayuwata ba, Saboda ni inason saurayi mai kuɗi mai masifar kudi fa Nene bawai kaɗan ba, kana ɗan gidan Sarauta maiji da jinin mulki,in ma so samune ya ƙasance sarkine,kana fari kyakyawa mi yalwataccem saje, kana karfaffa bawai soko ba, ina so in son samune ya kasance Soja ko Likita, cikin biyun nan dai, Dan bana da ra'ayin auran ɗan kasuwa saboda masifar matsolanci dabin ƙa'ida.
Cikin ta fasa zuciya da takaici Nene tace dan ubaki in sai dashi ake kije kisiyo mana kana da ba'ason asalin anguluba sai muce daga ƙasar masar take, ke nan har zaki zaɓi mijin da ke zaki lissafashi,to in saukin samu garai kije kisiyo,Shiyasa ko ɓera baita ɓa sallama dake ba.
Murmushi ta saki tace wallahi Nene in bansamu wanda na lissafamiki ba banayin Aure, Muddum mijina bai fito daga gidan sarauta ba bana sanshi, ko satin nan kamal ɗan gidan Gwamna Sani Baba yazo nemana, Amma karkiso kiga yanda namasa, saboda fatana in'samu masu takemun baya da kamar masu kudinsa kona tsohon sa, Dan bazan ɗauki talakaba dan som baison daraja mutane ba, kidubamun wancen wawan ƊAN DAKO, Yau ɗaya ya ɓatamun rai amm yakasa zuwa ya bani Hakuri.
Kuka Nene ta fashe dashi na takaici tare da tashi ta haye sama tana faÉ—in" na zauna wajen wannan yarin ya wallahi zuciyana bugawa zatai inma fulani na asara.
Amal tace Gaskiya " Aunty Amnah bakya kyutawa,ƙo fa babu komi ya girmeki kana ba ayiwa Allah haka, kedai ki nemi zaɓin Allah.
Shutt up kika sakemin magana zan wankamiki mari tsarar kice ni? tashi kiban waje.
Cikin ɓacin rai Amal ta tashi tayi ɗakin su dake nan gidan Nene tayi kwanciyar ta tana tinanin sadeeq , ita tarasa dalili tin jiya yaki barin zuciyar ta, koda wane lokaci tinani wani abun nashi take, yakan sata ɓata fuska ko tayi murmushi, A'hankali tace
Ga aji, ga kyau ,ga ƙasaita, ga rashin son Raini ,wallahi yah sadeeq kayi Allah yabani Mai irin halinka.
Jin ƙarar buɗe get ya sata tashi da sauri ta fito palo tare da leƙa wa anan ta hango shi ya danno hancin mota ya shigo.
ÆŠan Larai namai magana saikuma yaga al'majiran nan suntaso sunfara kwasar kayan da sauri.
Gefe ya koma ya naÉ—e hannuwa yana lumshe ido dan dama bayajin daÉ—i som.
Da sauri Amal ta nufi dakin Nene ta iske ta fito wanka .
Nan ta faÉ—amata ya dawo.
Da suri Nene ta canza kaya tace muje suka fito Tare.
Suna fitowa Nene ta kamo hannunshi tace" muje ciki Sadiq ka huta,yanaji hannunka da zafi ko baka lafiy ne.?
Kai ya gilgizamata tare da faÉ—in" Nainah lfyna fa kawai dai.
Kawai mi ? Nene tace.
Kai ya sosa yace muje inga É—akin naki ta yanda zansanu saukin kwasheki da daddare.
Dariya tayi tace haba dai yaro mukwashe juna dai ni ai da dare yayi nikeyin layar ɓata in bacce ɓat..
Kallonta yayi yasaki Murmushi har suk isa ciki.
Suna shiga ta nuna mai saitin kujera da Amnah take anan ya zauna danshi baima lura da ita ba kamar yanda batason sunshigoba hanklinta na ga abunda take kallo.
Fira Nene kemai yana É—an amsawa sama- sama daga baya yace mata zai koma .
Tace amma zaka dinga zuwa nan ko.
Yace" Azumi fa za afara, na daizo karɓa barka da sallah na.
Nene tace shikenan Allah ya nunamuna.
Ameen yace yana mikewa da sassar fa yayo hanyar fita, cikin akasi Amanah ta mike tsaye da sauri duk tinaninta Nene ce ke son leƙo ta.
Bam kakeji ta faÉ—a cikin kirjinshi.
Lumshe ido tayi jin wani irin sassanyan kamshin daya mamaye hancinta, kwakumeshi tasakeyi kasancewar cikin yanayi take wanda ita kanta batason miyakawo mata hakan ba.
Wata irin faÉ—uwar gaba ta kawomai ziyara jin yadda ta af'komai bisa kirji, kuma saitin zuciyan shi dakemai ciwo.
A fusace ya fisge ta tare da dannata bisa kujera yasaki tsaki ya wuce.
Ido ta É—ago cikin wani irin tashin hankali dajin tsanar kanta ta kalli bayan shi, Dan ko alama batason shibane, to taya tazo jikin shi? innalilli yanzu shikenan ya sake rainata.
Jikinta ta kallah tare da sinsunawa taji yssbon kamshin ma take akan nata, Amma dan sharri fuska ta yamutsa tare da faɗin ta yama zakaƙi hamami da wari kana aikin Dako , Dole in'sake wanka .
Nene ta kallah da Amal wand som hanklin su naga kallon da suke basu lura da abinda ya faru ba.
Da sauri ta mike ta shige toilet tayo wanka ta fito.
Koda ta fito ta shirya kanta tare da faÉ—awa kan gado ta fara tinanin abunda ya faru ,tsaki kawai take jerawa wani bayan wani.
Abangaran Sadeeq kuwa yana fita ya fara kakkaɓe jikinshi yana yatsina fuska, tare da faɗin ƙazama shashasha, marar kirki, wadda batason daraja mutane ba ,kawai kinfamamun ciwo hakanan kawai Makauniya.
Gidan Mamy ya koma ya faÉ—amata duk an'kammala !
Taita samai albarka tare da gashi wani sabon key na machine tace'' gashi kaima ka dinga hawa ka huta da zirga -zirga zuwa da komawa, kana akwai buhu shinkafa ,masara, gero, dawa ,alkama, sugar, taliya ,macaroni, indomie, ka kaima Ammin ka .
Kace ga kayan Azuminan ina gaidata, amma kyanshi ka fara kaisu a'mota suna store kason bazasu É—akku a machine ba .
Tsororo yayi yana kallonta cikin wani yanayi yace" Hajiya kintina kuÉ—in da kika bani jiya ,ga nama, wallahi kibar abinki nagode Allah ya saka da Alkhairi..
Mamy tace" sadeeq bakayi islamiya bane.?
Ido ya zaro tare da cewa nayi Hajiya mikika gani.?
"Tace to minene ribar abaka sadaka kace bakaso, ko rainawa kayi ne Sadeeq ?banaso daga yau in nabaka abu kanunamun yayi yawa ko kuma kuna dasu.
Yanzu in'ka kai mata wannan ai na tabbqta tana da yan uwa da makwafta da abokan arziki ko? ta ai'zata rabamasu kuma duk tarayya zamuyi cikin lada, dan haka ka kwashe kawai duk rabon azumine kuma kason Allah naso ka kyautatama mabukata a cikin azumi ta hanyar ciyar wa, kana ni ina jinka ajikina wallahi ba ɗauka ɗan aiki nikema ba,Aa jinka nake kamar jinina,ina jinka kamar babban ɗana wanda na haifa, ka ɗauka Allah ne ya haɗamu dan mu ƙaru da juna, wannn bakomi bane zaka iya tafiya.ta faɗa tana faɗawa ɗaki ta bashshi sake da baki.
Fitowa yayi jiki babu lakka ya ƙarasa store din da tace ya kwashe kayan, Anan yaga hadda jarkar Mai.
Kwashe su yayi ya tura a'mota tare da fita yayi gidan su yana tinanin maizaicema ammiyn shi dan abun ya fara bashi tsoro.
Yana isa gidan ya sakko daga motar anan ya fara.kwasar kayan ya saukesu tare da kammalasu soron gidan lana ya rufe motar ya fita
Kofar y atura da sallama yafara kai kayan .
Ammi ta fito tana faÉ—in ikon Allah sadeeq lafiya'n ka kuwa? wayannn kayan fa, bayan wayanda ka kawomana jiya?.
Saida ya kammala kana ya zauna ya koramata bayani tare fa faÉ—in" nifa Ammi banaje gidan su dan aita kashemun kuÉ—i ba ,,aa subani iya hakkina ya isa abun fa y isheni.
Murmushi Ammi tayi tace karka manta kila zakka Azumice, kaga kenan muma Allah yaci damu, dan haka muma bazamuci mu cinyeba zamu kyautatama wanda suke cikin yanayi, duk da bama shiga harkar kowa unguwar nan kuma babu mai shiga tamu, hasalima tsoronmu ake to amma zamu kyautata iya iyawar mu da yarda Allah.
Kai ya jinjina tare da faÉ—in in Baby?
Tace tana ciki ka sonta da bacci tinda mukai sallah ƙarfe ɗaya take bacci.
Yace shikenan tare da zaro wayar shi yace" bari in'kirata kimata godiya ko.
Ammi tace eh kirata kuwa kayi hangen nesa.
Mamy ya dan nama kira cikin lokaci ta É—auka.
Cikin natsuwa yace" Ammina zata miki godiya.
To Mamy tace tana sakin Murmushi.
Karba Mamy tayi suka gaisa a'mutunce a inda taita godiy da Addu'a buÉ—in Alkhairi.
Mamy taji daÉ—i ta amsa da ganan sukai sallama.
Abinci Ammi tamai tayi yace" yaci gidan Nene anan yabata labarin Tsohowa taita dariya itama tare da faÉ—in ai tsaffi akwai daÉ—in zama.
Gab da la'asar yace mata zaije masallaci daganan zai wuce, misuke buƙata na sahur dan ana sanya ran ɗaukar azumi yau.
Tace babu komi sai dai ko fura inzai dawo.
To" yace tare da fita.
Gab da sallah mangariba suna fira da baba madu su Amal suka dawo.
Anan take shedamusu da anga wata saudiyya.
Ido y lumshe tare da faÉ—in Allah yabamu ikon kyautata halshen mu da zukatan mu.
Ameen ta amsa ta wuce...
Bayan sun dawo isha yama Mamy sallah ma ya wuce.
Sai da ya tsaya ya saima Ammi fura mai kyau da yoghurt yayi ma Hamrat tsaraba kan ya kom gida da sabon machine É—insa.
Yana isa gida anan ya shiga da abin shi.
Da gudu Hamrat ta taso tayo wajen shi tana "oyoyo ga Baby yayi sabon machine zai kaini yawo'n sallah.
Da sauri ya gyara parking kana ya kama hannunta suka ƙarasa wajen ƙofa yana"oyoyo Baby acici harta ƙagara sallah tazo, to mikika tanadar mata?..
Tsalle tayi tace "Baby ice cream ,kadaiga wannan karan kana da machine bazaka ki ƙaini ba ko?
Rufe gidan yayi kana ya kamota suka dawo har gaban Ammi bayan sungaisa ya shedamata anga wata.
Addua tayi tare da fatan farawa cikin sa'a.
Hamrat tace baby baka bani amsaba?.
Murmushi yayi yace" insha Allah baby'n baby zamuje duk inda kike so, saboda banda wanda yafiki kedai kishirya kawai Allah ya nuna muna wannan lokacin.
Ameen ta amsa tana karba abinda yabata da godiya..
Da wuri suka rabu inda ya koma É—akinshi ya fara bincike a sistem É—insa saida ya daÉ—e kana ya kwanta.
3:30 ya tashi yafara nafilfulu har sai karfe 4:30 kan yayi sahur da tea da Ammi ta bashi, yana gamawa yayi raka'atul fijr kana ya wuce masallaci,bayan yayi sallah yayi azkar yayi karatu sai bakwai da rabi ya doso gida.
Cikin sauri ya shirya kanshi cikin wasu kaya dogon wando brown da yellow riga sunmishu masifar kyau.
Sallama yama Ammi tace mai da yamma ya dawo ya kai abincin masallaci lokacin ta kammala.
Yace insha Allah ya fita.
Bayan yaje gidan Mamy sun gaisa ta bashi ya karɓo musu kaji da yan ciki yana dawowa" tace shikenan zai iya zuwa ya kwanta.
Carfet ya ɗauka yatafi lambu ƙason bishiyar Mango ya kwanta ,sai azahar ya tashi.
Sallah yayi sai masallaci, bai fitoba sai biyar na yamma dan karatu ya yini yi.
Bayan ya fito ya É—auki mashin sai gidan su, anan ya iske Ammi ta cika manyan kuloli da waina da ruwa mai sanyi sosai.
DaÉ—i yaji ya kwasa ya kai masallaci biyu ya dawo, ta Zubamai kayan buÉ—a baki ya É—auka ya tafi.
Yana isa Amal na zuwa da kaya masu yawa ta bashi.
badan kar taga kamar wani Abuba ya karba Yamata godiya.
Ana kiran Sallah yaci Dabino da kankana ya tashi yatafi masallaci.
Bayan ya dawo sukayi buÉ—a baki awadace, ana sallah ya tafi masallaci sai tara na dare ya dosyi gidan su.
Haka sukaita rayuwa yayin da Azumi keta tsula gudu dan har yakai goma sha biyar suna ta rayuwa mai daÉ—i.
Aranar da aka É—auki na sha shidda yana zuwa Mamy ta shedamai zai kai su Amal kasuwa.
"Yace shikenan.
Bayan sun fito Amal ta shiga gaba Amnah ta zauna a baya.
Suna ɗaukar hanya Amnah ta fara sakin tsaki mai ƙarfi.
Amal tace mike damunki Aunty amnah?
Hancinta ta toshe da yatsunta tare da fiffita da gudan hannu tace" Amal bakyajin wani masifataccen wari da ƙarni kamar na jaɓa.?
Nifa bazan juri yawo da Gardiba wallahi saboda yana cutata,haka kawai n
Mamu ta HaÉ—amu da, masifa ,ni bazan jureba yazama dole Abba in yadawo a sallami wannan gardin ,yayi ale-ale cikin mota kamar ta tsohon sa.....
Wani wawan burki yaja daya tada hankalin mutane dake kan titin dana su Amnah.
Afusace tace kai talakka motar Uban nawa ka keso kamun asara? Harda neman bugama wani wawa gwame kawai babu abinda ka iya sai warin talauci.
Kanshi y dafe da masifar karfi yace Amalllll fi...t..ttah ya faÉ—a cikin ihu da in ina.
Hankali tashe tace ina zani Yah dadeeq.
Tsawa ya Sakar mata mai mugun tada hankali batason sadda ta buÉ—e ta ficce ba da sauri.
Belt ya sanya tare da tada motar da wni mahaukacin gudu.
Salati mutanan wajen suk saki ganin yanda motar ta wu....âœï¸
5/18/22, 09:34 - MY MTN 2: ƊAN DAKO 🌹
🌹MALLAKI
UMMY AYSHA 🌹
🅿ï¸1ï¸âƒ?3ï¸âƒ?&1ï¸âƒ?4ï¸âƒ?
""Salati Mutanan wajen sukai ta saki ganin yanda motar ta wullah saman titi har wani tsalle take saboda azabar gudu.
Wasu na faÉ—in É—an shaye- shaye ne wasu na faÉ—in Azumi ake kila motar ke janshi ,kowa da abinda yake faÉ—a dai.
Amal kam hannu ta É—ora akai ta saki wani siririn kuka.
To mizaima yar uwar ta?kodai da gaskiyar Nene Amnah akeso ya sace? innalillahi wa inna ilaihi Raji'un.
Ya zatace da Mamy? miyasa bai tattarasu suka tafi baki ɗaya ba?Ta yarda da magana Nene abinda babba ya hango yaro bazai taɓa hango sa ba.
Abangaran sadeeq kam wani mahaukacin gudu yake ido rufe , Da kuma hannu ɗaya, ga baki ɗayan idanuwan shi sun'mai duhu, har Yaji- Yaji, kwallah- kwallah yakeji masu tsananin Zafi a cikin idon sa, ga kanshi ga baki ɗaya saramai yake, fatan shi ya buɗe baki yayi magana amma yason in ina dake kawomai ziyara duk sadda yake cikin ɓacin rai bazata barshi ba .
Afusace ya tura hannunshi cikin yalwatacciyar sumar shi ya dinga bazata kota ina.
Amnah ga baki É—aya jikinta rawa yake ganin har sun fita daga garin Katsina sun naushi hanyar Dutsama.
Cikin Daure tsoron ta tace" kai ina zaka dani baka da hankaline.?
Kamar jira yake ya ƙarama motar gudu jikake fiiit -fiit yana wuce yan tsurarun motoci'n dake tafiya da dawowa.
Saida ya nausa da ita wani É—an daji mai yawan duwatsu kama yayi parking.
Afusace yafito ya buɗe inda take tare da buɗe idon shi dakyal ya watsasu bisa fuskar ta data zubami ido, A karo na farko kenan da suka tsaya sukaima juna kallon ƙurullah.
Abangaran Amnah kallon mamaki takemai dama haka yake.?
Shikuwa zallar tsanace afuskar shi tare da tinano irin fansar da zai É—auka akan iskancin da take mai harda zagin mahaifinshi dake kwance cikin kasa.
Cikin ihu da in ina yace" Fii..t.toooo.
Gabaki É—ayan jikinta ya saki jajayen idanuwanta ta É—ago ta yarfamai tare da faÉ—in" ina zaka kaini.?
Gi..dan uban..kiii...
Ya bata amsa a wahalce.
Ido ta zaro tare da fitowa tace'' kai ni kake zag...
Kanta ƙarasa ya bata wasu kyawawan maruka guda ukku wanda ya sata tintsurawa cikin wasu manyan Duwatsu.
Cikin wata tafiya ta Namiji duniya ya ƙarasa wajenta tare dasa ƙafarshi ya take yatsun hannunta da masifar ƙarfi ,wanda yasata sakin ihu da karfi tare da kallon shi da sauri..
"Bani da ra'ayin zalintar kowa, bakuma niso azalinceni, yau in namiji ne ɗan uwana yamun abunda kikamun Wallahi Wallahi ina mai shedamiki saina ɓatamai fuska ,ta yanda uwar da ta haifeshi bazata gane shi ba.
Kirike azziƙin ƙi da iskancin ki.
Nima kuma kikayale ni, in rike talaucina da mutuncin kaina.
Amma in kinƙiya ko gaban uwar kine zan casaki kamar gero, wawiya daƙiƙiya.
Wallahi billahi daga rana mai kamar ta yau kika sake zagina ko kuma ki kira mahaifina da baya raye saina ɓatar dake a faɗin duniya, daƙiƙiya jahila,tinda kika zama mai wannan halin ni ina da tantama akan asalinki wallahi.
Duk wanda yayo gadon Azziki baya iskanci da tinkaho, saboda abin a jininsa yake.
Dan haka kije kiyo binciken Asalinki karshenta ke agolace agidan da kike takama na ubanki ne, dan ita yar uwarki ina tinanin itace yar gidan da yake ita gadon azziki tayi ba haye ba gashinan ta rike mutuncinta tason daraja mutane.
Tashi muje jaka kawai. yadaka mata tsawa.
Gabaki ɗaya'n doguwar magana da yayi cikin in ina yake yinta wadda ta kara shagalar da ita wajen kallon pink lips dinshi dake motsi ahankali ga idon shi da suka canza kala kamar wanda ke tsaka da buƙatuwa.
Bata fara fahimtar miyake faÉ—a ba har saida taji ya fara Ai banta asalinta kana tafarajin faduwar gaba da wasu kwallah masu tsananin zafi.
Akaro na farko ta nuna kanta jikinta na rawa tace "ƊAN DAKO nikakema sharri? Nizaka aibantama Asali? Wallahi wannan magana Taka sai kayi dana sani? Court zata rabani dakai koda abinda na mallaka zai ƙare.
Tsaki yayi ya juya yayi gaba abinshi cikin ƙunar zuciya da bacin rai. tabbas yau sai ya ajiye aiki agidan su bazai jure ƙarama yarinya namai wulaƙanci ba.
Ganin yayi nisa yasata tashi duk jikinta ya lalace da ƙasa ga hannunta har yayi fushi.
Dakyal ta taso ta gangaro ta faÉ—a motar da kyal , Duk tsorace take dashi ga faÉ—uwar gaban da takeji in ta tino furucin shi.
Gudu da yake yafi wanda yazo dashi gaba É—aya hankalinta atashe yake, tana ganin tayi bankwana da gidan su kawai.
Cikin mintina ƙalilin ya isa inda ya sauke Amal, anan ya isketa zaune tayi zaman Dirshan tana ta kuka .
Som ta kasa kiran Mamy batason wane yanayi zata shigaba, gata da hawan jini.
Tana ganin mota ta tsaya gabanta da sauri ta tashi ta faÉ—a baya tare da tallabo Amnah tace.
"Aunty minene ya miki, ina yakaiku, dukanki yayi? Takarasa cikin kuka.
Kai Amnah ta gilgizamata tare da maida kanta cen gefe ta fara nazari Magan-ganu shi.
Hanyar kasuwa yayi Amal tace kabar ayhi ka maidamu gida.
Tsaki ya saki tare da juyawa ya doshi unguwar su.
Yana shiga ya buÉ—e motar ya fita tare da isa kofar palon Mamy cikin sassarfa.
Wayar shi ya É—auka ya kirata .
É—auka tayi cikin faÉ—uwar gaba tare da fadin sadeeq lafiya?
Alhamdulillah yace cikin kasa da murya tare da cewa "gani nan kofar palon ki.
Da sauri ta kashe wayar tare da fitowa ta buÉ—e.
dai- dai lokacin da Amal ta kamo hannu Amnah suka doso wajen.
Mamy na buÉ—ewa ta zubamusu ido cikin barin jiki tace "miya sameku.?
Amal tace" Mamy muje ciki babu komi fa.
Hanya ta basu suka wuce ta maida hankalinta ga sadeeq tace" ina jinka.
Hannushi ya tura cikin sumar shi tare da turata baya duka, har lokacin kuma muryar shi bata fita sosai.
Da kyal yace'' na ajiye aiki ga key dinki na gode da hidima da kikamun.
Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un, Hazbunallahu wani imal wakim," sadeeq minai maka ?
Babu abinda kikamun Hajiya.
Amma gaskiya bazan iya zama ƙalƙashin inuwa ɗaya da yarki ba,Saboda bata kauna haɗa jini da talaka,kana tana muzantani,Anan yafaɗamata abinda ya mata da wanda ta mashi. Daga karshe ya ajiye key ɗin ya juya abin shi..
Hankali tashe take kiranshi Amma yakasa juyowa .
Afusace tashig palon cikin matsanan cin fushi ta zari wayar charger tafara tsulama Amnah ajiki, Abinda bata taba yiba.
Ihu Amnah keyi sosai tana neman É—auki amma Mamy ido ya rufe bataji bata gani.
Amal ma kuka take tana neman agaji akan yar uwar ta , Amma babu wanda zai iya jiyota ,saida mamyy tayi mata RuÉ—u-RuÉ—u kana ta koma gefe tana sauke numfashi.
Dakyal Amnah ta mike ta haye sama tare da faɗawa toilet tayi wanka tana kuka sosai ta fito daga iya sai ƙaramin towel tayi kwanciyar ta, tana kara jin tsanar Sadeeq aranta sosai, duk da wani sashin na zuciyar ta na hasasomata yana masifar kama da irin mijin da take fatan samu.
Tsaki tayi a fili tace'' aiko nafasa bazan taɓa auran mai kama da talaka ba,Kuma Ɗan Dako.
Anan palo kam Amal ta Rarrafa ta rike ƙafar Mamy ta fara bata hakuri, sanin Mamy batada isashiyar lafiya tinda takasa magana abun ya dameta sosai.
"Mamy dan zatin Allah kiyi hakuri kar halin Aunty Amnah ya dameki,kibar wa Allah kitayata da Addua, ni kaina banajin daÉ—in abinda take .
Ajiyar zuciya Mamy ta sauke tace" Amal taya zan iya samun mai amana kamar sadeeq, nasha auna shi da bashi kudin da suka zarce da niyyar wani abu amma haka zai maidomun canji,ga natsuwa ,uwa uba ilimi, kinafa jin shi kullum cikin Lambu yana raira karatun Alkur'ani,baya wasa da sallah ko kaɗan, taya zanji natsuwa da farin ciki in irinshi ya kufcemun? Wallahi Amnah bata kyutamun ba som,Tinda taje US ta dawo iskancin ta ya ƙaru, ya zama dole ana gama sallah in ɗauki mataki a kanta, saboda lamarinta kullum gaba yakeyi ba baya ba.
Hakuri Amal taci gaba da bata har saida taga ta sakko.
Tace Mamy kibani number yah Sadeeq inje gidan Nene! Na son suna shiri sosai dan ko cikin azumin nan yana yawan zuwa tacemun, in'haÉ—asu nason zata lallaso miki shi.
Cikin farin ciki dajin daÉ—i ta bata.
Ita kuma batayi sanya ba ta fita ta hu mota sai gidan Nene.
Anan ta kora mata bayani saiga Nene na kuka tana tsinema Amnah.
Cikin kuka tace'' latsoman shi dan Allah, inji awane hali yake , Allah yasama bayyi zuciya ba ya hau saman titi ya kwanta yace mota tabi tasaman shi,Koda yake ƙatone bazai ji ciwo sosai ba.
Sai kuma ta kwaɓe bakinta tare da faɗin'' wannan ai fatar banzace ina azumi yan Ameen su amsa in'cuci maraya nima walakiri Yaci man uwa.
Arikice ta kwace wayar tan halo- halo Saddi dan Allah ka É—auka kar in'maka baki .
Abangaran Sadeeq kuwa yana fita masallacin dake kofar gidan ya shige yayo alwallah tare da ɗaukar Ƙur'ani ya fara karatu.
Take yaji zuciyar shi ta fara sanyi.
Jin ƙarar wayar shi ne yasa shi ɗauka da sallama.
Nene najin ya ɗauka tasaki shewa tare da amsawa tace" yawwa Abubakari kwandon sukari, Dan Allah kayi Hakuri kaje ga fulanina, Wallahi fulani kullum ceman take ita dai I lovulu to saddi , Amma kaga wannan yal banzar da batada kunya ta ganka Ƙato ita kuma tayi zubi da Buta lamba 2 tace zatama rashin kunya , Wallahi na baka dama duk in ta kuma kasanya makwal-kwasa ka fiddama shegiya rabin hakori,kai saddi kaji tsoron Allah rabi fa ba ɗaya ba, A'a toh karka maidata kamar kofar Rijiya, inki samun Dan jikallan da zai sota.
Nainah dama kina sya number nah amma baki taɓa kirana ba?
Yakatse Nene da keta zuba.
Nene tace
"Eh mana kwandon sukari ina da number ka. Kai wallahi karya haramun ina azumina yanzu Amalulu ta sanyaman , Uwar ta Fulani ta turota akan tazo ta ÆŠaukeni mufita gantalin nemanka, cikin rana da kishi, shine nace naga kason mutunci nah kuma kaga ina kyautatama , Nason kamun alfarma ka koma ko?
Shuru yayi yana murmushi jin yanda take rattafo zance.
Da kyal Nene tasha kanshi yace zaikoma yanzu insha Allah.
Dadi taji tace' um muah saddina, kason munyi zama da laraba ko Tusa ɗansu yayi sai sunyima Takashin yaron suu sunba,Suga Tantabaru iyayen kauna ,haba inama amfani wannan ai Iskancine da ƙazanta,Saddi kason nataɓa ganin wani Balarabe zaima matar shi a laɓɓ... .
Dariya ta bashi da sauri ya kashe wayar yana gilgiza kai.
Saida yayi Sallah kana ya koma gidan Mamy anan takara bashi hakuri yace mata ya wuce.
Ahankali kwanikka keta shudewa yau harya zamana sallah saura kwana ukku ko biyu .
inda kafatanin al'umar musulmi kowa shiri yake dan ganin ya kerema sa'a .
Aɓangaran sadeeq kuwa gabaki ɗaya cikin damuwa yake ta Rashin abinda zaima Ammin sa da Hamrat koda shi baisamu ba , Amma yason lokacin biyan sa baiba dole sai ranar Daran Sallah.
Bayan ya kammala komi kamar yanda ya saba ya shiga yima Mamy sallama anan ta tsai dashi ta shiga sai gata da manya ledoji guda biyu ,dakyal ta jawosu tace yawwa "sadeeq ga kayan sallah ku mai Ɗinki kane yabani matsala shiyasa ba a kammala da wuri ba, akwai na Ɗiyata Hamrat dana Ammi duka dai baki ɗaya, kana ina neman alfarma akawoman Hamrat ranar Sallah, kason gidan namu na cike da kewar ƙananun yara.
Kallon ledar yake yana kallon Mamy wai shi da minene zai sakama matar nan, yanzu kayan sallah tami shi kenan? Wani irin girma da darajata yaji sun lunku a cikin zuciyar shi ,yana rokon Allah ya bashi abinda zai faranta ranta kamar yanda take faranta nashi dana Ahalin shi.
Karba yayi ya mata godiya da addu'a da ganan sukai sallama yayo gida cikin farin ciki.
Koda ya iso ya shigo da kayan tsakar gida tare da komawa ya shigo da machine dinsa ya rufe gidan.
Sallama yayi ya shigo inda ya iske Ammi zaune tanata shafa kan Hamrat dake neman yin bacci.
Amsawa Tayi tana mai sannu da zuwa, tare da matsawa gefe ya zauna yana mai jan yatsun Hamrat yace'' Baby'n Baby tashi kiga abunda nakawomiki.
Da sauri ta tashi tana murza ido tare da turo baki tace ''baby munɓata yanzu baka da lokacina.
Dariya ya sanya sosai yana ganin yanda takeyi kamar budurwa.
Ammi ma cikin dariya tace" To ke Hamrat bakyaso Yayan naki yaje aikine yasamo miki abunda zakici?
Inso Ammi amma inason mudunga tafiya tare sai in ragemai wata wahala ko.
Dariya sukayi su duka yayin da ya fara buɗe ledojin da keta zuba kamshin da yarasa kona minene yana jin kamar ya son ƙamshin.
Lumshe ido Ammi tayi jin wani kamshi daya daki hancinta wanda ya sata tinawa da lokuttan baya,take jikinta ya fara bari ,wanda ya sata jingina da bango tana Addu'a dan samun sauki.
Saida yagama fiddo komi kana ya kalleta wanda hakan ya sashi faÉ—uwar gaba.
Da sauri ya ture kayan tare da kamo hannunta yace ''Ammi nah mike damunki ,ko bakya farin ciki da kayan, kinson bafa nina sayaba, Anan ya faÉ—amata abunda ya faru.
Ajiyar zuciya ta sauke tace" Dee ka tino wannan kamshin kuwa?
Nazari yashiga kamin ya shiga jijjigamata kai cikin cikowar hawaye yace'' Ammi nah natina, wallahi natina Ammi nah, Amma babu damuwa Allah yakai Damo ga harawa ko baici ba zayyi wawaso,Gaba kaÉ—an gaskiya zatai halinta,lokaci kaÉ—an yarage zaki yayi ciki da Kura Dan magance handamar ta,kimanta baya Ammi na mu fuskanci goben mu.
Kai ta gilgizamai tare da faÉ—in insha Allah" Dee .
Wasu tsadadun lace da atamfa ya daga masu kyau sunsha ÆŠinki ya ajiye gabanta yace "Ammi ga wannan nakine ,ga mayafi da takalma duk nakine .
Cikin murna da sa albarka ta gwada komi taga cif- cif da jikinta taita godiya.
Wasu zafafan dogayen riguna na yaran yan gayu masu tsananin kyau ya É—aga guda ukku masu masifar kyau.
Pink ,blue, milk sai sheki suke ya damkama Hamrat yace ''eyye Baby tayi kayan yan gayu.
Hawaye ya zuboma Ammi tace Allah sarki rayuwa! Hamrat ɗita tazama yar gayu, bana bazata sanya atamfa roba ba taƙarasa cikin hawaye.
Kai ya gilgiza cikin damuwa yace ''Ammi nifa som kayan nan sunfita raina,Duk Irin kyautar da za'aman wadda zata saki shiga wani yanayi inaji kwara Abar ta.
Kan shi ta shafa tace'' kayi hakuri sadeeq bamu da bakin magana wa baiwar Allah nan sai dai godiya.